BY MIEMIEBEE
PAGE 35
"Ka san Amal kuma ka yarda da ita? Lmao" wani kalan dariyan rainin hankali ya saki "So kake kace ka fini sanin halin matata ko mey Maza?"
"I dunno but I guess yes saboda komin yaya nasan Amal bazata ta6a aikata wannan aika-aika ba."
"Mak'aryaci ne ni kenan? K'arya nakeyi maka? Is that it?"
"Ba haka nake nufi ba Triple A amma da hankalinta kam Amal bazata ta6a aikata hakan ba, it's either she's possessed or something baka tunanin hakan?"
"You mean you deny ba ita tayi wannan rubutu ba?"
"Ba wai nace ba ita tayi bane it's crystal clear rubutun tane amma waya sani ko wani mental illness ne yake damunta wanda idan ya tashi yake sanyata yin abubuwan nan daka irgo saboda a gaskiya bana tsammanin kan Amal ya waye d'inda har zatayi wannan abubuwa. Triple A kayi tunani mana kai fa da kanka kake yabawa da irin kyawun halatayyar ta."
"Mental illness? Gani kake kaman tana da ta6in hankali? Just so you know har asibitin mahaukata na kaita aka kuma duba ta and you know what likitan yace ba abinda yake damunta idan kuma tunanin aljanu kake nan ma na kaita gun Malami anyi mata ruk'iya shima yace bata tattare da komai lafiyarta k'alau so stop giving me lame excuses."
"Wow! But what's really wrong? Ka sameta kayi mata magana? Kayi confronting nata? Maybe akwai wani 6oyayyan al'amari."
"Mey zance mata? Besides kasan ni ba d'abi'ata bane yima mutum magana idan yamun laifi idan shi hankalinsa be basa hakan ba ya nemi tuba ba sede a cigaba da zama hakan."
"Kana nufin tunda abubuwan nan suka soma faruwa baka ta6a yiwa Amal magana ba?" Ya tambayesa da mamaki gaskiya ne mey hali baya canzawa ko shi yana iya tuna lokacinda suka kusan shafe term d'aya (k'imanin watanni uku) a makaranta shi da Afzal lokacinda suke boarding house basu magana a sanadin wasu maganganun da abokansu suka je suka shiryawa Afzal cewan Sultan ne ya fad'a. Shiko Afzal ba bincike ba komai kawai ya hau kan magana ya zauna akai. Kyat kawai Sultan yaga Afzal ya dai na yimai magana da k'yar suka zo suka daidaita tsakaninsu. Tun daga wannan rana ya karanci halin Afzal ko meye mutum yayi masa bayi ta6a tinkarar mutumin da maganar sede yayita kallon meshi da abun har zuwa lokacin da mutumin zey gano yayi kuskure ya nemi tuba. Bayan nan Afzal ya kasance d'aya daga cikin jerin mutanen da basu tsananta bincike game da duk wani abinda aka fad'a musu wanda hakan yake babban hatsari. Su komai aka same su aka fad'a musu d'auka suke su zauna akai ba bincike ba komai wanda sam hakan be dace ba musamman ma ga magidanci kamansa mey mata biyu. Tabbas yasan a banza Afzal yake hukunta Amal baiwar Allan da bata ma san mey tayi ba yanzu. Ashe dalilin da yasa ta zube tayi duhu kenan bak'in ciki ne da tashin hankali ba stress na makaranta kaman yadda tace ba. Allah sarki.
"Maza that's so unfair hukuncin nan da ka yanke yayi wa Amal tsauri dayawa kuma wallahi bazan 6oye maka ba ba haka ake ajiye gida ba, ba haka ake handling mata biyu ba. Afzal da dayanzu ba d'aya bane, yaci ace ka zubar da mumunan d'abi'ar nan naka na kallon mutum da laifi ka fara tunkararsa da laifin da yayi maka kaji mey zece, kuma be dace a matsayinka na mey mata biyu ace dan uwar gidan ka ta fad'a maka abu kawai ka hau ka zauna akai ba kamata yayi ka tsananta bincike ka zaunar da Amal kuyi magana kaji nata 6angaren labarin itama na tabbata akwai ababen da Nazeefah takeyi mata wanda bata jin dad'insu amma ta za6i ta had'iye wa kanta dan karta had'a kanku haba maza! Wallahi sam baka kyauta wa Amal ba."
"Naji nasan bana tsananta bincike kuma bana confronting mutum idan ya mun laifi amma wallahi akan Amal na fara yin hakan bayan da Nazeefah ta irga mun komai nayi mata magana."
"And mey tace?"
"K'aryata komi tayi abinda ya fi bani haushi kenan, tayaya Nazeefah zata na sanin abubuwan da suke gudana a cikin gidan nan idan ba wai kirarta ake ana sanar da ita ba? Ai abinda zaka duba kenan."
"Wow! Ko ze iya yiwuwa hakan ne?"
"Hakan kaman ya?"
"Akan ba ita bace bata aikata abinda kake tuhumarta dashi d'in ba."
"Are you kidding me? Ka zauna kayi tunani Sultan ko tsinke na saya mata a gidan nan se naji labarin a bakin Nazeefah how on earth Nazeefah zata san abinda ke gudana acikin gidan nan idan ba wai kirarta ake ana fad'a mata ba? Ko so kake kace tana da CCTV ne?"
"No bawai haka nake nufi ba."
"Then tell me, tell me how exactly would Nazeefah know of everything da nakeyi wa Amal?"
"You have a point amma still da kayi mata uzuri sanin kanka ne Amal yarinya ce, halan yarinta ke damunta ka sameta kayi mata magana kaja mata kunne I'm sure zata saurareka ta kuma daina."
"Yarinta ko rashin tunani? Wallahi da gan-gan takeyin komai, and you seem to be forgetting her actual age, Amal is 21 years old Sultan she's nomore a child."
"Naji nan Amal bata kyauta ba tayi laifi, amma batun shigo da course mates nata maza cikin gidan nan fa? Ka ga hakan da idonka ne?"
"A'a amma ai 'yar aikinta ne ta fad'a mun."
'"Yar aikinta?" Yayi questioning nasa unbelievably '"Yar aikinta fa kace maza?"
"Yes ba ita take gida ba kullum ai tana sane da shigowa da fitan kowa."
"Amma Maza ka bani kunya, ban ta6a sanin kana da k'arancin tunani haka ba se yau ashe baka fasa halinka ba har yanzu wai tayaya ma zaka fara amincewa da abinda baka ji ba bale ka gani? Wallahi zato zunubi ne."
"Ce maka akayi zato nakeyi? Clearly 'yar aikinta tace sau biyu take ganin Amal na shigo da course mates nata har ragowan snacks da drink data basu ma na dawo gida na tarar ranan what else do you expect me to believe?"
"Ka tambayi me gadinka ne? Ka tsaya kayi wa ita Amal d'in magana kaji labarin daga bakinta? You have to listen to both sides before taking a decision Afzal dole ne ka zubar da wannan halin naka kafin lokaci ya k'ure kazo kana nadama, tabbas duk wanda baya tsananta bincike yana tattare da babban hatsari bana son kazo kayi nadama daga k'arshe."
"Kana tunanin Safiyya zatayi ma Amal sharri ne? Meye ribarta idan tayi hakan?"
"Kai kuma kana tunanin Amal zatayi maka k'arya ne da tace maka ita bata shigo da na miji gidan nan ba? Wai taya ma zaka fara amincewa da maganan mey aikinka akan na matarka ne Afzal? A ina aka ta6a yin hakan?"
"A gaskiya ka bani kunya maza yadda kana ganin gaskiya kake takewa."
"Ma tukun a ina ka tsinci wannan paper?"
"Cikin kayakina."
"Lmao cikin kayakinka? Wallahi ka bani kunya Afzal, it's so unfortunate that you're my friend. Har kana tunanin Amal zata rubuta wannan abu takuma sake ajiye maka shi acikin wardrobe inda ze fi sauk'in ka gani? A tunani na sede ta 6oye ba ta ajiye a inda zaka gani ba. Wallahi Allah this's a trap."
"Har wani marasa aikin ne ze zauna yayi wannan aiki? Kuma har ya iya yayi irin rubutunta sak?"
"The world isn't a safe place and there are toxic people everywhere so zan baka shawara ka zauna ka bi diddigin lamarin nan idan ma da hali ka zaunar da Amal d'in da Nazeefar da mey aikin nata da mey gadin naku duk gabad'aya kayi musu tambayoyi ka kuma saurari both parties am very sure zaka sha mamaki da sakamakon da zaka samu" yana kaiwa nan ya mik'e "wannan kuma" yayi nuni da takardan hannunsan.
"Duk da cewa rubutun Amal ne karara ajiki hakan baisa na yarda itace ta zauna ta rubuta ba kuma koda ma ita d'ince zan iya cewa tana da daman yin hakan tunda gashi a fili kake nuna mata rashin k'auna da adalci ta hanyan yanke hukunci ba tare da ka saurareta ba zan iya cewa abubuwan da kakeyi mata su suka tunzira ta har ta zauna tayo wannan rubutu, kai baka san the more kake k'untata mata the more kake sa take tunanin masoyinta Abdul take kuma kewon sa ba? Ko ka manta yadda kukayi auren nan ne Afzal? Yarinyar nan fa ba wani sonka take ba, lami lafiya suke soyayyansu da saurayinta suna building dreams nasu ka shiga tsakanin su haka dan ta ceto ranka ta sadaukar da farin cikinta da abin alfaharin zuciyarta. Kana ganin ta cancanci wannan walak'ancin da kakeyi mata? The earlier the better Triple A it's time for you to make things right idan kuma har bakayi ba toh ni zanyi da kaina" yana kaiwa nan ya ajiye takardan ya fice.
Mugun d'aurewa kan Afzal yayi gabad'aya ya rasa meke masa dad'i what if duk abubuwan da suka faru set up ne kaman yadda Sultan ya fad'an amma ai kuma wannan rubutu is real ko a mafarki aka nuna masa rubutun nan yasan na Amal ne. Amma kuma idan har ita ta rubuta ai baza ta ajiye a open place inda ze gani ba sede ta nemi wani 6oyayyan wajen ta ajiye, ya Allah what's really happening? Yini yayi gabad'aya ranan yana tunani ya kasa samun sukuni wajajen tara hak'urinsa ya k'are. Maybe is about time ya tunkari Amal suyita ta k'are.
D'akin ta ya nufa inda ya tsince ta zaune bakin gado tana karatu da mamaki ta tsaya tana kallonsa ba tare da tace komai ba. Takawa cikin d'akin yayi ya k'wace handout natan kafin tace zatayi magana yaja hannunta ya mik'ar da ita ya shiga janta waje.
"Yaya what're you doing? Ka sakeni let me go" ko sauraranta beyi ba seda ya kaita tsakan d'akin nasu. Wardrobe ya nufa ya zaro takardan har anan kallonsa Amal take yayinda zuciyanta yake bugun d'ari-d'ari dan yadda ta tsure a tunaninta gabad'aya dukanta yake shirin yi. Takardan ya bud'e a idonta "rubutun waye wannan?" ya tambayeta?
"Rubutu na" ta amsa a takaice.
Sa mata yayi acikin hannu "here read it" d'agawa tayi ta shiga karantawa layi uku ta karance ta shiga kad'a kanta yayinda idanunta suka ciko dam da hawaye amma Allah ya isa tsakaninta da Safiyya da Nazeefah. Tun a asibiti ta gano Nazeefah ba sonta take har cikin zuci ba, tun anan ta gano Nazeefah ba da zuciya d'aya ta d'auketa ba. Tun anan ta gano Nazeefah is behind everything that has been happening to her barin ma yadda ta dage ta rink'a nunawa Ummi cewa lallai-lallai ita ce ta sa zuciyan Afzal ya buga. Ta sani ba wanda zeyi mata wannan d'anyen aikin se su, Maamah batayi k'arya ba da tace suna aiki tare idan ba haka ba tayaya Nazeefah zata san takai Afzal asibiti idan ba wai kirarta Safiyya tayi ta sanar da ita ba.
"Wallahi Yaya bani na rubuta ba" ta sanar da shi cike da tashin hankali.
"Ba ke kika rubuta ba?"
"Yaya wallahi bani bace wallahi bani na rubuta ba" rantsuwa ta shiga yi yayinda hawaye ya fara tsiyaya daga idonta.
"Can you even listen to yourself Amal? Aljani kike son kice ya rubuta ko mey? Ko kin k'aryata wannan ba rubutun ki bane?"
"Yaya you have to believe me wallahi bani ce na rubuta ba bazan ta6a yin abu haka ba" ta sanar da shi cikin tsan-tsan kuka ransa ne ya gama 6aci gabad'aya besan a lokacinda ya damk'ota ya shiga jijik'ata ba "Why do you have to keep on lying to my face Amal? Why!?" Ya tsawata mata kakkarwa take sosai yayinda hawaye ya shanye mata murya "I love you Amal, I love you morethan anything in this world amma da abinda zaki sak'a mun kenan? Duk kalan halaccin da nayi miki a rayuwa you think I deserve this from you? Har ni zakice jikinki kawai nakeso ba zuciyarki ba? Ni Amal? In ba da mukayi aure ba ko hannunki na ta6a sha'awan rik'ewa ne?"
"Ya- Yaya please believe me" ta ce dashi muryanta na d'aukewa "Wallahi bani na rubut-"
"Damn it Amal!" Ya katse ta. "You're such a horrible liar, idan ba ke ba toh waye? Waye yake da irin sigar rubutunki bayan kanki? Answer me!" Ya sake daka mata wani tsawan da gabad'aya yasa jikinta rawa fiye da na da. Ita tsoronta ma kar gabanta ya cigaba da fad'i abu ya samu d'an cikin nata ne tunda de bawai cikin babba bane abu kad'an yana iya zubar dashi.
"Wallahi bani bace-"
"When will you stop lying to my face? When Amal?" tureta yayi kad'an ya rage bata sha k'asa ba "Stop lying to me already just admit it, confess all your crimes a shirye nake in yafe miki mu fara sabon rayuwa all over again Amal just admit it."
Cikin tsananin kuka tace, "I have nothing to admit Yaya saboda bani bace wallahi ba ni na rubuta wannan abu ba."
"You're still not telling me the truth."
"You have to believe me wallahi ba k'arya nake yi maka ba-"
"You're lying! Just admit it, admit it already."
"Yaya I have nothing to admit ya, taya kake tsammanin zan amince da laifin da bani na aikata ba? Wallahi bani bace wallahi bani na zauna na rubuta wannan abu ba, kana tsammanin har zan rubuta mumunan abu haka kuma se in ajiye a inda nasan idonka ze kai?"
"Fvck it!" Yayi growling yayinda yake wani irin nishi kaman zaki. "Amma rubutun waye ne?"
"Yay-"
"Just fvcking answer me!" Ya katseta cike da rashin hak'uri.
"Rubutu na ne amm-"
"Shhh!" Ya katse ta "Abinda nakeso inji kenan" hannu ya mik'a ya amshe paper'n "You've really hurt me Amal, you've hurt me so badly, kin karya zuciyan da take mutuwar sonki kin yasar, bazan ta6a mancewa da wannan abu da kikayi mun ba I might forgive you someday amma bazan ta6a mancewa dashi ba."
Cikin sautin kuka ta kira sunansa "Yaya-"
"Just get out" ya sanar da ita a hankali.
"Yaya dan Allah ka saur-"
"I said get out!" Ya daka mata tsawa a raunane ta tsaya tana kallonsa sannan ta shiga takawa a sanyaye ta bar mai d'akin. Tana isa d'akinta ta baje akan gado ta shiga raira kuka. Kuka take wane zata cire ranta har seda ta fara jin k'warnafi. Bayi ta fad'a ta shiga kwararo amai kaman ba gobe seda ta harar da duk wani abunda yake cikinta sannan ta lalla6a ta fito. Yanzu ta tabbata da abinda Maamah ta jima tana fad'a mata. For all these while Safiyya amanarta ta rink'a ci ita ta ringa zuba mata gishiri da borkono a girki, ita ta rink'a kwasan abinda Afzal ya keyi mata tana kaiwa Nazeefah, ita ce ta fad'a masa tana kawo maza gida, ita ta kira Nazeefah ta sanar da ita suna asibiti bayan da ta ajiye masa wannan takarda ya karanta. Wow!
Meyasa ta kasa gane gaskiya tun farko? Meyasa bata gane Safiyya ce behind everything ba? Tabbas ta tafka sokanci gaskia ne da Maamah tace mata yadda ka d'auki nutum da zuciya d'aya yanzu shi ba haka ya d'aukeka ba. Ko da wasa bata ta6a kawowa a ranta cewan Safiyya zatayi mata abinda tayi ba. Bature beyi k'arya ba da yace "Trust No One" tabbas da tun farko bata ajiyeta kusa da zuciyarta ba da tun kafin abu ya ta6ar6are haka zata gano gaskiya. Tsakaninta da Nazeefah kuma sede tace Allah, Allah kad'ai ze sak'a mata yabi mata hak'k'inta. Chan ta mik'e taje ta samu Safiyya a d'akinta.
"Sannu Aunty ya jikin naki?"
"Safiyya a iya zama na dake ban ta6a cutar dake ba, ban ta6a tokararki ba, ban ta6a tauye miki hak'k'in kiba a matsayin k'anwa ta ta jini na d'aukeki da zuciya d'aya shiyasa har yanzu na kasa gane dalilin da zaisa kiyi mun abinda kikayi mun." Cike da d'aurewan k'wak'walwa Safiyya ta tsaya kallon Amal yayinda cikinta ya d'au ruwa lokaci guda bade Amal ta ganota ba? Yau kashinta ya bushe ta shiga uku ta lalace.
"Mey na miki da kika za6i ki k'untata mun acikin gida na ki hana ni sakat? Mey na miki da kika za6i ki shiga tsakani na da mijina kisa har ya fara zargina akan ina ci masa amana? Mey na ta6a yi miki Safiyya? Amma ba komai ki kira uwar d'akinki ki sanar da ita cewan ta kwantar da hankalinta saboda burinta na rabani da Ya Afzal ya cika koda Yaya be sakeni ba ni zan tattara kayakina in bar gidan nan tunda kun riga kun juyar mishi da kai kunsa yana mun kallon munafuka, mak'aryaciya, annanimiya wace bata da aiki sena gulma. Ba gidan kukeso ba? Zan tattara kayakina in bar muku ita" bata jira jin mey Safiyya zata ce ba ta juya ta fice. Bayi Safiyya ta shiga a guje ta juye fitsarin da ya matseta a lokaci d'aya sannan ta fito ta d'au wayarta dan kiran Nazeefah se kakkarwa take yayinda jikinta yayi la'asar da irin kalamun da Amal ta fad'a mata sede sam layin Nazeefah yak'i shiga.
****
Babban akwatinta ta janyo daga d'akin da ta tarasu aciki ta nufi d'akinsu da Afzal sallama tayi sannan ta shiga ko kallan Afzal dake mik'e akan gado batayi ba ta zarce direct wajen wardrobe, da mamaki ya mik'e zaune yana kallonta sede bece da ita ko uffan ba. Kayakinta yaga ta shiga tattarewa na matuk'a ta basa mamaki shin mey take shirin yi? Tafiya? Tafiya zatayi ba tare da ya bata takarda ba? Ido ya cigaba da zuba mata yana ganin iya gudun ruwanta. Kayakinta ta cigaba da tattarewa tana had'awa tana gamawa da fannin kayakin ta zarce gaban mirror ta d'ibi mayukan shafawanta da turare da makamancin haka sannan taja akwatin ta fice har anan Afzal beyi mata magana ba. Handouts nata da littafafai da sauran muhimman abubuwan da zata buk'ata ta tarasu cikin wani akwati daban shima.
Na sosai Afzal ya kasa kunne yana jiran jin k'aran engine na mota inda ze tabbatar da tafiya Amal zatayi kokuwa kawai ta tare kayakinta ne ta k'aura izuwa d'akin da ta koma gabad'aya. Washegari da sassafe ko karyawa Amal batayi ba taja akwatinta ta fice. Ko da driver yace ze kaita inda zata hanasa tayi napep ta tsara a waje bayan d'an takawan da tayi ta wuce gida. Har bakin k'ofa ya sauk'eta sannan ta sauk'e kayakinta ta sallamesa ta k'arisa ciki.
Papi ta tarar a tsakar gida yana zaune yayinda suke hira da Mami dake kitchen tana shirya musu abun karin kumallo. "Baby!" Ya kirata da mamaki yana bin jakukkunan hannunta da kallo "Ya haka? Meya faru?" Ya jero mata tambayoyi. Ba shiri Mami dake kitchen ta sauk'e tukunyarta ta fito tana kallon abin al'ajabi. Ba k'aramin tsinkewa zuciyanta yayi ba ganin Amal da akwati haka, Allah de yasa ba abinda take zargi bane. Da sauri sukayi kanta suna tambayarta meya faru. Sede wane 'yi kuka' suka ce mata dan yadda ta rushe da wani irin masifaffen kuka, a rikice Mami ta jata jiki ta shiga hugging nata tana bubbuga bayanta yayinda Papi yaja akwatunan nata suka k'arisa ciki. Dan kukan da takeyi Papi ya rok'i Mami da tabar ta da tambayoyin haka ta bari se idan ta huta tukuna. Dan haka suka fita daga d'akin suka barta, kukan ta cigaba dayi har izuwa lokacin da wani wahalallen bacci ya d'auketa.
****
Wajajen tara da rabi Afzal ya tashi daga bacci bayan yayi wanka ya sanya shirt da shorts ya fito inda ya tarar da Safiyya na goge-goge. Cikinsu duka ba wanda yasan da tafiyan Amal banda mey gadi da driver. A cewan Safiyya har Amal ta irga wa Afzal halin da ake ciki ne don haka tayi surrender ta tsaya chak gu d'aya tana jiran sauk'an mari a fuska kawai setaji ya tambayeta "Ba gaisuwa ne?"
"Yi hak'uri ina kwana Uncle wallahi hankalina ya tafi wani gun ne" Ta gaishesa "Lafiya" ya amsa "Kiyi mun frying chips da two eggs."
"Toh barin kammala aikin nan" instead ya wuce d'akinsa se yayi tunanin lek'a na Amal inda ya tarar da d'akin empty, shiga yayi ya zauna yana jiran fitowarta dan a tunaninsa gabad'aya ta shiga bayi yin wanka ne sam be kawo a ransa wai har Amal ta tafi ba. A cewansa tunda bata tafi jiya ba that means ba yaji zatayi ba kawai ta tattare kayakinta ne ta dawo dasu nan gabad'aya. Sede da ya duba gaban dressing mirror ya tarar dashi empty ko vaseline babu. Tirk'ashi! Ba shiri ya mik'e yayi knocking bisa k'ofan bayin, jin shiru seya bud'e ya lek'a ciki inda ya tarar da bayin empty a guje ya fito yana tambayar Safiyya ko ina Amal taje sede kaman yadda baida masaniya itama hakan ne. Waje ya fita yana tambayan mey gadi ko yaga fitan Amal.
"Tabbas naga fitanta Ranka shi dad'e nima na bud'e mata k'ofar."
"Ina taje? Ita kad'anta ta fita ko kuwa da akwati?"
"Akwati har biyu."
"Damn it! Meyasa baka hanata fitan ba kokuwa ka kirani ka gaya mun? Shin baka san aikinka bane? Mstww!" ciki ya dawo ya d'aga wayansa har ya danna kan contact na Amal don kiranta se kuma ya fasa yayi sauri ya katse wato shi be yi zuciya ya ce ya saketa ba be kuma ce ta tafi gida ba itace take da zuciyan yin hakan? Ita gata tana da gun zuwa wato, da kyau ta kyauta taje duk inda zata je.
*****
Wajajen goma da rabi Amal ta tashi inda ta fara duban wayanta saidai da mamaki taga ko message Afzal be tura mata ba bale ya kirata, lallai yau ta gane waye Afzal. Wannan walak'anci da mey yayi kama? Ace yana kallonta tana shirya kayakinta amma ko yayi mata magana bale yayi tunanin hanata. Yanzu kuma da ya tashi yaga bata gidan meya kamata yayi? Lallai yau tasan inda ya ajiyeta, yau tasan matsayinta a zuciyansa, yau ta tabbata Yaya baya sonta.
Masa me kyau Papi ya aika aka siyo mata ta karya da shi tasha magunanta alai sannan Mami ta shigo suka gaisa.
"Bakida lafiya ne?" Mami ta tambayeta tana bin magunan dake gabanta da kallo.
"Eh Mami ban ji dad'i sosai ba kwana biyu."
"Allah sarki, Allah sawwak'e."
"Ameen."
"Ya baki ci masan ba sosai duka fa naki ne mu tun d'azun muka karya."
"A'a Mami na k'oshi na d'an ci ai anjima ma ina da test."
"Kai haba?"
"Wallahi around 1 haka."
"Toh Allah ya bada sa'a Papinki na buk'atan ganinki." Hijabinta ta sanya ta mik'e a sanyaye tabi bayan Mami bayan sun k'arisa d'akin nasa suka nemi waje suka zauna daga angles na d'akin. Gaisuwa suka fara yi bayan nan Papi yake tambayarta meke faruwa.
"Papi komai ma ya faru, ba abinda be faru ba ni kawai kar ku sake turani gidan Yaya dan Allah" seta rushe da kuka.
"Subhanallahi ya isa haka kinji? Ba wanda yace ze sake mai daki gidansa fad'a mun meya faru."
"Nazeefah ba kishiyar arziki bace after all, yadda na d'auketa da zuciya d'aya ba hakan ta d'aukeni ba, ashe duk shiri ne bawai har cikin zuciyarta bane tana so na, son munafurci take yi mun...." nan ta kwashe labarin duk yadda akayi tun daga kan lokacin da Safiyya ta fara zuba mata gishiri da borkono a girki zuwa kan lokacin da Afzal ya fara shasshareta zuwa kan lokacinda tayi masa magana yace tana kire-kiren waya tana baza sirrin gidanta a waje, zuwa kan lokacin da Safiyya tace ta fara kawo maza gida har izuwa na takardan da suka sa wa Afzal cikin kaya bata 6oye masu komai ba illa labarin cikin da take d'auke da shi.
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un" kawai Papi yake ta nanatawa da mamaki bayyane karara a fuskansa itakam Mami se tafe hannu kawai takeyi dan mamaki ko salatin ma ta kasa ambata.
"Kikace a idon shi kika tattare kayakin ki beyi miki magana ba?" Mami ta tambaya.
"Wallahi a idonshi Mami" ta amsa tana share hawayenta.
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un" ta sa salati.
"Har yanzu kuma be kira ki ba?" Papi ya tambaya.
"Be kirani ba."
"Kuma nima be kirani ba ko ya kiraki Jameela?"
"Sam" ta amsa tana kad'a kai.
"Tabbas Afzal zeyi nadama, ashe har za a fad'a mishi magana akanki ya hau ya zauna akai ba tare da ya tsananta bincike ba? Ashe har zega ayan tambaya akan tarbiyyan dana baki a gidan nan Baby? Har ke yake tsammanin zaki ci masa amana sabida 'yar aikinki ta ce hakan? Baze tsaya ya tambayeki yayi bincike ba?"
"Wallahi Afzal butulu ne" cewan Mami "Ko a mafarki aka ce mun zeyi haka wa Baby bazan yarda ba, wannan sigan walak'anci da mey yayi kama? Ai ko a bishiya ya 6alloki be kamata yayi miki haka ba ni fa ba abinda ya fi ci mun rai kaman da ya koraki daga d'akinsa. Wannan wani irin gori ne?" Ta tambaya cike da tsiwa.
"Ya isa haka Jameela ki kwantar da hankalinki uwata ta shi kije ki huta ai ba makaranta yau ko?"
"Akwai ina da test."
"Kinyi karatu?"
"Eh jiya nayi yanzu ma zan d'an ta6a kafin lokaci yayi."
"Toh uwata Allah bada sa'a kinji? Ina son ki kwantar da hankalinki ki cire Afzal daga zuciyarki. Nasani abinda yayi miki da zafi amma hak'uri ya zama dole mamana, dan shi baza ki bari ki cutar da kanki ba, in shaa Allahu shi yake tattare da asara ba ke ba gashi ai da kika cigaba da hak'uri kina kai kukanki wa Allah, Allah ya bayyano miki da komai kuma batun cewa za mu miyar dake gidansa k'arya ne, baki komawa har se idan ke kika ce hakan bazan mayar masa dake ba koda yazo yin bikon ki Baby zan nuna masa cewa ba wanda ya kai ya walak'anta mun ke muddin ina raye so ki kwantar da hankalinki kinji? Ki cigaba da karatu Allah yayi miki albarka."
"Ameen Papi nagode."
"Tashi Mamana" da haka ta mik'e ta fice zuwa d'akinta ta cigaba da karatu. "Amma Afzal be kyauta ba wallahi" cewan Mami bayan ficewan Amal.
"Dama na sani wataran se ya gorantawa Baby shiyasa ban goyi bayan ka sanar dashi asalinta ba tun farko."
"A gaskiya nima Afzal ya bani kunya yadda ba bincike ba komai ya yanke hukunci."
"Ai walak'anci ne ba komai ba wallahi kuma kasan meya fi 6atan rai? Yadda tana tattare kayakinta a gabansa amma ko k'ala be ce ba irin bata da gata bata da gun zuwa d'innan kokuwa duk inda taje zata sake dawowa da k'afarta."
"Ya isa Jameela ki kwantar da hankalinki in shaa Allahu ba shi ba Baby."
"Ahtoh dan wannan rashin mutunci ne a fili saboda bata da uba yake ganin ze iya walak'anta ta toh wallahi yayi k'arya Baby nada gatanta."
"Ki sauk'ar da muryanki kar Baby ta jiki dan Allah magana ya riga ya k'are muddin ba Baby ce tace zata koma gidan sa ba toh ba shi ba ita cin fuskan ya isa haka."
***Sha biyu nayi ta shiga shiri sallama tayi wa Mami sannan ta fice, tana gama test nata sukayi sallama da Maamah. Dama yawancin ana samun napep na jiddari (unguwansu) acikin makaranta se yau kuma Allah yayi babu dan haka ta taka har wajen gate ta shiga nema. Tazo tsallake titi kawai kaman daga sama wani mota mey d'ankaren gudu ya d'auketa ya wuce ko kewayowa beyi ba. Nan mutane suka duk'ufa sukayi kan Amal da tuni ta sume a wajen yayinda kanta yake bulbulan jini. Mota aka shiga nema wanda zeyi gaggawan kaita asibiti ana cikin haka sega wani babban motan daya fito daga cikin makarantar ya faka a dai-dai inda abun ya faru. Daga ciki babban mutum da ake ja yace da driver'n sa "Iliya sauk'a kaje ka taimaka musu mu kai yarinyar asibiti." Nan da nan aka d'auki sumemmiyar jikin Amal aka sata cikin motan inda suka wuce TH.
****
K'ofan ta rufe ta fad'a bayi a guje sannan ta d'aga wayan. "Hello Aunty?"
"Safiyya mission complete yau burina ya cika, na fidda Amal daga gidan Ya Afzal maganan da nake miki yanzu har mutanen nawa sun bigeta in shaa Allah se cikin ya zube."
"Aunty meyasa kika sa aka bigeta? Kin fidda ta daga gidan nan bey isheki ba har sai kinsa an bugeta? Seda na ce miki ya isa haka amma kika k'i ji wallahi abunda mukayi wa Aunty yayi yawa ni nayi nadaman fara aikin nan da ke."
"Mey kike cewa Safiyya? Bayan burin mu ya cika kike wannan banzan maganar? Kin manta da mak'udan kud'ad'en da na miki alk'awari ne?"
"Ban fad'a miki bane amma Aunty ta riga ta gane mu, ta gane muna aiki tare, kap abinda muka aikata ta irga mun jiya kafin tabar gidan nan."
"Sai mey? Ba ta riga ta bar gidan ba?"
"Aunty duk da haka da bakisa an bigeta ba wallahi Aunty bata cancanci abubuwan da mukayi mata ba."
"Kiji ni Safiyya wallahi idan kika kuskura kika 6ata mun aiki na sena tabbata na lahira ya fiki jin dad'i hello Safiyya? Safiyya? Hello?" Tuni Safiyya ta katse wayan. Tun tafiyan Amal yau ta kasa samun sukuni, sosai kalamun Amal suka ta6a ta suka sa duk ta tsani kanta. Bud'e k'ofan da tace bari tayi taga Afzal tsaye bakin k'ofan bayin yana wani irin nishi wane zaki ga yadda idanunsa suka kad'a sukayi ja zir, wai shin har yaushe ya shigo bata ji sa ba? Innalillahi ashe batayi locking k'ofar ba duk dan sauri ta d'auki call d'in Nazeefah kafin ya tsinke. Kafin ta hankara kawai taji ya fincikota da hannunta seda ya fiddo ta daga bayin.
Tsulewa tayi ta shiga yin kakkarwa yayinda idanunta suka ciko dam da hawaye.
"Da wa kike waya?" Ya tambayeta cikin wani irin salon da ya mugun sanyata jin fitsari. Kai zalla take iya kad'awa "Nace da wa kike waya?!" Ya daka mata wani irin tsawan da tuni ya sa ta shiga sake fitsarin da take ji tsabaragen tsoro.
"Uncle dan Allah kay-"
"Shut up you fool! nace da wa kike waya?" hannu ya mik'a ya fisge wayan nata tare da shiga call logs last numban da tayi waya da shi yayi dialing bada dad'ewa ba Nazeefah ta d'aga "Hello Safiyya? Hello Safiyya?" Wani irin rawa jikin Afzal ya fara lokacin da yaji sautin muryan Nazeefah acikin wayan. Kashe wayan yayi daga sama kawai Safiyya taji sauk'an mari a fuskanta tass! wani irin rikicaccen ihu tasa yayinda ta soma ganin stars suna bin kanta. Be bari tayi overcoming zafin marin ba ya k'ara mata d'aya kumatunta duka ta rik'e tana kuka.
"Abinda ta turoki gidan nan kiyi kenan ko? Ki shiga tsakani na da Amal is that it?"
"Uncle dan Alla-"
"Shut it!" Ya daka mata tsawa "wa kuka tura a kad'e?" Kai zalla take kad'a masa yayinda ta gama tsurewa "Nace wa kuka tura a kad'e?" Nan ma shiru "You fool I'm talking you" fincikota yayi had'e da kai mata wani marin again a rikice tace, "Aunty wallahi Aunty a ka kad'e ni bani bace."
"What?" Yayi exclaiming cike da k'in yarda. "Kun sa a bige Amal? Bakuda hankali ne?" Turata yayi har jikin bango sannan ya shak'ure mata wuya take idanun Safiyya suka kad'a yayinda ta shiga yin tari kad'an ya rage Afzal be kasheta ba sannan ya saketa nan ta sauk'a k'asa tana wani irin tari.
"A ina kuka sa aka bigeta?" Shiru tayi se kuka kawai take wani ball yayi da ita da k'afa "Nace a ina kuka sa aka bigeta?" Cikin tsananin kuka tace "Wallahi ban sani ba tunda Aunty tace zata sa a bigeta nace kar tayi amma tak'i jina" wani ball d'in ya sakeyi da ita "K'arya kikeyi nace k'arya kikeyi a ina kuka sa aka bigeta?"
"Uncle wallahi ba k'arya nakeyi ba tace de daga makaranta za a bi Aunty amma wallahi ban san a dai-dai ina bane dan Allah ka yarda dani."
"Wallahi tallahi kin de ji rantsuwa ba kaffara ko? Muddin wani abun ya samu Amal ki sani da hannu na zan kasheki" yana kaiwa nan ya fice daga d'akin makulli yasa ta waje sannan ya k'arisa d'akinsa ya d'au key'n motansa ya fice be tsaya ko ina ba se gidan Nazeefah. Tana zaune akan dining tana cin abinci kawai taga shigowan Afzal kaman diran yesu.
"Ya Rouhi?" Ta kira sunansa had'e da mik'ewa dan yi mai sannu da zuwa. Peck ta mishi placing a gefen kumatu "Ya Rouhi mey ka shigo yi? Ba se gobe zaka shigo ba?" Ko amsata ya kasa yi yayinda zuciyarsa ke raya masa kawai ya had'a kanta da jikin bango ya shak'ure mata wuya se idan ta daina numfashi tukun ya saketa danne zuciyan nasa yayi sannan daga gefe yayi dialing lambarta ta wayan Safiyya.
"Excuse me" tace da shi tare da nufan dining dan d'aukan kiran, ba k'aranin har6wa zuciyanta yayi ba ganin Safiyya ke kira shin wai meke damun yarinyar nan ne haka? Rejecting call d'in tayi take nan Afzal ya sake buga mata har rawa jikinta yake ta kuma rejecting juyawan da zatayi taga Afzal gab a bayanta.
"Muje ka watsa ruwa ko? Bari in sirka maka ruwan." Kafin tace zata taka k'afa Afzal ya rik'o hannunta "Who's calling?" ya tambayeta.
"Ermm.. ermm Airtel ne Wallahi kasan su da kiran mutum anyhow." Wayan Safiyya ya d'aga ya sake dialing lambar nata nan ya shiga ruri kafin tace zata katse yasa hannu ya hanata "Ba Safiyya ke kira ba? Ki d'aga mana." Kakkarwa ta shiga yi a wajen bata san lokacinda ta sake wayarta a k'asa ba da ta hango wayan Safiyya rik'e a hannunsa. B'ari bakinta yake yayinda cikinta ya d'ura ruwa.
"Ya Rou-" wani irin zafaffan mari me rikitarwa ya zabga mata, wani irin rikicaccen ihu tasa bata hankara ba ya sake kai mata wani abinku da farin fata take fuskan nata yayi ja yatsun Afzal biyar suka bayyana akai.
"Ya Afzal dan Allah kayi hak'uri" ta furta cikin wahala da tashin hankali har wani kurma-kurma ta fara jin kanta tsan-tsan zafin marin.
"I can't believe your guts Nazeefah, how could you? For all these while ashe wasa kike mun da hankali? Wace irin munafuka ce ke? Ma tukun mey Amal ta tare miki? Tell me mey Amal ta tare miki da kika za6i ki k'untata mata kisa in tsaneta ki shiga tsakanin mu haka? Baki tsaya anan ba har seda kika sa aka kad'eta? Are you forreal? So kike ta mutu?"
"Ya Afza-" wani marin ya sake kai mata dan yadda ko muryanta baya son saurara. Ihu Nazeefah tasa seda Hindu dake bacci ta fito daga d'aki a kid'ime ganin Afzal ne da kansa ta ja k'ofanta ta sa key.
"Mey ta tare miki nace?!" Hannunta ya damk'o yana yi mata wani irin rik'o tuni k'asusuwanta suka shiga yin k'ara "Ya Afzal dan Allah kayi hak'uri kar ka karya mun hannu."
"Answer me then mey Amal ta tare miki?"
"Zan fad'a maka zan fad'a maka amma dan Allah ka sakeni wayyo Allah na" sassauta rik'on nasa yayi. "Speak up! Idan kika bari na sake tambayanki wallahi na lahira seya fiki jin dad'i, mey Amal ta tare miki nace?"
RANA D'AYA!
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
13 comments:
Hehe! Kadan ma kika gani makira, ai sai kin bar gidan in shaa Allahu! Allah sarki amal, Allah ya tashi kaffadun ki😢... jazakallahu bil jannah miemie🖤😚
Ina masu son Nazeefah? Kuzo Ku kwashi kayanku, Allah ai ba azzalumin bawa ne Karma issa Bitch.
Oshey miemiebee aikinki nakyau Allah ya kara basira please yaya labarin BWMH?
Please update soon
Kai
Masha Allah, Allah yana tare da mai gaskiya, amal Allah ya baki lfy da abun da ke cikin ta.Nazeefa kuma idan Allah ya yarda sai ta bar gidan har abada.mie mie Allah ya kara basira tnx 4 dis episode
Omg dis episode yatafida imani nah
Allah sarki Amal kina ganin iftila'i i really pity u. Naxifa daman komai nisan jifa kasa zai dawo. daman can ba santa nake ba walh.. Afzal dokin zuciya ya kaika ya baroka. samun Amal 4 d 2nd tym ze maka wuya sosai. tnxs mie mie Allah ya karo basira... plxx update soon.
More Grace to your elbow habibty pls add me to ur whatsapp group 07069578048 am waiting durlin
More Grace to your elbow habibty pls add me to ur whatsapp group 07069578048 am waiting durlin
Can't stop smiling for d last chapter Dan Allah kiyi mana next one d wuri. Mungode
Wow am so happy tnx alot for dis episode
Miemie bee for life. ... Muna ta sa ido for next update Allah ya kara basira
Nyc one
Karma is a bitch nazeefah
Karma is a bitch nazeefah
Post a Comment