Monday 1 October 2018

RANA D'AYA!

BY MIEMIEBEE
PAGE 45




     "Ameen Alhj na."

  "Mey hakan ke nufi kenan Hjy Surayya? Kin hak'ura kin yafe mun kenan?"

  "We all make mistakes Alhj amma ba dukan mu bane muke gano kuskurenmu har ma mu nemi tuban wanda muka wa laifi, shin meyasa bazan yafe maka ba tunda har kai ka gane kuranka ka kuma nemi tuba? Na yafe maka Alhj Allah kuma ya yafe mana gabaki d'aya" ta k'arashe tana murmushi. Daddy baze iya kwatanta irin farin ciki da murnan da kalamun Mummy suka sanyasa ba. Da murmushi kwance fal a fuskansa ya mik'a hannunsa ya rik'o nata "Thank you so much Hjy Surayya I can say my life has never been better until I met you, Allah ya cigaba da miki albarka ya kuma barmu tare."

   "Ameen Alhj you're welcome."

  "Kinsan wani abu?"

  "Seka fad'a."

  "I love you" yana sanar da ita bata san lokacin da ta fashe da dariya ba "Ji Alhj de, yaushe kuma muka fara wasan nan?"

   "I'm serious Hjy Surayya saboda bana fad'a miki doesn't mean I don't love you, I love you like the day I just met you Hjy Surayya never forget that."

   "Thank you Alhj."

  "Thank you kad'ai? Ni bazaki cemin I love you in return ba?"

  "Ka ga La'asar ya kusa gara ka tashi ka fice muyi niyya duka."

   "Yau kuma? Toh sekin fad'a min zan bar nan."

  "Lallai kuwa, nikam ka ga tafiya na" bata kai ga mik'ewa ba ya dakatar da ita ta hanyan kama hannunta. "Alhj ka sakeni mana!"

  "Nak'i"

  "Zan tara maka jama'a fah."

  "Ni d'in Hjy Surayya? Ni d'in naki?"

  "Toh ka sakeni."

  "On one condition."

  "Name it."

  "Yaushe zaki dawo gida? Ina matuk'an kewarki."

  "Kai da zaka k'aro amarya kode ka manta ne?"

   "Amarya daban ke daban so yaushe zaki dawo keda 'yan'yan namu?"

   "Zamu dawo karka damu."

  "Promise?" Kai zalla ta gyad'a mar sannan ya saketa "Toh se anjima ki gaishe mun da Nazeefah da Khaleefah."

  "I'll semun sake magana." Da haka ta fice ciki inda shi kuma ya mik'e ya yi tafiyarsa.
  D'akinta da Nazeefah ta wuce direct inda ta tarar da Nazeefah mik'e kan gado kaman maciji ta zurfafa a cikin tunani ko makaranta tak'i fita. "Tashi ki zauna muyi magana" Mummy tace da ita bayan ta zauna a gefenta ta bakin gadon. Ba gardama ta mik'e ta zaune.

  "Ina son ki saurareni da kunnen masu hankali a matsayinki na musulma me kar6an k'addara me kyau ko akasin sa." Tun anan gaban Nazeefah ya fara bugun d'ari-d'ari dukda cewan bata fahimci inda Mummy ta dosa ba.

  "Ki sani cewa komai na faruwa ne bisa dalili fatan mu kawai Allah ya sa hakan kawai shi ne mafi alkhairi a gareku gabad'aya."

  "Mummy ban fahimce kiba shin mey kike fad'i? Meya faru?"

   "Ga wannan takardan ki ne Afzal ya kawo wa Daddy jiya yana mey baki hak'uri kuma" ta fad'a had'e da mik'a mata. Jiki na k'yarma Nazeefah ta mik'a hannu ta amsa had'e da bud'ewa sannan ta karance hawaye kawai Mummy taga na gangara daga idanunta ba makawa.

  "Nazee-"

  "Noooo!" Tasa wani irin d'ankaren ihu "Noo this can't be happening, bani Ya Afzal yayi niyyan saka ba na tabbata munafukan chan ce ta tilasta mai ya rabu dani wallahi bani yayi niyyan saka ba Munmy."

  "Nazeefah ya isa" Mummy ta fad'a tana k'ok'arin shawo kanta saidai hakan sake tunzirata yayi. Zabura tayi tana kad'a kai yayinda hawaye ke ambaliya a fuskarta "Mummy wallahi bani Ya Afzal yayi niyyan saka ba ki yarda dani."

   "Nazeefah please-"

  "Tsaya kiga ina key'n mota na inje in samesa kiji bani bace wannan takardan Amal ne ba nawa ba."

  "Wani irin banzan magana kike Nazeefah? Bayan ga sunanki nan boldly rubuce akai? Taya zakice ba naki bane na Amal ne?"

  "Wallahi Allah ba nawa bane ina key'n mota na yake?"
 
   "Shin wai ina zakije?" Ta tambayeta. "Zan je in samesa saboda bani yayi niyyan saka ba."

  "Nazeefah there is no point kiyi hak'uri ki rungumi k'addarar ki kowa yasan rabuwa da masoyi da zafi amma ba yadda kika iya."

  "Hak'uri? Hak'uri Mummy? Wallahi inde akan Ya Afzal ne bazan ta6a hak'ura ba."

  "Toh ya zakiyi? K'addara ta riga fata, the earlier kikayi accepting gaskiya the better."

  "How Mummy? So kike kice mun shikenan na rasa Ya Afzal a rayuwa na kenan? So kike kice in nad'e hannu in bar Amal ta sace mun miji ina ji ina gani?"

  "Kema kinsan Amal baza ta ta6a yin hakan ba, Amal ba ita ta sace miki miji ba Nazeefah, Allah ne ya k'addara rabuwan ku."

  "No Mummy kinyi kuskure, idan ba mutuwa ba banga abinda ze rabani da Y Afzal ba" mayafinta ta sanya ta janye key daga gaban dresing mirror da niyan ficewa inda Mummy ta cafke mata hannu.

  "Bada yawu na zaki fita ba Nazeefah."

  "Just let me go" tace da ita had'e da fisgan hannunta. Kaman a kyaftawan ido Mummy ta isa bakin k'ofa ta kulle da key had'e da zarewa ta rik'e a hannunta.

   "Mummy ki matsa mun."

 "Ba inda zakije Nazeefah saki ne ya riga ya auku ba abinda kika isa kiyi da zeyi reversing case d'in sede hak'uri kawai, ki d'au komi a matsayin k'addara ki yi tawasalli."

   "Na gaya miki Mummy inde akan Ya Afzal ne bazan ta6a hak'ura ba har se sakin nan ya koma kan Amal, bazan rasashi ni kad'ai ba se inde mu biyu duka mu rasa sa so move out."

   "Ina nan tsaye anan ba inda zaki." Dube-dube Nazeefah ta shiga yi a d'akin chan ta hango wuk'a a kan bed side drawer nan da nan taje ta d'auka ta saita dai-dai wuyan hannunta (wrist) "Ko ki matsa ko in yanke kaina in mutu" Baki Mummy ta hangame cike da mamaki da k'in yarda tana kallon Nazeefah, batayi tsammanin rashin sanin addinin nata har yakai matakin da za tayi tunanin d'aukan ranta da kanta ba.

  "Nazeefah?" Ta kirata da d'umbun mamaki. "Da hankalinki?"

  "Mummy banida wata amfani tunda na rasa Ya Afzal gara in mutu in huta kowa ma ya mutu."

  "Da hankalinki kike tunanin d'aukan ranki da kanki? Shin baki san hukuncin hakan bane a addinance?"

  "I don't care Mummy amma bazan iya rasa Ya Afzal ba I can't because I love him, I love him so very much and Amal stole him away from me, what else can I do?"

  "Idan kika hak'ura komi mey wucewa ne Nazeefah wataran se labari."

  "No Mummy I can't move on, bazan ta6a iya son wani bayan Ya Afzal ba, I can't do without him dan Allah ku bashi hak'uri ya mayar dani d'akina."

  "'Yar uwarki Amal kuma fah? Ya kikeson ayi da ita?"

  "Ki daina kwatanta ta da 'yar uwata, idan da ta d'aukeni a matsayin 'yar uwarta da bazata sace mun miji ba so ki matsa ko kuma in yanke kaina."

  "It doesn't have to be this way Nazeefah" Mummy ta sanar da ita tana mey matsowa kusa da ita a hankali.
 
  "Mummy stay away."

  "Nazeefah dan Allah kiyi hak'uri karki yanke kanki" ko kallon ta Nazeefah batayi ba ta sa wuk'an ta yanke hannunta wani irin ihu Mummy ta k'urma had'e da k'arisawa kan Nazeefah da ta shiga zamewa k'asa. Tarota Mummy tayi suka sauk'a k'asan atare tana mey bubbuga fuskanta yayinda idanunta suka cigaba da kakkafewa. "Nazeefah? Nazeefah? Innalillahi dan Allah ki tashi Khaleefah!" Ba shiri ta saketa ta d'auko wayanta had'e da kiran Daddy. A karo na farko ya d'aga, ko daman magana bata basa ba tace, "Alhj ka juyo ka juyo da wuri Nazeefah ta yanke kanta."

   "What?!' I'm on my way" U-turn yasha nan take ya dawo ba tare da 6ata lokaci ba akayi da Nazeefah nearest clinic inda akayi emergency room da ita.

  _53 minutes later_
  Da wani irin gudu Afzal ya shiga haraban asibiti sannan ya nemi waje yayi parking ya fito ya k'arisa ciki. Tsaye a inda akayi mai kwatance ya same su da tashin hankali bayyane karara a fuskokinsu.

  "Afzal?" Daddy ya kirasa yana mey mamakin yadda akayi yasan halin da suke ciki.

  "Afzal waya sanar da kai muna nan?" Mummy ta tambaya.

  "Mummy nine" Khaleefah ya amsa.

  "How's she?" Afzal ya tambaya. Shiru ne ya d'auki wajen se chan Mummy ta amsa "Muma jira muke likitocin su fito tukuna."
  15 minutes more sega emergency room d'in ya bud'u nan duk suka duk'ufa sukayi wajen kowa da abinda yake tambaya. Nan Dr'n ya musu bayanin komai yakuma tabbatae musu cewa cut d'in beyi affecting Radial artery nata ba in less than an hour zata farfad'o. Godiya suka masa sannan ya fice.

   "Daddy, Mummy I'm so sorry I'm terribly sorry nasan duk laifi na ne."

  "Ko kad'an Afzal" Daddy yayi saurin katsesa "you're not to be blamed for anything, idan har akwai mey laifi anan toh nine so kabar damuwa."

  "Mummy I'm sorry."

  "Don't be Afzal mungode da kulawanka in shaa Allahu zan sanar da Nazeefah zuwanka."

  "Thank you Allah ya bata lafiya."

  "Ameen mungode Khaleefah ka rakasa" cewan Mummy.

  "No don't bother" Afzal yayi saurin amsawa sannan ya fice. Gida ya wuce direct sede tun shigansa Amal ta karanci yanayinsa wani iri. Bayan ta mar sannu da zuwa ta d'auko masa ruwa ta zauna a gefensa. "Ya Omri lafiya?"

  "Babu" ya amsa sama-sama.

   "Kaman ya babu Ya Omri? Tell me kaji."

   "Nagaji ne kawai barin je in watsa ruwa in huta" hannunsa tayi saurin kamawa" kafin ya mik'e "Please tell me Ya Omri nasan akwai abinda yake damunka."

   "Rania I'm sorry."

  "Why what for?"

  "Rania it's Nazeefah tana kwance a asibiti yanzu haka as we speak."

   "Subhanallahi meya sameta?"

  "Yanke kanta tayi."

   "Nazeefan? Dalili?"

  "Batun takardan ta, yanke kanta tayi in attempt to kill herself."

  "I want to go and see her Ya Omri."

  "Rania-"

  "Please" tayi saurin katsesa "Ya Omri ji nake kaman duk laifi na ne, komin mey Nazeefah tayi laifi na ne."

   "Kar kiyi magana haka Rania, in har akwai wanda za ayi blaming anan mahaifinku ne and he's sorry mu taya Nazeefah da addu'a kawai Allah yasa ta gane gaskiya da wuri."

  "Ameen but I still want to go and see her please kar ka hanani Ya Omri." Hannunta ya d'au ya rik'e a cikin nasa "Okay zanyi wa Mummy magana se muje."

  "Thank you."

  "Don't mention so me kika girka mana? I'm hungry."

  "Spaghetti ne kawai nima ban dad'e da dawowa daga school ba."

  "Oh! Muje toh."

****
   Bayan Maghrib Afzal yayi wa Mummy waya inda ya tabbatar da cewa ba a sallamesu ba har anan sannan yace mata suna shigowa shi da Amal. Acikin k'ank'anin lokaci suka isa inda Mummy ta taresu ta k'arisa ciki dasu. Nazeefah na ganin Amal taji tsikan jikinta gabad'aya na tashi yayinda ta shiga yi mata wani irin tsananin tsana.

  "Mey wanann take mun a d'aki Mummy? Send her out send her out!"

  "Nazeef-"

  "Bana k'aunan ganinta a kusa dani ku fitar mun da ita daga d'aki" ta katse Mummy da hanzari.

  "Nazeefah please" Afzal ya sa baki. "Kiyi hak'uri."

  "Hak'uri Ya Afzal? Da abinda zaka sak'a mun kenan? Ashe for all these while k'arya kake mun? I never expected this from you, I thought you love me ashe ba haka bane, ka sani daga kai har matar taka bazan ta6a yafe muku wannan abu da kuka mun ba Mummy send them out."

 "Nazeefah dan Allah kiyi hak'uri" Amal tace da ita.

  "Ko da wasa karki kuskura ki sake kiran suna na Amal saboda keba 'yar uwata ba ce. You ruined my life, first you stole my father away from me and then now my husband, meyasa kike nok'e-nok'e? Ki fito fili kice kina son ki zama ni kina son ki sace nun rayuwa. Amal na tsaneki, na tsani duk wani mey sonki, ba kuma abinda ze fi mun nishad'i da jin dad'i kaman inga gawanki bana k'aunanki in har kina son kanki ki ficemun daga d'aki you have absolutely no right to speak to me get out." Hawaye Amal ta shiga yi yayinda Afzal ya janyeta jikinsa "Ku fice mun daga d'aki bana k'aunan ganinku duka."

  "Nazeefah meyasa bakida mutunci ne?" Mummy ta tambayeta tana mey tsananin jin takaicin abinda Nazeefah ta aikata.

  "Shikenan Mummy zamu koma" fad'in Afzal "Nazeefah Allah ya baki lafiya we mean you no harm" daga fad'in haka ya sauk'o da ganinsa akan Amal "Let's go Amal." Badan Amal na so ba ta amince ya jata waje se kallon Nazeefah take tana kuka itako Nazeefah ko sake kallon 6angarensu batayi ba.

   "Meyasa baku barni na mutu ba Mummy? I hate my life I hate Amal."

   "Nazeefah it pains me as a mother ace ni na tsuguna na haifeki, Allah ma shaida ne ni ba tarbiyyan dana baki ba kenan, bansan a ina kika d'auko wannan banzan hali ba dan bazan ce na mahaifinku bane saboda koda wasa be ta6a gigin d'aukan ransa da kansa ba. Kuma Amal da kike gani kika raina wataran zaki nemata hannu bibbiyu ki rasata kuma ko kin k'i kin so 'yar uwarki ce ba abinda zaki iyayi da ze canza hakan. Ki tashi ki ci abinci yanzu za'a sallameki zamu koma gida."

   "Wani gida?"

  "Ban gane wani gida ba gida gida mana."

   "Meya samu hotel da muke zaune aciki?"

   "Zamu koma gida gun Daddy'nku nide na fad'a miki."

  "No Mummy ni bazan koma gun Daddy ba, a dalilin mey? Bayan duk bak'in ciki da k'uncin da nake ciki shine sanadi."

  "So? He's still your father nothing can change that."

  "Ni gaskiya bazan bi ku ba."

 "Ni na fad'a miki" tana kaiwa nan ta fice had'e da rufo mata k'ofan.
 
****
  Tun da suka shiga mota har suka isa gida Amal take ta kuka.
   "Amal it's okay with time in shaa Allah Nazeefah zata fahimci komai kukan ya isa haka" Afzal yace da ita bayan sun k'arasa ciki yana mey share mata hawayenta.

  "Yaya I feel so responsible for everything Nazeefah is going through, Nazeefah tana sonka har yau har gobe tana sonka she can't ever stop loving you."

  "And you too Lily, you love me don't you?"

  "I do Yaya amma Nazeefah kuma fah? Yaya har ranta fa ta so d'auka akan soyayyar ka."

  "Amal you matter to me more than anyone morethan Nazeefah kibar tada hankalinki kinji? I love only you" rungumeta yayi a hankali itama ta zagaye hannayenta a bayansa tana mey lumewa acikin rik'onsa yayinda kalamun Nazeefah suke faman yi mata wasa a kai.

****
   Washegari...
  Dawowan Daddy daga gidansu Mami kenan amma sam babu walwala tattare da shi. Yana shigowa Mummy da ta karanci yanayin nasa tayi mai sannu da zuwa.
   "Tak'i amincewa?" Ta tambayansa a hankali.

  "Hjy Surayya ko bani dama in nemi tubansu sun hanani bale in sanar dasu k'udurina, Jameelah tana matuk'ar fushi dani haka ma mahaifinta. Ban san ya zanyi ba muddin tak'i yafe mun, alhak'in ta ya cigaba da bina kenan idan da ma akaina kad'ai ze tsaya da da sauk'i amma har ku baku tsira ba, bana k'aunan sake ganin ku cikin k'unci Hjy Surayya bana son abinda ze sake raba kanmu yadda na samu da k'yar Nazeefah ta amince ta biyoki kuka dawo mun."

  "Ka kwantar da hankalinka Alhj."

  "Ta yaya Hjy Surayya? Ta ina hankalina yaga ta kwanciya bayan rayuwan mu duka yana cikin gwagwarmaya."

  "Ni da kaina zanje in samu Jameelah gobe muyi magana in shaa Allahu zata yafe maka komai ta kuma amince da k'udurinmu."

  "Keda kanki?" Ya tambaya yana mey kasa 6oye mamakin da ya sha.

   "Baka yarda bane?"

  "Hjy Surayya a ina aka ta6ayin haka? Dan Allah karki baiwa kanki wahala-"

   "Kabar zancen nan Alhj" tayi saurin katsesa "Ai mun wuce haka yanzu try not to worry Allah kaimu goben."

  "Ameen Hjy Surayya banida bakin yi maki godiya, Allah saka ya biyaki da gidan Aljannah."

   "Toh kuma godiyan mey kake? Muje kaci abinci."

  "Ya jikin Nazeefah?"

  "Da sauk'i tana kwance a d'aki tana bacci."

  "Toh madallah".****

   Tamkar mey ta6in hankali haka Nazeefah ta zame musu a gidan ko abinci tak'i ci tun dawowansu daga asibiti jiya da dare har izuwa yinin yau. Allah ma yaso ana sa mata ruwa. Banda kuka ba aikinta a gidan, Mummy tayi mata nasiha tayi mata fad'a amma ina tak'i ji haka zata kafa hotunan auransu da Afzal tayita kalla ba fashi. Washegari kamar yadda Mummy ta d'au alk'awari ita da Daddy suka jesu gidansu Mami inda ya tsaya daga waje ita kima ta k'arasa ciki. Sallama tayi yayinda take sa kai cikin gidan, Mami dake gida ita kad'ai ce ta amsa. Kallo d'aya tayiwa Mummy ta tabbata mahaifiyar Nazeefah ce saboda tsan-tsan kaman da sukeyi.

   "Mahaifiyar Nazeefah?" Ta tambaya. murmushi Mummy ta saka had'e da gyad'a mata kai. "Bismillah ki shigo" tabarma ta shimfid'a musu inda suka zauna sannan suka gaisa.

  "Bari in kawo miki ruwa."

  "A'a 'yar uwa ba amfani."

  "Toh lafiya dai ko?"

  "Lafiya k'alau batun Abdallah nazo muyi magana."

  "Kiyi hak'uri maman Nazeefah amma in har abinda ya kawo ki kenan saidai ki koma."

  "Nasani 'yar uwa nasan abinda Abdallah yayi miki da zafi da ciwo amma abu ne ya riga ya faru ba abinda zamu iyayi da zai canza hakan saidai muyi gyara. Kiyi hak'uri ki yafe masa, shi yafiya ba kowa bane Allah yake basa iko da zuciyan yi amma na tambayeki ne saboda nasan zaki yafe masa saboda ko ban tambaya ba nasan a wajenki 'yarki Amal ta yo gadon kyawawan d'abi'unta. Idan muka ce zamu biye ta zuciyoyin mu toh wallahi ba abinda zamu tsinana wa kanmu na arziki. Ko ban fad'a miki ba nasan kinsan irin tsanan da ke tsakanin yaran mu Nazeefah da Amal. Duk yadda Amal ke son shirya tsakaninta da 'yar uwarta hakan ya gagara kuma ba wanda ze iya had'a mana kawunan yaran nan sama da ke."

   "Ban fahimce kiba Maman Nazeefah ta yaya zanyi hakan?"

   "Ki amince ki auri Abdallah."

 "Iyyeh?" Mami ta zaro ido wuru-wuru waje. "Kikace?"

  "Eh, ki amince ki auri mijina ta hakan ne kawai zamu iya gyara zuri'ar mu mu had'a kawunan yaran nan dan Allah ki amince."

  "Kiyi hak'uri Maman Nazeefah amma bazan iya cika miki wannan buri naki ba, bazan iya auran Khaleefah ba bazan iya ba."

  "Zaki iya 'yar uwa muddin kika yarda da hakan, dan Allah karki bari tsanan dake tsakanin yaran nan yayi tsamari iche tun yana d'anyensa ake iya tank'warasa, muddin ba'a sa musu a jiki cewa mun zama abu d'aya ba yanzu toh wallahi gaba tsanan da zasu tashi dashi a cikin zuciyoyinsu baze so yayi kyau ba ki taimaka."

  "Maman Nazeefah tunda nake ban ta6a jin inda uwar gida tazo taya mai gidanta k'aro aure ba ko da kuwa a radio ne, saboda haka ban san abinda ke cikin zuciyarki ba keda mijinki, bansan mey kuke shirin yi mani ba amma koma menene kuyi hak'uri ku janye ni daga cikin matsalarku tunda na samu auren 'yata be mutu ba Alhamdulillah koni na mutu a haka bazan damu ba."

  "Jameelah da zuciya d'aya nazo na sameki bada wata manufa ba, Jameelah har yau har gobe nasan Abdallah yana sonki, kema kin sani ba sena fad'a miki ba, ni kuma har ga Allah har cikin zuciyata tun cemin da Abdallah yayi bakida aure naji tausayinki ya shige min zuciya nasan ba komai ya hanaki yin aure ba illa idan kika juya baya kika ga abinda Adallah yayi miki, shi ya lalata miki rayuwa dan haka kuma shi ya tantanci yayi making everything right don haka na basa goyin baya na bashi shawaran ya auro ki. Kuma kinga ta hakan ne kawai zamu iya had'a kawunan yaran mu. Zan barki kiyi tunani anytime your mind is made up ga lamba na" ta fad'a had'e da ajiye mata wani gajeren paper data rubuta number'nta ajiki "Seki kirani, hope to hear from you soon ni zan wuce."

   "Toh bari in rakaki."

  "Ba amfani 'yar uwa yi zamanki nagode da wannan lokaci da kika bani se anjima." Tun fitan Mummy Mami ta shiga tunani, gabaki d'aya kanta ya d'aure se bata jikinta yake trap su Mummy suke shirin shirya mata in ba haka ba har a ina uwar gida ta ta6a aran bakin mijinta dan nema masa mata?

    Daddy kuwa a gida ya sauk'e Mummy ya wuce gidansu Amal, yasani it's now or never. Bayan mey gadi ya bud'e mishi gate ya k'arasa ya samu gu yayi parking sannan ya fito ya nufi entrane door inda yake ta knocking amma ba response kasancewar bacci da suke duka daga ciki. Ganin ba mahalicci se Allah kawai seya kira wayan Afzal. Kaman a mafarki Afzal ya soma jin ringing na wayansa dake ajiye akan side drawer'n kansa kafin ya mik'a hannu ya d'aga har Amal itama ta farka. Sorry go back to sleep" ya sanar da ita rik'e a hannunsa yana mey sake daidaita kanta a k'irjinsa sannan ya d'au wayan inda ya tarar da missed call na Daddy nan take ya kirasa back, "Halo Daddy?

  "Na'am Afzal gani a bakin k'ofan gidanku fa amma shiru ko bakuwa nan ne?"

  "Afuwan Bacci ne ya d'auke mu bari inyi ma mey gadi magana ya bud'e maka."

  "No already ina ciki ya riga ya bud'e mun ina bakin parlour ne."

  "Sorry bari ina fitowa yanzu" ya fad'a had'e da kashe wayan sannan ya sauk'o da kallonsa akan Amal "Rania bari in fita Daddy yazo yana waje." Kai zalla ta gyad'a masa sannan ta koma gefe ta cigaba da kwanciyanta. Jallabiyansa ya sanya ya fito ya bud'e wa Daddy yana mey sake basa hak'uri. Ruwa da juice ya d'auko masa inda suka gaisa yake tambayansa ya jikin Nazeefah.

   "Da sauk'i Alhamdulillah."

  "Toh Allah k'ara mata lafiya."

  "Ameen yaya Amal kuma?"

  "Lafiyanta itama."

  "Ina sake baka hak'uri game da abinda Nazeefah tayi muku ranan, ni kaina I'm having a hard time with her kuyi hak'uri kuyi mata uzuri."

  "Ba komai Daddy duka nan mun san what she's going through is not easy fatan mu Allah kawo mata sauk'i."

  "Ameen Afzal thank you."

  "Ba komai Daddy."

 "Yauwa dama batun Amal nazo ne Afzal, ina son muyi magana da ita in kuma bata hak'uri gameda duk wani abinda nayi mata, Afzal ka sani a addu'a I want to make everything right I want to marry Amal's mother." Mamaki da dad'i ne ya ziyarci zuciyan Afzal wanda ya kasa 6oyewa "Tabbas kayi tunani Daddy, Allah sanya alkhairi acikin hakan ya biya maka buk'atunka na alkhairi."

   "Ameen Afzal zan iya yi ma Amal magana."

  "Sure tana bacci bari in tayar da ita."

  "No no in tana bacci ka barta kawai ko gobe ina iya dawowa."

  "A'a don't worry." D'akin nasu ya koma yaje ya samu Amal ya shiga tada ita. "Rania?"

   "Uhmmm?"

  "Daddy yazo."

  "Uhmm?"

  "Yana son ya ganki kuyi magana." A hankali ta bud'e idanunta "Yaya I don't want to face him ban san mey zance mishi ba."

  "I know Rania, I know kiyi hak'uri kije kiji mey zai ce miki."

   "Yaya-"
   
  "Kar muyi haka dake kinji? Tashi hungo kayanki kisa" da kanshi ya mik'ar da ita zaune ya sanya mata kayan da hijabi suka fito suka zauna a kan two seater.

  "Ina yini Daddy?" Ta durk'usa har k'asa ta gaishesa.

  "A'a please Amal koma ki zauna Afzal ce mata ta zauna" duk da haka Amal tak'i mik'ewa seda ya amsa tukuna. Gaisawa sama-sama sukayi sannan ya fayyace mata dalilinsa na zuwa dan ya nemi tubarta.

  "Nasan na cuceki a rayuwa Amal, nasan nayi depriving naki duk wani right da gatan da kika cancanta a rayuwarki, nasan ban kyauta miki ba ban kuma kyauta wa mahaifiyarki ba amma gani yau nazo neman tubanki" ya k'arasa had'e da sauk'a k'asa akan guiwoyinsa. "Daddy please ka tashi" tayi saurin cewa amma yak'i. "I'm dearly sorry Amal, kiyi hak'uri ki yafe mun I'm here and ready to take full responsibility for everything ki bani dama in cika aiki na a matsayina na mahaifinki, ki bani dama in kula dake in soki a matsayina na mahaifinki da jini na ke gudana a jikinki. Amal I'm so sorry" Afzal be ji tashin Amal ba kawai ganinta yayi gaban Daddy tana k'ok'arin d'agosa "Don't be Daddy komai ya riga ya wuce ka kuma sani ni na riga na yafe maka komai da jimawa Allah ya yafe mana gabad'aya."

   Rungumeta tsam yayi a jikinsa cike da farin ciki yayin da duk suke zubda hawayen jin dad'i "Oh Amal thank you so much Allah cigaba da yi miki albarka  bansan da wani bakin zan yi miki godiya ba." Itama a hankali ta zagaye hannunta a bayansa "Ameen Daddy ka daina yimun godiya." Se murmushi Afzal dake ganin komi kaman a mafarki yake faruwa, this's all he's ever wanted, ranan da Allah ze bayyana musu mahaifin Amal ya nemi tubanta su shirya se gashi Allah ya kawo musu ranan.

    "Amal?"

  "Na'am Daddy" ta amsa.

 "Amal nasan kinsan yadda Mahaifiyarki ta tsaneni ko?" Shiru tayi bata ce komai ba. "Amal I need your help, Mahaifiyarki tak'i ta bani dama in bata hak'uri bale in nemi tubanta Amal a shirye nake da in auri Mahaifiyar ki in har zata amince."

   "Zaka auri Mami?" Ta tambayesa d'auke da d'unbun mamaki.

   "In har zata amince, eh."

   "Mummy kuma fa? Bana son abinda ya faru tsakani na da Nazeefah ya faru dasu suma, in har Mummy bata goyi bayan zancen nan ba babu amfani Daddy."

  "Hasali Mummy'nku nema ta kawo shawaran nan Amal, Mummy'nku batada matsala da hakan idan har keda mahaifiyarki kun amince."

  "Kayi wa Mami magana ne?"

  "Naso amma tak'i bani dama d'azu nida Mummy'nku mukaje tayi mata magana sede har yanzu bata shirya bamu had'in kai ba please help me Amal nasan bani da daman tambayan hakan daga gareki but Amal I love your mom, har yau har gobe ina sonta kuma ina son in aureta." Na matuk'a Amal taji dad'i ta juma tana mafarkin rananda Mami zata shiga d'akin mijinta itama koda sau d'aya ne taji dad'i a rayuwanta. Inde hakane kuwa se inda k'arfin ta ya k'are inshaa Allahu bazata gaji ba seta shawo kan Mami waya sani ko da haka Nazeefah zatayi accepting nata ta bata chance suyi working out relationship nasu.

  "Amal? Bazaki iya ba ko? Bakiya son mahaifiyarki ta kasance tare dani ko? Look I'm terribly sorry wallahi nayi nadaman abinda nayi muku please forgive me."

  "Ko kad'an ba haka bane Daddy hasali nayi murna da farin cikin wannan labari in shaa Allah kuma zan tayaka yima Mami magana."

   "Nagode sosai 'yata Allah miki albarka sak'a miki da alkhairi."
 
  "Ameen Daddy."

  "Toh ni bari zan koma."

  "Da wuri haka Daddy?" Fad'in Afzal "kabari mana muci dinner."

  "A'a karka damu."

  "Please stay Daddy" Amal ta sanya baki.

  "Tunda 'yata tasa baki na isa ince a'a? Se in jira d'in." Dad'i sosai both Amal da Afzal suka ji haka Daddy ya yini musu koda Mummy taji shiru ta kira ta tambayi dalili kuwa ce mata yayi se zuwa dare ze shigo, zeci dinner a gidansu Amal. Kafin su dawo daga masallaci Amal har ta gama tsara kan dining da had'ad'd'un dishes ta bi gidan da turaren wuta. Nan tayi musu magana suka k'ariso se yaba abincin nata Daddy yake Afzal na ta jin dad'i ana yaba girkin matarsa. Hira suka sha kaman ba gobe anan Daddy ya gano ababe da dama tattare da Amal, he's in every way submissive to be a great Dad to Amal. Da yazo tafiya kuwa har wajen motansa suka rakasa sannan Amal tace a gaishe mata da Nazeefah.

   Washegari...
   Wajajen sha d'aya Amal ta dawo daga school bayan morning lectures nata ya k'are. Tana dawowa ta kama shara bayan ta gama ta aza tukunyan tuwo sannan ta d'au waya ta kira Mami wacce ta d'aga a karo na farko.

  "Halo Mami."

  "Na'am Amal ya kike?"

  "Ina yini Mami? Ya kike ya Papi?"

  "Lafiya k'alau ya Afzal?"

  "Yana office."

  "Makaranta fah?"

 "Alhamdulillah ban jima da dawowa bama kinsan mun kusa fara exams."

  "Aww haba? Se part 4 kuma ko?"

  "Eh in shaa Allah."

  "Toh Allah sanya alkhairi ya bada sa'a mamana."

  "Ameen Mami."

  "Ba wata matsala dai ko?"

   "A'a ba komai."

  "Toh madallah."

 "Mami jiya Daddy yazo."

  "Wani Daddy d'aya?"

  "Daddy mahaifin Nazeefah."

  "Kuma mahaifinki ba."

  "Eh" ta amsa tana murmushi "jiya yazo muka yini se bayan Isha ya tafi."

  "Allah sarki."

  "Yazo ya nemi tuba na."

  "Kin yafe masa?"

  "Eh Mami."

 "Madallah toh yayi kyau."

  "Mami kefa?"

  "Baby-"

  "Mami kiyi hak'uri komi ya riga ya wuce Daddy yace min yana son ya aureki."

  "Baby ke kanki kinsan baze yiwu in auri mahaifinki ba ko?"

  "Dalili Mami? Hasn't it always been your advocate to get married someday?"

  "Yes Baby amma ba ga mahaifinki ba."

 "Meyasa Mami? Didn't you loved him? Dan Allah kar kiyi ma Daddy haka."

  "Baby bazaki gane bane."

  "Toh meneh Mami? Daddy yana sonki har yau har gobe kema kin sani."

  "Baby ba wannan bane matsalar."

  "Toh meye ne?"

  "Mahaifiyar Nazeefah."

  "Mummy? Me tayi?"

 "Baby bakiya ganin kaman wani muguntan suke shirin yi mun? In ba haka ba a ina ne kika ta6a ganin inda uwar gida tazo nema wa mai gidanta aure?"

  "Gaskiya ba a ta6a yin hakan ba amma kuma I trust Mummy na tabbata Mummy baza ta ta6a aikata abinda ze cutar dake ba Mami."

   "Wai meyasa kike biye wa Mahaifin naki ne haka?"

 "Because he loves you Mami and he's sorry mey aciki idan kin yafe masa kunyi reconciling? Duk mun san abinda Daddy ya miki da ciwo da zafi amma yayi nadama Mami please kiyi hak'uri ki yafe masa ki sauraresa."

  "Baby-"

  "Please Mami do this for me" rok'an kanta Amal ta rik'a yi amma ina Mami fa sam babu a ranta ta auri Daddy. Suna gama wayan Amal ta kira Papi ta irga masa komai mamaki yasha yadda har abu haka ze faru amma Mami bata sanar da shi ba. Chan dare bayan sun k'are cin abinci yayi gyaran murya had'e da kiran sunanta.

   "Na'am Abba wani abu ne?"

   "Tun shekaran jiya kika ce Khaleefah be sake shigowa ba?" Dum taji zuciyanta ya tsinke amma sam bata kawo a ranta har Amal zata kirasa ta sanar da shi komai ba dan haka se tayi masa k'arya "A'a wani abu ne?"

   "Meyasa kike yi mun k'arya Jameela? Yaushe kika fara haka?"

  "Abba-"

  "Ashe har matarsa ya turo da ta baki hak'uri amma kika k'i sauraronsu?"

  "Abba ba haka bane."

  "Dakata tukuna, shi fa d'an Adam ajizi ne kuma dukan mu nan ba wanda zece baya yi wa Allah sa6o amma kuma mey? Da zaran muka tuba kuma muka nemi yafiyarsa yana yafe mana ba wanda yace Khaleefah ya kyauta abinda yayi miki amma tunda ya gane kuransa yana son ya dai-daita komai meyasa bazaki basa had'in kai ba?"

   "Abba ba haka bane."

   "Jameelah har yanzu ke yarinya ce shekarunki dududu nawa ne? Kin kai arba'in ne?"

  "A'a Abba"

  "Toh haka kikeson ki k'are rayuwarki ba aure? Bakiya son ki bar yaran da zasu yi miki addu'a bayan kin rasu? Ko gani kike Amal ita d'ai ta isheki? Kisani fa dan ba na nuna miki bawai hakan na nufin ina jin dad'in zamanki a haka bane, kiyi wa kanki fad'a ki dubi tuban mutumin nan ku rufa wa junanku asiri." Shiru tayi batace ko k'ala ba "Ko baki ji ba?"

  "Naji Abba."

  "Toh tashi ki tafi."

  "Toh seda safe." Ko bacci Mami ta kasa yi ranan se tuna abunda Amal da Papi suka fad'a mata take gabad'aya ta rasa mey take ciki ita har ga Allah bata k'aunan abinda ze sake had'ata da Daddy saboda kasa mancewa da abinda yayi mata da take. Duk sanda ta kallesa se ta tuna da wancan mumunar ranan taji ta tsanesa. Amma ya ta iya yanzu tunda har Papi yasa baki? Bayan nan kuma kaman yadda Mummy ta fad'a ko ba dan tana so ba kamata yayi ta amince saboda su gyara zuri'a su had'a kan yaransu. Daga k'arshe de kawai ta yanke hukuncin yin Istikhara duk abinda Allah ya za6an mata shi zata bi.

  _One week later..._

    Cikin satin nan da aka shiga su Amal da Nazeefah suka fara exams har yau Mummy bata sake ji daga Mami ba shima Papi be sake yi mata magana ba as ya zuba mata ido yaga iya gudun ruwanta. Amal da Afzal suna zaune a parlour se faman kallo yake a laptop nasa yasa earpiece a kunne ita kuwa se karatu take kasancewar tana da paper k'arfe d'aya gobe. Wayanta dake gefenta ne ya shiga ringing dubawanda zatayi taga new number, without hesitation ta d'aga tare da yin shiru.

  "Assalamu Alaikum" akayi sallama daga d'ayan 6angaren.

  "Mummy?"

  "Ashe 'yar tawa zata gane muryan uwarta."

  "Mummy ina yini?"

  "Lafiya k'alau ya kike ya gida ya Afzal kuma?"

  "Alhamdulillah dukan mu lafiya."

  "Ya exams toh?"

  "Alhamdulillah Mummy ya Nazeefah? Jiya ma Khaleefah ya kirani muka gaisa."

  "Allah sarki ya Mami?"

  "Lafiyarta k'alau."

  "Kwana biyu shiru banji daga gareta ba nace ko zaki iya mun texting number'nta."

  "Sure Mummy bari in miki texting yanzu."

  "Yauwa 'yata thank you Allah ya bada sa'an jarabawa."

  "Ameen Mummy seda safe" nan tayi hanging take tayi mata sending numban Mami, itama Mumny tana gani tayi replying nata da 'Thanks.'

   "Lafiya dai ko?" Afzal da ya zare kunnen earpiece nasa d'aya ya tambaya.

  "Lafiya kawai tana son su gaisa ne."

  "Oh Rania I'm hungry."

  "Toh Ya Omri baga kitchen ba."

"Aww ma ni zanyi girkin da kaina?"

  "Toh Ya Omri karatu fa nakeyi" ta fad'a cike da shagwa6a.

  "Ni o'o" ya fad'a harda doke kafad'a wanda hakan yasa Amal dariya. "Toh mey kakeso kaci?"

  "Na fasa chin abincin ma I just want to sleep."

   "Tun yanzu?" Ta tambaya had'e da duban agogo "it's just 9 O'clock."

  "Yes Rania na gaji kallon ma na fasa."

  "Toh sekaje ka kwanta ai seda safe."

  "Ni kad'ai?"

  "Toh Ya Omri baka ga karatu nakeyi ba?"

  "Nasani anan nake nufi" kafin ta karanci abinda yake shirin yi kawai taji ya sauk'e kansa a k'irjinta ita ta rasa damuwansa, ga gado amma yace shi se a jikinta ze kwanta adjusting kansa yayi ya kwanta da kyau a jikinta "Toh goodnight" tace da shi.

  "Goodnight Rania I love you."

  "I love you too Ya Omri" ta amsa had'e da placing peck a cikin gashin kansa. Handout nata ta d'auka ta cigaba da karatunta haka har bacci ya d'auketa itama. Se chan wajajen k'arfe biyu Afzal ya farka se jin numfashin mutum yake a kansa shafawa da yayi ya gano Amal ce. Murmushi ya saki sannan ya rik'e kanta ya janye nasa a hankali. Handout na hannunta ya cire ya d'agata ya kaita d'aki suka kwanta.

   Washegari Mummy da Daddy suka jesu gidansu Papi kaman yadda Munmy ta sanar da ita cewan zasu shigo sede bata ce da Daddy ba sam Mami batayi farin cikin zuwansu tare ba amma ya ta iya? Sannu da zuwa tayi musu ta shimfid'a musu tabarma sannan ta kira Papi inda duk suka gaisa.

   "Toh ga Jameelah nan sama da sati kenan yau ina jiran ji daga wajenta amma shiru se jiya da daddare bayan da Surayya ta kira take fayyace mun cewa tayi Istikhara kwanaki hud'u da suka wuce za6i kuma Allah yayi mata" se kuma yayi shiru.

  "Muna jinka Abba" Daddy da ya kasa hak'uri ya tambaya.

  "Khaleefah zan d'auki amanar 'yata in baka ba wai dan ka cancanta ba se don yin hakan ne ya kamata kodan mu samu mu had'a kawunan yaran nan. Kai ba yaro bane ka riga kasan komai ba sena sake nanata maka ba seka taimaki kanka kayi abinda ya dace wannan duka matanka ne ka kwatanta yin adalci a tsakaninsu Allah ya baku zaman lafiya gabaki d'aya batun yafiya kuma duka mun yafe maka Allah yafe mana gabaki d'aya."

  "Ameen Abba nagode sosai in shaa Alalhu zaka sameni mey rik'on amana Jameelah nagode Allah sak'a da alkhairi."

  "Ameen" duka suka amsa.

  "Abba in ba matsala bana so a jinkirta auren."

  "Toh Khaleefah gaskiya seka d'an bamu lokaci mu shirya."

  "Wani shiri Abba? Ba shirin da zakuyi zan d'au nauyin komai da komai ni kawai kar mu jinkirta."

  "Toh madallah zamuyi magana duk abinda tace haka za'ayi."

  "Toh nagode, nagode sosai zamu koma."

  "Toh Surayya kekuma Allah ya sak'a miki da alkhairi ya baki riban hak'uri tabbas irinku acikin mata d'ad'd'aiku ne Allah ya baku zaman lafiya mai d'aurewa."

  "Ameen Abba nagode" ta amsa.

  "Toh zamu koma ga wannan" Daddy yayi maganan had'e da zaro wani bak'in leda daga aljihunsa wanda yake d'auke da kud'i.

  "Na mey kuma? Kaga kar mu fara haka da kai."

  "Abba dan Allah kar kayi rejecting mu tafi Hjy Surayya." Duk yadda Papi beso kar6an kud'in ba seda ya kar6a saboda yadda Daddy yayita insisting.

   Da Maghrib bayan Daddy ya dawo daga masallaci Nazeefah tayi sallama ta shiga d'akinsa inda ta tarar da Mummy aciki. "Ya Nazeefah lafiya?"

  "Daddy ina son bayan graduation namu inyi proceeding masters program d'ina."

  "Toh masha Allah anan Unimaid zakiyi?"

   "A'a a UK."

  "K'asar waje?" Mummy tayi sayrin tambaya.

  "Eh Mummy."

  "Ko meyasa?"

  "Achan nafi so inyi yafi sauk'i."

  "Toh shikenan se ayi making arrangements amma ai sekin jira results naku sun fito."

  "Zan tafi tun yanzu in results d'in ya fito seku amsa min a tura mun achan, Nagode" tana kaiwa nan ta mik'e ta fice. Bayanta Mummy ta biyo "Why the sudden decision Nazeefah? I thought ke kikace bakiyason fita k'asar waje karatu?"

  "I changed my mind Mummy."

  "Saboda mey?"

 "Babu."

  "Saboda kiyi nesa da Amal yeah???"

  "Mummy Amal ba matsala ta bace bani da damuwa da ita I'm doing this for myself."

  "Ke Nazeefah bakiya tunanin mutuwa ne? Rayuwan ma nawa take da har kike neman gujewa 'yar uwarki haka?"

   "Amal ba 'yar uwata bace stop referring to her as one."

  "Da kin k'i da kin so Amal 'yar uwarki ce yanzu maganan da muke da Daddy'nku ma shirin auro mahaifiyarta yake Jameelah."

   "What? Wa d'in?"

   "Mahaifiyar Amal, Jameelah."

  "Wannan wani irin abin kunya ne? Kuma kika amince?"

 "Hasali ni na kawo masa shawaran ma saboda mun riga mun zama abu d'aya yanzu."

  "What? Mummy are you okay? Taya zaki amince Daddy ya k'ara aure, auren ma wai mahaifiyar Amal of all people? Wallahi baza ayi abun kunyan nan da ni ba."

  "Ya kika iya? The earlier the better Nazeefah just accept it mu da su mun zamo abu d'aya."

   "No Mummy bazan ta6a accepting su Amal as one of my own ba duk abinda kuke shirin yi count me out cause I'll never welcome their kind into my family."

  "Yayi miki kyau."

  ****
  Acikin wata d'aya Daddy yagama had'a d'akin Mami, an sa rana nan da sati uku. Da ikon Allah kuma su Amal suka k'are exams nasu results yafito alhamdulillah duk sunyi passing. Ba yadda Mummy batayi da Nazeefah ba da tabari se bayan d'aurin auren tayi tafiyan nata amma tak'i. Ana saura sati d'aurin aure tabar Nigeria.

   ****
   "Rania lafiya?" Afzal daya kasa hak'ura dan jin meke faruwa ya tambaya.

   "Ya Omri" kawai seta rushe da kuka.

  "Subhanllahi!" da sauri yayo kanta hugging her in his arms yana bata hak'uri. "Ya Omri ta tafi" ta amsa at last.

   "Ita wa?"

  "Nazeefah" ta sanar dashi yana share mata hawayenta.

  "Ta tafi ina?"

  "UK tabar Nigeria tace bazata sake dawowa."

   "What? Meyasa?"

  "Ya Omri har yau Nazeefah takasa acepting d'ina da Mami tun kafin ma taji Daddy ze auri Mami tace ita zata wuce Uk tayi proceeding masters nata yanzu kuma dataji gaskiyan al'amarin jiya bayan sunyi landing ta kira Mummy ta jaddada mata cewa bazata sake dawowa ba."

   "Shhh it's okay sooner ot later zata gano gaskiya in shaa Allah kuma da k'afarta zata dawo."

  "I really do hope so Ya Omri bana son Nazeefah tayi nesa da gida the more she stays away from us the more lost she'll be."

  "I know but don't lose hope okay? Nasan Nazeefah she'll soon come around."

  "Thank you Ya Omri."

   "Anytime, still zamu fita d'in ko?"

  "Yes."

  "Alright toh."

***

   Mami ce zaune a d'akinta ta baje zannuwa da dama a gabanta tana za6an wanda zata kai d'inki. Tana cikin haka sega wayanta dake gefenta ya shiga ruri dubawan da zatayi taga Daddy ke kira. 'Yar murmushi ta saki sannan ta d'aga.

  "Amarya bakiya laifi koda kin kashe d'an masu gida ne."

 "Haka de kace" ta amsa tana murmusawa.

  "Toh ya kike?"

  "Lafiya k'alau ya 'yar uwata?"

  "Lafiyanta k'alau yanzun tace tasan kanki yayi zafi k'ila ma kina jin yunwa amma ba hankalinki."

   "Ai kuwa wallahi ina ta sorting kayakin nawa."

  "Toh mey kikeso ayi miki ordering wai?"

  "Laaa kace mata kar ta damu zan dafa taliya in ci."

 "A'a nikam kinga aikana tayi fad'a mun."

  "Toh inde haka ne kace mata duk abinda ya sawwak'a."

  "Toh shikenan ki gaishe min da Abba."

 "Zeji se anjima."

  "Yauwa" da haka sukayi sallama.

  "Mey tace wai?" Mummy dake gefensa ta tambaya. "Cewa tayi akai mata duk abinda ya sauwak'a."

  "Toh se a sai mata fried rice and chicken ai ko ya kace? Ita da Abba."

  "Se abinda uwar gida tace."

  "Kai Alhj bana son zolaya fa."

   "Ai gaskiya ce."

  "Nifa har yau fushi nake da kai."

  "Afuwan in uwar gida na fushi dani a ina zan sa kaina?"

  "Eh mana kak'i had'ani da 'yar uwata a gida d'aya."

  "Ba wai nak'i bane Hjy Surayya."

  "Kak'i ne mana tun yaushe nake binka ayi a had'a ginin nan kak'i."

   "Ai kinga har yau aikin ake kan yi in shaa Allahu ana kammalawa zan dawo da ita nan chan d'in temporary ne."

   "Promise?"

  "I cross my heart."

  "Toh Allah nuna mana ."

  "Ameen Hjy Surayya nawa na kaina, bari in je in siyo ma 'yar uwar taki abinci."

  "Gaskiya kam kar mu bar amarya da yunwa."

  "Toh a dawo lafiya."
 
 ***
  Ranar Asabar aka d'aura auren Alhj Abdallah da Jameela Muh'd akan sadaki dubu d'ari da sisin gwal arba'in. D'aurin aure kawai akayi da yammacin ranan aka kai amarya d'akinta. Se wani tattalinta Daddy yake, bayan sunci kajin amarcinsu Daddy yasa su sukayi raka'a biyu dan yima Allah godiya.




RANA D'AYA!
#RD

 King miemiebee👄

6 comments:

Unknown said...

Tnx...its been a while.

Unknown said...

Osheey Miemie Allah ya kara basira
Nazeefah Allah ya shiryeki kedai

fatima said...

am going to miss u beautiful #nazeefa...duk abun nan da tayi i can't stop loving her
Allah ya Kara basira update soon

Unknown said...

Toh! Su Mamie anyi Aure Allah yabada zamn lfy ,ita kuma Nazeefa Allah ya shiryeta ta game gsky tadawo gida.

Unknown said...

Nazeefa Allah shiryeki ki gane cewa ,amal bata cucekiba kuma ba laifinta bane sakin da afzal ya miki. Sakayyan abinda mahaifinta ya shukane?

Blog27999 said...

Strange "water hack" burns 2lbs overnight

Over 160 000 men and women are hacking their diet with a easy and SECRET "water hack" to burn 2 lbs each night as they sleep.

It's effective and it works all the time.

Here's how to do it yourself:

1) Grab a clear glass and fill it half the way

2) Then follow this awesome HACK

and you'll be 2 lbs lighter the next day!