BY MIEMIEBEE
PAGE 34
Ko makaranta Amal ta kasa fita washegari saboda yadda jikin nata ya tsananta, gashi de ta fara shan maganin amma ba sauk'i. Kaman yadda Maamah ta d'au alk'awari haka tazo ta duba Amal da soft drinks nata, Safiyya ce ta amsa ta sa a fridge sannan ta kai ta d'aki inda Amal ke kwance akan gado ta duk'unk'une kanta acikin bargo se kakkarawa take. K'arya ne mutum ya ganta be tausaya mata ba.
"Subhanallahi Amal!" Maamah tayi exclaiming cike da tashin hankali. "Amal dan Allah karki mutu" take idanunta suka ciko da hawaye tsan-tsan tausayi.
"Amal mey kike yima kanki haka? Meyasa baki kira Mami ba? Meke damunki dan Allah?"
"Maamah calm down ki kwantar da hankalinki."
"Ya jikin naki? How are you feeling?"
"Da sauk'i zuwa anjima zazza6in ze sauk'a morning fever ne."
"Subhanallahi sannu ai baki fad'a mun zazza6in yayi tsanani haka ba what's wrong?"
"Maamah I'm pregnant" ta sanar da ita.
"You're what?!" Tayi exclaiming had'e da zaro ido waje.
"Maamah ina d'auke da cikin Yaya" ta jaddada mata yayinda ta rushe da kuka. Hugging nata Maamah tayi tana kukan tare da ita sun dad'e a haka sannan ta janye Amal a hankali tana mey share mata hawayenta.
"Amal I'm so happy for you, Allah ya inganta idan lokacin yayi ya raba lafiya."
"Ameen" ta amsa chan ciki-ciki.
"Ya Afzal ya sani?"
"Ke na fara fad'awa ko Mami ban kira na sanar da ita ba."
"Amal why? Ai Ya Afzal ya kamata ya fara sani ke bakisan wannan news shi ze zame sanadin shirya tsakaninku ba?"
"Shirya tsakanin mu?" Ta tambayeta had'e da sakar da murmushin takaici "Maamah things just got worst kin san mey Yaya yamun?" Kai Maamah tayi saurin kad'awa.
"Korana yayi daga d'akinsa shiyasa kika ganni anan bayan nan jiya yake ja mun Allah ya isa idan har na sake shigo masa da na miji gida Maamah zargi na Yaya yake, gani yake kaman duk zaman mu cin amanan sa nake."
"Innalillahi wa inna ilai raji'un the fuck is wrong with Ya Afzal? Ya yake abu kaman wanda baida ilimi? Ai yaci ace yasan abinda zaki iya aikatawa da abinda bazaki iya ba daga gun wani d'an jakar uban yaji wannan batu? Waya gaya mishi kina shigo da maza gidan nan?"
"Wallahi ban sani ba Maamah kinsan zurfin cikin Yaya bayi ta6a fitowa fili ya fad'awa mutum abu."
"Amal dan Allah ki tattara kayakinki kibar mai gidan nan haka wannan walak'anci dame yayi kama? Se kikace mishi mey dayace kibar masa d'akin nasa?"
"Mey kuwa zance masa? Pillow na kawai na ja na fice mey zance masa?"
"Hmm wallahi munafukar mey aikin ki d'innan nake zargi da ganin yadda fuskanta yake bak'i k'irin d'innan haka zuciyarta take in ba haka ba ina Ya Afzal zeji batun nan? Bawai zama yake a gida koda yaushe ba dole gaya mishi akeyi."
"Na gwada mata magana tace ba ita bace banida lafiya ban so jan maganan ba nace kawai shikenan."
"Wallahi itace kinji rantsuwa ba kaffara ina gaya miki Nazeefah ba kishiryar arziki bace wallahi aiki suke tare da 'yar nan dalilin daya sa tun farko ta kawo miki ita kenan. Wallahi aiki suke tare."
"Nazeefah kuma?"
"Don't be fooled by her kind gestures makashinka na nan tare da kai duk inda kake, kiyi tunani ita munafukar Safiyyan ce take kai wa Nazeefah rahoton komi a gidan nan ita kuma mak'irar seta ce ke ce kika kira kika sanar da ita."
"Maamah ni bana son abu da tashin hankali da tada magana idan ma aiki suke tare wataran dubunsu ze cika dukda cewan ban yarda da hakan ba I know Nazeefah baza ta ta6a yimun haka ba."
"Hmm Amal kenan ki bud'e idonki kisani yadda ka d'auki mutum ba haka yake d'aukanka ba ko a jinki kowa ne keda zuciya d'aya kamanki? Wallahi ba haka bane, balle wai har kice kin aminta da kishiyarki? Kishiyan da ba wacce take gaba dashi a fad'in duniya kaman ka? Ki bani izini inyi questioning mey aikin kin nan kawai."
"Maamah please ki barta bana son k'ananun magana" Maamah bata saurareta ba ta mik'e "Maamah dan Allah ki dawo" ficewa tayi ta dawo da Safiyya biye a bayanta "Bani wayanki" ta buk'aceta.
"Waya na kuma?"
"Eh wayanki."
"Lafiya?"
"Wani abun kike 6oyewa ne?"
"Wani irin magana kuma kike Aunty? Mey zan 6oye?"
"Good then pass me your phone" hannu ta mik'a mata tana jiran ta sanya mata shi aciki bayan Saffiya ta d'au lokaci ta sanya wayan cikin hannun Maamah cike da fargaba.
"Amal ya numban Nazeefan yake?"
"Maamah dan Allah ki bata wayanta ni bana son matsala."
"Mstw" wayan Amal taja ta bud'e ta latsa numban Nazeefah had'e da zubawa cikin wayan Safiyya sede da mamaki taga babu numban a wayan Safiyya how can it be possible? Ta tambayi kanta.
"Babu ba?" Amal ta tambayeta kai zalla ta gyad'a "Ai na fad'a miki ba su bane dan Allah ki bata wayarta amshi Safiyya kiyi hak'uri."
Amsa tayi tace "Ba komai Aunty Allah k'ara miki lafiya" da haka ta fice.
"This can't be possible wallahi ina ji a jikina 'yar nan munafuka ce."
"Maamah please enough gashi de kin gani ko lamban Nazeefah bata dashi kuma bataje boko ba bale kice ta haddace lamban ne akanta ranan lamban ta na tambayeta amma bata sani ba, babu yadda za'ayi kuma ace ta haddace na Nazeefah, na gaya miki ba had'in Safiyya da Nazeefah."
"Hmm toh mey gadin kine? Wallahi dole akwai wanda yake fad'awa Ya Afzal abubuwan nan ko kina tsammanin shi yake zama yake shirya zancen?"
"I will not be surprised idan shi yake shirya komi Maamah saboda a fili yake nuna mun na fita a kansa baya sona ban ta6a tsammanin Yaya zemin haka ba watarana wallahi yanzu nake nadaman auransa da nayi nasan ko da wasa Ya Abdul baze ta6a yimun haka ba."
"Kar ki ce haka Amal Ya Afzal mijinki ne har yanzu."
"Maamah I miss Ya Abdul I miss him so much" hugging nata Maamah tayi yayinda ta cigaba da bata hak'uri.
"Amal be kamata mu nad'e hannu mu zubawa koma wa yake miki wannan aika-aika ido ba we have to do something."
"Mey zamuyi toh Maamah? Ba muda hujja bamuda komai."
"Ido ya kamata ki sawa mey aikin kin nan wallahi ina ji ajikina itace munafukar lamarin nan."
"Nace miki ki cire Safiyya daga lamarin nan."
"Hmm toh ke yanzu haka zaki cigaba da zama a gidan nan Ya Afzal na cusa miki bak'in ciki yana miki walak'anci har seya kasheki tukuna? Da wanne zakiji? Da laulayi ko kuwa da masifan miji?"
"Maamah tunda nasan ni banyi masa komai ba ya cigaba da koma mey yakeyi tabbas wataran Allah ze wanke ni kuma shi zeji kunya, zan cigaba da kai kuka na wa Allah ai shi ba azzalimin bawa bane."
"Haka wannan yake amma ki kira Mami ki sanar da ita wannan k'aruwan da kika samu."
"I'll amma ba yanzu ba saboda nasan one way or the other magana ze kai kunnen Yaya idan har na sanar da Mami abinda bana so kuma kenan bana son Yaya yasan ina da ciki."
"Amma ai ya kamata ya riga kowa sani tunda shine mahaifin abinda ke cikin naki, Amal you can't do this on your own."
"Ki yarda dani idan nace miki Yaya yana iya denying baby'n nan yace ba nashi bane tunda har ya iya bud'an baki yace mun ina kawo masa maza gida."
"Wallahi Ya Afzal na tattare da babban asara tunda de kome aka gaya mishi hawa yake ya zauna akai ba tare da yayi bincike ba, sannu kinji?"
****
Yini ranan Maamah tayi mata se wajajen biyar da rabi ta tafi. Seda Safiyya ta tabbata Amal tayi bacci ta dannawa Nazeefah kira lokacinda tasan Afzal bai gida ya fita masallaci.
"Hello Aunty?"
"Ya zaki kirani warhaka idan da Ya Afzal na gida fa?"
"Aunty naga kaman lokacin isha yayi ya fita sallah ne."
"Idan da kuma bai fita ba fah? Ba nace se ya fita office zaki na kirana ba?"
"Aunty kiran gaggawa ne."
"Meya faru?"
"Wallahi Aunty ciki take dashi."
"Ci mey!" Nazeefah tasa wani d'ankaren ihu.
"Wallahi ciki take dashi."
"Innalila..inna..innalila" dan rikicewa tama kasa k'arisa salatin yayinda cikinta ya d'au ruwa. Yau ga ranan da ta jima tana gudu. "Amal nada ciki kikace?"
"Eh Aunty."
"Wayyo na shiga uku na lalace ya kika gane? Kinsan ba a wasa da zancen ciki ko?"
"Wallahi ba wasa ba Aunty, tun rananda Uncle ya tafi ta ke zazza6i da amai d'azu wata k'awarta tazo sena ji suna tattauna wallahi ciki ne da ita."
"Yau na mutu na lalace taya Amal zatayi ciki gabani na? Wallahi baze yuwu ba koda sama da k'asa ne zasu had'u se na san yadda zanyi na zubar da cikin nan wallahi bazata haifesa ba."
"Aunty gashin be isa haka ba? Wallahi Aunty ta fara zargi na kokuma ince k'awarta, k'awarta ta fara zargi na d'azu harda amsan wayana ta zuba lamban ki aciki da ace nayi saving da shikenan sun kama mu."
"Wata mak'irar k'awarce take neman rusa mun plan bayan na kusan cimma burina?"
"Wata wai Maamah."
"Safiyya aikin mu ya koma baya be kamata ace Amal nada ciki ba nashiga uku amma Ya Afzal be sani bako?"
"Gaskiya da wuya kinsan basu magana."
"This's the only opportunity I have ya zama mun dole in zubar da cikin nan kafin su shirya dan muddin suka shirya shikenan nawa ya k'are ya zamuyi? Be kamata mu bari Ya Afzal ya gano Amal na d'auke da cikinsa ba."
"Toh ya zamuyi Aunty ni Wallahi tsoro nakeji kar a kama ni, ko a haka muka bar Aunty ta sha wuya, ya isa haka please."
"Wawiya ki saurareni gobe Afzal ze dawo mata inason ki taho mu had'u dake inda muka saba an gama rubutun zan baki seki je ki sa mun cikin wardrobe nasa ta k'ark'ashin kayakinsa kina jina?"
"Eh Aunty."
"In shaa Allahu daga gobe zaman Amal a gidan ya k'are na tabbata idan Ya Afzal ya karance rubutun nan se ciwon zuciyansa ya kusan tashi daga nan seya buga mata saki ta tattara tabar gidan mu samu mu zubar da cikin kowa ya huta."
***
Ba k'aramin rama Amal tayi ba acikin wannan kwana biyu sosai cikin yake bata wuya d'an kumatun da take da shi ma tuni suka zube ta kuma yi duhu. Yau da yamma ana neman shida Afzal ya dawo gida sannu da zuwa Safiyya tayi masa sannan ya wuce d'aki ya rage kayan jikinsa ya bud'e wardrobe nasa ya sanya wasu files aciki ya sake kullewa sannan ya fito parlour.
"Amal na gida ne?" Ya tambayi Safiyya.
"Eh tana d'akinta."
"Batun maganan da kikayi mun ranan shin dagaske ne Amal ta shigo da wani gidan nan?" Har yau zuciyarsa ta kasa aminta masa da hakan.
"Uncle meyasa zan fad'a maka abinda idanu na basu gane mun ba? Ni tasa na kawo masa drink da snacks wallahi ka yarda dani."
"In tambayi mey gadi? Kisani idan har sharri kikayi mata ina iya 6a6alla ki a gidan nan." Sosai cikin Safiyya ya d'au ruwa yadda Afzal yake maganan sam ba wasa tattare da shi.
"Kasan Malam Ahmad da zama a majalisa kuna fita shima yake fita se lokacin dawowanku ya ke shigowa da k'yar idan yana nan Aunty ta shigo in kuma baka yarda dani ba muje a gabanta ka tambayeni a idonta in shaa Allahu amsan dana baka zan sake nanatawa saboda ba k'arya nake yi maka ba."
Sajen fuskansa ya shafe cike da mamaki da kuma rashin sanin abunyi gabad'aya kansa ya d'aure. "Shikenan mey kuka girka?"
"Babu Aunty bata ji dad'i ba kwana biyu so bata girka komi ba nima batace in girka komi ba kuma."
"Bata da lafiya?"
"Eh."
"Meyake damunta?"
"Toh nima ban sani ba gaskiya."
"Ina take?"
"Tana kwance a d'akinta tana bacci nakega."
"Jeki ce mata ta shirya driver ya kaita asibiti."
"Toh" ta amsa ta fice sallama tayi bakin k'ofan Amal sannan ta shiga ta k'arisa ciki had'e da durk'usawa daga gefen gadon.
"Wani abu ne?" Amal ta tambaya.
"Uncle ne ya dawo."
"In yunwa yake ji seki dafa masa abinci kinsan banida lafiya ban iya nayi girki ba."
"Eh na sanar dashi."
"Rashin lafiyan nawa?"
"Eh."
"Meya kaiki? Ni na aike ki?"
"Kiyi hak'uri Aunty yanzu de yace ince miki ki shirya wai driver ya kaiki asibiti."
"Kice mishi nagode bana buk'ata."
Sak abinda Amal ta fad'a mata taje ta fad'awa Afzal a fusace yace, "Ki ce mata ta shirya ba wasa nake ba." Haka ta dawo ta fad'awa Amal inda Amal ta sake turata kice mishi "Nace bazan je ba."
"Uncle wai bazata je ba" a fusace ya k'arisa d'akin had'e da bankad'e k'ofan na sosai Amal ta tsorata.
"Ki tashi a kaiki asibiti nace."
"Nace bazan je ba nagode."
"In ta halin ki za a bi a jinki ko kallon ki zanyi ne a gidan nan? Karki 6ata mun rai Amal ki tashi driver ya kaiki asibiti."
"Nace bazan jeba Yaya ana dole ne?"
"Rashin kunya kuma zakiyi mun? Ki cigaba Amal zamuga inda wannan banzan d'abi'ar zata kaiki" bata sake ce masa komai ba har yaja k'ofan ya fice. Wani irin masifaffen kuka ta rushe da, maghrib nayi ta mik'e tayi niyya bayan sallan Isha ta sanya hijabi ta fito waje takawa take wane wacce k'wai ya fashewa aciki har ta wuce Afzal dake zaune a parlour yana aiki akan laptop nasa, be ce mata komi ba itama bata ce da shi ko k'ala ba. Chan bada dad'ewa ba yana zaune kawai ya fara jin sautin amai daga kitchen besan lokacinda yayi wulli da laptop nasa ba ya nufi kitchen d'in inda ya tarar da Amal tsugune jikin sink tana ta kwararo amai. Na matuk'a ta basa tausayi kad'an ya rage beje ya rungumeta ba amma ya dakatar da kansa. Kallonta ya cigaba dayi har tagama ta d'auraye bakinta zamewa k'asa tayi don yadda bata da k'arfin ko sisi sosai Afzal yake ji ajikinsa duk yadda yaso shareta hakan ya gagara besan a lokacinda ya k'arisa ciki ya shiga d'agata ba.
"Ka sauke'eni bana so I can take care of myself" ta fad'a a galabaice sede be saurareta ba ya d'agata sama chak be sauk'eta a ko ina ba se akan kujera a parlour "Safiyya!"
"Na'am Uncle" ta amsa had'e da fitowa daga d'akinta.
"Wuce ki d'auko mun key'n mota na."
"Ki dawo Safiyya nace maka bazan je asibiti ba" Amal ta fad'a a kasalance "Zo ki tayani in mik'e Safiyya" ta buka'ceta har Safiyya ta shiga takowa gun Amal Afzal ya dakatar da ita "Nace kije ki d'auko mun key'n mota na ko?"
"Uncl-"
"Bakiya ji ne?" Har ta shiga takawa zuwa d'akin nasu Amal ta tsayar da ita "Nace kizo ki tayani in mik'e baki jini bane?"
"Uncle dan Allah ka bari in taimaka mata kayi hak'uri" ta fad'a tana kakkarwa.
"Kije idan kika kashe kanki seki huta kowa ma ya huta" yace da Amal ko kallonsa batayi ba ta jira Safiyya ta taho ta taimaka mata ta kaita d'aki.
"Sannu ko Aunty?"
"Ki had'a mun black tea please."
"Toh Aunty" da haka ta fice nan da nan ta had'o mata tean tazo wucewa d'akinta Afzal ya kirata chak ta tsaya had'e da tsugunawa.
"Na'am Uncle?"
"Meyake damun Amal? Karki yi mun k'arya."
"Uncle wallahi ban sani ba zazza6i tace mun."
"Kin ganta taje asibiti?"
"Gaskiya a'a tunda ka tafi ko makaranta bata sake fita ba" ta mai k'arya gudun kar ya gano gaskiyan al'amarin.
"Ya jikin nata?"
"Tace in had'a mata tea."
"Shikenan kina iya tafiya." Yana kammala abinda yakeyi ya rufe laptop d'in ya koma d'akinsa towel yaja ya shiga bayi ya watsa ruwa fitowansa ya nufi wardrobe nasa yana neman shorts da ze sa k'ark'ashin wani wandon da yakeda niyyan sanyawa da fari Safiyya ta ajiye takardan da Nazeefah ta bata har ze janye wandon seya fasa ya hango wani a sama, zara yayi ya sanya sannan ya kwanta sede ya kasa yin bacci se tunanin Amal kawai yake tuna yadda take amai d'azu kaman wacce ke neman harar da hanjin cikinta. Shin meyake damunta? Ko da wasa k'wak'walwarsa be kawo masa ciki ne da ita ba.
Washegari Amal ta d'an samu sauk'i don haka ta shiga shirin makaranta koda ta fito ta tarar da Afzal zaune kan dining yana karyawa bata yimai magana ba harkan gabanta kawai ta cigaba da yi. Sosai ya sha mamakin yadda ya ganta back on her feet contrary to yadda take jiya kaman wacce zata mutu. Sosai yake son tambayarta ya jiki amma ya kasa har yanzun haushinta yake ji na abubuwan data ringa yi masa tana gama abinda zatayi tayi ma Safiyya sallama yana jiran ko zata tambayesa kud'in makarantar ta yaga kawai ta fice.
K'arfe biyu Afzal ya dawo daga office lokacin Amal ma har ta dawo tana zaune a d'akinta tana karatu, d'akinsa ya wuce bayan Safiyya tayi masa sannu da zuwa. Kayan jikinsa ya rage ya fad'a bayi ya watsa ruwa fitowansa ya nufi wardrobe nasa dan neman kayan da zaisa a garin haka takardan da Safiyya ta sanya a tsakankanin wandunansa ya fad'i hannu yasa ya d'aga tare da bud'ewa in da ya soma karancewa kaman haka;
_To my most beloved soul on earth (Ya Abdul) I write this with a very heavy heart. Darling words cannot describe how much I miss you, I miss you terribly I wish I hadn't sacrificed your love for Ya Afzal cause it's true he doesn't deserve my love, I regret the day I chose him over you, Ya Abdul I wish you were here to cry along with me and take my sorrows away, I wish you were here to fight for me and set me free from this miserable torture. If I were to be given another chance, I would choose you a thousand times over Ya Afzal. Ya Afzal is such a heartless demon now that I've thought of it I just realized it was never love he really felt for me but rather lust. All these while he's been after my body and now that he's gotten what he's wanted he treats me more like a maid than his wife, Ya Abdul you're the one I truly love and not Ya Afzal I'll never love a heartless demon like him, I so hate him and I hate destiny even the more for separating me from you. My love for you will never die Habibi it's still fresh like an open wound and I shall continue to hold onto it, I believe that one day you'll come back to me, I will forever love you Ya Abdul. Life without you is so dull and colourless I need you to brighten up my world and wake me up from this horrible nightmare-_
Afzal be k'arisa karancewa ba ya fad'i a k'asa bisa ga wani irin k'una da ciwon da zuciyansa ya shiga yi masa birgima ya shiga yi wajen yana rik'e dai-dai saitin zuciyansa yayinda idanunsa suka kad'a sukayi ja zir cike da wahala ya d'age carpet ya 6oye takardan aciki. Wayansa ya shiga lalima amman yayi masa nisa haka ya cigaba da birgima a wajen har seda ya sume chan Safiyya da ta gama had'a masa abincinsa tayi sallama bakin k'ofan.
"Uncle na gama" takai minti biyu tana magana bakin k'ofar amma shiru dan haka taje ta samu Amal.
"Lafiya?"
"Aunty uncle ne yace in dafa masa farar spaghetti ya taho da sauce gashi na gama naje kiransa ina ta sallama bakin k'ofar d'akinsa amman shiru."
"Hala wanka yake ki jira idan ya fito."
"Toh" da haka ta fice bayan minti kusan biyar amma bata ji hayaniyan Afzal ba ta koma bakin k'ofan inda ta cigaba da yin sallama amma ba response d'akin Amal ta koma ta sanar da ita shiru fa har yanzu.
"Safiyya kina damuna kije mana ki lek'a d'akin halan bacci yake." Da haka ta koma d'akin ta bud'e k'ofan wani irin rikicaccen ihu ta k'urma bisa ga sumammiyar jikin Afzal da ta tarar a k'asa.
"Auntyy!!!" ta k'urma wa Amal kira ba shiri Amal dake kwance ta zabura tana tambayan ko lafiya har ta iso bakin k'ofan inda Safiyya keyi mata nuni da cikin d'akin a rikice. Lek'a d'akin da Amal tace zatayi itama ta k'urma wani d'ankaren ihu had'e da k'arisasa da salati a guje tayi kan Afzal had'e da aza kansa akan cinyarta tana bubbuga fuskansa "Yaya? Yaya? Yaya please wake up" ba shiri ta shiga yin kuka "Yaya I'm terribly sorry dan Allah kayi hak'uri ka tashi na shiga uku Safiyya kije ki kirawo driver" a guje Safiyya ta fice Amal se kuka take a wajen yayinda take kakkarwa "Yaya dan Allah karka tafi ka barni I'm so sorry please don't go." Mik'ewa tayi ta janyo kayansa ta sanya masa sannan driver ya k'arisa ya cicci6esa sukayi mota duka har da Safiyya. Tunda aka shige da Afzal emergency room Amal keta safa da marwah bakin corridon gabad'aya ta rasa nutsuwarta tsabaragen yadda ta tsule ko Mami ta kasa kira bale su Ummi. Safiyya ce ta kira Nazefah ta sanar da ita, ita kanta Nazeefah bata d'au hakan ze tayar wa Afzal ciwonsa ba sosai ta rikice yanzu idan hakan kuma ya zame sanadiyan mutuwansa? Da ko itace da babban asara. Sarai tasan Afzal bayi so idan ciwonsa ya tashi iyayensa su sani amma da gan-gan dan aga laifin Amal ta kira Ummi ta sanar da ita akan Afzal ya samu attack ba shiri Ummi ta kira Abba ta sanar da shi.
Kaman daga sama kawai Amal taga Nazeefah na shigowa bada dad'ewa ba sega Ummi har ma da Abba. Yau nata ya k'are 'hasbunallahu wa ni'imal wakeel' kawai take ta nanatawa. Kanta suka yo duka suna tambayarta meya faru Amal ta kasa magana se hawaye kawai daga k'arshe suka koma kan Safiyya.
"Wallahi ban sani ba ya shigo gida yace in dafa masa spaghetti bayan da na gama naje nayi mai sallama amman shiru se nida Aunty mukayi zaton ko wanka yakeyi chan da shirun yayi yawa na sake duba shi bud'e k'ofan da zanyi kawai na tarar da sumemmiyar jikinsa a k'asa."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Ummi ta furta cike da tashin hankali.
"Dole akwai abinda akayi masa" cewan Nazeefah dake ta faman kukan munafirci "Sanin mune nan duka ciwon Ya Afzal bai ta6a tashi kazai haka dole saida sanadi" Nan ta kewayo kan Amal da gaban hijabinta ya jik'e jak'ab da hawaye. "Amal mey kikayi wa Ya Afzal? Sanin kowa ne kece sanadin ciwon sannan mey kikayi masa?"
"Nazeefah wani irin magana kike haka? Har kina tunanin zanyi wa Yaya abinda ze tayar masa da ciwonsa da gan-gan? Wallahi banyi wa Yaya komai ba wallahi ban mishi komai ba Ummi" ta sanar dasu cikin tsan-tsan kuka.
"Taya zakice baki yi masa komai ba Amal bayan kinsan kece sanadin ciwon nasa? Bayan sarai kinsan da zaran kinyi masa abinda zuciyar bata so ciwon na iya tashi yet you still went ahead kika k'untata masa. Idan ban manta ba jiya kafin Ya Afzal yabar gidana seda yace kina yi masa abubuwan da baya jin dad'insu amma baze yi miki magana ba saboda yana gudun 6acin ranki meyasa ke bazaki mishi haka ba ki nisanci duk abinda ze 6ata masa rai?"
"Nazeefah ki yarda da ni Ummi, Abba wallahi ban yi wa Yaya komai ba."
"Ummi wallahi ita ce ita ta janyo komi koda rasa ransa Ya Afzal yayi kisani kece sanadi Amal kuma bazan ta6a yafe miki ba idan wani abun ya samesa" nan ta fad'a jikin Ummi tana kuka.
"Amal me kikayi wa d'ana? Mey kikayi wa Prince? A tunani na kece mace ta k'arshe da zata guji yi masa abinda zuciyarsa bata so meya faru Amal?"
"Hajiya Mariam ya isa haka please mu jira likitan su fito tukuna" da haka Abba ya samu ya toshe wa Nazeefah da Ummi baki koda kowa ya nemi waje ya zauna Amal ta kasa zama se safa da marwah take a wajen chan globe na bakin k'ofan da akeyi wa Afzal aiki aciki ya mutu nan suka duk'ufa suna jiran fitowan Dr. Kusan a tare duk suka jefa masa tambaya.
"Humm!" Dr'n ya sauk'e nauyayyan numfashi "Bazan 6oye muku ba ku sani by each attack da yake samu hakan na weakening rate and efficiency na heartbeat nasa ku magance masa matsala tun ba yau ba kun kasa kun zuba masa ido ranan da zuciyan ta buga gabad'aya shikenan se ku huta muma mu huta."
"Yanzu ya jikin nasa?" Abba ya tambaya.
"Munyi masa abinda zamu iya sauran ku jira ya farfad'o d'ayan ku ya biyoni ya amshi list na drugs da za'a sai mishi." Abba ne yabi bayansa ya rage su Ummi.
"Ummi dan Allah kibar kukan haka" cewan Nazeefah tana share mata hawaye. "Amal kin de ji abinda Dr'n Ya Afzal yace ko? Rayuwan Afzal yayi depending akan ki ne dan Allah ki kiyaye k'untata masa idan baki damu da shi ba mu nan we love and care about him."
"Nazeefah-"
Katse ta tayi da wuri "Ummi wallahi tun ba yau ba Ya Afzal yake mun complaining akanta gashi yanzu seda ta kwantar mana da shi."
"Nazeefah wallahi bani bace dan Allah ki yarda dani."
"Toh wa kikeso a zarga idan ba ke ba Amal? Ummi dan Allah ki sa baki."
"Amal dan Allah ba dan ni ba dan Allah nace kiyi hak'uri ki rufa mun asiri ki na yima Afzal abinda yakeso kin fi kowa sanin halin da yake ciki" Ummi ta rok'eta cikin kuka. "Na sani ba koda yaushe Afzal yake da dad'i ba amma dan Allah kina hak'uri da shi kina yi mishi abinda yakeso please Amal I can't afford to lose him shi kad'ai Allah ya bani."
"Ummi dan Allah kiyi hak'uri I'm so sorry, please forgive me."
"Shikenan bari in shiga in duba sa" ta kai kusan minti goma aciki sannan ta fito har anan Afzal be tashi ba tana fitowa sega Abba nan shima ya dawo da magunan Afzal wanda ya mik'a wa Ummi. Bayanta ya bi ya shiga ya duba Afzal shima bayan ya fito ya buk'aci Nazeefah next da ta shiga, k'arshe Amal ta shiga. A hankali ta k'arisa cikin d'akin ta zauna daga gefensa tare da sa hannunta cikin gashin kansa tana shafawa a hankali.
"Yaya I'm so sorry dan Allah ka tashi ka fad'a musu bani bace" kuka ta shiga yi sosai a wajen a hankaki ta kwantar da kanta a k'irjinsa yayinda kukan nata ya tsananta "Yaya please wake up wallahi ban aikata ko abu d'aya daga cikin ababen da kake tokari na dasu ba wallahi wasu ne suke neman shiga tsakanin mu Yaya bazan ta6a aikata abinda nasan ze 6ata maka rai ko zubar maka da mutunci ba you have to believe me and stop bothering yourself I beg of you please" a hankali ta d'ago da kanta tare da had'a hannunsu gu d'aya "I love you so much and no matter what I'll never leave your side" a hankali ta sauk'e light kiss akai. Har ta kai ga mik'ewa taga ya motsa yatsansa zamanta ta gyara ta shiga kiran sunansa har seda ya bud'e idonsa.
"Yaya you're back!" Tayi exclaiming ba shiri tayi hugging nasa sede ko ta6a jikinta beyi ba gabad'aya ji yayi ta haramta masa tunda har yanzu Abdul ne a zuciyarta. A hankali ta d'ago daga jikinsa "Yaya what happened?" ta tambayesa had'e da zira hannunta cikin gashin kansa. Kan nasa ya shiga girgizawa da nufin baya so a hankali ta maida hannun nata "I'm sorry" tayi apologizing.
"Su Ummi suna waje bari inyi musu magana su shigo" kansa taga ya kawar gabad'aya dan ko kallon ta baya sha'awan yi ko a mafarki akace masa Amal zatayi masa haka baze yarda ba kuma ba abinda yafi tsana kaman wannan munafikin halin hawainiyan nata, zatayi abu kuma ta zagayo kaman batayi komi ba tana proving innocence. Ko a ina yaci karo da rubutun chan yasan nata ne.
"Yaya har yanzu fushi kake dani? Yaya wallahi ban aikata ko d'aya daga cikin abubuwan da kake tokarina dasu ba Yaya sanin kanka ne ina sonka kuma bazan ta6a yin abinda ze 6ata maka rai ko zubar maka da mutunci ba you have to believe me."
"Ki kira mun Ummi da Nazeefah" yace da ita zalla ba tare da ya kalleta ba hawayenta ta share sannan ta mik'e "Allah baka lafiya" ko ta kanta beyi ba har ta fice
"Ya Afzal ya farfad'o Ummi."
"Ya farfad'o?" Ummi ta tambaya had'e da mik'ewa. Haushi Nazeefah taji wato seda Amal ta shiga ne ya ga daman tashi akan duk uban kalaman soyayyan da tayita fad'a masa? Duk su kwantar da hankalinsu soon enough ze saki Amal d'in.
"Yana buk'atan ganinki da Nazeefah."
"Alhamdulillah! Alhamdulillah" ta mik'a godiyar wa Allah.
"Abba fah?" Amal ta tambaya.
"Ya koma" Nazeefah ta amsa. Tana ganin shigewansu ta kira Safiyya suka koma gida tunda baya buk'atan ta na mey zata cigaba da zama?
"Prince!" Ummi ta kira sunansa had'e da hugging nasa "Prince dan Allah kayi a hankali wallahi likitanka na jiye maka."
"Ummi please it's okay I'll be fine."
"Welcome back Ya Afzal" Nazeefah dake tsaye akansa ta fad'a mai.
"Thank you Rabba'atul Bait" ya amsa yana mata murmushi.
"Prince meya faru? Mey Amal tayi maka?"
"Amal kuma?"
"Ka fara da zurfin cikin nan naka ko? Nazeefah ba ke kikace Amal ce bata kyautata masa ba?" Ido ya d'ago yana kallon Nazeefah da cikinta ya d'au ruwa tuni ta shiga rarraba ido.
"Haka nace miki?"
"Ya Afzal naga.. ermm... Toh ai sanin kanmu ne duka nan Amal ce sanadin ciwon naka Ya Afzal ko ba kai ka fad'a mun ba?"
"Se kuma nace miki Amal ce bata kyautata mun?"
"Toh waye ne?" Ummi ta tambayesa "Wayene idan ba Amal d'in ba?" Shiru yayi bece komai ba dan haka Ummi tayi tunanin ko bayi son yayi maganan a gaban Nazeefah ne. "Ermm nace mey kakeso kaci Prince Nazeefah ta girka ta kawo maka? Girkin waye ne acikinku?" Ta tambayi Nazeefah.
"Girkin Amal ne amma ba damuwa zan girka in kawo masa mey kakeso Ya Afzal?"
"Boiled potatoes da egg sauce" ya sanar da ita.
"Toh bari inje zan dawo yanzu in shaa Allah." Tana ficewa Ummi ta dawo da kallonta akan Afzal "Toh Nazeefar ta tafi gaya mun meke faruwa?"
"Ummi babu" mari me zafi ta kai masa akan cinya. "Ummi please! Kin fa san hannunki da zafi."
"Ina tambayanka abu kana kallon cikin idona kana mun k'arya? Nace meya faru? Wallahi ka kuskura kayi mun k'arya toh ni da kai."
"Ummi misunderstanding muka samu."
"Fad'a kukayi?" Kai ya gyad'a mata "Amma mun shirya shigowantan nan."
"Ka tabbata?"
"Eh Ummi."
"Ba senayi mata magana ba?"
"Babu amfani komi ya wuce."
"Toh koma meye ne de ka daina bin komi da zuciya haka kasan yadda zuciyar taka take da rauni please Prince Abbanka ma na nan ai d'azun ya tafi."
"Allah sarki ku daina tada hankalinku please I'll be fine."
"Zaka kwana ko zaka koma gida a yau?"
"Kwana kuma? Na samu sauk'i se in kwana a asibiti? Nazeefah na kawo mun abinci naci zan koma gida."
"Kana buk'atan wani abu toh?"
"A'a zaki iya tafiya Ummi thank you so much."
"Don't mention my boy Allah baka lafiya ko?" Kai ya gyad'a tare da amsawa yanayi mata murmushi. "Bari inyi ma Amal magana tazo ta tayaka zama kafin nan." Da mamaki ta nemi Amal bayan fitanta ta rasa ta dawowa ciki tayi tace, "Ban ganta ba fa, kode ta tafi ne?"
"Ohh ban fad'a miki ba ko? Na ce ta koma kinsan itama kwana biyu bata ji dad'i ba zazza6i ya sata a gaba."
"Haba! Shiyasa na ga ta rame Allah sarki Allah shi bata lafiya."
"Ameen Ummi." Zama ya cigaba dayi cikin d'akin har zuwa lokacinda Nazeefah ta kawo masa abincin ita da kanta ta basa bayan da ya gama tayi ma likitin nasa magana akayi discharging nasu. Kasancewar kwanan Amal ne har cikin gida Nazeefah ta kaisa sannan ta juya ta wuce nata gidan. Sannu da zuwa Safiyya tayi masa lokacinda ya shigo ciki.
"Ina Amal?" Ya tambayeta.
"Tana d'akinta" k'arisawa d'akinsa yayi ya zaro takardan d'azun had'e da ninkewa ya adana. Wayansa ya d'aga dan kiran Sultan inda ya tarar da missed call na Abba nan take ya kirasa back suka gaisa Abba yake mishi jaje. Suna k'are wayan ya kira Sultan.
"Maza yane?"
"Ba lafiya ba yanzu haka daga asibiti nake."
"Subhanallahi meya faru ciwon naka ne?"
"Yes and alot has happened Sultan ka shigo gobe kaji?"
"Toh sannu ya Amal ko gun Nazeefah kake?"
"Ni seka shigo kawai" tun daga amsan sa Sultan ya gane akwai matsala "Allah kaimu goben toh."
"Ameen" Afzal ya amsa had'e da katse wayan. Zama ya cigaba dayi a d'akin chan bayan sallan Maghrib Amal tayi sallama cikin d'akin nasa shiru yayi yak'i amsawa dan haka ta bud'e k'ofan ta shiga kansa yayi saurin kawarwa.
"Yaya-"
"Get out Amal bana k'aunan sake ganinki a cikin d'akin nan in shaa Allahu burin ki ya kusan cika kiban lokaci kad'an."
"Yaya mey kake nufi? Wani buri?"
"Just get out Amal in kuma fitan ne bazaki iya ba ina iya bar miki gidan gabad'aya."
"Allah huci zuciyanka" tace mishi zalla ta juya ta fice d'akinta ta koma inda ta kwanta kan gado ta shiga kuka sosai.
Washegari kaman yadda Sultan ya mar alk'awari haka yazarce gidan nasu daga office da Amal suka fara had'uwa lokacin tana zaune a dining tana cin abinci sannu da zuwa tayi masa tasa Safiyya ta kawo masa drink da snacks.
"Kinyi wuyan gani amarya."
"Ji Ya Sultan nice amaryar?"
"Amaryar amini na ma kuwa ke baki san yadda nake ji dake ba ko?"
"Uhm haka de kace amma ka barni da makaranta yana ta bani wuya."
"Karde shiya ramar dake haka? Har kun fara tests ne?"
"Ai mu kullum cikin tests muke Ya Sultan se a hankali."
"Allah sarki ba three kike ba yanzu? Kinyi mey wuyan ai Allah sa albarka."
"Ameen Ya Sultan yasu Umma?"
"Lafiyansu k'alau Afzal fa yana gida?"
"Eh ba motansa na waje ba?"
"Na sani koya fita strolling ya jikin nasa?"
"Toh Alhamdulillah de bari inyi mishi magana" nan ta mik'e ta nufi d'akin nasa sallama tayi amma be amsa ba dan haka ta bud'e ta shiga akan gado ta tsincesa yana bacci k'arisawa tayi had'e da tapping nasa a k'afa a hankali.
"Yaya? Yaya ka tashi Ya Sultan yazo" a hankali ya shiga bud'e idonsa har ya bud'e su duka ganin ita ne yayi saurin kawar da kansa "Bance kar in sake ganin ki acikin d'akin nan ba?"
"I'm sorry Ya Sultan ne yazo ya turo in kira ka" da haka ta juya ta fice. Brushing yayi ya wanke fuskansa sannan ya sanya shiry akan gajeren wandonsa ya fito ya sami Sultan. Bayan sun gaisa ya ce mishi su k'arisa ciki.
"Meya samu nan d'in? Ko so kake mu koro Amal waje ita da gidanta?"
"Bata d'akin come in" be sake musu ba ya mik'e suka k'arisa d'akin. Note na Amal ya d'au ya wulla wa Sultan akan cinya "Wannan fah?" Sultan yayi saurin tambaya.
"Ka bud'e kayi observing handwriting dake ciki" yadda aka ce da shi haka yayi bayan ya karance rubutun ya d'ago kai "Ehen?"
"Here take a look at this handwriting" yayi maganan yana zaro takardan d'azun daga inda ya 6oye "Handwriting na mutum d'aya ne ko kuwa?"
"Of course na mutum d'aya ne mana" Sultan ya amsa bayan yayi comparing handwriting d'in.
"Thank you ka zauna da kyau ka karanta content d'in." Hankali ya miyar kai ya shiga karancewa yayinda mamaki ya mamaye mai fuska da zuciya.
"Waya rubuta wannan maza?"
"Ka duba sunan dake jikin littafin" Afzal ya umarcesa.
"You don't mean this!" ya furta bayan daya duba yaga sunan Amal rubuce a bangon littafin.
"Yanzu zaka ga laifina idan na yanka mata ko wani irin hukunci?"
"Ban fahimce ka ba Triple A kana nufin Amal ce ta rubuta wannan?" Ya tambaya da d'umbun mamaki.
"Baka iya karatu bane?"
"I'm just confused Triple A, Amal de? Har Amal ce zata rubuta wannan abu? Kode kafin kuyi aure ne?"
"Kana ganin sabon paper sabon rubutu kana zancen kafin muyi aure?"
"Amma meya faru? Meyayi zafi da har Amal zata rubuta wannan abu a matsayinta na matarka?"
"Gata chan a chan d'akin kana iya zuwa ka tambayeta."
"Wow!" Ya numfasa totally speechless.
"Maza ban san meyake damun Amal ba yarinyar nan ta sauya gabad'aya ta koma wani abun daban banda munafurci da had'a kaina da Nazeefah ba abinda takeyi ko tsinke na sai mata seta buga waya wa Nazeefah ta fad'a mata knowing right ba duka abinda nakeyi mata nakeyi wa Nazeefah ba sedan kawai ta 6ata ni idon Nazeefah tasa Nazeefah tayi mun kallon maras adalci hakan be isheta ba har course mates nata maza ta fara kawo mun cikin gidan nan suna zama a kujera d'aya."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un wacce Amal tukuna? Amal Amal naka da na sani?"
"Ita de Amal ta cikin gidan nan."
"Maza are you sure of what you're saying? Amal ce har zata shigo maka da gardawa cikin gidan nan?"
"In kira maka mey aikinta ne ka tambayeta?"
"Subhanallahi meya sameta?"
"Waya san mata ne?"
"Mey kake nufi kenan yanzu kana nufin kana zargin Amal kenan? Kana zargin tana ci maka amana?"
"Nooo not at all nasan Amal baza ta ta6a cin amanan aurena ba, ko tunanin yin hakan ma baza tayi ba I know that."
"Toh mey kake nufi da tana shigo maka da maza gida?"
"Yes ta daina shigo mun da coursemates nata saboda ba'a san abinda shaid'an ze iya raya musu ba wataran koba d'abi'arta bane wataran shi gardin ze iya kwad'aitar mata da hakan ko ba ka gane abinda nake nufi ba?"
"Sosai na fahimce ka amma Afzal I'm still shocked Amal da muka sani ce ta sauya haka take yin ababen nan da ka irgo? Innocent Amal taka?? Na tabbata haka kawai Amal bazata sauya halayanta ba sede idan kai kayi pushing nata don't you forget that for every reaction there's an action."
"Mey zanyi mata maza? Kafi kowa sanin irin son da nake yiwa yarinyar nan, Wallahi Amal bata ta6a neman abu a guna ta rasa ba komi ina yi mata da iyayenta amma ka kalli da abinda zata sak'a mun kuma abinda yafi bani haushi shine k'aryata komi da takeyi har yanzu ita bata amince da laifukanta ba bale ta nemi tuba mu sasanta tsakanin mu ni bazan iya ba, I can't do this anymore I'm tired of her sick behavior."
"Mey kake shirin yi?"
"Ba Abdul kowa take so ba? Seta je ta samesa."
"Wani irin magana kake haka Afzal? Da igiyan auranka akanta kake son taje ta auri wani?"
"Sawwak'e mata zanyi."
"Mey?? Kana da hankali kuwa Afzal? Wani irin zafin kishi ne da kai haka?"
"Toh mey kakeso inyi? Ba gara na sawwak'e mata ba taje ta samu shi wanda take son? Bazan iya zama da ita ba knowing zuciyarta na tare da wani gara na rasata gabad'aya dan idan har na cigaba da zama da ita toh zan cigaba da kallonta da abin ne wanda zuciya ta baza ta iya d'auka ba wataran sede ta har6a tabar aiki."
"Idan ka sawwak'e mata ta koma gun Abdul kai kuma fah?"
"Na sani sena fita shan wuya bayan rabuwan nan amma ka gaya mun mey riban ajiyeta a wajena idan zuciyarta na tare da wani daban Sultan? I love Amal kuma har duniya ta nad'e bazan fasa sonta ba but this is not reason enough to keep her with me tunda gashi da hannunta ta rubuta bata sona tayi nadaman aurena. Kaji fa har cewa take wai dama tun fari tasan jikinta kawai nake so yanzu da na samu abinda nake nema gashi ina walak'anta ta. Ni fa Maza? Ni d'in da ko hannunta ban ta6a sha'awan rik'ewa ba... excuse me" tari ya shiga yi yayinda zuciyansa ya fara tashi yana yi masa k'una tsan-tsan takaici da bak'in ciki da 6acin rai.
"Dan Allah kayi a hankali ba senun sake kaika asibiti ba it's okay ya isa."
Gyaran murya yayi ya cigaba "So I think it'll be better idan na barta taje ta samu shi wanda take so d'in ta huta kowa ma ya huta."
"Kai kuma fa Triple A? Ya zakayi da rayuwanka idan kuka rabu? Shin ka manta rayuwanka gabad'aya yana revolving ne a jikin na Amal? Shin ka manta idan ba soyayyarta zuciyarka bazata iya aiki ba? Shin ka manta idan ba ita a kusa da kai rayuwarka tana cikin gwagwarmaya? Ina ka mance da dukkan hakan Afzal har kake tunanin sawwak'ewa Amal? Besides ni ban yarda ma innocent Amal d'in da na sani zata iya aikata wannan munanan abubuwan da kake tokarinta da su ba. She's too innocent to do all these I know Amal kuma na yarda da ita."
RANA D'AYA!
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
13 comments:
Ya salam . I hope ba ze sake taba. thanks dear please we need more update.
Gaskiya Afzal u r so a disappointment. How can you not c
Allah sarki Amal ðŸ˜ðŸ˜ðŸ˜ðŸ˜ðŸ˜Allah ya sa sultan ya ganar dashi akwai boyayen abun anan yasa cctv camera agidan nashi...
Eyya amal na. Allah ya Kara basira miemie can't wait for d next update
Allah yasa ya gane before it's too late,jzk khrn more greese to your elbow. Looking up for more updates
Thank u sis pls kici gaba kar ki barmu jira Allah yakara mini basira
Allah yasa afzal Santa secret CCTV a gidan gaba daya. miemie Allah ya kara basira.don't Allah a danyi kokarin yimana update da dan wuri
More grease to ur elbow
Oh my God,Afzal am so disappointed u can't tink out of d box,tnx girl u d best
More grease 2 ur elbow Miemiebee we will be waiting 4 d nxt page pls kar Afzal yayi sometin he will regret later
Allah sarki amal! Allah na tare da me gaskia😢😢😢... and nazeefa keep up with the act one day you'll be d one suffering far worst than this, if ba'a koraki daga gidan bama kenan sai muga karyan makirici irin taki! In Shaa Allah sai kin bar gidan nan.
Allah ya kara basira miemie update sooooon pls
eyyah I feel so sorry for amal...Allah yasa afzal ya gane da wuri before it is too late...and I can't wait to see the end of naxeefah..keep it up dear waiting for update
Post a Comment