Friday, 7 September 2018

RANA D'AYA!

BY MIEMIEBEE
PAGE 41




   _Assalamu Alaikum readers, I would like to show my deepest appreciation to each and every one of you that took a minute or so out of their precious times and asked, prayed or checked up on me. I really am grateful and feeling much better Allah yabar zumunci ameen. 😘 Before proceeding on, I would like to dedicate and give this chapter to SADNAS marubuciyar •miemiebee a wanki garori• and her amiable group members, thank you so much for the love and support wannan chapter'n naku ne! Xoxo 😘❤️_



     Cike da jin dad'i da rawan jiki ta d'auko akwatin ta ajiye kan gado sannan ta shiga fiddo da kayakinta daga wardrobe tana jerasu aciki, taci rabin aikin Mummy tayi knocking bisa k'ofan d'akin. "Come in" ta amsa sannan ta bud'e ta shiga.

   "Ya da shirya akwati haka ina zuwa?" Ta soma da tambaya.

  "Mummy Ya Afzal yace gobe zezo ya mayar dani d'akina" ta sanar da ita cike da jin dad'i.

  "Kai haba!" Mummy ta tambayeta unbelievably tana mey tayata murna.

  "Wallahi ai tun last two weeks yaso mayar dani amman bakwa nan yace in hak'ura sekun dawo."

  "Allah sarki Afzal, toh Alhamdulillah yayi kyau sosai Allah kaimu."

  "Ameen Mummy" ta amsa delightedly.

   "Kiga duk kalan rashin hankalin da kika tafka hakan be hanasa yafe miki ba har yake shirin mayar dake d'akinki. Sekiyi ma kanki fad'a Nazeefah ki kiyaye 6ata masa rai, kuyi zaman lafiya da 'yar uwarki ba abinda hakan ze ragar miki."

  "Hakane Mummy in shaa Allahu komai ya wuce har gida zanje in samu Amal in bata hak'uri."

  "Masha Allah, Allah baku zaman lafiya duka."

  "Ameen Mummy."

  "Toh kinata hanzari haka ko gobe bazaki had'a kayakin bane?"

  "Toh Mummy in kuma da safe zezo fah? Ai gara nayi na gama yanzu tunda ba abinda nakeyi."

   "Toh ki sauk'o muci abinci dinner is ready."

  "A'a nikam zan sauk'o daga baya sena gama had'a kayakin nawa tukuna."
 
  "Toh barin sanar da Daddy'nku."

  "Yauwa do please thank you" nan Mummy ta fice ta ja mata k'ofar. Bayan sun gama cin abincin tayi gyaran murya, "Alhj?" Ta kira Daddy.

  "Na'am Hjy Surayya."

  "Errm batun Nazeefah ne daman, Afzal yace gobe zezo ya mayar da ita d'akinta." Dummm! Zuciyan Daddy ya buga ko motsi ya kasa yi.

  "Alhj lafiya?" Mummy data karanci yanayin da ya fad'a nan take tayi saurin tambaya.

  "Lafiya ba komai."

  "Nace Afzal ze zo bikon Nazeefah gobe."

  "Bazata koma masa ba" ya fad'a zalla. Da mamaki Mummy ta tsaya kallonsa "Dalili Alhj?"

  "Nace bazata koma ba zuwa zeyi ya bata takardanta zamansu ya k'are."

  Mummy ta kasa amincewa da abinda kunnuwanta ke jiye mata da mamaki tace "Alhj ka ko san me kake fad'i? Har mun samu yaron nan ze mayar da ita d'akinta kake cewa bazata koma ba? Ko kai zaman 'yarnan a gidan nan haka na maka dad'i ne? Ko so kake ka mayar da 'yar taka bazawara?"

  "Nide na fad'a miki kije ki sameta kice mata ba inda zata" yana kaiwa nan ya mik'e ya nufi d'akinsa. Kai Mummy ta kewayo tana kallon Khaleefah da shima ya tsaya kallonta da d'umbun mamaki d'auke a fuskokinsu. Daga bisani ta mik'e ta je ta samu Nazeefah a d'aki, lokacin har ta gama had'a kayakin nata tana cikin tattare jakukkunanta da takalma.

   "Nazeefah wani abun ya had'aki da Daddy'nku ne?" Mummy ta tambayeta bayan ta zauna bakin gado.

  "A'a wani abu ne?"

   "Gashi ina mishi maganan gobe Afzal zezo ya d'aukeki yana cewa ba inda zaki."

  "Ba inda zani kuma?" Nazeefah tayi exclaiming cike da k'in yarda.

  "Haka yace wai zamanki da Afzal ya k'are."

  "Dalili? Ya Afzal yayi mishi wani abu ne?" Ta tambaya a rud'e.

  "Anya kuwa? D'au waya ki kirasa muji" ba makawa ta janyo wayanta ta shiga kiran Afzal sede yayi ta ruri har ya tsinke be d'aga ba kasancewar ya riga ya kwanta. Three missed calls ta masa be d'aga ba ta hak'ura.

  "Mummy he ain't picking up."

  "Kode yayi bacci ne?"

   "Might be amma meyasa Daddy ze hana Ya Afzal mayar dani d'akina?"

  "Shine nima ban sani ba Nazeefah."

  "Mummy dan Allah kiyi mishi magana Mummy bana son abinda ze rabani da Ya Afzal please dan Allah Daddy ya rufa mun asiri."

  "Karki damu zanyi masa magana ki kwantar da hankalinki nake ga sun d'an samu sa6ani ne."

  "Please do Mummy."

 "I'll je kici abinci kinga dare nayi."

  "Ni bana jin yunwa."

  "Toh kiyi sallah ki kwanta seda safe" da haka Mummy taja mata k'ofar ta fice taje ta samu Daddy dake mik'e akan gado ya zura wa ceiling ido. Sallama tayi amma ko amsawa beyi ba don yadda hankalinsa sam baya jikinsa.

 "Alhj?" Ta kirasa bayan ta zauna a gefensa nan ma shiru k'arshe seda ta d'an ta6asa sannan ya dawo hankalinsa. "Alhj dan Allah ka tashi muyi magana."

  "Wace magana ce zamuyi? Na gaya miki 'yar nan bazata koma gidan Afzal ba ko baki ji bane?"

  "Naji Alhj amma-"

  "Amma mey?" ya katseta a fusace "Ni da 'yata kike son nuna mun iko akanta? Bazata koma ba bazata koma ba."

  "Bawai haka bane Alhj a tunani na koda sa6ani kuka samu da shi Afzal d'in be kamata ka hana sa miyar da yarinyar nan d'akinta ba tunda tana sonsa yana sonta-"

   "Surayya dan Allah nace kiyi min shiru" ya katseta cike da rashin hak'uri "Idan kuma shirun ne bazaki iya ba ina iya bar miki d'akin."

  "Allah huci zuciyanka gobe zamuyi magana" Daddy be sake ce mata komai ba. Abinda ya kama daga kan shi harma Mummy da ita Nazeefar bawanda ya iya samun baccin kirki ranan barin ma Daddy da yake ganin asirin sa ya kusa tonuwa besan da wani idon ze sake kallon iyalansa ba.

****
    Kiran Afzal ne ya tada Nazeefah daga bacci washegari ba shiri ta d'aga wayan.

  "Good morning Baby" ya fad'a a karo na farko.

  "Ya Rouhi" ta kirasa cike da tashin hankali.

  "Yes is everything okay?" Yayi saurin tambaya.

  "Ya Rouhi wani abu ya had'aka da Daddy ne?"

  "Nop why?"

  "Ya Rouhi cewa yayi wai bazaka miyar dani d'akina ba."

  "What?!" Yayi exclaiming had'e da dropping cup na tea da yake sha.

  "Ya Rouhi please do something I don't want to be separated from you."

   "Karki damu I'm on way now" daga haka ya katse wayan ya fad'a d'aki ya d'au key'n motansa. "Rania?" yayi knocking bakin k'ofan bayin.

  "Yes Ya Omri?" Ta amsa daga ciki.

  "Zan fita ina zuwa."

  "Toh seka dawo" be 6ata lokaci ba ya fice.

****
  Mik'ewa tayi ta fad'a bayi tayi brushing ta canza kayan jikinta sannan ta sauk'o k'asa dan karyawa. Hayaniyan data jiyo ta gun d'akin Daddy yasa ta k'arisa gurin inda ta tarar da Mummy da Daddy se faman fad'a sukeyi.

  "Haka kawai bazan zuba ido ka mayar min da 'ya bazawara ba wallahi Afzal zezo kuma ze tafi da yarinyar nan" Mummy ta fad'a cike da tsiwa kaman ba ita ba.

   "Idan ke kike iko da Nazeefar se mu gani" Daddy ya mayar mata.

  "Daddy dan Allah kayi hak'uri" Nazeefah da idanunta suka ciko tim da hawaye ta tsoma baki "Daddy dan Allah karka rabani da Ya Afzal Daddy idan wani abun ya maka I'm sorry on his behalf please don't separate us two."

   "Kiyi hak'uri Nazeefah amma rabuwa da Afzal ya zama dole" kuka ta shiga yi na hak'ik'a "Daddy dan Allah kar ka min haka dan Allah kayi hak'uri I'm so sorry" har cikin zuciyansa Daddy yaji ba dad'i ashe akan 'yarsa Allah ze rama wa Jameelah abinda yayi mata, why not akanshi? Meyasa se akan 'yarsa? Ashe anan Allah na nuna masa kamar yadda alheri yake d'anko shima sharri haka ne muddin baka shuk'a me kyau ba toh 'ya'yanka ma bazasu ga mey kyau ba.

   "Ki barsa" Mummy tace da ita tana mey janta jiki "Afzal d'in ai zezo se ya hanaki binsa muga" tana kaiwa nan taja Nazeefah d'akinta ta shiga lalashinta amma inaa Nazeefah se kuka. Ba'a dad'e ba sega Afzal ya taho yana isa ya kira Nazeefah inda ta tura Khaleefah ya shigo da shi zuwa parlourn Daddy sannan ya shiga daga ciki yayi ma Mummy magana. Mayafi ta yafa ta fito da Nazeefah biye a bayanta. Bayan sun gaisa take tambayarsa ko abu ya had'asa da Daddy.

  "Wallahi ba komai Mummy kema kinsan bazan so abinda ze shiga tsakani na da Daddy ba kodan Nazeefah."

  "Hakane Afzal yanzu abinda nakeso da kai ka d'au Nazeefah ku tafi karka sauraresa."

  "Nace baze tafi da ita ba" suka jiyo muryan Daddy kaman daga sama nan take duk suka kewayo suna kallonsa.

   Har k'asa Afzal ya sauk'a ya gaishesa amma ko amsawa beyi ba "Ka rubuta mata takardanta yanzun nan bazata bika ko ina ba."

  "Daddy ban fahimce ka ba."

   "Sakin ta nake so kayi yanzun anan" ya jaddada masa.

  "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ya sa salati "Daddy idan wani abun nayi maka kayi hak'uri amma karka rabani da Nazeefah dan Allah."

  "Baka ji me nace bane?"

  "Daddy naji dan Allah kayi hak'uri."

  "Ai ni na rok'eka da ka aureta daman tun farko yanzu kuma ina rok'onka da ka sawwak'e mata zaman ku ya k'are."

  "But Daddy I love Nazeefah, ina sonta bana kuma son in rabu da ita."

  "Zaman ku ya k'are nace Afzal ka sakar min 'ya."

  "Wai Alhj meke damunka ne? Haka kawai kake shirin shiga tsakanin yaran nan a ina aka ta6a yin hakan?"

  "Hjy Surayya banyi magana dake ba saboda haka ba ruwanki."

  "Niko nake da ruwa acikin zancen nan taya zaka sa na dole miji ya rabu da matarsa?"

  "Afzal ka rubutawa yarinyar nan takardanta nace" yace kaman wanda beji abinda Mummy ta fad'a ba.

  "Daddy dan Allah kayi hak'uri" Nazeefah ta rok'esa cikin tsan-tsan kuka saidai ko kallonta beyi ba. "Idan kuma ranka ya 6aci ne game da dawo dani gida da Ya Afzal yayi kayi hak'uri amma bashida laifi, nice nayi mar laifi a matsayinsa na mey mata biyu kuma dole ya kwatanta yin adalci tsakani na da 'yar uwata. Tunda ni nasa Amal tayi yaji na raba ta da gidanta nima dole a rabani da nawa. Amma ka duba yanzu da Amal ta dawo ba gashi yana son ya miyar dani d'akina ba? Kuma seka hana hakan Daddy? Please don't." Na sosai maganganun Nazeefah suka shige jikin Daddy suna masu samun mazauni a birnin zuciyansa. Ba shi kad'ai ba kowa seda kalamun nata suka ta6a sa a gurin amma haka na dole Daddy yayi banza da ita. "Afzal ba magana nake ma ba?"

  "Daddy I'm terribly sorry idan mayar da Nazeefah gida da nayi na kwanakin nan ne ya 6ata maka rai kamar yadda Nazeefah ta fad'a. I had no option but please don't be mad, I'm sorry and I do love Nazeefah."

   "Ka rubuta mata takardanta nace-"

  "Baze rubuta ba Alhj nace baze rubuta ba" Mummy da ranta in yayi dubu be 6aci ba ta katse sa.

   "Afzal baka jina ne?"

  "Daddy ina ji" ya amsa na dole.

   "Ka rubuta mata takardanta nace." Kuka Nazeefah ke sosai tace, "Please don't do this Daddy, please."

   "Me kake jira ne har yanzu Afzal?" Daddy yayi kaman be jita ba "Biro ne ko takarda baka da ita? Khaleefah wuce d'akinka ka d'auko mar."

   "Daddy kayi hak'uri amma ka sani bazan iya rubutawa Nazeefah takardan saki haka kawai ba please understand me."

  "Daddy kayi hak'uri mana" Khaleefah da ya zuba musu ido tun d'azun ya fad'a.

  "Daddy please don't do this" Nazeefah ta kar6esa, "Please don't Daddy, Afzal is sorry kayi hak'uri ka barni in tafi dashi."

  "Nazeefah kiyi hak'uri amma gaba kad'an zaki gane am doing this for your own good."

   "Which good Daddy? Kana shirin raba ni da mijina wanda yake sona nake kuma sonsa kake cewa you're doing this for me? How? Mummy how is this going to be of help to me?" Ta jiyo cikin tsananin kuka tana kallon Mummy data janyota jiki.

  "Zaman ki da Afzal ya haramta Nazeefah bazeyi ki cigaba da zama da shi ba dan haka ya zamanto dole ya sakeki ya sauwak'e miki."

  "Kaman ya zamansu ya haramta Alhj? Wani abun sukayi ne da zakace zamansu ya haramta?" Mummy tayi saurin tambayarsa "Dan na d'an wata ya korota gida kuma akan gaskiyansa se kace zamansu ya haramta? A ina ne idan mace tayi laifi akace miji baze hukunta ta ba? Tell me!" Tayi demanding.

  "Nide na fad'i nawa zamansu ya haramta don haka ya k'are, Khaleefah yi maza ka d'auko mar paper da biro kar ka bari in nanata kaina."

  "Khaleefah zauna ba inda zaka" Mummy ta dakatar da Khaleefah daya zabura.

  "Daddy I'm sorry amma bazan iya rubutawa Nazeefah takardanta ba" Afzal ya fad'a had'e da mik'ewa "I'll get going ina zuwa amma."

  "Afzal! Afzal!" Kiransa Daddy yake amma ko kewayowa beyi ba. Gidansu ya wuce direct unfortunately Abba bayi nan yayi tafiya Ummi kad'ai ya tarar. Irga mata halin da ake ciki yayi inda ta sha mamaki na sosai.

   "Toh yanzu ya zamuyi? Amma meya samu Alhj Abdallah haka?"

  "Wallahi Ummi I don't know and he seem so serious about it."

   "Subhanallahi meya buga masa kai toh? Kode koran Nazeefah gida da kayi d'inne ya 6ata mar rai haka?"

  "Amma ai ba koran walak'anci nayi mata ba Ummi besides Nazeefah was at fault dole in hukunta ta kodan inyi ma Amal adalci."

  "Tabbas Prince kuma nima bawai nace kayi laifi bane am just surprised gashi Abbanka baya nan."

   "Se yaushe ze dawo?"

   "Yau yace."

  "Toh kafin nan kije ki samu Daddy kiyi mishi magana please."

  "Ni kuma Prince?" Ta dafe k'irji.

  "Eh Ummi I don't want to lose Nazeefah please go" ya fad'a cikin tsananin tashin hankali.

  "Prince ta ina zanje in fara yi wa Alhj Abdallah magana a matsayinsa na sirki na? Ai beyi fasali ba kade bari Abban naka ya dawo zuwa anjima."

  "Ummi please" ya rok'eta abin tausayi.

  "I'm sorry Prince but I can't" kafad'ansa ta dafe "Abbanka ze dawo anjima I'll be the one to explain everything to him kayi hak'uri kaji? I'm sorry" kai zalla ya iya gyad'a mata.

   "Ka karya ko tukuna?"

  "Na karya" ya amsa.

  "Toh ka kwantar da hankalinka, muyi fatan Allah dawo da Abbanka lafiya."

   ***
  Wajajen sha biyu Amal da ta ji shiru daga Afzal ta d'au waya ta kirasa lokacin har bacci ya fara d'aukansa zaune a kan kujera a parlour, ba makawa ya d'aga inda ta soma da "Halo Ya Omri?"

  "Na'am Rania."

  "Ina ka shige? Shiru tun d'azu."

 "Rania akwai matsala" ya sanar da ita.

  "Subhanallahi ina dey kana lafiya ba abinda ya same ka ko?"

  "Not at all."

  "Alhamdulillah" ta saki ajiyar zuciya "toh meya faru?"

  "Rania sena dawo gida kawai I'm on my way."

  "Toh Allah dawo da kai lafiya I love you."

  "I love you too" ya amsa sannan ya katse. Duban agogo yayi yaga pass 12 "Ummi!" Ya shiga kiranta chan sega ta tashigo. "Lafiya? Naji kana kirana."

  "Ummi se yaushe Abba ze shigo?"

  "Zuwa anjima yace Prince bansan yaushe flight nasun ze tashi ba."

  "Ummi I don't want to lose Nazeefah please do somethibg."

  "In shaa Allahu ba abinda ze faru kai de ka kwantar da hankalinka kaji?"

  "Zan wuce gida idan Abba ya shigo seki kirani."

  "Toh shikenan Allah ya kare." Be kai ga tada engine na motar sa ba sega Nazeefah na kiransa. Nan take ya amsa "Halo Nazeefah?"

  "Ya Afzal..." ta kirasa kawai seta rushe da kuka.

  "Ohh dear!" Ya ambata had'e da murza temple nasa "Rabba'atul Bait please kibar kukan haka ba shida amfani."

  "Ya Rouhi tayaya ne bazan yi kuka ba bayan Daddy yana shirin rabani da kai?"

   "I'm not going to let that happen kinji? Abba is on his way idan ya dawo zezo ya samu Daddy yayi mishi magana in shaa Allahu ze sauk'o ya amince in dawo dake d'akinki okay?"

  "But Ya Rouhi he seem so serious wallahi se rok'onshi muke tayi amma ko sauraron mu beyi I'm scared."

  "Don't be sweetheart in shaa Allahu mutuwa ce kad'ai zata raba mu dan bazan ta6a aikata abinda Daddy ke cewa inyi ba because I love you okay?"

  "I love you too Ya Rouhi promise me komin yaya bazaka rubuta mun takarda na ba."

  "I promise darling" ya sanar da ita.

   "Thank you Ya Rouhi."

  "Yanzu share hawayenki kibar kukan haka toh sena shigo anjima."

  "Okay take care" daga nan ya katse ya sa key ya wuce gida inda Amal ta taresa. Bayan ta kawo masa ruwa yasha take tambayar sa meke faruwa nan ya labarta mata komai inda itama tayi mamaki na sosai sannan ta shiga kwantar masa da hankali.

  ***
  Se wajajen hud'u jirginsu Abba ya sauk'a driver yaje ya d'auko sa daga airport. Ruwa ya watsa sannan suka ci abinci da Ummi inda take basa labarin halin da ake ciki. Kansa ne ya mugun d'aure akan mey Alhj Abdallah zece a sakan masa 'ya? Shin meya faru? Nan da nan ya kira Afzal a waya yake tambayarsa kode wani abun ne ya had'asa da Daddy amma Afzal ya nuna sam ba komai banda mayar da Nazeefah gida da yayi akan laifin da ta aikata. Take a lokacin Abba yaje ya samu Daddy saidai Daddy na kan bakansa har yanzu shi a sakar mishi da 'ya ba yadda Abba beyi da shi ba, ba kalan hak'urin da be basa ba amma ya dage ina shi a sakar mishi da 'ya kawai irrespective of abotakan dake tsakaninsu. Na matuk'a ran Abba ya 6aci be ta6a tsammanin haka daga gun amininsa ba, ai ko da ma ace laifi Afzal yayi masa be kamata yayi haka ba.

  "Na d'au zamuyi magana man-to-man mu fahimci juna da kai Alhj Abdallah a matsayinka na amini na ashe ba haka bane."

  "Kayi hak'uri Alhaji Amin ko ni ban so abubuwa su kasance haka ba amma ya zama dole in raba auren yaran nan ne badan son ra'ayi na ba nima."

   "Sai don mey toh? Idan wani abun ne ka sanar dani mana kar fa kamanta aminin ka ne ni."

  "Ina sane da hakan Alhj Amin amma kayi hak'uri bazan iya sanar da kai dalili na ba ni kawai asa Afzal ya sawak'e wa 'yata."

  "Kaine mahaifin Nazeefah kuma se yadda kace za'ayi amma a tunani na zaka sanar dani koma meye dalilin, in shaa Allahu zanyi maka kyakkyawar fahimta."

  "Kayi hak'uri Alhj Amin komin yaya naso sanar dakai bazan iya ba shiyasa nake sake baka hak'uri kayi hak'uri."

  "Shikenan tunda abinda kake so kenan Allah yasa hakan shi yafi alkhairi."

  "Ameen nagode da fahimta ta da kayi ina fatan hakan baze 6ata tsakanin mu ba?"

   "In shaa Allahu ka gaishe da Madam." Har bakin gate Daddy ya rakasa sannan ya koma ciki Abba ya k'arisa gida. Tun daga bakin k'ofa Ummi ta soma tambayarsa yaya.

   "Yace shi a sauwak'e wa 'yarsa" ya sanar da ita.

  "Innalillahi! Toh Alhj ya zamuyi? Prince fa? Wallahi yana son yarinyar nan ina gudun kar hakan ya jefa sa cikin wani halin."

  "Toh mahaifinta yace ga abinda yake so mun isa muce a'a ne?"

  "Eh mana ai wannan bayi bane wallahi taya haka kawai ba k'wak'k'waran dalili se don an kora 'yarsa gida akan laifin data aikata ze shiga tsakanin masoya biyu yace se an rabasu, rabawan ma wanda ba komawa?"

  "Toh ya zamuyi Hjy Mariam?"

  "Muko muke da abinyi wallahi mu kai k'ararsa kotu na tabbata bazasu goye masa baya ba."

  "Mey yayi zafi har da zuwa kotu Hjy Mariam? Shi prince d'in bashida mata a gida ne? Kokuwa Nazeefar ce k'arshen halittu?"

  "Ko d'aya Alhj amma ai zaka duba halin da d'an nan ze iya fad'awa cikine. Yaran nan yana son yarinyar nan haka kawai kuma a rabasu wallahi babban hatsari ne ga rayuwansa harma da ita d'in."

   "Ina sane da dukkan hakan Hky Mariam kuma idan da akwai wani hanyar da zanbi da na bi dan in dawo masa da matarsa amma gar-da-gar Alhj Abdallah yace shi a sakan masa 'ya baya son jin komai mey kikeso inyi? Zancen kai k'ara kotu kuma ma be tashi ba idan dey mata ne Allah ya haliccesu dayawa ko a gobe yakeso yakan k'ara wani auren."

  "Hakane kam amma Alhj Abdallah bai kyauta ba ai ko dan abotakan dake tsakaninku ma be kamata yayi haka ba."

  "Zuwa gobe zan kira Afzal yazo anan ya rubuta mata takardanta a kai musu mu rabu dasu lafiya."

  "Oh! Duniya, toh shikenan Allah ya kaimu bari in k'arisa site d'ina."

 "Alright."

*****
   "Ya Omri ka kwantar da hankalinka haka, everything is going to be alright."
 A raunane ya d'ago lumsassun idanunsa ya kafa mata.
  "Rania I'm sorry" ya furta a hankali sam ba a son ransa bane ya nuna tsan-tsan damuwa akan Nazeefah a gaban Amal haka amma ba yanda ya iya ne abun ne yafi k'arfinsa.

  "Why?" Ta tambayesa cike da rashin fahimta.

  "For showing concern over Nazeefah like this nasan be kamata in nuna tsan-tsan damuwa akanta a gabanki haka ba but I just can't help it, kaman yadda nake sonki haka nake son ta itama.  Kuma kaman yadda bazan so abu ya shiga tsakanin mu dake ba ba ita ma haka ne Rania. I can't afford to lose her, I just can't" ya fad'a cikin raunannen murya.

    Baza tayi k'arya ba da fari taji haushi da kuma kishin yadda ya shiga matuk'an damuwa akan Nazeefah amma sanin yadda zafin rabuwa da masoyi yake musamman ma na dole irin wannan se taga ba laifinsa bane, ta tabbata idan da itane a position na Nazeefah zeyi haka ko fiye da hakan ma, toh kishin mey zatayi? Matsowa kusa dashi tayi sannan a hankali ta kwantar da kansa a k'irjinta tana mey shafe gashin kan nasa a hankali "Don't be sorry Ya Omri, na fahimci yanayin da kake ciki and I'm here for you, feel free to cry in my arms I love you so much." Hannayensa ya zagaye a 'yar kunkuminta yayinda hawaye ya shiga tsiyaya daga idanunsa sun dad'e a haka har seda wahalallen bacci ya d'aukesa. Cike da dabara ta kwantar dashi kan gadon ta gyara mai kwanciya sannan tayi zamanta a gefe tana mamakin dalilin da zaisa Daddy ya aikata abinda yayi.

  Chan wajajen Isha sega kiran Ummi da hanzari Amal ta mik'a wa Afzal kiran inda ya d'aga. "Ummi?"

  "Na'am Prince."

  "Ummi ina kika jefa wayarki ina ta kira switched off?"

  "Wallahi bak'i nayi d'azun suna ta game daga nan suka kashe min wayar suka yasar a lungu se yanzu na samu."

  "Ohh na d'au wani abu nema ya sameki ya Abba? Ya dawo?"

  "Eh ya dawo" ta amsa a sanyaye.

  "Yaje ya ma Daddy magana?"

  "Eh ya mishi."

  "And???"

  "Prince-" se kuma tayi shiru.

  "Please speak up Ummi" ya fad'a cikin tsananin fargaba.

  "An yi mishi magana amma he's not willing to back out Prince yace lalle-lalle se ka sakar masa da 'ya."

  "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ya saki salati "No Ummi."

  "I'm truly sorry Prince amma abinda yace kenan gobe da La'asr Abbanka na buk'atan presence naka. Seda safe ka gaishe da Amal" tana kaiwa nan ta katse wayar. Ko sauk'e wayar daga kunnensa Afzal ya kasa Amal ce ta tako daga gaban dressing mirror ta amshe wayan had'e da mik'ar da shi ta rungumesa tsam a jikinta tana basa hak'uri. Kaman d'an yaro ya zage yana kuka a jikinta ba makawa. A dalilin mey Daddy zeyi masa haka? No he can't stand by it, baze iya jure rabuwa da Rabba'atul Bait tasa haka kawai ba sabida selfish interest na mahaifinta. Tunda yana sonta tana sonsa toh in shaa Allah ba abinda ya isa ya rabasu he don't care koda maganan zata kai kotu. A shirye yake da yayi filing case akan Daddy, ya tabbata kotu zata dawo masa da matarsa.

  ****
   Washegari da safe suka shirya tsaf da Amal yayi dropping nata a school. Wajajen sha d'aya Nazeefah ta kirasa bayan sun gaisa ta buk'acesa da ya taho school a waje kaza yazo ya sameta. Be 6ata lokaci ba ya fice be tsaya ko ina ba se inda tace su had'un. Yana sauk'a daga motan ta ruga a guje taje tayi hugging nasa tana kuka har na fitan hankali. Rungumarta yayi tsam a jikinsa shima yayinda yake danne hawayen dake k'ok'arin ku6uce mar. Sun dad'e a haka sannan a hankali ya shiga raba jikinsa daga nata sede ina se sake matsesa Nazeefah ke da k'yar ya samu ya d'agota ya shiga share mata hawaye yana bata hak'uri yayinda take ta kad'a mar kai.

  "It's okay calm down I'm here."

  "It's not okay Ya Rouhi it's not" ta sanar dashi cikin tsananin kuka.

   "Look at me" ya buk'aceta "Look at me okay?" Cikin sanyi ta d'ago jajayen idanunta ta kafa mai. "Nothing in this world will ever seperate me from you except for death okay?"

  "How Ya Rouhi? Tayaya? Abba ma ya mishi magana jiya yak'i ya sauraresa se kai ne ze saurareka?"

  "I know it's not possible just trust me."

   "I really want to but I'm scared, tsoro nakeji Ya Rouhi."

  "Kar fa ki manta nike da ikon rubuta takardan nan ko ba haka ba?" Kai ta gyad'a yayinda ya cigaba "Idan ban rubuta ba kuma Daddy be isa ya miki wani aure akan igiyan aure na ba ko ba haka ba?" Nan ma kan ta kuma gyad'awa "Excellent ni kuma ko da kasheni za'ayi sama da k'asa su had'u bazan rubuta miki takardan nan ba Nazeefah I'll never do it."

  "I know Ya Rouhi amma kuma ko da hakan Daddy baze ta6a barina in koma a gareka ba ya gwammace in cigaba da zama a gida da igiyan auranka akaina daya amince ka miyar dani d'aki na."

  "I'm coming to beg him again later today idan har be amince ba zan kai k'ara kotu Rabba'atul Bait akan ki a shirye nake da inyi breaking rules and even worse saboda bana son rabuwa dake, da a rabani dake gara na rasa komi nawa dana malakka I love you Nazeefah, I love you so very much." Kuka ne yaci k'arfinta ba shiri ta fad'a jikinsa tana kuka shima ba don ya danne hawayen ba da tuni ya jonata sunyi kukan tare. A hankali ya rabata daga jikinsa ya rik'o 'yar fuskanta cikin hannunsa yana mey share mata hawayen nata "Your home will forever be here with me Darling" ya sanar da ita be hankara ba yaji tayi owning lips nasa kissing him so dearly. Kasancewar wajen ba mutane shima se be 6ata lokaci ba ya shiga sumbatarta in a soft demanding way. Sun dad'e a haka sannan yayi breaking kiss d'in daga bisani yayinda suka shiga mayar da numfashi.

  "Don't cry anymore okay?"

  "Okay" ta amsa tana gyad'a kai fuskarta ya d'ago yadda take kalon setin idanunsa "I won't rest har se idan na dawo dake d'akinki Nazeefah you have my words."

  "I trust you Ya Rouhi and I love you so dearly."

  "I love you too Darling."

  "Ka koma haka nan nima I have a class to attend."

  "Alright se na shigo anjima da yamma okay?"

  "Okay Allah kaimu."*******

    _3:47pm_

  Yana cikin tattare kayakinsa da shirin kulle office sega wayansa ya shiga ruri dubawanda zeyi yaga Amal ke kira. Be 6ata lokaci ba ya d'aga "Hello Rania?"

   "How're you Ya Omri?"

  "Alhamdulillah what about you?"

  "Lafiya k'alau."

  "And my baby?"

  "Itama lafiya."

   "Yau kika galabaitar mun da ita ko?"

  "Toh so kake inyi ta zaman gida ina tara wa kaina carrovers?"

   "A'a Mummy'n Baby yi hak'uri kunci abinci?"

   "Eh na dafa indomie."

  "Akwai wani abinda kike buk'ata?"

   "A'a I'm just missing you yaushe zaka dawo?"

  "Abba requested to see me so daga chan zan wuce gida okay?"

  "Batun Nazeefah koh?"

  "Yes."

  "Everything will work out fine in shaa Allah."

  "Thank you baby I love you."

  "I love you too seka dawo."

  "Sleep until then sena zo in tada ke." Da murmushi kwance fal a fuskarta ta amsa "Toh shikenan take care" nan ta katse. Be kai ga ajiye wayan nasa ba sega kiran Abba na shiga be hankara ba ya d'aga inda suka gaisa.

   "Ermm nace Umminka ta sanar da kai cewa ina buk'atan ganinka ko?"

  "Eh Abba I'm on my way."

   "Alright Allah ya kare."

  "Ameen" da haka ya katse ya gama tattare kayakin nasa ya fice. Direct gida ya wuce inda ya samu Abba da Ummi zaune a parlour suna jiransa. Ba tare da 6ata lokaci ba Abba ya sanar da Afzal gaskiyan al'amarin inda yayi mar nasiha sosai akan cewa ba komi mutum yake so yake samu a duniya ba dole wataran se an k'ara da hak'uri amma ina Afzal tamkar kurma haka ya zame a wajen maganganun Abba kawai suna shiga ta kunnensa suna fita ta d'ayan ne shi bega abinda ze rabasa da Nazeefah ba bayan mutuwa.

   "Saboda haka ga takarda nan da biro ka rubuta mata takardanta kuma saki ba d'aya ba, ba biyu ba yake nema saki uku yake so."

  "No Abba" ya sanar dashi ciki rud'ani "I can't do this."

  "I know Afzal amma ya zame maka dole ba muke iko da Nazeefah."

  "Abba baka gane bane? Bazan iya rubutawa Nazeefah takarda ba I can't."

  "Prince kayi hak'uri" fad'in Ummi.

  "No Ummi I can't zan je in samesa inyi masa magana in shaa Allah ze sauk'o."

   "Umminka bata sanar da kai cewa da kaina naje na samesa bane? Alhj Abdallah ya riga yayi making up mind nasa ba abinda zakayi da zaisa ya sauk'o."

  "I'll still try my luck Abba idan kuma be hak'ura ba then I have no choice dole in kai maganan nan kotu dan idan ba mutuwa ba banga abinda ze rabani da matata ba."

   "Nima haka nace mu kai k'aranshi kotu tunda de ba zaluntar yarinyar nan kakeyi ba kotu zata tsaya maka ta dawo maka da matarka."

  "A'a Hjy Mariam seda na fad'a miki ki yasar da maganan nan kink'i akan mey zamu kai maganan nan har kotu? Nazeefar itace autar mata ko mey?"

  "Ba itace k'arshen halitta ba Abba amma bazan iya rabuwa da ita haka kawai saboda selfish interest na Daddy ba."

   "Afzal kar ka manta Nazeefah 'yarsa ce kuma bamu keda iko da ita ba."

  "No Abba, Nazeefah matata ce kuma nafi Daddy iko da ita shiyasa nake rok'onka da ka bani dama inje in samesa inyi masa magana."

  "Afzal wai kam mey kakeyi haka? Akan rashin mutuncin da Alhj Abdallah yayi maka ya kuma yi wa mahaifinka ai yaci ace ka fita daga harkansa da 'yartasa gabad'aya. Ka sani suke da asara ba mu ba, idan aure kake so ka k'ara ko a yau ka kawo mace gidan nan zan aura maka ita, infact ko uku kakeso ka k'ara zanyi maka komai balle ma kai da kake da mace a gida? Mene Nazeefah za tayi maka wanda Amal baza ta iya yi ma ba? C'mon man up."

   "Abba ba haka bane, baza ka ta6a ganewa ba Nazeefah and Amal are two different people dan Allah ka bani dama inje in sake basa hak'uri in shaa Allah he'll come around."

  "Alhj kayi hak'uri ka barshi yaje d'in hala rabonsa ya ratse" Ummi ta fad'a.

  "Shikenan kaje amma ni ba ruwana na riga na fad'a maka abinda ya kamata."

  "Nagode" yace zalla had'e da mik'ewa "Ni zan koma duk abinda akwai I'll let you know." Da haka ya fice dai-dai gaban gidansu Nazeefah yayi parking ya k'arasa ciki.

   "Ka kawo takardan nata ne?" Daddy ya tambayesa bayan gaisuwan da sukayi.

   "Daddy ba abinda ya kawo ni ba kenan dan bazan ta6a iya rubutawa Nazeefah takarda ba haka kawai. Hak'uri nazo baka, dan Allah kayi hak'uri."

   "Shin mahaifinka be sanar dakai abinda nace masa bane?"

  "He did Daddy amma bazan iya ba, wallahi ina son Nazeefah kuma bana k'aunan rabuwa da ita idan wani laifin nayi kayi hak'uri-"

  "Dakata Afzal!" Daddy yayi saurin katsesa "Idan ba so kake ranka ya 6aci ba ka bani takardan 'yata zaman aure ne nace bazaku k'ara ba."

    "Shikenan Afzal ka mik'e ka tafi zamuyi magana" Mummy dake la6e tun d'azu jikin garu tace.

  "Mummy dan Allah ki basa hak'uri wallahi bazan iya rabuwa da Nazeefah ba."

  "Na gane Afzal just go zamuyi magana." Ba dan yana so ba ya mik'e ya fice. Acikin mota ya zauna ya shar6i kuka kaman ba gobe.

    Daddy da yaga dagaske Afzal yake baze iya rabuwa da Nazeefah ba ya shiga nazari, yasani koda kotu ya kai k'ara da k'yar su biye masa sabida bashida wata k'wak'k'warar dalili, da ace Nazeefar ne bata son auren da rabasa bazeyi wuya ba amma yasan komin yaya Nazeefah bazata ta6a amincewa ta rabu da Afzal ba. Ya zeyi toh?
 
   Chan bayan sallan Isha Mummy na zaune a d'akin Nazeefah tana ta faman bata hak'uri Daddy yayi knocking bisa k'ofan ya shiga.

   "Ermm Hjy Surayya ki tattaro min passports naku."

  "Passports? Kayi mey dasu?"

  "Kede kam ki tattaro mun mana ina ruwanki?"

  "So kake ka d'ibe mu kaje ka jibge mu a wani k'asan saboda selfish intrest naka?"

  "Ba abinda na tambaya ba kenan ki bani passports naku."

  "Bazan bada ba."

  "Nazeefah ina passports naku?"

  "Daddy dan Allah kayi hak'uri Daddy meyayi zafi kake shirin kaimu wani k'asan? A dalilin mey?"

  "Saboda bana son abinda ze sake had'aki da Afzal."

  "Daddy da igiyan auren Ya Afzal akaina kake son inyi tafiya ba tare da izininsa ba?"

  "Sau nawa zan fad'a miki Afzal ba mijinki bane? Zaman ku ya haramta."

  "Ya haramta kaman yaya wai? Idan wani abun ne ka fito fili mana ka sanar damu Alhj meye amfanin wannan 6oye-6oyen da kakeyi?" Mummy ta tambayesa.

   "Ina jiran passports naku muddin Afzal baze sauwak'e wa 'yar nan ba toh barin k'asar nan ya zama dole."

  "Daddy makaranta na fah? Khaleefah ma fa?" Nazeefah dake kuka ta tambayesa sede ko ta kanta beyi ba ya ja k'ofan ya fice. Fad'i tayi jikin Mummy tana kuka. "Wallahi wallahi kinji ko? Ba inda zamu. Iyayin Daddy'n naku ya soma isa na Allah kaimu gobe k'ara zan kai kotu akan mey dan na zuba masa ido ze tsaya yana yin son ransa a cikin gidan nan? Ki kwantar da hankalinki Allah kaimu goben.".****

   Chan wajajen goma Nazeefah ta d'au waya ta kira Afzal, ringing d'aya biyu ya d'aga.

  "Hello Rabba'atul Bait?"

   "Ya Rouhi please help me Ya Rouhi bana son in rasaka."

   "Wani abu ya sake faruwa ne?"

  "Ya Rouhi Daddy na shirin relocating namu out of Nigeria gabad'aya."

   "What?!"

  "Wai muddin bazaka bani takarda na ba zamu bar k'asar, d'azun yazo ya tattare passports namu Ya Rouhi please help me out."

   "Shhhh its okay don't cry ina Mummy?"

  "Mummy tace zata kai k'aransa kotu."

  "Ki kwantar da hankalinki kinji? Sena shigo gobe kibar kukan haka."

  "Please come."

  "I'll, you should get some rest I love you."

  "I love you too" ta amsa sannan ya katse. Safa da marwah ya shiga yi a parloun yana nazari sannan chan yaje ya samu Amal a d'aki suka kwanta.

     Washegari bayan sallan Azahar Afzal ya taho gidansu Nazeefah ba irin hak'urin da be bawa Daddy ba amma ina ko sauraronsa Daddy baiyi ana cikin haka Mummy dake sauraronsu tun d'azu ta sanya baki.
   "Toh tunda de haka ne Afzal ni na baka dama kaje kayi filing case a kotu se muga idan kotun zata basa goyin baya ya raba wannan aure." Wani irin har6awa zuciyan Daddy yayi tabbas idan ya bari maganan nan yakai kotu toh asirinsa ze toni kenan. Ya zeyi?

   "Ni kike shirin kaiwa kotu Hjy Surayya?"

  "You give me no option Alhj. Idan wani abun ne kake 6oye mana tell us we're your family zamuyi maka kyakkyawn fahimta amma zancen canza mana gari be tashi ba."

   Kai ya shiga girgizawa "No Hjy Surayya bazaku ta6a fahimta taba, ba don ni ba dan Allah kuyi hak'uri a raba auren nan."

  "Trust me Alhj zamu fahimceka just tell us" a hankali ta shiga yi mai magana cike da kissa amma inaa Daddy ya kasa bud'e baki yayi magana se kad'a kai kawai yake.

  "Toh inde haka ne mu ma bazamu amince mu bika koma ina ba kuma mayar da yarinyar nan d'akinta ba fashi."

   "Afzal ka rubuta wa 'yar nan takardanta nace auren ku ya haramta!"

   "A dalilin mey ya haramtan?" Itama Mummy ta mayar masa cike da tsiwa.  Dai-dai lokacin Nazeefah da Khaleefah suke sauk'owa daga sama. A bakin stairs d'in suka tsaya suna sauraron iyayensu.

   "Ya haramta nace kuyi wa Allah ku raba auren nan."

   "Mey sukayi da zaka haramta musu aure? A dalilin mey?"

   "Ya haramta Hjy Surayya ki yarda da ni."

   "Na yarda da kai Alhj, just tell us ka gaya mana dalilin da yasa ya haramtan, muddin kaine da gaskiya na maka alk'awarin tayaka raba auren nan just tell us."

   "Bazan iya ba ku gafirceni." Na matuk'a kan kowa ya d'aure a wajen, ba wanda ya fahimci inda ya dosa gashi duk sun k'osa suji dalilin da yasa yake cewa auren ya haramta.

   "Alhj dan Allah kayi magana, ka fa sani rik'e maganan nan ba shine mafita ba, we're your family komin yaya bazamu guje ka ba just tell us."

   "Ya haramta na fad'a muku ya kuke so inyi? Kar ku biye ma Afzal. Tunda baze saki 'yar nan ba ku amince ku bini mu tattara mu bar k'asar nan shine kwanciyan hankalin mu gabad'aya."

   "Tayaya Alhj? Mene wannan abu da kake k'in gaya mana? Toh inde haka ne ina Nazeefah? Ku sauk'o mu bi Afzal mu bar mai gidan idan tayi tsami maji."

   "Hjy Surayya dan Allah karki tozartani a idon jama'a haka, kar ku tafi ku barni ku kad'ai gareni."

  "Fine seka sanar danu wannan magana da kake 6oyewa kokuwa mu tafi."

   "Ni koda zaku tafi ku amince a raba auren nan, na yarda ku tafin amma a raba auren yarannan tukuna."

   "Haka kawai ba gaira ba dalili kake son a shiga tsakanin masoya biyu? Toh wallahi kayi k'arya Alhj."

   "Sau nawa san gaya miki auren nan ya haramta?! Sau nawa!" Ya daka mata tsawa.

   "Sau nawa nima zan gaya maka muddin banji dalili ba bazan yarda a raba auren nan ba?!" Itama ta mayar masa a tsawace.

    "Ya haramta nace!"

   "Mayar da aure ba fashi ku sauk'o mu tafi Nazeefah."

  "Kar ku tafi ko ina, auran Afzal da Nazeefah ya haramta saboda Amal da Nazeefah 'yan uwa ne!" Ya sanar dasu a fusace ba tare da yasan yaushe ba.






RANA D'AYA!💖
#RD

Love... King Miemiebee👄✨

9 comments:

Unknown said...

Oyoyo miemienmu, allah Ya qaqa basira. Gaskiya kin daga mana hankali. Alhamdulilllah kina lafiya. Mun gode mun gode.

Unknown said...

Mungode Miemie. Allah ya qara basira da hikima.

Unknown said...

You're Welcome 😊

Unknown said...

Amin

Unknown said...

You're welcome

Unknown said...

Godia babu adadi miemie, Allah ya kara miki lafiya yakumasa zakkan jikine
Please update soon.

Unknown said...

Tnx sis

Unknown said...

Ameen thank u in shaa Allah

Unknown said...

Uw