BY MIEMIEBEE
PAGE 30
Getting enough of her strawberry lips, a hankali yayi breaking kiss d'in had'e da mik'ar da ita suka zauna "Ya kamata kayi wanka Habib Albi akwai office gobe."
"Kin manta tare zamuyi wankan ne?"
"Toh tashi muyi ka samu ka huta ka kwanta."
"Ni massage (tausa) nakeso."
"Komey kakeso zanyi maka Habib Albi yanzu de ka mik'e tukun."
"Kafin nan" yayi maganan had'e da zaro roban da Nazeefah ta basa akan ya bawa Amal "Ga wannan daga gun 'yar uwarki" amsa tayi tare da kaiwa hancinta don shinshinawa "Wow turaren wuta!" Ta fad'a cike ca jin dad'i. "Allah sarki Nazeefah yanzun zan kirata inyi mata godiya kafin in manta."
"Yakamata kam."
"D'an mik'o mun wayana" nan da nan ta kira Nazeefah tayi mata godiya inda ita kuma ta nuna mata ba komai.
"Yauwa Kitten may I ask you something?" Ya tamabyeta bayan ta ajiye wayan.
"Anything Habib Albi."
"Shin ya kikesa turaren wutan kine?"
"Mey kaga?"
"Unlike na Ummi da Nazeefah naki hayak'in baya yin yawa se k'amshi zalla."
"LOL Habib Albi kai baka san shuwa da turaren wuta bane? I think tun ina shekara goma na fara kunna turaren wuta."
"Nasani I'm just curious so tell me."
"LOL okay ni ba se dab zaka dawo nake sawa ba, timing lokacin da zaka shigo nakeyi se in kunna 20-25 minutes before haka."
"Window a kulle ko a bud'e kike sawa?"
"Ina kulle windows in sauk'ar da curtains, idan nabi gidan da turaren gabad'aya se in bashi kaman 10-12 minutes ya kama haka sannan in bud'e windon kad'an in kunna fan hayak'in ya fita, yana d'an fita se in sake kullewa kar k'amshin yabi iska shima a hankali har hayak'in ze watse gabad'aya yabar k'amshi."
"No wonder mana kullum inyita mamaki."
"Yanzu ka gane?"
"Yes Kitten" ya amsa nan da nan suka d'aura towel suka nufi bayi inda sukayi wanka, sun dad'e aciki sannan suka fito d'aure da alwala. Sallan isha suka idar suka kammala Azkhar nasu sannan suka sanya kayakin baccinsu. A hankali ta kwantar da Afzal akan k'afarta sannan ta shiga yi masa tausar, kasancewar hannayen nata sirara suke kuma k'anana se ji yake kaman cakulkuli takeyi masa. Duk lokacin da ta ta6asa seya sa dariya haushi ya bata k'arshe ta turesa daga jikinta.
"Ni na fasa yi" ta fad'a a fusace had'e da gangarawa wajenta. Bin ta yayi ya haye kanta ya shiga showering mata kisses tun daga wuya har izuwa fuska yana teasing nata sannan ya mik'a hannu ya kashe musu wutan d'akin. Xxx
Washegari bayan sun idar da sallan Asuba ta taya Afzal shiri dukda cewa da yayi karta damu ta koma bacci ze iya shirya kansa, seda ta rakasa har waje sannan ta dawo ciki ta koma bacci. Kaman yadda yake kiran Amal kowace safiya da yake gun Nazeefah haka ma ya kira Nazeefar yau suka gaisa seda ya tabbata bata da wata matsala sannan sukayi sallama.
Wajajen k'arfe biyu Amal ta d'au waya ta kira Afzal bayan ta tamabayesa ya aiki tayi gyaran murya "Habib Albi se nawa kake tashi daga office yanzu?"
"Wani abu ne Kitten?"
"I miss Mami and Papi" ta sanar dashi.
"Kina son kije ki dubasu?"
"Eh."
"Toh ba ga motarki ba?"
"Toh Habib Albi na iya tuk'i ne?"
"Haka kuma fa semun koya miki a hankali."
"Nifa tsoron tuk'i nake."
"Toh haka zaki ta kallon motan naki Kitten?"
"A'a in zaka iya seka nemo min driver yana kaini duk inda nakeso amma nikam bazan iya tuk'i ba."
"Me zai hana ki Kitten? We'll discuss that later so kikace kinason ki duba su Mami?" Kai ta gyad'a wane yana gabanta.
"Alright bari inyi clearing schedule d'ina se in taho muje."
"Dagaske Habib Albi? Ban shiga ma hak'k'in office ba ko?"
"Ai aikin office na zuwa ne a bayan farin cikin Kitten d'ina so I'll be home in a jiffy kinji?"
"Toh Habib Albi seka zo I love you."
"I love you most Kitten" da haka ta katse wayan. Girkin nata tayi sauri ta kammala ta zubawa mai gadi nasa sannan ta shirya kan dining. Bayan nan ta tsaya yin shawara ta kunna turaren wuta ne kota fara shiga wanka daga k'arshe de ta fara da shiga wankan. Bayan ta fito ta shafa mai ta tsara kwalyarta sannan ta sa wata bak'ar lace da touches and stone works na golden sannan ta fice parlour. Show glass nata ta bud'e ta ciro kwalban data juye turaren wutan da Nazeefah ta bata, haka kawai taji bari ta gwada kunnasa taji k'amshinsa yau. Gawayinta na kamawa ta zuba cikin kasko sannan ta barbad'a turaren akai se sauri take kar Afzal ya taho yanzu ya tarar da hayak'i. Tana zuba turaren akan gawayin kawai wani irin hayak'i ya shiga tashi tunda take bata ta6a ganin abu haka ba hurawa ta shiga yi a hankali amma ina se k'aruwa hayak'in yake har yana sanyata tari, shin wani irin turaren wuta ne wannan Nazeefah ta bata? Gashi nan da nan ya k'one ya fara bada warin k'onuwa da hanzari ta fita waje dashi ta k'ofan kitchen ta zubar.
Sabon gawayi ta d'ibo zata had'a kwatsam taji k'aran motan Afzal sosai gabanta ya fad'i parlourn ta dawo da wuri amma ta rasa ta ina zata fara fidda wannan uban hayak'i. Inda ma ace hayak'i ne zalla da da sauk'i amma ga warin k'onuwa gabad'aya ya d'umama gidan yau ta shiga uku. Afzal na bud'e k'ofan parlourn yayi sauri ya koma baya dan wani irin hayak'in dayaci karo da.
"Subhanallahi!" Yayi exclaiming da sauri had'e da zaro hanky yana toshe hancinsa. "Kitten ki fito kafin hayak'in ya miki illa" yace da ita yana mamakin ya akayi take tsaye har yanzu cikin tsabar hayak'in nan. "Kitten hurry!" kamar wacce k'wai ya fashe ma aciki ta fito ta samesa a waje.
"Ya haka meya faru?" Yayi saurin tambayanta.
"Yaya-" se kuma tayi shiru, gabad'aya ta kid'ime.
"Abu ne ya k'one miki?" Kai zalla take iya kad'a mai "Ya gidan da hayak'i haka toh? Ga kuma warin k'onuwa." Har ta bud'e baki zata sanar da shi turaren wutan da Nazeefah ta bata ne ba kyau se kuma ta tuna nasihan da Mami tayi mata na cewa;
_Ko da wasa karki fara ki had'a kansa da na matarsa, komin mey ta miki kar kice zaki kai k'ararta gunsa idan har kece da gaskiya toh Allah da kansa ze wanke ki dan shi ba azzalimin bawa bane_ wannan lafazi yasa ta canza ra'ayinta tayi shiru.
"Yes??" Ya sake tambayarta jin tayi shiru.
"Ermm... Naje ina kula da girki ne se har turaren ya k'one akan gawayin I'm sorry."
"Shikenan ba komai ina de baki k'one ba?"
"A'a."
"Shikenan don't worry mu zauna anan se hayak'in ya ragu kafin mu shiga."
"Barin shiga in bubbud'e windows d'in in d'aga labule zefi fita da wuri."
"So kike ki shak'i wannan uban hayak'i har seya miki illa Kitten?"
"Toh Yaya in ba haka ba baze fita da wuri ba har ka samu kaci abinci mu fita."
"Toh muje in tayaki se muyi da sauri."
"A'a ka jirani anan."
"No Kitten I insist" haka suka k'arisa ciki suka shiga bubbud'e windows d'in, da hanky mak'ale a hancin Afzal amma dukda haka wari da hayak'in be barsa ba, gabad'aya jikin Amal yayi sanyi sam ba haka taso abinta ba. A waje suka zauna seda hayak'in ya ragu sannan suka koma ciki bin parlourn tayi da turaren Khumra don kashe warin. Bayan ta sirka masa ruwa yayi wanka suka fito dining don cin abinci sede tun d'azun yake kallonta gabad'aya tayi shiru ba walwala tattare da ita.
"Kitten?"
"Na'am?" Ta amsa tana d'ago kai.
"Yau achan zaki zauna?" Kai ta gyad'a zalla "Why?"
"Yaya I'm sorry."
"Why? What for?"
"For the inconvenience wallahi ban san ya akayi turaren ya k'one haka ba please forgive me."
"Ohh Kitten!" Ya numfasa "Come here" ba gardama ta mik'e daga kujeran nata ta samesa, a cinyarsa ya zaunar da ita "It's really okay dear, kullum kinayi me kyau dan an samu akasai yau kuma seya zama abun magana? Kidena damun kanki kinji? Ni baki mun komai ba."
"Thank you" tace dashi cikin sanyi, shi da kansa yayi serving nasu sannan ya shiga feeding nata seda suka k'oshi tukun suka jira La'asr yayi suka yi sallah suka shiga shiri, se wajajen biyar da rabi suka dawo gida se hira Mami take jansu da.
Bayan sallan Maghrib Amal da Afzal suna zaune a parlour Afzal ya mik'ar da k'afafunta akan cinyansa tana tayasa kallon sports se wayanta ya shiga ruri dubawan da zatayi taga Nazeefah ke kira bata hankara ba ta d'aga.
"Assalamu Alaikum."
"Wa'alaikumus salam Nazeefah" ta amsa '"Yar uwa ya kike?"
"Lafiya k'alau ya gida da wahala kuma?"
"Wani wahala ne kuma, gida k'alau ya Ya Afzal?"
"Lafiyanshi k'alau."
"Nace kinyi amfani da turaren wutan nan kuwa?"
"Eh."
"Gosh! Dama kira nayi ince karkiyi amfani dashi bashida kyau yanzu Mummy ta kirani take sanar dani matar da ta sayar matan ta cuce tane" ta shirya mata k'arya don dama da gan-gan ta bata turaren wutan sanin bashida kyau.
"Ayyah wallahi har na kunna d'azu."
"Ba dad'i ko?"
"Unfortunately gashi yata hayak'i kuma yana k'onewa gabad'aya ya d'umamamun gidan."
"Subhanallahi Ya Afzal na gida kuma? Kinsan bayi son hayak'i."
"Wallahi abun beyi ba sam, ina cikin sawa ya dawo."
"Allah sarki kiyi hak'uri dan Allah ban san bashida kyau ba da ban baki ba."
"Ba komai Nazeefah ai bazaki cutar dani da gan-gan ba."
"Toh bari in barki haka kar in shiga hak'k'in Ya Afzal."
"A'a fa karki damu."
"Toh ki gaishesa seda safe."
"Allah bamu alkhairi" da haka sukayi sallama. "Huuh!" Tayi exhaling had'e da ajiye wayan "Waye ne? Nazeefah ce?" Ya tambayeta.
"Eh tana gaisheka."
"Ina amsawa maganan mey naji kuke haka?"
"Batun turaren wutan ne kasan wanda ta ba nin na kunna ashe wai bashida kyau matar data had'an bata k'ware ba seta damfari Mummy dama kira tayi tace kar in kunna nace ai tun d'azu na kunna."
"Ayyah kinga bama laifinki bane kike ta tada hankalinki daga turaren wutan ne."
"Ai toh naga baka son hayak'i ne shine hankalina ya tashi."
"Next time ki kwantar da hankalinki kinji?" Kai ta gyad'a mar a hankali sannan ya shiga tickling toes nata ya na mata cakulkuli, dariya ta tsaya yi na sosai chan wajajen tara da rabi suka kashe TV'n suka yi wanka suka kwanta.
Washegari da yamma Afzal ya koma gun Nazeefah, tsaf ta gyara gidan ta itama ta kunna turare sede hayak'in ne yayi yawa. Bayan sun yi Sallah sun ci abinci suna zaune a parlour Afzal yayi gyaran murya ya kira ta "Rabba'atul Bait?"
"Na'am Ya Rouhi" ta amsa.
"Shin ya kike sa turaren wutan ki ne kam?"
"Mey kaga?"
"I'm just curious ya kike sawa?"
"Dab zaka zo nake sawa."
"Shiyasa hayak'in yake yin yawa."
"Yana damunka ko?"
"I'm sorry but yes kinsan bana son hayak'i."
"I'm sorry a haka fa na bubbud'e window ma dan ya d'an ragu."
"Kinsan ya Ummi takeyin nata?" Beso ya ambaci sunan Amal ba gudun kar hakan ya sanyata kishi. Kai ta kad'a a nitse.
"Kunnawa take 20-25 minutes idan tana expecting bak'o saboda hayak'in ya tafi."
"Toh Ya Rouhi k'amshin ai se k'are kafin nan."
"Nop kinga zaki kulle windows ki sauk'ar da curtains seki sa ki basa like 10-12 minutes haka ya kama, then ki d'an bud'e window ki kunna fan ya tafi da hayak'in yana d'an fita sekiyi shutting back windows d'in kinga haka k'amshin ki yana nan hayak'i kuma ya tafi."
"Kai amma Ummi akwai fasali na gane Ya Rouhi nima haka zan fara sawa in shaa Allah."
"Yauwa Rabba'atul Bait shiyasa nake sonki."
"Uhm Ya Rouhi?"
"Yes Babe?"
"Wallahi wata tambaya nake son inyi maka amma bana son kamin mumunar fahimta."
"What is it? Feel free to ask me."
"Bazaka mun mumunar fahimta ba?"
"Just ask me Nazeefah."
"I've been curious for a while tun da aka kusan auranka ciwon zuciyanka be sake tashi ba shin dama mey dalilin? Meyake jawo maka attack d'in?"
"Naze-"
"Please tell me Ya Rouhi the last time I asked you banji dad'in yadda ka nuna mun a fili bazaka iya sanar dani ba I felt like you didn't trust me as your wife."
"Ba haka bane Nazeefah of course I do trust you."
"Toh yaya ne Ya Rouhi ai idan da ka yarda dani komi naka zaka iya sanar dani nasan da Amal ce ta tambaya da tuni ka sanar da ita."
"No please don't ever say that again kaman yadda Amal take matata kema haka ne so ki daina tada hankalinki kina ganin kaman nafi sonta fiye da ke, I love you both okay?"
"Okay Ya Rouhi kayi hak'uri idan magana na ya 6ata maka rai."
"Ba komai ya wuce."
"So zaka iya fad'a mun?" Nauyayyan ajiyan zuciya ya sauk'e "I'm very sorry Nazeefah amma Amal ce sababin ciwon nawa, rashinta a kusani dani shi yake haddisa mun ciwon nawa."
"Amal?" Ta tambaya cike da mamaki bil adad "Rashin Amal Ya Rouhi?"
"Yes Nazeefah, Amal."
"Wow!" Ta numfasa yanzu akan Amal Mummy ta mareta ranan a fuska? Yanzu akan Amal tsakaninsu da Ummi ya kusan 6aci? Wow! Ai dama seda jikinta ya bata haka amma tak'i amincewa ashe gaskiya ne in bahaka ba kanta ya mugun d'aurewa yadda ciwon nasa be sake tashi ba tun da ya kusan aure.
"Amma ban fahimce ka ba Ya Rouhi shin ba auran soyayya kukayi da ita Amal d'in bane dama har kake tsoron rasata haka?"
"It's a long story Nazeefah."
"Will it be okay if you tell me?" Numfasa yayi sannan ya fara kaman haka;
"I've known Amal for three years now tun kafin muyi aure muke tare da ita amma ba a matsayin saurayi da budurwa ba don daga baya ne nayi developing feelings mata lokacin kuma ita har sunyi nisa da wani saurayinta Abdul kin gane sababin ciwon nawa?"
"Anytime ka gansu tare se ciwon naka ya tashi kai kuma ka kasa sanar da ita kana sonta?" Kai ya gyad'a zalla.
"Toh ina shi saurayin nata yanzu?"
"Yana Canada."
"Ya sadaukar maka da soyayyanta kenan?"
"Yes Nazeefah."
"Allah sarki gaskiya na ji ma wannan masoya guda biyu Allah sa hakan shi yafi alkhairi a gareku duka."
"Ameen Rabba'atul Bait I hope I've answered your question."
"Yes you did Ya Rouhi muje ka watsa ruwa mu kwanta gobe office ko?"
*****
Haka kwanaki suka ta shud'ewa yayinda shak'uwa da soyayya keta dad'uwa tsakanin Afzal da Amal, a yau jirginsu na zuwa Saudi ya tashi kad'an ya rage Amal batayi kuka ba sanda jirginsu yazo tashi tsabaragen tsoro.
Da zuwansu yau sun samu sati kenan lafiya k'alau suke zaune, kullum suna cikin fita shopping da wajajen shak'atawa, tsaraba da dama Afzal ya sai wa Nazeefah wasu ababen ma Amal ce ke cewa ya saya mata, sosai yake jin dad'in yadda Amal ta d'au Nazeefah da zuciya d'aya.
Yau a d'aki sukayi deciding su yini Amal na mik'e akan gado tana latsa wayarta yayinda Afzal ke tsaye gaban mirror ko mey yakeyi oho.
"Arghh!" ya saki k'ara bisa yankewan da yayi da reza.
"Subhanallahi lafiya?" Amal ta tambaya. Ba shiri ta mik'e lokacin da taga jini na bulbula daga yatsn nasa.
"Innalillahi! Habib Albi!" Tissue taja da wuri gaban mirron ta shiga tare mai jinin "Omg I'm so sorry sannu" tace dashi a rikice tamkar zatayi kuka da mamaki Afzal ya tsaya yana kallonta shi da ya yanken ma hankalinsa be tashi ba kaman yadda nata ya tashi. Iska take hura masa tana ce mai sannu ba makawa.
"Kitten calm down yanka nefa kawai."
"But yankam ai deep ne Habib Albi sannu" iska ta cigaba da hura masa sannan tajasa izuwa bayi, spirit ta bud'e "Ka rufe idonka zeyi zafi" dariya sosai ta basa "Ce miki akayi rago ne ni?" A hankali ta shiga bulbula masa akan ciwon, wincing kad'an yayi Amal kam sekace ita aka sawa akan ciwo se tashi tsikan jikinta yake. Cike da lalashi tana hura mai iska tana ce mishi sannu ta mishi dressing ciwon ta tasa bandage. Se kallonta yake yayinda wani irin wutan sonsa yake ruruwa a zuciyansa.
"Kitten it's okay."
"It's not Habib Albi baka ga yadda yata jini bane?" hannun nasa ya zame daga nata had'e da rik'o k'aramar kunkuminta seda ya matso da ita kusa da shi "Bade kuka kike shirin yi ba Kitten?"
"No" ta amsa ciki-ciki mik'awa yayi had'e da kissing soft lips nata, sun d'au tsawon lokaci suna abu d'aya sannan a hankali tayi pulling out. "Thank you Kitten" ya furta yana maida gashin ta baya.
"What for Habib Albi?" Ta amsa tana zagaye hannayenta a wuyansa.
"For everything sweetheart, I can't imagine life without you, Allah yayi miki albarka I love you so much."
"Ameen Habib Albi I love you most" peck ta masa placing a kumatu "Muje ka huta" d'akin suka koma ta mik'e akan gado tana duba messages nata yayinda ya canza kayan jikinsa da jini yad'an 6ata. Hankalinta gabad'aya ya duk'ufa akan chatting da takeyi da Maamah kawai taji Afzal ya k'wace wayan kafin tace ya bata ya mik'e a jikinta had'e da kwantar da kansa a saitin k'irjinta wane d'an wani yaro.
"Habib Albi-"
"Lets sleep Kitten bacci nakeji."
"Toh ka tsaya in gyara kaji?"
"Ni haka nakeso" murmusawa tayi sannan tayi placing mai light kiss acikin gashin kansa yayinda take shafashi a hankali. A haka har bacci ya d'aukesu duka.
Sati biyu sukayi sannan suka dawo Nigeria, a ranan da suka dawo Nazeefah ta shirya musu abinci da dama ta kai musu haka Ummi da ma Mami, washegari sukayi sorting out tsaraban kowa suka kai musu, da yammacib ranan ya wuce gidan Nazeefah. Bayan sun k'are dinner sun dawo d'aki ta zaune gefensa akan gado inda take sanar da shi batun makaranta akan cewa in a week time zasu bud'e.
"Yes haka Amal tace kekam final semester d'inki kenan ai ko?"
"Yes Ya Rouhi."
"Toh Allah nuna mana graduation nakun."
"Ameen thank you nace ba.." se kuma tayi shiru.
"Yes what is it?"
"Ya Rouhi are you okay with it in d'auko mey aiki? Kaga semester'n nan na neman concentration sosai bazan zo in iya da aiki da shara d'innan ba shine nace idan ka amince na riga nayi magana da wata mata yaranta are ready to work for me and Amal."
"Itama Amal tace tana buk'atan mey aikin ne?"
"Bata fad'a ba amma nasan zata buk'ata ai Ya Rouhi ita da course nata yafi nawa wuya ma ai kaga zata fini buk'ata ma."
"Hakane kam so masu aikin kwana ne ko na jeka ka dawo?"
"Na kwana ne saboda daga k'auye za'a kawo su bawai anan suke da zama ba."
"Masu aikin kwana kuma Rabba'atul Bait?"
"Ya Rouhi nasan me kake gudu karka damu yara ne fah Khaleefah ma ya girmesu d'ayar 16 d'ayar kuma 14 kaga ai baza a samu wata matsala ba in shaa Allahu."
"Toh zanyi ma Amal magana."
"Yauwa duk abinda akwai seka sanar da ni muyi making arrangements ya zammana de sun fara aikin tun yanzu ba se an bud'e makaranta ba."
"Jazakillahu khair Rabba'atul Bait yadda kikeso wa Amal abinda kikeso wa kanki."
"Ameen Ya Rouhi an zamo d'aya ai yanzu zamu kwanta ko?"
"Wallahi kaman kin sani a gaje nake."
"Akwai gajiya ai ko nayi maka tausa tukun?"
"Baki gaji ba?"
"Ai bana gajiya when it comes to you" mik'ewa yayi kan gadon ta shiga yimai tausan a hankali tana relieving mai tension.
*****
Kwana biyu yayi mata sannan ya dawo gun Amal.
Amal fa ba wasa kitso taje aka rangad'a mata k'anana sannan ta sha lalle ja a tafin hannu ta baya kuma akayi mata bak'i irin na zamanin nan mey kyau. Kafin Afzal yazo ta gama girkinta ta bi gidan da turare se k'amshi zallah ke tashi.
"Oyoyo Habib Albi" taje tayi hugging nasa da gudu.
"Oyoyo my Kitten" sun d'au kusan minti d'aya manne a jikin juna sannan ya d'agota a hankali "Masha Allah kin ganki kuwa?"
"Nayi kyau?" Ta tambayesa tana wasa da yatsun hannunsa.
"Yes Kitten yakamata in biya kud'in wankan nan."
"Awwn thank you Habib Albi" ciki suka k'arisa suka nufi d'akinsu inda ya rage kayan jikinsa suka haye kan gado "Yau mey aka girka mun Baby?"
"Your favorite!" Ta sanar da shi.
"Spaghetti?
"Uhumm."
"Wow! Ya kike toh?"
"Lafiya k'alau ka baro Nazeefah lafiya?"
"Lafiya k'alau tace in gaisheki."
"Ayya ina amsawa jiya ma Mami tana nan ai tazo muka yini mun."
"Allah sarki ya take?"
"She's fine" ta amsa se kuma taga yadda Afzal keta kallonta tun d'azu da fari ma tsarguwa tayi kode jan bakinta ya hau kan fuskanta ne?
"Habib Albi lafiya?"
"Matso kiji" matsowa tayi kusa da shi hakan be masa ba seda ya aza ta kan cinyansa "Kitten?"
"Yes?"
"Anya kuwa?"
"Anya kuwa mey Habib Albib? Wani abun ne?"
"Anya babu ajiya na anan?" Ya tambayeta had'e da aza hannunsa kan cikinta wani kunya maras misaltuwa taji ya rufeta "Kai Yaya" nan ta shiga kare fuskanta.
"Seriously naga kin k'ara freshness ne ai skin naki se wani glowing yake."
"Toh Yaya naje k'asa me tsarki ba dole ba ko ka manta kwanana na hud'u kacal daga dawowa daga Saudiyya?"
"Ina sane kawai de ina tambaya ne."
"Toh ka kwantar da hankalinka ba komi anan" ta fad'a tare da aza hannunta akan nasa dake manne da cikinta.
"Kai Kitten kode 6oye mun kike ne?"
"A dalilin mey zan 6oye maka Habib Albi?"
"Toh yaushe rabon ki da kiga period naki."
"Ni bana son tambaya" ta fad'a tana neman mik'ewa hannunta yayi saurin ja "Ai sai kin amsani."
"Yaya mana hannu na" saketa yayi a hankali "So answer me."
"Yaya jiya fa nayi wankan sallah."
"Kitten k'arya kike mun ko?"
"Yaya na ta6a maka k'arya ne?" Ta maraice fuska.
"Toh shikenan very soon nasan seed d'ina zeyi germinating."
"Muje kaci abinci toh."
"Yauwa Nazeefah tace in fad'a miki ta sama muku masu aiki tunda kun kusa komawa school kar aikin gida yayi interfering muku da school."
"Mey aiki kuma Habib Albi?"
"Yes haka tace."
"Na mey? Ni bana buk'atan mey aiki da safe kafin in fita school zan iya kammala aiki na, ranan da nake da lectures 7 kuma idan na dawo gida se inyi abu na."
"Gajiyan baze zo ya miki yawa ba Kitten I think shawaran Nazeefah fa yayi mey aikin zata taimaka miki kinga kafin ki dawo daga school ta gama miki komai kika dawo girki kawai zakiyi ki huta."
"Habib Albi ni gaskiya bana so."
"Toh yanzu ya kenan? Ince wa Nazeefah bakiya so? Ai bazata ji dad'i ba tunda har tayi wa mutanen magana kuma tun daga k'auye tace za'a kawo su."
"Kyansa dama ta tambayeni ko kai kafin tayi musu maganan."
"Hakane amma ai ita bata d'au zaki k'i taimako ba."
"Ba wani nak'i bane Yaya kawai ina ganin bana buk'ata ne."
"Zaki buk'ata fa Kitten keda kike yin tough course aikin gidan zezo yayi miki yawa."
"Toh shikenan tunda kaima ka goyi bayan hakan."
"I'm sorry if I'm forcing you into this kinsan halin Nazeefah ba sena fad'a miki ba kina k'i yanzu zata ce bakiya appreciating effort nata ne ta fara k'ananun suratai kawai kiyi hak'uri ki amince shine kwanciyan hankalinmu duka. Bazan 6oye miki ba ko ni banji dad'in yadda seda ta gama komai sannan ta sanar dani ba amma haka nima nayi hak'uri."
"Hakane kam ba komai zan kirata inyi mata godiya."
"That's by Babeh let's go eat toh I'm craving for your delicious already." Hannunta acikin nasa suka nufi dining suka ci abinci ba da dad'ewa ba Maghrib ya shiga ita kad'ai tayi nata kasancewar Afzal ya soma fita Masallaci yanzu.
Washegari***
"Ya Babe shiru har yanzu? Cewan Rumaysa daga d'ayan 6angaren.
"Wallahi layin Ya Afzal nake ta gwadawa amma bai d'auka nakega suna meeting ne so nike in tambayesa izini kamin in fito."
"Toh ina jiranki." Kashe wayan tayi 10 minutes later ta sake trying numban Afzal amma still baya d'agawa. Se chan k'arfe uku taga call nasa na shigowa da hanzari ta d'aga.
"Babe ina ka ajiye wayanka?"
"I'm sorry meeting muke se yanzu muka fito ya akayi?"
"Izini nake son nema zani gidan k'awata."
"Toh bismillah go ahead you're permitted."
"Thank you Ya Rouhi."
"Aha bye." Dama ashirye take key'n motarta ta d'auka kawai ta fice chan gidansu Rumaysa ta wuce inda ta nuna mata 'yan matan. Bayan sun gaisa Rumy ke tambayarta "So wacce zaki d'auka?"
"K'aramar kai ai babban zata fi mana harka da kyau senu kaiwa Amal babban."
"Toh Hindu ga Aunty'nki Nazeefah ita zata d'aukeki aiki ke kuma Safiyya zamu kaiki wa amaryarta" kai duka suka gyad'a "kina iya tafiya ko Hindu na?" Cewar Nazeefah "Bari muyi magana da yarki" ba musu ta mik'e ta fice.
"Yauwa kaman yadda na fad'a miki wannan itace Aunty Nazeefar itace wacce mukeso ki bamu had'in kai dan fitar da shegiyar da ta aure mata miji."
"Duk abinda kukace shi za ayi Aunty."
"Yauwa Sofin gaye ga waya nan Aunty Nazeefah ce tace a sai miki za kuna waya da ita ta ciki koda wasa kuma kar kiyi saving lambarta saboda ba'a san yadda abu ze zo ya kasance ba da kinga lamba me 08102 toh nata ne kin gane?"
"Na gane."
"Good kuma kina yi mata ladabi da biyayya kinji?" Nazeefah ta kar6e Rumaysa "Sunanta Amal amma Aunty zaki na ce mata duk aikin da takeso a gidan kinayi mata shi ba ruwanki da yi mata sata, duk abinda kikeso ki kirani zan baki kina ji na ai?"
"Eh Aunty."
"Yauwa zuwa gobe zan zo in d'aukeki da 'yar uwarki in kaiki gidan nata."
"Toh Aunty."
"Rumy ta fad'a muku albashinku ko?"
"Eh dubu goma."
"Yes sannan naki zanna k'ara miki extra dubu goma akai ko wani k'arshen wata idan har zakiyi mun aiki me kyau zuwa lokacin da zan samu in cimma burina."
"Toh Aunty godiya nake."
"Yauwa bayan nan kuma ko k'anwarki ce karki sanar da ita, wannan magana ya rage sirri a tsakanin mu kin gane?"
"Na gane Aunty."
"Toh Babe barin koma." Har waje Rumy ta rakata sannan ta dawo ciki.
Washegari kaman yadda suka tsara Nazeefah tazo ta d'aukesu gidan Amal suka fara wucewa lokacin Afzal ma bai gida ya fita office. Sannu da zuwa Amal tayi musu ta shigo dasu "Bari in d'auko muku ruwa."
"A'a 'yar uwa (yadda take kiran Amal) karki damu ai daga gida nake wannan ne masu aikin zan d'au k'aramar in baki babban tunda daman ke yayata ce."
"Kai Nazeefah ai kece babba a gidan nan."
"Toh nide zan d'au k'aramar Hindu ke kuma babban Safiyya."
"Toh Safiyya sannu da zuwa:"
"Yauwa Aunty nagode."
"Safiyya ban da rashin kunya kinji ko? Yi kinyi bari kin bari."
"In shaa Allah Aunty."
"Toh bari zamu wuce gida muma."
"Toh kin shigo da kayakin ki duka ko?" Amal ta tambayi Safiyya.
"Eh Aunty" ta amsa.
"Toh bari mu raka ku" nan suka rakasu har gun mota bayan sun dawo ciki Amal ta kai Safiyya d'akin data bata wanda zata na kwana aciki. D'aki ne harda bayi aciki ga gado da drawer harda dressing mirror. Yadda ake kunna shower da kuma yadda ake flushing ta nuna mata sannan ta bata waje ta watsa ruwa.
Bayan Afzal ya dawo daga aiki ya watsa ruwa ya d'an huta take sanar da shi akan cewa Nazeefah ta kawo mata mey aiki d'azu "Bari inyi mata magana ku gaisa."
"Ko gobe ma baza mu gaisa bane Kitten?"
"Toh ai kana fita office da wuri bari de ku gaisa yanzun lemmi speak with her" Nan ta mik'e, tare suka taho da Safiyya tana binta a baya daga baki bakin parlourn ta tsuguna ta gaishe da Afzal cike da ladabi da biyayya, shima ba yabo ba fallasa ya amsa.
Washegari bayan Amal ta shirya Afzal office ta dawo ciki ta koma bacci se wajajen goma ta tashi, wanka tayi tasa kaya sannan ta fito da mamaki ta tsaya tana bin parlourn nata da kallo yadda Safiyya ta share tayi mopping, dining ta zarce nan ma ko ina sparkling yake. "Wow!" Ta furta wai ita da take shirin koya mata yadda zata na yin aikin?
"Safiyya!" Ta k'wala mata kira.
"Safiyya!"
"Na'am Aunty" ta amsa tana shigowa ta k'ofar kitchen. "Ina kwana?" ta tsuguna ta gaisheta.
"Lafiya kin tashi lafiya?"
"Lafiya k'alau Aunty."
"Sannu da aiki ga ko ina yayi kyau."
"Nagode Aunty Tv'n ne banso in goge ba kar in ta6a wani abun."
"That's so thoughtful of you, zan gwada miki da kaina amma kafin nan kin karya?"
"A'a tukuna."
"Toh bari in shirya mana breakfast" nan da nan suka shiga kitchen d'in Safiyya tana tayata, bayan sun gama tayi wanke-wanke sannan Amal ta nuna mata yadda zata na goge TV da stand d'insa. Bayan sun gama Amal ta sallameta ta wuce d'akinta. Tana cikin buga game a wayarta Nazeefah ta sa mata kira nan ta d'aga tare da kashe muryarta yadda ba waje baze jita ba.
"Assalamu Alaikum Aunty."
"Wa'alaikumus salam Safiyya ya kike?"
"Lafiya Aunty ina kwana?"
"Lafiya k'alau ya wajen aikin naki? Ba wata matsala ko?"
"Babu komai."
"Ta baki abun karin kumallo?"
"Eh flask d'in ma ta ajiye mun a gaba na wai in d'iba da kaina."
"Mak'ira kawai, ke kika shirya wa Ya Afzal breakfast ko ita da kanta?"
"Ita da kanta nace zan tayata tace zatayi da kanta inje in kwanta."
"Mak'ira mey ta girka masa?"
"Dafaffen dankali ne da sauc da wani abu kaman nama nama aciki."
"Lallai aikin ki na kyau kwanan nan zamu fara aikinmu akanta kede ki tabbata kina mata duk wani ladabin da ya kamata."
"Toh Aunty."
"Yauwa karki manta kina goge lamba na daga call logs naki duk sanda muka gama waya."
"Toh Aunty ki gaishe mun da Hindu."
"Tana bacci idan ta tashi zan sanar da ita sai anjima."
"Yauwa nagode" da haka sukayi sallama.
RANA D'AYA!
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
23 comments:
Nazeefs adai guji zuwa rafi don Wanda yake tare da Allah ya wuci vaban wasa. May Allah continued to guide you with a lot of basira.
Tnx dear pls try and update in time.
Mukam dae bamu abnda akema nazeefa gsky.....bama team Amal ..zamanin ynxu ba'a biye qawaye.. Allah ya Kara baseera
Kuma gaskiya kikafadi don yanzu idan ka bite was kawa zata kaika ta baroka don wata kawar tana jin haushin abinda mijinka take maka don it's mijin NATA baya biya mata dukkan buka tunta.
Kuma gaskiya kikafadi don yanzu idan ka biye wa kawa zata kaika ta baroka don wata kawar tana jin haushin abinda mijinka yake maka don ita mijin NATA baya biya mata dukkan buka tunta.
Wae nikam Nazeefa da Amal ba sisters bane...nidae bana son afzal da amal gsky... Miemie Allah ya kara baseera... Amma fa idan ubansu daya kome ya kwabe'RANA DAYA' nasan ana iya kashe nazeefa wayyo Allah na gashi kuma ni nafison wurin wollah
Sannu miemie da kokari... Ashe bani kadae ke nazeefa ba.. Tab gsky kam idan babansu daya akwae mtsala.. Muna gdia... We really appreciate your efforts cous u try to update daily gsky munji dadi
Finally..... I have been trying to post comments but i didn't get the procedure until now... We really love the write up.. Yehh ashe bani kadai bace amal bata burgeni
Hhhhhh nidai amal nakeyi thanks miemie
Osheey miemie! Uhm uhm fa Nazeefah ayi dai a hankali
Assalamu-alaikum
Don Allah miemiebee pls am interested to join ur WhatsApp group ,don Allah a taimakeni here are my digit 08022841445 ,pls I beg ur pardon
Mudai muna team amal😁
Team amal all the way
Uw in shaa Allah
Lol 😂 bari muga yadda za a kaya
Ameen you're welcome 😊
Lol Amal nada makiya haka dama?
You're welcome 😊
Ai kuwa dai
🙌🙌
🙌🙌
Sis I seem not to find this number on whatsapp check it carefully
Team amal all the way! Allah ya kara basira Aameen🤗😉💞
Team amal. In Baban su daya kawai ya zaba amal. Tunda nazeefa makira ce
Post a Comment