Friday, 10 August 2018

RANA D'AYA!

BY MIEMIEBEE
PAGE 33



   Se yamma Amal ta dawo gida bayan sun k'are karatu da Maamah. Driver na sauk'eta ta zarce d'akinsu inda ta tarar da Afzal yana shirin komawa gun Nazeefah ko sannu da zuwa beyi mata ba hasali yi ma yayi tamkar be ganta ba. Itace tayi gyaran murya ta gaishesa tukun ya amsa sama-sama.
  "Zan koma gida gun Nazeefah ga kud'inki ajiye a gaban mirror" ya sanar da ita.

  "Habib Albi tun yanzu zaka tafi?" Ta tambayesa tana mey duban agogo dududu 5:17 ne amma yake zancen nan bayan se pass 6 yake tafiya kullum.

  "Eh wani abu ne?"

  "Habib Albi ko ka mance da alk'awarin da kayi mun?"

  "Na mey fa?"

  "Kace kafin ka tafi zamuyi wanka tare I miss bathing with you Habib Albi, I really do" tayi admitting abun tausayi. Kau da kansa yayi gudun kar tausayinta ya kama sa.

  "Nata jiranki baki dawo ba Amal ni kuma sauri nake maybe next time."

  "Abinci fa kaci? Nasa Safiyya ta maka microwaving sauce d'in ta dafa maka white rice tayi?"

  "A k'oshe nake karki damu na wuce."

  "Yaya" ta kira sunansa da sauri lokacinda ya shiga takawa chak ya tsaya had'e da kewayowa.

  "Wani abu ne?" So take tayi masa magana kaman yadda Maamah tace da ita amma inaa bata jin zata iya, mugun nauyinsa takeji bata son a sanadin hakan yaga kaman rashin kunya take son yi masa don haka kawai tayi shiru. "Sauri nake" ya sanar da ita.

  "Ermm nace Allah dawo da kai lafiya ka gaishe da Nazeefah idan ka isa."

  "Kaman dagaske" ya furta chan ciki-ciki.

  "Na'am?" Ta tambaya kasancewar bata jisa da kyau ba.

   "Nace naji" da haka ya fice Allah kare Safiyya dake sharan parlour tayi mishi sannan ya k'arisa.

   Safiyya na ganin fitansa tayi hanzari ta kammala sharan nata da wuri ta wuce d'akinta inda tasa key ta danna wa Nazeefah kira bayan sun gaisa take ce mata, "Aunty bazaki amince da abinda nake shirin fad'a miki ba."

  "Mene meya faru?"

  "Hmm yanzun Uncle ya bar gida toh kafin ya fito ina cikin share corridon d'akinsu naji su suna magana da Aunty."

  "Wai mey suke cewa?"

  "Nide ban gane kan zancen nasu ba amma naji tana ce masa wai yayi mata alk'awarin zasuyi wanka tare se gashi kafin ta dawo daga makaranta har yayi wankansa ya gama shiri."

  "Wanka tare?!" Nazeefah ta tambaya da d'umbun mamaki "Wanka tare de?" Ta sake nanatawa yayinda ta kasa amincewa da hakan.

  "Wallahi Aunty."

  "Kaiiii inaaaa! Baki ji su da kyau ba, wannan k'arya ne."

  "Wallahi na jisu da kyau Aunty kuma daman tun ba yau ba ina zaton hakan dan akwai ranan da abokin Uncle yazo Uncle Sultan se yace inje inyi ma Uncle magana toh dana k'arisa d'akin nasu sena tarar da k'ofan a bud'e nayita sallama amman shiru chan dana kasa kunne najiyo hayaniyansu acikin bayin."

  "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un wallahi Amal mak'ira ce, shegiya 'yar asiri toh dan ubanta bazeyi wankan ba kiji mun karuwanci fah! Wato har wanka ma sukeyi tare? Chab!"

  "Hmm wallahi ko amma kuma kinsan tun dawowan Uncle wannan karan ko fita sau d'aya basuyi ba? Jiya kanma da tayi masa breakfast k'in ci yayi yace wai nice zan yi masa baya son nata. Bayan nan zama da sukeyi a parlour suyi kallo ma basuyi yanzu gashi banda d'ad'd'aure mata fuska ba abinda yakeyi yau tana da makaranta da safe amma yak'i kaita sa6anin kullum yace se de driver ya kaita shi yana da gun da zasa. Maganan da nake miki yanzu ko tsinke ban ga ya siyo mata ba tun zuwan sannan."

   "Ai kibari kad'an ta gani da izinin Allah se Ya Afzal ya tsani taka k'afa acikin gidanta kede kiyi k'ok'ari ki sato min littafin makarantar ta guda d'aya mu samu copy na handwriting nata, zata gani ba har wanka sukeyi ba? Allah kawo shi gida."

  "Zanyi k'ok'ari in samo miki bari in gudu ina kan aiki."

  "Jeki Safiyya aikin ki na kyau se anjima."

  "Toh se anjima" da haka sukayi sallama.

   Fresh flowers Afzal ya tsaya ya amsa mata a florist shop sannan ya k'arisa sede har ya shigo parlourn bata mik'e tayi masa sannu da zuwa ba ko sallamansa ma k'in amsawa tayi. Da mamaki kwance a fuskansa ya k'arisa kan kujerar da take zaune ya zauna daga gefe.

  "Rabba'atul Bait I'm home" ya sanar da ita.

  "Sannu da zuwa" tace da shi zalla ba walwala tattare da ita.

  "Rabba'atul Bait what's wrong?" Hannunta ya gwada rik'ewa wanda tayi saurin wabcewa "Sweetheart please talk to me keda nake marmarin in dawo wajenki saboda ki cire min bak'in cikin da 'yar uwarki ta cusa mun kuma kike haka? What have I done this time?"

  "Ai mey hali bai ta6a fasawa amma nagode." Cike da rashin fahimta ya tambayeta "Mey kike nufi Rabba'atul Bait please talk to me."

  "Ni de wallahi na gaji bazan iya ba da rashin mutuncin nan da tokari tunda baka sona kawai ka sallameni in tafi gida gun Mummy yaso ka cigaba da sha'aninka da amaryarka."

   "Wani irin magana kuma kike haka Rabba'atul Bait sanin kanki ne ina sonki kuma bazan iya rayuwa ba ke ba."

  "Wallahi baka sona Ya Rouhi" ta fad'a tana cika idonta da hawayen munafirci.

  "Please don't cry darling."

  "Ka daina kira na darling tunda ba sona har zuciya kake ba, idan da har ka d'auke ni da muhimmanci kaman yadda na d'auke ka da Amal baza tana kirana tana mun gori ba."

  "Amal?"

  "Eh ita."

  "Oh Dear! Mey wancan ta kira kuma ta sake ce miki? Wallahi we're not on good terms with her girkinta haka ban d'ana ba tun zuwa na, mey tace miki?" Ya tambayeta ransa na 6aci.

  "Ni baza ka ji komai daga bakina ba har ga Allah bazan so in had'a kanku ba amma de ka cigaba wallahi ranan da komi ya isheni tattara kayakina zanyi in koma gida inyi ma Daddy magana asan ya za'ayi tunda gashi a fili ka nuna baka sona kuma baza ka iya yin adalci a tsakanin mu ba. Ka nunawa Amal ni ba kowa bace banida daraja a idonka idan ba haka ba taya zata na kira na tana gaya mun magana iya son ranta?"

  "Nazeefah please calm down ke kanki kinsan I'll never do this to you, I love and respect you alot, dan Allah ki daina magana haka kiyi hak'uri mey yayi zafi da zakice zaki koma gida? Believe me duk abinda Amal ta kira tace miki nayi mata wallahi k'arya take don ko tsinke ban sai na bata ma tun komawa na."

   "Ai idan da har ba kayi mata abubuwan dagaske da koda wasa bazata kira tace mun gashi ba nasan ba k'arya take mun ba."

  "Ni ke miki miki k'aryan kenan Rabba'atul Bait? Please tell me what is it that Amal told you."

  "Ka kirata ka tambayeta da kanka ni bazan had'a kanku ba."

  "Ita d'in ba so take ta had'a kanmu ba take kiran ki take miki k'arerayi a waya? Please tell me."

  "Dan tamun haka nima senayi mata? Ai ko addini cewa yayi karka sak'a wa mutumin da yayi maka sharri da sharri Allah ma shaida ne ni da zuciya d'aya na d'auki Amal amma ita kam ba haka bane."

   "Rabba'atul Bait wallahi ba k'arya nake miki ba I and Amal aren't even speaking to each other ko tamun magana shareta nake saboda na gaji da kalan abubuwan da take yi miki, I'm tired."

   "I'm not buying any of your lies again Ya Rouhi zaka ce mun bakuwa magana da Amal bayan d'azun nan na kirata dan mu gaisa take ce min kana jiranta a tub zakuyi wanka tare."

  "Amal d'in?"

  "K'arya zanyi maka ne?" wayanta ta janyo ta shiga call logs ta nuna mai wayan da sukayi da Amal d'in. Kuma tabbas ta kirata d'azu sun gaisa amma bawai Amal tayi mata magana makamancin haka ba.

  "Innalillahi!" Ya furta cike da tashin hankali "Wallahi tallahi k'arya take yi miki Nazeefah-"

  "A'a Ya Afzal" tayi saurin katsesa "Karka 6ata lokacinka, ba seka mun bayanin komai ba na riga na fahimceka na sani kafi son Amal akai na dama idan ba ni da shashanci bama taya zan had'a soyayyan da kake mun da wacce kake yima Amal ita da take matar so a gareka bayan ni auran had'i akayi mana? Ni abu d'aya nake buk'ata kawai ka sawwak'e mun in koma gida bazan iya ba da wannan walak'anci da cin fuska" ta k'are tare da rushewa da kuka. Sosai ransa ya mugun 6aci yayinda wutan tsanan Amal ke sake ruruwa a zuciyarsa. Gabad'aya ji yayi ta fita masa a rai, amma ko tana tattare da babban asara.
   "Rabba'atul Bait" ya kira sunanta cike da tausayi yana mey k'ok'arin rungumarta sede tayi saurin janye jikinta yayinda ta cigaba da kuka.

  "Nazeefah dan Allah kiyi hak'uri kibar kukan haka I'm dearly sorry."

  "Ka rik'e hak'urinka Ya Afzal ba laifinka bane don zuciyarka ta fi kwanciya da Amal akai na, ni kawai ka sawwak'e mun zey fiye mun kwanciyan hankali idan ina gida gun iyayena."

  "Please don't talk like this wallahi k'arya Amal take yi miki you have to believe me" a hankali ya janyota jikinsa yana hugging nata "Idan kika tafi wa ze zame Rabba'atul Bait d'ina? Please stop crying I love you and you know it isn't that all that matters Sweetheart? By Allah duk abinda Amal ta ce miki nayi mata k'arya ne ki yarda da ni" be d'agota ba seda tabar kukan munafircin nata. Hak'uri yayi ta bata ranan throughout chan dare da yazo yin wanka yace suyi tare Nazeefah tana so tana kaiwa kasuwa wai ita baza tayi ba. Lalashinta yata yi har seda ta amince suka shiga bayin wasa suka yita yi sannan sukayi wanka a k'arshe ya sanyata sukayi alwalan bacci kaman yadda Amal ke tunasar masa kullum. Da kansa ya sanya mata kayan baccinta sannan suka kwanta inda yata tattalinta yana mata wasu irin abubuwan da tuni yasa ta fita daga hayyacinta. Wani irin so na musamman Afzal ya shiga nunawa Nazeefah na d'an kwana biyun da sukayi, ji yayi kaman kada ya tafi da kwanansa ya k'are sam baya sha'awan komawa gun Amal gabad'aya ta fita akansa da abubuwan da takeyi.

  "Ya Rouhi har six baka fara shirin tafiya ba ka manta yau kwanan ka ya k'are anan?"

  "Ba se gobe ba?"

  "Gobe kuma? Da Allah ka tashi ka shirya kar mu shiga hak'k'in Amal."

  "She can wait se bayan Maghrib zan tafi."

  "Ni baza ayi rashin adalcin nan da ni ba gaskiya."

  "Tashi ka shirya Ya Rouhi."

  "Zo ki d'agani toh."

  "Ni da kai wa ze d'aga wani?"

  "We wouldn't know until you give it a try so zo ki d'agani" bata sake musu ba ta k'arisa kan gadon. Hannun sa ta kama ta shiga ja sede ko motsawa baiyi a lokaci d'aya ya jata bata sauk'a ako ina ba se akan jikinsa inda sukayi gware.

  "Awch!" Ta furta tana murza goshin nata "Ya Rouhi!" Tayi exclaiming.

  "Toh ai na fiki jin zafi."

  "Tayaya?"

  "Ba goshinki yafi nawa tudu ba."

  "Wallahi k'arya ne banida goshi" ta fad'a had'e da kai masa bugin wasa a k'irji.

  "Mu gwada ne?" Yace yana mata dariya.

  "Ban sanin ba ni ka sakeni" ta fad'a tana k'ok'arin mik'ewa, kankameta ya sakeyi a jikinsa tare da placing mata kiss a gefen baki hannu tasa ta dirje ita a dole tayi zuciya yace mata mey goshi at once yayi flipping position nasu ya zammana shi a sama ita a k'asa.

  "Babe you're the most beautiful girl I've ever seen."

  "Ba wanin nan nice mey goshi ba? Tashi ka barmun gida jeka samu amaryarka."

  "Haba Rabba'atul Bait idan kika koreni gun wa zanje?"

  "Amal mana of course."

  "Nifa nace ki daina kawo mun magananta."

  "Nide d'agani."

   "Haba my beautiful Rabba'atul Bait" yayi maganan had'e da matso da fuskansa gab da nata yayinda ta zagaye hannayenta a wuyansa "I love you Babe" ya sanar da ita.

  "I love you too Darling" a hankali ya sauk'e lips nasa akan nata ya shiga kissing nata yayinda take miyar masa da martani kaman wasa suka fara wuce gona da iri kafin su hankara har sun wula wani duniyan daban. Bayan sun gamsar da juna suka yi wanka tare Nazeefah na mik'e akan gado tana kallon Afzal cike da adoration da soyayya yayinda yake faman neman kayan da ze sa a wardrobe. Wayansa dake kan gado ne ya shiga ruri ko motsawa Nazeefah dake kan gadon batayi ba ina irin ita ba ruwanta da yi mai shisshigi d'innan shi da kansa yace "Who's calling?"

  "I don't know" ta mayar masa tana gyara d'aurin towel nata.

  "Duba" ya umarceta. Lek'awa tayi taga Kitten❤️💍🔐 na flashing akai ga picture'nsu da yayi saving contact natan dashi wani selfie'nsu ba hassada sunyi kyau.

   "Amal ce" ta amsa tana k'ok'arin 6oye kishin daya rufeta lokaci guda "Ayya taji shiru."

  "D'aga kice mata idan nayi sallah zan shigo."

  "Ya Rouhi kana ganin yin hakan ya dace?"

  "Toh ki bari seta ga shigowa na kawai" ya amsa tare da juyawa yana mey cigaba da neman abinda ze sa. Bada dad'ewa ba sega Amal na sake kira wayan ta d'aga tayi answering had'e da yin shiru.

  "Halo Habib Albi?"

  '"Yar uwa Nazeefah ce" ta sanar da ita.

  "Oh Nazeefah, ina yini?"

  "Lafiya k'alau, kinji Ya Afzal shiru ko? Yana hanya abu ne ya rik'esa."

  "Ayya ba komai seya shigo toh."

  "Aha seda safe" da haka sukayi sallama sauk'e wayan tayi tana ma Afzal murmushi yayinda shima ya miyar mata yana mey mamakin hali irin na Amal ace duk yadda Nazeefah ke sonta har take kirarta da 'yar uwa amma se tana kiranta tana irga mata ababen da tasan zasu 6ata mata rai. Seda sukayi sallan Maghrib sannan Afzal ya tafi yau har doubling kud'in daya saba ajiye musu yayi wa Nazeefah ita kam dad'i kasheta she can't wait ta gama aikin ta akan Amal ta fiddata daga gidan finally.

  Yana isa gida Amal ta bud'e k'ofa tayi masa sannu da zuwa tana cewa bari tayi hugging nasa yaja da baya. Dama a cike take dam tunda ta kirasa taji Nazeefah ta d'aga wayansa gashi yau se bayan maghrib ya shigo abinda be ta6a yi ba. Kuka kawai ta rushe da sede da mamaki taga ko d'aga kai Afzal beyi ba bale yasan tanayi. "Excuse me" yace da ita yana neman wuceta hannu tasa ta dakatar da shi.

  "Yaya mey nayi maka haka ka za6i kana shareni kana wulak'anta ni a gidan nan? Idan wani laifin nayi maka dan Allah ka fad'a mun a shirye nake da in baka hak'uri" ta sanar da shi cikin tsan-tsan kuka. Shi dariya ma ta basa bayan duk rashin hankalin da take tafkawa still tana da bakin da zata tambayesa mey tayi? Lallai she thinks she's smart. Kallonta kawai ya tsaya yi ko uffan bece mata ba.

  "Yaya please talk to me I can't do this anymore yau kwana nawa idan ka shigo mun sede kayita d'aura mun fuska, ka daina cin girki na, d'an gifts da ka saba siyo mun ka daina, ka daina kwanciya da ni yanzu ko jikinka kana neman hanani ta6awa baka tunanin hukuncin nan da ka yanka yayi tsauri dayawa?"

  "Yayi tsauri fa kikace Amal? I'm truly disgusted at you I never expected this from you how could you stoop this low? Tell me mey kikayi benefiting da wannan abun kunyan da kikayi mun kika kuma yi wa kanki?" Ya tambayeta cike da tsiwa. Hawaye take sosai yayinda kanta ya d'aure shin mey yake fad'i? Wani abun kunyan tayi masa?

  "Yaya wani irin magana kakeyi? Wani abun kunya nayi maka please talk to me ban fahimce ka ba."

  "Ai dama baza ki ta6a fahimta ta ba Amal you know what? I don't have time for this idan kinsan k'arya zaki tsaya kina mun just forget it."

  "Yaya dan Allah kar kayi mun haka I beg of you wallahi ba k'arya nake maka ba" ta rok'esa cikin tsananin kuka.

   "Ohhh itace take k'arya kenan?"

   "Ita wa?"

  "Seriously Amal? Har tambayana kike ita wa? Kin d'au magana baze zagayo kunne na bane? Kede ki cigaba."

  "Wallahi ban fahimceka ba Yaya bansan akan mey kake magana ba kuma a iya sani na ban yi maka wani abun ba sede ban sani ba ko a bisa rashin sani yet still zan baka hak'uri dan Allah kayi hak'uri ka rage wannan hukunci wallahi yayi mun tsauri dayawa Yaya can't you see? I'm slowly losing my mind and going crazy fushinka a gareni ba k'aramin tashin hankali bane please kayi hak'uri ka gafirceni I'm dearly sorry."

  "Idan ba kiya son ina fushi dake se ki iya bakinki ki koyi rik'e sirrin gidanki ki dena buga waya tako ina kina irga wa mutane abinda mijinki yake miki, how could you Amal? I thought kina da hankali kuma kinsan abinda ya kamata ashe ba haka bane, wallahi ba halin ki bane ban san ki da halin nan ba."

  "Ni Yaya? Wa na kira na sanar dashi sirrin gidan nan? Wallahi ban buga wa kowa waya ba ko Mami."

  "Kiji I don't have time to listen to your lies because a sane nake da komai don haka ba abinda zakice da zaisa in amince dake I've heard enough and I'm very disappointed with you ban ta6a sanin kina da wannan mumunan hali ba amma ki cigaba ni bazan miki baki ba sede inyi miki fatan shiryuwa idan ma k'awaye kike bi suke rud'anki suke d'aura ki akan gur6arcacciyar hanyan nan gara tun wuri kin rabu da su ina Safiyya!" Nan Safiyya dake lek'ansu ta koma cikin d'akinta a 360 seda ya sake kiranta a karo na biyu sannan ta fito tana wani hamma irin bacci takeyi ya kirata d'innan.

  "Ina yini Uncle?" ta gaishesa.

  "Lafiya ki dafa mun indomie biyu da k'wai biyu kiyi sauri I'm hungry."

  "Akwai abinci fah Rice and Stew Aunty ta girka."

  "Ina sane ai nace ki dafa mun indomin."

  "Toh" da haka ta wuce kitchen d'in wani pathetic look ya bawa Amal ya wuceta ya shige d'akinsu. Har k'asa ta sauk'a tana kuka wajen gabad'aya ta rasa mey ke mata dad'i sam bata da masaniya ga abinda Afzal yake cewa mey yake nufi da ta daina kiran mutane tana yad'a musu sirrin aurenta a ina tayi hakan? Ita da ko da iskokai suka shafeta ma bata kira Mami ta sanar da ita ba wani sirri yake nufin tana yad'awa idan akwai mutumi d'ayan da ta mar maganan aurenta itace Maamah kuma ta yarda da Maamah tasan Maamah baza ta ta6a ci mata amana ba. Kuka tayita sha wajen har zuwa lokacinda Safiyya ta gama abincin Afzal ta ajiye masa kan dining gun Amal ta k'arisa ta durk'usa.

  "Aunty kiyi hak'uri dan Allah ga abincin Uncle yayi."

  "Kije kice mishi ya fito."

  "Da kaina?" Kai zalla ta gyad'a mata nan ta wuce bayan tayi mar sallama ta sanar dashi ta gama godiya yayi mata sannan ta dawo kan Amal tana cigaba da bata hak'uri kaman dagaske.

  "Kije d'akinki Safiyya ba komai" haka Afzal yazo ya tarar da ita zaune a wajen, ko kallonta beyi ba ya k'arisa dining. Da k'yar ta tattara kanta ta koma d'aki Qur'ani kawai ta d'auka ta shiga karancewa shi kad'ai take jin ze iya rage mata wannan k'unci da bak'in cikin da takeji. Bayan Afzal ya gama cin abinci yazo shiga d'akin yaji sautin karatunta na tashi, na d'an lokaci ya tsaya ya saurareta sannan ya koma parlourn ya cigaba da zama be sake kewayowa d'akin ba se da ya tabbata tayi bacci wajajen sha d'aya kenan. Tsince akan gado tana bacci ya tarar da ita da alama karatu take bacci ne ya d'auketa don ga handouts nata baje a gabanta, Jallabiyan jikinsa ya tu6e sannan ya tattare handouts d'in ya ajiye a gefe ya gyara mata kwanciyan nata ya haura ya kwanta daga chan gefe shima had'e da kashe musu wuta.

   Haka ya cigaba da d'aga mata kai yana shareta, washegari Amal tayi kuka har ta godewa Allah test da ta rubutan ma dukda cewan tayi karatu batazo ta gane mey ta rubuta ba saboda gabad'aya ba hankalinta a jikinta.

   "Amal kiyi hak'uri haka kukan nan ba shida amfani" fuskanta daya kumbura tim ta d'ago daga kan benchi tana share hawayenta "Maamah a rayuwa ba abinda na tsana kuma yafi k'ona mun rai kaman banyi abu ba ace nayi fisabilillahi ko ke na ta6a sanar dake sirrin gida na ne in ba wannan karan da matsaloli suka yi mun yawa ba?" Kai Maamah ta kad'a mata a hankali cike da tausayi "Amma cemin yayi wai ba aiki na se buga waya wa mutane ina sanar dasu sirrin gida na harda wai ya d'au ina da hankali ashe babu duk na munafirci ne Yaya fa Maamah, Yaya yake kwatantani da wannan munanan kalamu" ta sake rushewa da wani kukan.

  "Amal ki kira Mami ki sanar da ita kawai taya Ya Afzal ze miki haka ina laifin ma ya sanar dake laifin da kika yin amma haka kawai ya barki acikin duhu ai ba yi bane hakan."

   "So kike ya gama tsanata idan na sanar da su Mami? Ban kira kowa bana yace ina kiran waya ina yad'a sirrin gida na bale har in kira Mami? Hmm ashe ina tona kabari na da kaina kenan."

  "Toh ya zakiyi Amal? Ni anya kuwa ba kishiyarki bace take neman had'a kanki da Ya Afzal?"

  "Nazeefah wai?"

  "Sosai ma kiyi tunani mana mey yake nufi da yace miki ita take k'aryar? Nazeefah yake nufi."

  "Da wuya idan itace I trust Nazeefah bata da wani mugun hali kuma kinga ita bama zuwa gida na take ba bale ace taga wani abun taje tayi mai gulma."

  "Don't get too confident trusting her Amal wallahi halin mutum se Allah idan ba haka ba waze shiga tsakaninki da Ya Afzal haka?"

  "Maamah ban sani ba amma zan cigaba da addu'a har se idan Allah ya amsa kuka na."

  "Toh Allah taimakeki ya shige miki gaba Amal shi kuma Ya Afzal Allah sa ya gano gaskiya ya sani cewa idan mutum yayi laifi confronting nasa ake bawai a rik'e shi a zuci ana k'untata mai ba."

**
  Washegari kasancewar Amal tana iya kai har yanma a school ta yi girkin rananta tun da safe kafin ta fita. Abinda Safiyya zatayi kawai tayi wa Afzal microwaving ne idan ya dawo daga office that is idan ze ci ma kenan tunda yanzu ya k'aura daga cin girkinta. Tun k'arfe sha biyu ya dawo gida yana shiga ciki yaga cup da snacks haka akan table sekace anyi bak'o sallama yayi Safiyya ta fito tayi mai sannu da zuwa.

   "Auntinki na gida ne?"

  "A'a ta fita school."

  "Wannan fah?" Ya nuna cup d'in "Kinyi bak'uwa ne?"

  "A'a Aunty ne ta shigo bada dad'ewa ba ita da wani."

  "Excuse me?!" Yayi exclaiming had'e da zaro idanunsa waje.

  "Yanzu suka bar nan."

  "Ita da wa?"

  "Ita da wani na miji suka shigo ta d'au wasu takardu suka d'an zauna se suka sake fita tace tayi mantuwa ne."

  "Amal ta kawo na miji gidan nan?" Sam ya kasa amincewa da hakan.

  "Ni na d'au ma ko d'an uwanta ne yadda suka zauna a kujera d'aya."

  "A kujera d'aya!?" Ya sake tambaya idanun nan kaman zasu fad'o a k'asa dan mamaki. Dan yadda zuciyarsa ta shiga k'ona ko k'ala be sake cewa da Safiyyan ba take idanunsa suka kad'a sukayi ja. Cikin wani irin taku ya k'arisa d'akin nasu kawai ji Safiyya tayi ya buga k'ofan wane yana neman 6allesa, d'aki ta koma jiki na rawa ta kira Nazeefah.

  "Aunty na aikata, kuma wallahi ya amince."

  "Kai haba!"

  "Bakiga yadda yake ta nishi ba kaman zaki."

  "Kinyi dai-dai ai in shaa Allahu kwanan Amal a gidan nan ya kusa k'arewa aikinki na kyau."

  Amal baiwar Allah da tun fitanta k'arfe sha d'aya se biyar ta dawo bata san meyake jirarta ba a gida. A galabaice driver ya dawo da ita tana shiga parlour ta tarar da Afzal zaune kan kujera ko d'aga ido beyi ba bale yasan mutum ya shigo gidan se harkan gabansa kawai yake itama bata yi mai magana ba sanin ko tayi ba amsata zeyi ba. Da mamaki ya bita da kallo wato ma ko magana baza tayi masa ba lallai rainin har ya kai haka? Bayan ta kawo masa k'ato gida ta dawo kuma bazata iya ce mai sannu ba, wuyanta ya kai yanka. Da abinda zata sak'a masa kenan duk kalan halaccin da yayi mata a rayuwa? Wajajen goma ya koma d'akin kwance akan gado ya tarar da ita a galabaice.

   "Kibar min d'akin nan kije ki kwana wani wajen" yace da ita zallah.

  Da mamaki ta tsaya kallonsa ashe Allah ze kawo ranan da zeyi mata gori akan abubuwan da yayi mata a rayuwa? Ko k'ala bata ce da shi ba ta d'au pillonta da waya ta bar masa d'akin bayanta yabi yayi locking k'ofar sannan ya dawo ya kwanta yana mamakin wannan sabon d'abi'artan wato ma tsabagen tasan halinta ta kuma san mey takeyi shiyasa ko a bakin zaninta bale ta tambayesa dalilin da ze hanata kwana masa a d'aki ba. Toh ta cigaba.

  Ta d'ayan fannin kuka Amal ta kwana tana yi bata jin zata iya da wannan walak'anci mey yayi zafi da ze koreta daga d'aki? Saboda bata kawo ko tsinke gidan ba? Da k'yar bacci yazo ya d'auketa. Kasancewar tana da morning lectures washegari bayan Asuba tayi wanka sannan ta wuce d'akin nasu dan d'auko kayan da zata sa sallama tayi jin shiru seta bud'e k'ofan amma bata gansa a ciki ba don haka kawai ta yanke hukuncin yana bayi ne. Wajen wardrobe ta nufa ta shiga fiddo da kayan da zata sa tana cikin hakan Afzal ya fito daga bayi ko juyawa ta kallesa batayi ba harkan gabanta ta cigaba da yi daga wajen wardrobe ta k'arisa gun mirror ta tattara man shafawanta da turare da sauran abubuwan da zata buk'ata ta fice. Binta da kallo yayi shima bece da ita ko k'ala ba. Tana gama shirinta tayi ma driver magana ko tambayan Afzal kud'in makaranta batayi ba sallama kawai tayiwa Safiyya ta fice. Yau ma kaman jiya Afzal ya riga Amal dawowa and thesame thing cup ya tarar a kan centre table da plate na abinci daya tambayi Safiyya still ta basa amsa irin na jiya akan Amal ce ta shigo da wani basu jima da tafiya ba. Na matuk'a ransa ya 6aci yau kam baya jin ze iya d'aukan rashin hankalin nata abun ya ishesa zama yayi a parlourn yana jiran dawowanta chan bada dad'ewa ba ta iso yau ma a galabaice. Kanta ta sunkuyar lokacinda ta shiga parlourn har ta kai ga wucesa ya kira sunanta chak ta tsaya had'e da kewayowa.

   "Wa kika kawo mun gidan d'azu?"

   "Mey kake fad'i Yaya?

  "I'm not repeating myself Amal wa kika kawo mun gida d'azu?"

   "Wa zan shigo maka dashi gida Yaya? A iya zama na da kai na ta6a shigo maka da na miji gidan nan ne? Why don't you believe me Yaya? Na d'au ko da an fad'a maka hakan bazaka amince ba saboda a tunani na kafi kowa sanin hali na, a tunani na kafi kowa sanin abinda zan iya aikatawa da abinda bazan iya ba I'm so disappointed with you Yaya" ta tsaya ta numfasa yayinda hawaye yake ciko mata a ido "Ina soyayyar da kake ikirarin kana mun? Ashe za a iya fad'a maka magana akaina ka hau ka zauna akai ba tare da kayi bincike akai ba?"

   "Stop acting like you're the Amal I used to know saboda gabad'aya kin canza, I can't trust you anymore Amal yau komin ya girman laifi yake aka ce mun kin aikata zan amince saboda I've lost my trust in you since the day kika fara d'iban sirrin gidan ki kina yad'a wa jama'a."

  "Allah ma shaida ne ban ta6a kwasan abinda kake mun a gidan nan na fad'awa kowa ba not even Mami" ta amsa tana share hawayenta.

  "Ki bud'e kunnenki ki saurareni da kyau ban yafe ba idan kika sake kawo mun wani k'ato cikin gidan nan."

  "Yaya please idan wani abun nayi maka ka fito fili ka fad'a mun amma ka daina cemun nayi abinda ban aikata ba, yaushe na shigo gidan nan tun fita na bale har in shigo da wani?"

  "Da ace ban shigo na tarar da ragowan snacks da drink da kikayi serving nasa bane se ki gaya mun maganan banza."

  "Drink? Wallahi ni ban kawo wani gidan nan ba ka kira driver ka tambayeshi ko ya dawo dani gida tun fita na da safe in ba yanzu ba."

  "You're not as smart as you think you're Amal and ki cigaba."

  "See Yaya idan gajiya dani ne kayi kawai ka fad'a mun I'll understand you it's too early for this, taya banyi abu ba ina ji ina gani zaka na mun sharri da fari kace ina kire-kiren waya ina baza sirrin gida na a waje yanzu kuma zargi na ka fara? Har kana tunanin kai na ya waye da zan fara kawo maka maza a gida? Wallahi a da koda wasa aka cemun zaka yi mun abinda kakeyi mun yanzu bazan amince ba amma ka cigaba dama nasani dole wataran zaka goranta mun tun da har ka iya ka koreni daga d'akinka jiya." Bata jira jin mey zece ba ta wuce d'akin data koma a guje. Kuka ta shigayi daga haka har ta fara yin amai, bata tsaya ba seda ta harar da abincin cikinta tas har jiri na neman d'ibanta. Da rarrafe ta k'arisa d'akin ta kwanta ahaka har wahalallen bacci ya d'auketa. Next da ta tashi Safiyya ke ce mata Afzal ya riga ya tafi kai kawai ta gyad'a mata har ta tashi zata tafi seta kira ta.

  "Na'am Aunty?"

  "Mey kika cewa Ya Afzal jiya da bana gida?"

 "Game da mey Aunty?"

  "Kinsan mey nake nufi ai."

  "Wallahi ban fahimce ki ba dan ni magana ma be had'ani da Uncle ba."

  "Waya ce mishi na shigo da na miji gidan nan?"

  "Na miji? Wallahi bani bace Aunty dan meyasa zan miki sharri? Wallahi bani bace."

  "Shikenan tashi ki tafi." Chan bayan sallan Isha ta fito kitchen dan had'a custards ta sha sanadin wani irin yunwan da ya dameta. Tana tsaye a kitchen tana jiran ruwan ya tafasa Safiyya ta shigo zata dafa indomie.

  "Ki d'au k'wai biyu ki soya" tace da ita.

  "Toh Aunty nagode" jiki na rawa ta bud'e fride d'in ko ya akayi kawai d'aya ya ku6uce daga hannunta ya fad'i ya fashe.

  "Subhanallahi! Ya akayi haka Safiyya?" Amal tayi saurin tambaya tana neman toshe hancinta.

  "Aunty dan Allah kiyi hak'uri wallahi ban sa ya akayi ba bari in goge da wuri ina tissue" kafin ace mey k'arnin ya mamaye kitchen d'in gabad'aya gas d'in Amal ta kashe da wuri sannan ta juya sink ta shiga kwararo amai, amai tayita yi wane zata harar da hanjinta yayinda Safiyya ke bata hak'uri. Bakinta ta wanke Safiyya ta taimaka ta jata izuwa d'aki.

  "Sannu Aunty kina buk'atan wani abun?" Kakkarwa take sosai ta kad'a mata kai "Ki had'a mun black tea kawai."
 
  "Toh ina zuwa" nan da nan ta had'o ta kawo mata.

  "Shikenan kina iya tafiya."

  "Ba wani abinda kike buk'ata?"

  "Babu kar ki damu."

  "Allah sawwak'e."
Da k'yar Amal ta samu ta sha rabin tea d'in taji ta k'oshi zazza6i ne ya rufeta a lokaci guda ko makaranta ta kasa fita washegari ga shi jikin nata ya d'au zafi. Maamah ce da ta jita shiru ta kira dan tambayan ko lafiya.

  "Wallahi zazza6i Maamah kaman zan mutu."

  "Allah sarki shafakillahu habibty Allah baki lafiya."

  "Ameen nagode."

  "Na yi miki assignment d'in na mana submitting."

  "Allah sarki Maamah kaman kinsan ina ta bi a raina wallahi nagode sosai Allah ya bar zumunci."

  "Ameen munyi waya da Ya Abdul ma yace in gaisheki."

  "Allah sarki ina amsawa."

  "Ya Afzal fah? Be kaiki asibiti bane?"

  "Ya koma gun Nazeefah tun jiya ai."

  "Baki kira kin sanar da shi bakida lafiya bane?"

  "Ko nayi mey zai mun? Kin manta ba wanda ya tsana kaman ni ne a duniyan nan yanzu?"

  "Allah sarki Amal do you need anything? Wallahi Ya Afzal bai kyautawa."

  "Ba komai Nazeefah wataran se labari nagode" ta amsa hawaye na tsiyaya mata daga ido.

  "Gobe zan shigo in duba ki in shaa Allah ki huta kinji? I love you."

  "I love you too sekinzo."

****
  Se wajajen sha biyu Amal ta samu k'arfin jiki a gida ta yini ranan ba inda taje, chan Maghrib nayi kuma zazza6in ya sake tashi ga amai idan ta fara kaman zata harar da kayan cikinta sosai Safiyya ta tausaya mata take kuma k'ok'arin kula da ita. Har anan Afzal be san mey ake ciki ba kaman yadda be kira Amal ba haka itama bata kirasa ta sanar da shi batun rashin lafiyarta ba ko Mami bata kira ba.

  Bayan Safiyya ta tattare plate d'in ta fita dashi Amal ta janyo wayanta ta shiga calender tana counting yau kwana uku kenan da missing period nata anya kuwa lafiya? Kode? Subhanallahi it can't be possible Allah yasa ba abinda take zargi bane inde haka ne ya zamo dole gobe taje asibiti ta tabbatar da koma mey amma fatanta Allah yasa ba abinda take zargi bane. Se sha d'aya ta fita washegari bayan da zazza6in nata yad'an sauk'a. A wani private clinic Driver ya sauk'eta inda ta k'arasa ta bud'e file tukun ta shiga ganin doctor tayi mata bayanin yadda takeji. Murmushi likitan tayi mata tace "Amma Amarya ce ke ko?" Kai Amal ta gyad'a mata cike da rashin fahimta.

  "Shiyasa ai."

  "Ban fahimce ki ba Dr Sadiya."

  "Congratulations you're pregnant Mrs Abdallah."

  "Pregnant?" Amal ta nanata cike da k'in yarda "Taya bakiyi mun gwaji ba bakiyi komi ba kice ina da ciki?" Murmushi ta saki kad'an "ni da aiki na kuma Mrs Abdallah ai ko ban miki gwaji ba idanunki kad'ai ma shaida ce kina d'auke da juna biyu."

  "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" taji Amal ta furta.

  "Lafiya?" Tayi saurin tambaya.

  "Dan Allah kiyi mun tests d'in tukuna I can't be pregnant at least not when babu jituwa tsakani na da mijina, I can't be pregnant Dr please do something" ta fad'a cike da tashin hankali.

  "Subhanallahi please calm down, taya zaki k'i kyauta daga Allah haka Mrs Abdallah?"

  "Ba haka bane Dr matsaloli sunyi mun yawa and cikin nan will only add to it please help me."

   "That's where you're wrong wannan ciki sede ya warware miki duk wani matsalan da keda mijinki kuke fuskanta, ki yarda dani mijinki na jin wannan news ze sauk'o daga kowani irin temper yake kai, kede ki godewa Allah kawai" ta sanar da ita ta na wani rubutu jikin wani paper "Ga wannan kije next room zasu yi miki scanning mu gano sati nawa ne duk abinda akwai zasu sanar dake kafin ki fara zuwa pre natals naki, congratulations once more." Jiki na k'yarma Amal ta amshi paper'n "Don't be afraid Mrs Abdallah in shaa Allahu juna biyun nan shi ze zame sanadin shirya tsakaninki da mijinki."

  "Toh nagode Dr."

  "Sey kuma ga wannan magunan basuda k'arfi in shaa Allah baza suyi komi wa cikin ba, zasu rage yawan jin jiri da kuma yawan yin amai da zazza6in duka, Allah inganta."

  "Ameen Dr nagode se anjima." Next room ta shiga inda akayi mata scanning cikin. Kwata-kwata ma cikin sati uku ne sede maimakon Amal tayi murna tun dawowanta gida take aikin kuka gabad'aya ta rasa meke mata dad'i bata ma san wa zata fara kira ta sanar da shi wannan labari ba abu d'aya da ta sani shine Afzal ne mutumi na k'arshe da zata kira ta sanar da shi. Tunda ya fara zarginta yanzu ai da k'yar ma idan ze amince cikinsa ne a jikinta, ya zatayi? Wannan musiba da mey yayi kama??





RANA D'AYA!
#RD

Love... King Miemiebee👄✨

17 comments:

Unknown said...

Innalillahi plz dan allah kar yasake tah tanquu

Unknown said...

Innalillahi plz dan allah kar yasake tah tanquu

Unknown said...

Tirkashi, Dan Allah kada Amal tasha wuya da yawa

Unknown said...

Speechless. Thanks dear

Unknown said...

Allah sarki snap😢
Ina yinki sis Miemie

Unknown said...

Gaskiya Afzal beyi daidaiba ay kamata yayi ya gaya mata Kazan saga cikin abinda ta aikata kafin yaci gaba da hukuntata. Kuma idan Amal zataci amanarsa at yaci ace yasani sun zuciya ne kawaj yyi mass yawa

Unknown said...

Ina wayon shi yake

Unknown said...

Gaskiya kam shine girma na kasa dakai yayi laifi call her attention yagaya mata komai yaci amanar amal wlhy he's so selfish... Tnx meemee bee

Unknown said...

I pray that heartless human being that call her self nazeefa suffer 1000tyms dan amal nd she loses him for good

Unknown said...

Afzal din da take ikki rarin girma,sani da kuma wayo toh a ina ya aji yesu.da har baze gane cewa Amal ba zatayi wani abunba.tun da dey have been 2geda 4 long

Unknown said...

Gaskiya afzal baikyauta ba itakuma nazeefa abin yayi yawa.Allah sarki amal

Unknown said...

Ni afzal din ma yafi bata min rai walhy

Unknown said...

Wlh fa tnx

Unknown said...

Eyya amal kaddarant knn,auren nazeefa na rawa allah y shiryeta. thank you miemie bee Allah karo basira.

Unknown said...

plxxx don Allah abar Amal haka kar abin ya mata zafi biyu ga ciki ga bakin ciki. plxx let asirin nazifa ya tonu walh da wuri

Unknown said...

tnxs much

Unknown said...

Ina masu son Nazeefah? Sai kuzuba ruwa akasa kusha
Nazeefah kiciga akwai randa dubunki zai cika