*BY MIEMIEBEE*
Page 59
FEBRUARY, 2017
Toh kode ya fad'a mata ne? Shawara ya tsaya yi, dai-dai lokacin da ya yanke hukuncin gaya mata gaskia batun auren da ze sake yi a dai-dai lokacin ne Mama ke fitowa daga d'aki da alama ta koma tasa kaya ne. "Ahh barka baka tafi ba, ai na sha ma koka riga ka wuce."
"A'a Mama ina jiran fitowanki ne toh ni zan wuce." Yayi maganan yana miqewa da Ramlah a hannunsa.
"Ke kuwa Ramlah haka akeyiwa bak'o ne? Seki d'ale jikinsa haka." Cewar Mama da mamaki.
"A'a Mama bar jikar takin nan zan zo in d'auke ta ta kwana min ma."
"Dagaske Uncle Soldier?" Tayi maganan with zealous flavor.
"Ji wani suna wai Uncle Soldier" Mama tayi maganan tana dariya. Raka Al'ameen duka sukayi seda yayi dagaske Ramlah ta yarda ta sauk'a. 5k ya bata inda Mama tayi godiya sannan taja hannun Ramlah dake ta faman yiwa Al'ameen ba-bye shiko se biye mata yake, dana Ummie sukayi ciki.
"Toh Zainab zan wuce."
"Toh Ya Al'ameen ka huta gajiya mun gode."
"Ba komai" har an bud'e mai k'ofan mota ya kusan shiga Zeezee ta kirasa a nitse. A hankali ya juyo yana kallonta wani k'war jini taga ya sake mata all she wants is HIM.
Shiru tayi kuma ta kasa magana se kallonsa take "Zainab?" ya kira sunanta.
"Na'am." Ta amsa a hankali idonta a k'asa.
"Lafiya koh?" Takawa tayi seda ta matso d'an kusa dashi kad'an sannan ta soma da cewa;
"Ya Al'ameen don Allah kayi hak'uri ka yafemin rashin hankalin da nayi ta maka lokacin da nake gidanka, I want you to know that I've regretted every single thing I've done to you. Alhak'inka ba k'aramin bina yayi ba, please forgive me Ya Al'ameen am truly sorry." Totally speechless ya tsaya yana kallon Zeezee dama tana da hankali ta kuma iya tsara magana haka? this is where she is wrong saboda tun rananda ya sake ta ya yafe mata komi. Tausayi sosai Zeezee ta basa, he never wished for her life to turn out this way. Me take nufi da alhak'insa ya riga binta? Is that the reason why suka rabu da mijinta? Maltreating nata yayi tayi shine har ta zube ta rage haske haka? (Wai anan ma don be ganta time da ta fito sabo-sabo ba daga gidan Adeel.)
"Zainab..." ya kira sunanta finally cike da tausayi.
"Ya Al'ameen I know its hard for you to believe me but wallahi na tuba please forgive me ko I can be free nima."
"Zainab" ya sake kiran sunanta this time more slow.
"You can't forgive?" Hannu tasa ta share rolling tears nata, "I've asked too much huh? nasan abubuwan da na maka are unforgettably unforgivable ina me sake baka hak'uri Ya Al'ameen. Even though bazaka yafemin ba just know that I'm deeply sorry for the fact that I disrespected you as my husband, I can't ever be in peace har se in ka yafemin, thank you listening to me anyway." Tana kaiwa nan ta juya cikin kuka zata koma ciki. Da sauri ya rik'o hannunta restraining her, kasa juyawa ta kallesa tayi saboda yadda kuka yaci k'arfinta wanda ba mugun d'agawa Al'ameen hankali yake ba.
"Zainab" ya sake kiran sunanta a hankali. "Turn around kinji?" Sam ta kasa juyawan "turn around and look at me." Da k'yar ya samu ta juyan da water bags a idanunta.
"Look at me" ya buk'ace ta. Kai zallah take kad'a masa. "Look up kinji?" Instead ta kalle san se kallon hannunsa daya rik'e nata take. Da ya gano hakan se yayi sauri ya saketa "I'm sorry" ya fad'a calmly. Nan ma kai ta kad'a mai nufin its nothing.
"Zainab I'm sorry kinji? I'm sorry for what you've gone through. Ni na jima da yafe miki a very long time ago regarding dukkannin abubuwan da kikayi min fid duniya wal akhira, kinji?"
"Are you sure Ya Al'ameen?" Ta d'ago kai tana kallonsa a yayinda hawaye ke ambaliya akan kumatunta. "Ka yafemin duk abubuwan da na maka? All of it?"
"All of it Zainab." Hawayen jin dad'i ne kuma suka shiga tsiyaya daga idanunta. "Thank you, thank you Ya Al'ameen finally my mind can be at ease." Hannu ya mik'a a aljihunsa ya fito da hanky tare da mannawa akan cheeks nata yana share mata rolling tears natan a hankali. Duk anan binsa da kallo kawai take a yayinda wutan sonsa ke sake ruruwa a zuciyarta. She don't think akwai wanda ze iya gane mata just how much she loves Al'ameen. Seda ya gama share mata hawayen sannan ya d'aga hannunta ya sa mata hanky'n a ciki tare da kullewa da other hand nasa. "Don't cry again kinji? "Kai tamai nodding tana forcing out a smile. "Thank you Ya Al'ameen."
"Always welcomed Zainab, koma ciki kinji?" Be shiga mota ba se da yaga shigewar Zeezee ciki.
Zeezee na k'arisawa ciki ta ruga d'akinta a guje tare da wurga kanta bisa gado ta shiga rusa kuka. Hanky'n daya batan ta rungume tsam-tsam a daidai wajen zuciyarta tana kuka sosai. Tana cikin wannan kuka Mama da jikokinta suka shigo, tana ganinsu ta juya musu baya tana me cigaba da kukan.
"Granny mesa Aunty Zeezee ke kuka?" Cewar Ramlah.
"Ungo Ramlah rik'e hannun Ummie kuje kuyi wasa a parlour banda duka, ina zuwa."
"Toh Aunty Zeezee fah? Mesa take kuka?"
"Kuje ina zuwa." A hankali ta fito dasu Ramlah sannan ta koma ciki ta samu Zeezee.
"Zeezee kuma kukan meh haka kike a idon su Ramlah?" Banza da ita Zeezee.
"Keda Ya Al'ameen ne?"
"Mama I love him and I want to go back to him." Tayi maganan in between tears.
"Toh Zeezee kika sani ko ya sake wani auren?"
"Mama be sake ba he told me himself."
"Zeezee kin manta da labarin Maman shi da sister'n shi ne?" Ita Zeezee gabad'aya ma ta manta da rashin hankalin da tayi musu se yanzu da Mama tayi maganan su.
"Mama I'll call them each and ask for their forgivenesses I love Ya Al'ameen."
"Zeezee kina ganin yin hakan ba komai?"
"Mama bana son wata ta rigani auran Ya Al'ameen I can't take it."
"Toh nikam bansan me zance ba a irin wannan al'amari sekace Ya Al'ameen d'inne autan maza."
"Just pray for me Mama, its all I ask."
"Toh Zeezee."
"Thank you."
"Toh kibar kukan haka ya isa."***
Kwana zaune Zeezee tayi a daren ranan tana tunanin ya zata 6ullowa Al'ameen da wannan lamari, shi kam tasan mutum ne me sauk'in kai, problem d'in da za'a samu daga gun Mom nasa ne da sistersa Sadiya. Washegari Zeezee ta saci idon Mama ta d'au wayarta ta shiga contacts inda ta k'wak'ulo numban Mama Babba dana Hjy Sadeeyah ta zuba a wayarta. D'akinta ta koma inda seta soma dialing numban Mama Babba sekuma ta katse, tayi hakan kusan sau hud'u ana biyar ne tabari ya shiga inda tayi mata one missed call amman bata d'aga ba kasancewar bata kusa. Se a karo na biyu ta d'aga tare da yin sallama nan itama Zeezee ta amsa tare da gaisheta.
"Ina kwana Mama?"
"Lafiya k'alau" ta amsa ba fara'a sosai kasancewar bata gane wake maganan ba.
"Zainab ce Mama."
"Toh Zainab, Zainab wacce kenan 'yata?"
"Zainab ex wife na Ya Al'ameen."
"Aww Zeezee?"
"Eh Mama."
"Kina nan ashe, sannun toh Zeezee."
"Ina nan Mama."
"Ya hak'uri kuma? Baba lokaci yazo yayi, Allah ya jik'anshi da rahama ya cigaba da baku ikon juriya."
"Ameen ameen Mama nagode. Mama don Allah kiyi hak'uri regarding abinda nayi maki da Hjy Sadeeyah back then, I was young and stupid ku gafirceni don Allah na tuba bazan k'ara ba."
"Masha Allah, Zainab naji dad'i da har kika gano kuranki kika gyara sannan kuma kika nemeni musamman don jin yafiya na, I want you to know a matsayinki na 'yata na yafe miki kinji?"
"Alhamdulillah Mama, jazakillahu khairan. Naji dad'i sosai thank you so much Mama."
"Ba komai Zeezee ya mamanki?"
"Lafiyarta k'alau tana gaishe ki ma."
"Toh ina amsawa, ya mai gidan naki kuma?" Shiru Zeezee tayi tama kasa amsata "hello Zeezee?"
"Na'am Mama?"
"Ba ki jina ne? Nace yamai gidan naki?"
"Mama ina gida ne yanzu, auren nawa ya jima da mutuwa tun kafin Baba ya rasu. Wallahi hak'k'in Ya Al'ameen, da naku dana su Mama da Baba shi ya rink'a bina tabbas nayi nadaman duk wani abinda na aikata, rashin kyautatawa Ya Al'ameen dana rink'ayi shi na tarar a gidan Adeel, I hated myself for going against umarnin Baba and disrespecting you guys all, ina me sake baku hak'uri."
"Allah sarki Zeezee, we all learn from our mistakes ina fatan de bazaki sake tafka wannan mistake ba saboda shi mu'mini ba a sokinshi a rami biyu."
"In shaa Allahu Mama nagode."
"Ba komai, ina miki fatan Allah kawo miji na gari." Da k'yar ta iya cewa "ameen" a zatonta ma ko Mama Babba zata ce mata zata dawo da ita gidan Ya Al'ameen ne, amman ashe ba haka abin yake ba.
"Jiya ma Ya Al'ameen yazo nan har gida yayi mana ta'aziyyah."
"Ayyah Allah ya bada lada, yazo Bauchi duban abu ne kinsan ya kusa aure shima zamu aura masa wata 'yar uwarsa anan Kaduna." Dum! Zeezee taji zuciyarta ta buga sosai, she couldn't hold back the tears anymore, zuba kawai suka soma shikenan abinda take gudu ya riga ya faru, wata ta riga ta sa'an Ya Al'ameen. Just how bad ta cuci kanta a rayuwa? Da k'yar ta iya cewa "ayyah, Allah shi basu zaman lafiya."
"Ameen" Mama Babba ta amsa.
"Toh Mama se next time nagode ki gaishe dasu Aysha."
"Yauwa ki gaishe da Mamanki zasu ji" anan ta katse. Kuka me sauti sosai Zeezee ta rushe dashi a d'akin.
Bata bar kukanba har seda bacci 6arawo ya saceta. Koda Mama ta dawo daga islamiyyar safenta ta tarar da ita tana bacci bata kawo tunanin komi a ranta ba taja mata k'ofar. Se chan da Azahar tazo tada ita Sallah inda anan tayi noticing yadda idanun Zeezee suka kumbura.
"Lafiya da kumburarrun idanuwa haka Zeezee?" Kai zallah ta gyad'a tana k'ok'arin shiga bayi.
"A'a dawo nan, dawo ki zauna."
"Mama babu zanyi alwala ne."
"Nace ki dawo" bata sake gardama ba tazo ta zauna a gefenta.
"Kuka kikayi koba haka ba?" Batayi k'arya ba ta gyad'a kai.
"Dalili?"
"Mama..." sekuma tayi shiru.
"Ehemm ina jinki."
"Mama I called Mama Babba..." duk yadda sukayi da Mama Babba ta gayawa Mama tana kuka sosai. Kwantar da kanta Mama tayi a jikinta tana bubbuga bayanta "shhh its okay kinji? Kede ki cigaba da addu'a kawai Allah ya kawo miki miji na gari ba lallai se Ya Al'ameen ba."
"Mama but ni shi nakeso, banason kowa se shi."
"Toh Zeezee ya zakiyi? Wata ta riga ta rigaki dole ki rungumi k'addara kiyi hak'uri."
"Mama banjin zan iya hak'ura da kalan soyayyan da nakeyi wa Ya Al'ameen, this feeling has never happened to me. Gani nake as if idan ban sake kasancewa matarshi ba ina iya rasa raina gabad'aya." Da sauri Mama ta d'agota daga jikinta, "kinada hankali kuwa? Banason sake jin maganan nan daga bakinki kina jina ko?"
"Mama all I want is to be with him and make him happy, I love him so much."
"I know shiyasa nace ki dage da addu'a, idan you and Ya Al'ameen are destined to be together once again you two shall remarry have faith okay?"
"Okay Mama thank you."
"Tashi kiyi alwala kiyi sallah na riga na had'a lunch."
"Toh Mama thank you." Mama na ficewa ta nufi bayi tayi alwala ta idar da sallanta. Hanky'n Al'ameen daya bata jiya wanda ta adana sa ta ciro tare da kaiwa kan hancinta tana shunshuna daddad'an turarensa me sanya mata kwanciyar hankali. Kaman jiya yau ma ta yini tana tunanin Al'ameen. Da daddare kamin ta kwanta ta kira Hjy Sadeeyah inda ta gaisheta, bayan gaisuwa Hjy Sadeeyah tayi mata ta'aziyya sannan Zeezee ta nemi gafararta itama sosai. Tun Hjy Sadeeyah batayi niyyan yafe mata ba amman jin yadda Zeezee tad'an bata highlights kad'an daga kalan rayuwar auren da tayi living with Adeel yasa tuni ta yafewa Zeezee takuma tausaya mata sosai inda tayi mata addu'a kan Allah ya kawo mata miji na gari daze kula da ita. Zeezee na son sanar da Hjy Sadeeyah akan tayi mata hanya ta dawo da ita wa Ya Al'ameen koda kuwa as his second wife ne zata dawo, she don't care tanaso muddin she'll be able to show him love and comfort amman ta kasa gaya matan saboda batada courage haka tana ji sukayi sallama. Kuka kuma ta d'auro daga nan har bacci 6arawo ya sace ta inda tayita mafarke-mafarken Al'ameen. Washegari da safe bayan ta gama chores nata ta lalimo wayan Mama ma yau ta kofi numban Ya Al'ameen. So take ta kirasa taji idan still yana gari amman ta gagara seya kusan shiga seta katse. At long last ta samu ta kira san.
"Hello" ya fad'a a lokacin da yayi picking. Muryansa da bata iya ignoring ne ke neman wullata dreamland wanda tayi sauri ta amsa da "Ina kwana Ya Al'ameen?"
Yana jin muryar ya gane nata ne, "Zainab."
"Na'am Ya Al'ameen ina kwana?"
"Lafiya kin tashi lafiya?"
"Lafiya ya gajiya kuma?"
"Alhamdulillah."
"Uhn nace kana gari ne ko har ka tafi?"
"Ina nan se gobe zan tafi yau zan kammala abinda ya kawoni in shaa Allah."
"Toh Allah ya taimaka, ko me ya kawo kan amma?" So take taji ko ze iya fad'a mata da bakinsa aure ze sakeyi. Shiru yayi na d'an wani lokaci sannan ya amsata finally, "Allah ya sake azurta ni ne Zainab, I'll be getting married in some couple of months." Hannu tasa a face nata inda tajiyo hawaye sosai nata kan zuba, rawa muryanta ke tace "Allah sarki, Allah baku zaman lafiya toh ya kuma tabbatar da alkhairi. Whoever she is, she should know that she is lucky to be blessed with an affectionate and patient husband as you, Allah bata ikon farinta maka." Besan me ba amman seyaji dama be sanar da ita ba, ko be tambaya ba yasan kuka Zeezee ke don jin yadda muryarta ke rawa sosai. Amman kuma why is she crying? Does she wants him back? So take ta dawo mishi ne komeh? But anya? Ai Zeezee never loved him. Ignoring this thought ya amsa addu'o'in da tayi mai da "ameen Zainab thank you kema Allah had'aki da wanda zaki so ya kuma soki." A ranta tace that person is you.
Hawayenta ta share sannan tace, "kana gida ko?"
"Eh ina gida Zainab wani abu neh?"
"Lunch nakeso na kawo maka."
"No please you don't have to karki gajar da kanki zansa asiyomin."
"No please I insist Ya Al'ameen don't reject my offer please."
"Zainab seriously I don't want to be a burden to you."
"Shikenan toh" tayi maganan sounding sad and defeated.
"But in kinga its okay with you, ba komai nine da godiya."
"Thank you Ya Al'ameen."
"It is I who should be thankful."
"Sena shigo toh."
"Ki taho min da Ramlah."
"Ramlah zata islamiyya by then" ta amsa da murmushi kad'an a fuskarta wane yana gabanta.
"Ayyah to ki gaishemin ita."
"Yauwa se anjima" jira tayi yayi hanging sannan ta sauk'e wayar ta ajiye a gefe. Tunanin me zata girka masa ta shiga yi amman kwata-kwata she can't think of anything. Haushin kanta taji for not paying attention before to know what dish was her husband's favorite. Zama tayi ta shiga tunani sosai wani abinci yafi son siya adan? miyan ganye da tuon shinkafa yafi siya da kuma rice and stew. Sanin bata iya yin miyan ba yasa ta yanke hukuncin yi mai rice and stew.
In less than 3 hours Zeezee ta gama had'a basmati rice and stew nata daya sha kaji dakuma co-slow nata a gefe together with kidney sauce. Cikin had'ad'd'un food warmers na Mama da ake sawa Baba abinci aciki ta zuba mishi abincin, tana d'ago flask d'in kawai ta tuna da Baba. Zama tayi a kitchen din tayi mai addu'a da dama harda 'yar k'wallarta sannan ta tofe ta juye abincin ciki ta shirya komi cikin wata fancy basket sannan ta ajiye kan counter ta nufi d'akinta don yin wanka ganin sha biyu ya wuce.
Tana cikin wankan ne Mama ta dawo daga islamiyya inda ta nufi kitchen dan shan ruwa, achan ta tarar da basket da Zeezee ta had'an. Bata ta6a ba ta wuce d'akin Zeezee anan ta tarar da ita tana wanka. Zama tayi ta jira fitowarta inda take tambayarta "waya kawo basket dake kitchen?"
"Ba kawowa akayi ba Mama."
"Ba kawowa ba? Ban fahimta ba."
"Ni na girka naki dana Ya Omar nakan dining table."
"Wancan kuma fa?" Tayi maganan tana pointing direction na kitchen.
"Na... na..." sekuma tayi shiru.
"Ki gayan mana na waye?"
"Na Ya Al'ameen ne."
"Oh ni Hafsah! Yanzu girki kikayi ma bawan Allan da bakisan ko yana gari ba kokuwa a'a?"
"Mama I called him and asked yace min se gobe ze tafi."
"Toh me had'in ki da kai masa abinci? Se ya fassaraki tukun ko?"
"Mama fassaranin nake so yayi saboda yasan I love him ko ze tausaya min ya dawo dani koda as his second wife ne ni ban damu ba."
"Oh! Toh nikam babu bakina acikin wannan abu."
"Eh naji amman please kice Allah bani sa'a kinji Mama?" Shiru Mama tayi danko Zeezee bata isheta da kallo ba. "Please..." ta sake pleading.
"Naji Allah baki sa'a."
"Ameen Mama thank you."
"Ze aiko masu gadinsa ne su zo su kar6o koya?"
"Ni zan kai masa."
"Oh! Zainab!"
"Please Mama karki min baki kince Allah bani sa'a ya isa kinji please." One more look Mama tayi mata sannan ta miqe tare da ficewa.
Nan da nan Zeezee ta shafa mai tasa kaya tayi Sallah sannan tayi applying light makeup wanda ya mugun amsarta ba kad'an ba. Material gown na tiger design red and brown tasa tare da yafa red gyale a kanta ta nannad'e a wuyanta. Shoe and bag nata ma red tasa, tana cikin aikin feffesa turare wayarta ya shiga ruri. Ganin Ya Al'ameen na flashing akai tayi sauri ta d'aga "hello Ya Al'ameen?"
"Zainab nace ba sekin fito ba I'll send Saje yazo ya kar6a abincin kinji? " Shi Al'ameen besan zuwanta da biyu bane, k'arya ta had'a mai tace ta riga ta fito saboda zata wuce gidan friend nata daga nan.
"Oh, toh shikenan sekin iso." Nan ya katse. Tana gama abinda zatayi tayi sallama da Mama sannan ta fice. Tun rabuwanta da Al'ameen bata sake taka corner'n gidan nasu ba se yau, ji take ina ma ace ya dawo da ita d'akinta ne. Tana k'arisawa gaban gidan tayi parking a waje sannan ta fito da basket d'in ta danna bell. Within seconds guard yazo ya bud'e tare da yi mata sannu da zuwa. Basket d'in yaso amsa amman ta hanasa, sebin gidan take da kallo a yayinda take sake missing gidanta sosai. A parlour ta tarar da Al'ameen yana sanye da farar vest revealing his muscular body da kuma sky blue wandon jamfa. Tana shigowa ya miqe tare da yi mata sannu da zuwa, se kallonsa take ta kasa dena staring. "kuma su Saje suna kallonki basu kar6eki ba?" Kai tayi shaking da wuri;
"No ni na hanasu, its no big deal" ta amsa tare da ajiye basket d'in kan centre table.
"Toh Zainab thank you kinji? Ya Mama."
"Lafiyanta k'alau" ta amsa still a tsaye tana wasa da bakin gyalenta. So yake yace mata ta zauna amman kuma ganin how awkward it'll sound yayi shiru. "Toh ni zan koma."
"Toh Zainab thank you" d'aya daga cikin throw pillows dake kan kujeran da ya tashi akai ne ya d'aga tare da d'ago kud'in dayasa cikin wata envelope.
"Zainab" ya kirata alokacin da har ta juya ta soma tafiya. Chak ta tsaya tare da amsawa "na'am?"
*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*
Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
3 comments:
Tanx sis, Allah ya kara basira. Wayyo major general! Dan Allah kadawo da zeezee dakinka
MIEMIEBEE pls we r waiting ....
Allah sarki zeezee kiyi hakuri komi lokacine yime naki na nan zuwa
Post a Comment