Monday, 12 December 2016

‘YAR GATA CE!

BY MIEMIEBEE
PAGE 12
    _Heres a page in honour of you sweetheart divas๐Ÿ˜ป *Maryam (Abmar), Deeylerhh* and  *MeenoUr,* my boo thang thang, ILY'all!๐Ÿ’•_




    9:14PM Omar yayi sallama d’akinsu Mama ya ajiyewa Zeezee jakarta tare da yiwa su Baba seda safe. Bayan Mama ta fito daga wanka ta kalli Zeezee data d’ale tsakiyan gado tana shirin bacci tace, “jibi abin kunya” sannan ta k’arasa gaban mirror tare da jan kujera ta zauna ta soma shafa mai, jira take Baba ya tanka ta taji yayi shiru hakan ya sake bata daman magana “ace yarinya shekarunta shida almost getting to seven amman a tsakiyan iyayenta take kwana ko a ina aka tab’ayin haka oho.”
   “Ji yadda kike magana kaman kinyi mata d’aki tak’i kwana ciki, bansani ba ko a parlour kikeson tana kwana.”
  “Kamar ya a parlour? Baga d’akin su Yasmeen ba.”
  “Wai kina nufin Zeezee ta soma kwana da su Mariam? Mugayen can!”
  “Eh mana!” ta basa amsa take. “Ba yayyun ta bane?”
  “A dalilin meh zan tura K’anwata kwana da wad’ancan mugayen? Ba abinda ze kai Zeezee d’akinsu Mariam kiji ki sani.”
  “Lallai kuwa!” Tayi maganan tare da miqewa ta nufa gun wardrobe nata searching for her night gown “shikenan kullum damu zata na kwana?”
  “Eh har sena mata d’akinta itama.”
“D’aki?! Ta zaro ido waje a ina zakayi mata d’akin?”
  “Wannan kuma is for me to know and you to find out kin gama feshe-feshenki ki kashe mana wuta, Allah bamu alkhairi” yana kaiwa nan yaja musu comforter da Zeezee sukayi baccinsu comfortably as always.
 
  ~* ~* ~*
_Monday morning, 6:10AM_
  “Ke! Zeezee wallahi ki tashi kona zuba miki ruwan sanyi iskancin banza shekaranki nawa da shiga makaranta amman ace kullum sekin bawa mutum headache kafin ki tashi a wani gidan ma ke za kina yin wanka da kanki, tashi!” Yasmeen ta k’are maganan cikin sautin tsawa ganin ko kad’an Zeezeen dake baccinta tana tsotsan thumb finger’nta bata motsa ba, hakan ya sake k’uludda ita “wallahi zan mareki tunda Baba bayi gida.”
  “Mareta wallahi” cewar Mama ai tana jinki. Tas! Yasmeen ta wanke d’uwawun Zeezee da mari da force ta miqe zaune tare da sa ihu.
  “Wallahi barin je makarantan ba muguwa kawai.”
“Huummm!” Yasmeen ta toshe hanci “ji warin baki sekace latrine, k’azama kawai tashi da Allah!” haka da k’yar Yasmeen ta samu tasa Zeezee toilet nan ma zama tayi kan toilet sit tak’iyin brushing da ya kamata tayin, bayan 2 mins Yasmeen ta dawo ready to bath her taga ko brushing Zeezee batai ba hasali ma bacci take comfortably kan toilet sit d’in, ruwan sanyi ta tsiyaya daga famfo ta fesa mata a fuska firgit har tana neman fad’i daga kan sit d’in ta farka “meh haka? Muguwa kawai, Allah ya isa” tasa ihu “Allah ya isa mumuna kawai.”

      “Fad’i koma meh wallahi yau tunda Baba bai gida se kin gommaci kid’a da karatu, maza sauk’o daga kan sit d’in.”
  “Toh kin min tsarki ne da zan sauk’on?” Ta watsa mata harara.
  “Yanzu fitsarin ma se an miki tsarki?”
  “Pupu nayi.”
  “Mschww dirty girl kawai”
  “Niba ke ce zakimin ba Ya Omar nakeso.”
  “In zaki tsaya ki tsaya” aiko Zeezee ta bijire mata itafa se Omar ze wanke mata pupu. Mama ce tasa baki a  k’arshe ta tura Yasmeen kirawo Omar.

***
   Bayan ta samesa a d’akinsu ta isar masa da sak‘on.
  “Wallahi bazan jeba kashin ya bushe a jikinta inde ni zan wanke mata.”
  “Kaine kashi ze bushe a d’uwawunka ba ita ba d’an banzan yaro kawai maza tashi!” Scolded Baba “bazaka tashin bane sena gaggaura maka mari?”
  “Allah sarki Baba yarinyan nan fa yaci ace ta soma tsarki da kanta she is almost getting to seven (7) years”
   “Eh bazata wanken ba seta cika seven (7) d’in wuce nace mana!”  Haka yana kumbure-kumbure yaje ya wanke mata pupun Yasmeen ta mata wanka. 6:40AM Yasmeen ta kawo wa Zeezee breakfast nata na chips and eggs aiko tana gani ta soma rigima “ni bance chips nake so ba ni indomie zan ci.”
  “Kinga ba time yanzu K’anwata yi hak’uri kici wannan d’in.”
   “O’o tahau shure k’afafu ni indomie nakeso.”
  “Oya Yasmeen kiyi sauri ki dafa mata kiyi amfani da ruwan kettle seya dahu da wuri.” Kamar wacce zatayi kuka Yasmeen tace, “wallahi Baba ba ci zatayi ba yanzu da indomien aka dafa cewa zatayi chips takeso neman sa mutum aiki ne kawai.”
  “Banason suratan banza kije ki dafa mata nace!” In 18 mins indomie’n Zeezee ya iso kad’an taci ta jagwal-gwala saura as expected, Mama ta zab’a wai ta sama ta uniform, bayan an sa mata ta d’ago socks nata ta samata anzo sa takalmi aikuwa Zeezee tace ba wannan zata sa ba yau bayan taga shi Omar ya mata polishing, haka yana ji yana gani Baba yasa sa sake mata polishing wani sam be damu ba saboda yasan meya shirya mata a school yau.

            AT SCHOOL *~ *
  “All stand!” Ordered Mrs. Audu (form teacher’n su Zeezee) nan da nan su Zeezee da sauran class members nata suka mik’e suna nan har yanzu class da seat nasu d’aya da Lubiee they must be best friends now. “Submit all of your homeworks row-by-row all at once.” Nan da nan d’aliban suka fiddo da homeworks nasu su kayi kamar yadda teacher’n sun ta buk’ata.

_7 minutes later..._
    “Zainab Isma’il Yusouf!” Called Mrs. Audu angrily, “come here!” Zeezeen da batasan me tayi ba ta mik’e a sanyaye “yes Ma’am.”
  “Whats wrong with you? How can you fail all of your homeworks?”
  “Me?” Zeezee ta dafe k’irji.
“Yes or do you need some proof?” Mrs. Audu ta d’ago mata zeron da takama a duka homeworks natan “shame on you! class say shame on Zainab” nan ‘yan aji suka hau yima Zeezee shame shame shame illa Lubiee ce bata mata ba. Kuka Zeezee tayi tayi ranan ana fita break ta tarke wata Deborah a lungu tayi mata d’ankaren duka sannan tayi warning nata kan inta kuskura ta kai k’ararta seta mata wanda yafi wannan. Kuma badan komi ta daki yarinyan ba sedan wai ta lura da Aunty tasa su yi mata shame duk Deborah tafi yi da ihu. Baba na zuwa d’aukanta ta nuna mishi homework da Omar ya mata ta fad’i.

*** _Back home..._
  “Omar! Omar! Zo nan!” Omar dayasan this was coming ya mik’e yaje “na’am Baba” wulla mai littafin Baba yayi, “explain this, meh haka?” Bayan ya k’are wa makeken zeron dake kan fejin kallo yayi k’ok’ari ya had’iye dariyan sa sannan yace,
  “Jiya ina kiranta tazo muyi mata homework d’in tak’i ta gudu nikuma... Nikuma...”
  “Kai kuma kayi deciding da kayi failing nata har kasa ayi mata wak’a gaban aji koh? Toh maza ka bata hak’uri.” Ai atapir Omar yace baze bada ba seda Baba yayi dagaske yabata hak’urin aka wuce wajan. Fita Baba yayi kafin nan yace, “kice Mamanku tayi miki homework naki kinji?”
  “Toh ba-bye”

   Mama dake kitchen ne ta fito tana yi mata sannu da zuwa se gani tayi fuskan Zeezee da alaman yak’ushi. “Ya haka waya miki wannan abu a fuska?”
  “Babu” tabada amsa tana cigaba da tafiya.
   “K’arya kike fad’a kikayi ko?”
  “Nikam ki barni” daga nan ta wuce ciki, bayan tagama wulli da socks da takalmanta as always tabar vest da panties zallah sannan ta fito da school bag nata zuwa d’akin Mama “wai aji Baba kimin homework d’ina.”
  “Yau kuma? Ki jira yayyun naki suka dawo su maki.”
   “Ba kina gani ba Ya Omar ya jefar dani da gan-gan naci zero ni kimin.”
  “Kawo toh” bayan ta fito da homework d’in Mama ta buk’aceta ta faddo da pencil pack nata sede wayam ba komi ciki.
  “Ina pencils nakin suka je?” Shiruu ba amsa, “dake fa nake magana? Ina sabin pencils dana sa maki ciki jiya?”
  “Haaa’a! babu sun b’ata ki d’auko min wani” hannu Mama takai bakinta ta bige da k’arfi seda Zeezee tasa ihu, “idan baki bar min magana da rashin kunya ba na riga buge bakin naki kenan.”
   “Allah ya isa” ta fad’a tana riqe da bakin nata.
  “Ina pencils d’in suke? Ko ki fad’a ko in miki d’ankaren duka.”
  “Ni shikenam kullum kiyita duka na Allah ze sak’amin.”
  “Ina pencils d’in?!” ta daka mata tsawa, itama a tsawacen ta miyar mata da amsar;
  “Sun b’ata babu!”
  “Toh wallahi ki bud’e wannan kunnuwan naki da kyau ki jini, zan sa miki wasu biyun kika b’atar da wayan charger na zan chod’e wannan k’afafun naki kinji na rantse” haka da rigima suka samu suka k’are homework d’in.

  Baba na dawowa gida that was by 4:23PM kenan Mama taje ta irga mai kan Zeezee taje tana fad’a a school, atapir Baba yace be yarda ba a kira Zeezeen yaga fuskan. “Zeezee! Zeezee! Zo” Mama ta kirata, d’akinsu Mariam ta shiga da wuri ta lak’uto foundation da concealer nasu ta shafa gun ta rufe tabon yak’ushin sannan taje “meneh?”
  “Zo ina gunda k’awar taki ta yak’ushe kin?”
  “Nifa ba a yak’usheni ba.”
  “Maqaryaciya kawo fuskan” ba musu taje Mama ta duba gun tarasa ciwon.
  “Ina yake toh? Neman yima yarinya sharri kawai.”
  “Wallahi Alhj akwai-” katse ta yayi “seki nuna ai in akwan!”
  “Laaa! Bade foundation kika shafa ba?” Mama tayi maganan tana murza hannun ta don gaskata abinda idonta ke fad’i mata. Jin haka Zeezee taja baya da wuri “Baba kaga Mama tana min sharri ba?”
  “Karki kulata K’anwata jeki sa hijabi yau malamin ki ze fara zuwa.”

  “Yau Baba?!” Tayi exclaiming.
“Eh Zeezee zaki fara karatu.”
  “O’o ni bana so suna duka.”
  “Wannan bare dake kiba” haka da k’yar ta amince 4:30PM malaminta ya iso tayi karatu tak’i tayita shiririta ita wai bataso. Haka rayuwan Zeezee ya cigaba da kasancewa har ta gama primary one rigimin yau daban na gobe daban ta gagari kowa a gidan.
 
   Washegari da safe Baba yakai Zeezee asibitin ido kasancewar complaining da take, bayan an auna idon nata aka gano tana suffering from short-sightness take gun aka auna idonta aka bata eye glasses aiko Zeezee tace ita bataso ‘yan ajinsu zasu mata dariya kasancewar wani film data kalla UGLY BETTY.

  Suna dawowa gida tacire glass d’in ita bataso da k’yar Baba yayi convincing nata ta miyar, Ibraheem da Mariam zaune suka tarar a tsakar gida kasancewar yau baida lectures da safe ita kuma Mariam ta gama makaranta tana jiran admission. Gani kawai sukayi Zeezee da glass se binta suke da kallo a yayinda take watsa musu harara ganin sun kusan shiga ciki yayyun nata basuyi mata glass yayi kyau ba tasa kuka “ya haka kuma? keda waye?” Baba ya tambayeta.
  “Su Ya Ibraheem basu cemin glass d’ina yayi kyau ba ni banaso” tasake sa ihu har seda Mama dake ciki tafito.
   “Har kun dawo ne? Ya Zeezee da glass haka? Idon bai gani ne?” Ta tambaya, nan Baba yayi mata bayanin komai “ayya auta ta Allah baki lafiya” maimakon Zeezee tace ameen seta kuma rushewa da sabon kuka “toh ni kuma menace?”
  “Bakice min yayi kyau ba ni banaso.”
  “Haba! Kin ganki kuwa? Dr. kawai, Dr. Zainab.”
  “Su Ya Ibraheem basu ce min yayi kyau ba.”
  “Barsu, bara ku ce mata yayi kyau bane? Sam baku iya zama da k’annenku ba” Baba yayi scolding nasu, da k’yar Mariam ta iya shanye dariyan ta “yayi kyau” suka fad’a in unison.
  “Aikin banza kawai mu shiga ciki K’anwata” haka koda su Omar suka dawo suma basu cemata glass nata yayi kyau ba tayita kukan banza.

~* ~* ~*
   The following day as always da k’yar aka samu aka shirya Zeezee, k’iriniyarta ta yau tafi ta kowani rana sabida Baba baya gida, tun fitan sa sallan Asubah be dawo ba da alama wa’azi ya rik’e shi. Bayan an gama shiryata Mama ta feffesheta da turare sannan ta wuce gaban dressing mirror dan d’auko wa Zeezee eye glasses nata wayam! Ta duba gun da ta ajiye jiya babu ta tambayi kowa a gidan duk sukace basu gani ba, nan fa aka shiga neman glass na Zeezee ana cikin haka dai-dai 7:08AM kenan Baba ya dawo gida “hope kun gama shiri, oya kufito mu tafi.”
   “Alhj ko kaga eye glasses na Zeezee?” Mama tayi tambayar tana duban cikin wardrobe nata.
  “Ba gaban mirror kika ajiye jiya ba?”
  “Toh gashi babu ba inda ban duba ba duk babu.”
  “Kamar ya babu Hafsah? So kike kicemin glasses d’in yayi k’afa ko meh? Ni wallahi bana son carelessness yanzu ya kikeson taje makarantar?”
  “Alhj ji yadda kake magana kaman da gan-gan nayi misplacing ni wallahi am certain agaban mirror na ajiye.”
  “Seki d’auka ai in achan d’in kika ajiye.” Bin Zeezeen dake zaune kan gado Mama tayi da kallo tace, “Ke ina kika kai glasses nakin?”
 
  “Aww yanzu kuma sharri zakiyi mata? Kuma ban hanaki ce mata ‘Ke’ ba?”
  “Ai tasan me nake nufi ina kika kai glasses d’in?”
  “Ni ban d’auka ba, Baba kaga Mama koh?”
  “Barta K’anwata zo abinki.”
  “Ai tun jiya take cewa batason glass d’in ba tantama ita ta d’auka ta b’oye.”
  “Kede kice kinason mata sharri kawai K’anwata ke kika d’auka?”
  “A’a” ta kad’a kai.
  “Tsakanin ki da wa?” Baba ya tambayeta, Shiruu Zeezee bata ce komai ba “Zeezee ke kika b’oye wai?”
  “Dagaske bani bane Baba.”
  “Za kiyi wa Baba k’arya?” Kai ta kad’a “to gayamun ina glasses nakin yake?” Baki ta turo “ni banaso.”
  “Bakiji me Dr. yace bane Zeezee? Idon ki na ciwo only if kina sawa idon zasu gyaru ko kinaso ki tsufa ba ido?”
  “O’o”
  “Good then you must wear your glasses temporarily kinji? Yi hak’uri kije ki d’auko min.” Zatayi magana Baba yayi saurin katse ta “shhh! And je ki d’auko min” haka ba yadda ta iya tabi Mama da dirty look sannan ta fice babban parlour inda ta b’oye glasses d’in in between cushion na 3 seater tasa hannu ta zaro ta kaiwa Baba yasa mata da kansa sannan suka fice se kumbure-kumbure take a motan haka har suka isa school.

             AT SCHOOL...

    Kap ‘yan ajin su Zeezee se binta suke da kallo ganinta da sukayi da eye glasses wanda ba k’aramin ci mata rai yake ba, ji take kamar ta cire glasses d’in ta b’oye.

  Ana fita break Zeezee ta tarke yarinya a lungu tayi mata dukan tsiya itama de ta bugu sede ba kamar yadda ta daki yarinyan ba agarin haka ta samu cizo babba a hannunta. Suna cikin damben Allah ya kawo teacher wucewa nan da nan ya rabasu akayi dasu admin block, tsawata musu sosai headmaster yayi sannan ya kira iyayensu sam Baba yak’i yarda da aka cemai wai Zeezee tayi fad’a a school ashe de ba k’arya ba Mama kemai ba last time data ce masa Zeezee tana fad’a a school. Hak’uri sosai Baba da parent na d’ayan yarinyan suka tayi ta bawa headmaster d’in in bahaka ba yace sam se an basu punishment na picking after every school day for the whole week. Bayan an samu an shawo kan komi Baba yayi godiya yaja hannun Zeezee suka fice “haba K’anwata wani irin hali ne haka na fad’a school? Bafa haka takwararki take ba.”

   “Toh Baba kasan me tamin ne?”
  “Koda me ta miki be kamata ki tuhumeta da dambe ba, kai k’aranta zakiyi wa form teacher’nku.”
  “Kai k’ara Baba ai se ‘yan class namu sumin dariya ni ta sake kallo na wallahi dukanta zanyi.”
  “Aww bazakiji maganan Baba ba kenan? Inda kuma yanzu kin ji mata babban ciwo ko kin fasa mata kai fah?” Shiru tayi batace komi ba har suka isa gida, isarsu ta fito ita kad’anta Baba na binta da jakanta da lunch pack suna shiga ciki sukayi karo da Mama tana kwashe kayan shanya kan igiya sannu da zuwa ta musu data lura da yadda Zeezee ke cinno k’aramin bakinta tagano da akwai matsala. “Mekuma ya faru yau? Alhj ko kunyi fad’a ne?” Kan wanda bazeyi magana ba yace;
  “Ke yanzu da zaran na fad’a miki meya faru seki hau cewa ai dama na gaya maka” Baba na maganan Mama kuwa na bin Zeezee da kallo nan ta hango babban shatin cizon dake hannun damanta.

    “Hohoho dambe ma tayi yau a school kenan, no wonder ka fita d’auko ta yau da wuri halan ma har headmaster’s office aka kaita ko? Ko sunsa sunanta a black list?”
  “Ke da Allah bakin ya isa haka ba sunanta da aka sa a balck list.”
  “Me za’a fasa dama mutuwa ko hisabi? Mena gaya maka kwanaki? Ai wallahi kad’an ka gani wataran seta fasa ma wata kai a school a kaiku duka police station anan ne zakuyi hankali.”
  “Toh ya isa da Allah muguwa kawai abinda dama kika iya kenan baki wa mutane instead kijata kiyi mata nasiha kina cewa har station se an kaita to tare zakuje kiji in gaya miki.”
  “Ai ba nasihar da zan mata kanku akeji tunda cikin sauran ‘ya‘ya na k’waya hud’u ba wanda aka tab’a kawo min k’ararsa yana fad’a a school dan anyi akan Zeezee se meh? Kai ka lalata mata tarbiyyarta saboda haka ba abinda zance mata kai d’in daka b’ata seka gyara” tana kaiwa nan ta gama sauk’e kayakin daga igiya tayi ficewarta.

  _Wednesday afternoon, 2:35PM_
   Chess of drawer’n Mama wanda ake adana mata socks nata ta fito dasu, sanye take da black english wear kanta a tsefe an kamasa sakwa-sakwa. A dai-dai tsakar gida ta ajiye sannan ta d’ago new pair of socks tasa ta tattara teddy bears nata ta jerasu kan table da bulala rik’e hannunta wai tana musu lesson. Mama na gama cin abinci tafito kai plate kitchen ta tarar da Zeezee da socks tana yawo tsakar gida “haba! Zeezee wani irin sabon salon iskanci ne wannan? An tab’a sa farin socks a gida ne? Bana school bane?”
  “Ni ki banni ai ba naki bane nawa ne.”
  “Oya maza cire socks d’in ki mayar”
   “O’o” ta fad’a stubbornly, idanun Mama na sauk’a kan drawern ta da Zeezee tayi wurgi dashi tsakar gidan ta fusata, kanta tanufa ta nad’a mata na jaki ta kuma sata ta miyar da drawer’n ciki, kuka Zeezee tayi tayi har seda Baba yadawo as always ya bata gaskiya ya yita balbale Mama yana ikirarin ze soma jan Allah ya isa next time ta sake tab’a masa Zeezee’nsa.

     ★★★★★
   Days, months and even years passed by Zeezee nada eleven (11) years yanzu tana matakin Jss 1 a LYS still, yarinya a kullum dad’a kyau take ga tsawo masha Allah bata da wani kauri ‘yar slim to fashion take. Yasmeen kuwa nada seventeen (17) years last year ta gama makaranta tana jiran admission a ATBU into physics education. Omar kuwa is twenty and half (20½) years old an zama saurayi se rawan kai yana ATBU shima studying computer engineering. Mariam kam ma preparation na bikinta ake she is twenty-two (22) years old, last year tayi graduating daga ATBU in microbiology, bikin ta bayan babban sallah in Allah ya yarda. Ibraheem yaya babba kuwa is now twenty-four (24) years old, two (2) years back yayi graduating from ATBU in Petrochemical engineering (course d’in manya!) Saurayi son kowa k’in wanda ya rasa yayi service nasa yanzu haka ya fara aiki a NNPC, kud’i yake samu sosai har ya sai motarsa k’irar Honda Anaconda new model.

  *ZEEZEE...*




     *© MIEMIEBEE*
  ๐Ÿ‘„๐Ÿ‘„๐Ÿ‘„๐Ÿ‘„๐Ÿ‘„
www.beeenovels.blogspot.com

1 comment:

Anonymous said...

Allah yasaka da alkhairi