Sunday, 11 December 2016

‘YAR GATA CE!

BY MIEMIEBEE
PAGE 11


 
      Isarsu gida Baba yasa Ibraheem ya ciro motar Zeezee daga mota, duk yaran se bin motan suke da kallo sun kasa zama gu d’aya a babban parlour ya dire motan Yasmeen da couldn’t hold it in anymore tace, “Baba motan waye?” Kafin Baba ya amsa Zeezee ta amsa, “nawa ne.”
  “Ja chan gefe waze sai miki wannan k’aton mota?” Baban dake jinsu ko k’ala bece ba.
  “Baba kaji Yashmeen wai ba nawa bane.”
  “Seta hanashi zama nakin ai muga.”
  “Baba wai dagaske motan Zeezee ne wannan?” Asked Omar.

    *** Around 9:23PM
  Zeezee fa ba wasa se tuk’i take ta shiga d’akin Mama ta fito tayi d’akinsu Mariam tayi parlour, ba inda bata shiga da motar tata har bathroom, Yasmeen da takeson tad’an d’ana itama taje ta samu Zeezee kafin ta baro parlour. “Zeezee ta d’an ara min motarki na nad’a kinji?”
  “O’o manya bashuwa chiga.”
  “Manya erinsu Adda Mariam da Ya Ibraheem ba? Yi hak’uri.”
  “Ni o’o banasho.” Da k’yar Yasmeen ta iya shawo kanta ta yarda ta bata dan d’anawa, dududu da shigan Yasmeen befi minti d’ai ba Zeezee ta soma k’iriniya ita a bata motan ta Yasmeen da mota ya mata dad’i kuwa tak’i. D’an karen banzan ihu ta saki tare Baba ya shigo yana tambayan ko lafiya “ya haka? Me kikeyi k’atuwa dake cikin motan Zeezee?”,Yayi tambayar wa Yasmeen dake ta raba ido bayan ta fito daga motar. Nan Zeezee tamai bayanin komi, “yi hak’uri K’anwata kekuma ki sake shiga mata mota kiga k’atuwar banza kawai.”

  Washegari da safe bayan sun karya Yasmeen ta saci jiki tayi store room da ledarta a hannu, gongonin madaran Zeezee ta bud’e tana d’iba tana cikin haka Zeezee ta shigo d’aukan juice ta ganta “laaaa!! Yashmeen!” Ihunta yasa Yasmeen b’arar da madaran dake hannuntan. “Wayyayi sena gayawa Baba kina d’iba min madala” nan danan Yasmeen tashiga tarawa “yi hak’uri Zeezee dan Allah karki fad’a mai zemin masifa.”
  “Wayyayi shena fad’a” nan ta juya
  “Tsaya kiji, zan had’a miki naki kema a leda seki sha da akwai dad’i sosai.”
   “K’alya kina shon kimin wayo.”
  “Wallahi ba k’arya ba” wasu ledan ta sake cirowa tasawa Zeezee madara da milo ciki sannan itama tayi haka anata sede nata yafi na Zeezee yawa aikuwa uwar rigima ta hau ihu  “wayyayi naki yafi nawa yawa ki k’aya min.”
  “Toh kiyi shiru mana sekin fallashemu ne.”
  “Ni sekin k’ala min” tasake sa kuka ai kafin su hankara Mama ta diro d’akin tare da kamasu red-handed. Take Yasmeen ta b’oye ledarta a baya Zeezee kuwa se fitina take “ni ki k’ala min”
   “Me za’a k’ara mikin?” Ido Yasmeen tama Zeezee nufin tayi shiru ta b’oye nata itama amman ina ita bata nan take ba, “Yasmeen ne tasha min madala kad’an nata da yawa.”
  “Madara!” Exclaimed Mama, “Yasmeen ban hanaki d’iban madara kina sha ba?” Kame-kame Yasmeen ta shiga tana b’arin baki.
  “Ni ki k’ala min” Zeezee tayi breaking silence d’in.
  “Oya kawo madaran nan dukan ku” ba musu Yasmeen ta kai nata “kema Zeezee bani naki” kaman dagske ta nufa wajen Mama kamar kyaftawan ido tabi gefenta tasa gudu taje ta samu Baba tasha madaranta tayi nak!

    Da Azahar bayan fitan Baba, kowa na zaune tsakar gida yana harkan gabansa Mama ta duba ta duba bata ga Zeezee ba haka kawai jikinta ya bata aduk inda take b’arna take “Yasmeen jeki dubo min me Zeezee take, shirun yayi yawa” da ‘toh’ ta mik’e cikin gidan kap ta duba bataga Zeezee ba chan bayan BQ ta tsince ta da irin manya-manyan dusten goge k’afan nan ta had’a ruwan kumfa tana dirje k’afanta dashi in aka tambayeta haka taga me wankin su nayi any moment ya gama wanki. “La ha ilaa!! Mama zo kiga abinda Zeezee keyi dirje k’afanta take da dutsen Sabi’u.” Daga tsakar gidan Mama tace, “wallahi Zainab ki tashi kibar wajen kamin na iso, ke ina kika ga k’afan ma bale kice zaki wani dirje, bar gun nace kokuwa inzo in miki shegen duka gashi dama Babanku bai gida.”
 
   “Kuma wayyayi balin shake baki shweet d’ina ba tunda kin fad’awa Mama.” Zeezee tayi maganan wa Yasmeen tana barin gun, koda tazo shigewa ciki bata ce wa Mama dake ta faman kiran sunanta ko uffan ba. D’akin Mama ta nufa ta tara teddy bears nata sannan ta bud’e turaren Mama ta zazzage kan teddies d’in k’amshi har waje malam!
   “Tsaya wannan ba k’amshin turare na bane?” Mama tayi maganan tare da miqewa ta nufi d’akinta. “Ai ba turare d’aya bama” cewar Mariam. Mama na tabbatar da hakan ta kama Zeezee ta mammaketa bada jimawa ba Baba ya dawo sarkin d’aure wa k’arya gindi, balbale Mama ya shiga yi bayan na ya lallashi Zeezee.

   Can da yamma, bayan fitan Baba masallaci yaran kuma Islamiya Zeezee tayi parlourn Baba kawai setaji bari ta gwada cin buttons na remote yau, one-by-one ta soma bi seda ta cinyesu tas sannan ta ajiye. Ta ajiye kenan kafin ta bar gun Baba ya dawo harfa yayi d’aki wani abu yace mai ya dawo dan yadda yaga Zeezee na raba ido “Laaa’ila!” Yayi exclaiming, gudu Zeeze tasa zata bar gun ai tuni ya kamota yana bin remote na Plasma TV’nsa da kallo yace, “meh haka? Remote abinci neh da zaki kama ki cinye buttons d’in!” Lamo tayi tana kallonsa a yayinda idanunta ke cikowa da hawaye “dan bana zaneki koh?” A dai-dai nan Mama tashigo parlourn “ya haka nakejin hayaniya?”
  “Kalli fah! Remote d’i TV’n ta cinye kap! Abin naki lafiya kuwa Zeezee?”
  “Ahap! Ai kad’an ka gani wallahi wataran tab’arya zata d’au ta fasa TV’n nan naka dashi ba wai kai komi tayi dai-dai neba, this is just the begining Zeezee kinyi dai-dai.”

  “Wani irin magana kike haka Hafsah, kamar ya zakice mata tayi dai-dai? Remote fa ta ci.”
  “Da take kira na da suna na kota zagen kota min b’arna me kake cewa? Yarinya ace abarta koba haka ba? kaima seka barta yanzu yarinya ce, Auta ta taho muje kici abinci” da gudu Zeezee tayi gun Mama ta d’aga ta.
   “Wallahi kin kyauta ke kuma wai bakinki razor ba ki sake cimin remote kigani mschww!”
  “Ramin mugunta tauna shi gajere!” Mama tayi stating tare da baro parlourn.

~* ~* ~*
  Monday morning as always and usual Zeezee tayi ta daru da k’yar aka samu aka shiryata school seda taga Lubiee hankalinta ya kwanta.
  Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa Zeezee, rikicin yau daban na gobe daban ga wani masifaffen rashin kunyan da take tashi dashi kuwa ba wanda ya isa ya tab’ata a gidan, ka tab’ata ma jikin ka ze ma bayani. Ba yadda Mama batai da Baba asa Zeezee a islamiya ba sam yak’i wai seta k’ara girma. Ana cikin haka bikin ‘yar Aunty SDY ya iso duk events da akayi Mama tasamu hallara, sauran kai amarya Kano da za’ayi da kuma yin dinner da ya rage, cikin sauk’in kai ta tambayi Baba izini ya kuma bata.
   Kayakin Mama ne baje kan gado se had’a akwatin ta take tana cikin yin hakan Zeezee ta shigo d’akin delibrately matching Mama’s ironed clothes da motan ta.
 
   “Sabon iskanci nekuma haka Zeezee kina ji kina taka min kaya matsa min!”
  “Toh ba na miki honk ba” ta murgud’a baki.
  “Dake da honk d’in uwaku.”
  “Kema-”
“Wallahi kika kuskura kika zageni dukan ki zanyi a d’akin nan” Mama tayi saurin katse ta. “Ni thank god ma gobe zanyi tafiya in huta wallahi.”
  “Nima shena biki.”
  “Ai da inyi tafiya dake gwara na fasa tafiyan” ba tare da Zeezee ta tanka Mama ba taja motan ta tayi d’akin Baba kukan munafirci ta soma tana mishi bayanin abinda ya faru ba tare da b’ata lokaci ba ya mik’e suka dawo d’akin Mama aiko tana ganinsa jikinta ya bata Zeezee ce takai k’ararta.   “Wallahi Ahj inma batun inbawa Zeezee hak’uri kazo yi is better ka koma dan ba bata zanba yau abin nata is getting out of hand.”
  “Kinsan kinyi laifi kenan, anyways ba abinda ya kawoni ba kenan ki had’awa Zeezee kayakin ta itama da ita zakiyi tafiyan.” Zumbur Mama ta mik’e tsaye tana zaro ido, “da wa zanyi tafiyan? Wallahi baran je ko ina da wannan maras kunyan ba.”
  “Kin de jini” ya fad’a authoritatively.
  “Wallahi bazan yi tafiya da yarainyan da bata jin magana naba, kalan taje tabani kunya a idanun jama’a, ace yarinya sede bata ga abu gun yara ba tace itama se an siya mata kuma da kake wani cewa zata bini makarantar ta kuma fa? Kai zaka je mata?”
 
 
  “Ba yau Thursday ba, Friday ne kawai bazata jeba ai, Sunday kun dawo Monday ta wuce school koba haka ba?”
   “Wallahi ba haka ba, ba inda zanje da wannan yarinyan ehe!”
“Ni shena biki Hafsah!” Zeezee tayi maganar cike da tsiwa da fitsara.
  “Nifa na gaya miki Hafsah.”
  “Wallahi da inje da ita gwara na fasa tafiyan ai dama anyi me yawan, dinner ne daman kawai ya rage se in fasa zuwa.”
   “Eh sede ki fasan amman muddin zaki sekinje da Zeezee.”
  “Eh nafasan...” Bayan ficewar Baba, Mama ta d’au wayarta takira Aunty SDY tayi making up excuses kan bazata samu zuwa ba dan ta gwammaci missing bikin da tai tafiya da Zeezee.

★★★
   Haka Allah ya cigaba da raya Zeezee har takai matakin primary 2 a karatu tanada actual 6 years kenan, tana girma se dad’a kyau take sede wani hanzari ba gudu ba, hak’waran gabanta duk sun zube se gib’i kake gani in ta washe bakin hakan yasa siblings nata suke making jess of her suyi ta mata dariya itako tayita kuka tana jan Allah ya isa in Baba ya dawo ta gaya mai ya d’au mataki. Zeezee de kam ta gagari kowa a gidan rikicin yau daban na gobe daban, bata jin maganan kowa se na Baba.

  _Saturday evening, 4:38PM_
  Mama ce zaune tsakar gida tana gyaran farce Zeezee ta shigo sanye take cikin wani ‘yar kanti iya gwiwarta, kitson shuku biyu ne akanta wanda ya sha beads. “Mama!” Banza da ita Mama tayi “Mama!” Ta kira for the second time.
  “Meh? Meh? Meh kuma kikeso yau?” Tayi maganar tare da d’ago kai tana k’ura wa Zeezee ido.
  “Kibani d’ari cikin kud’in da Ya Zannah yabani ranan.”
  “Wai shin an gaya miki kud’in naki haifafa yake ne? Dubu biyu ne kacal kuma a tambayan k’ananun canji duk kin k’arar da dubu biyun, d’arin dana baki jiya shine k’arshen kud’in naki.”
   “Wallahi k’arya ne kina son ki kashe min kud’ina ne kuma wallahi bazan yarda ba” tayi maganan tana bubbuga k’afa. Dirty look Mama ta watsa mata sannan ta cigaba da yankan farcenta ganin haka Zeezee ta wuceta takai dab da shiga d’akin Mama kenan Mama ta sa mata kira “Zeezee! Wallahi kika kuskura kika tab’amin kud’i kinji na rantse dukan ki zanyi na gaya miki kud’inki ya k’are.”
  “Wallahi zaki gani” cewar Zeezee in a very low voice hawayenta ta share sannan ta d’au hanyan barin gidan “kuma ki dawo ki sa hula kafin ki fitan.”
  “Barin sa ba” ta murgud’a baki sannan ta fice. Gidan Ummu Mufeeda ta nufa bayan tayi sallama ta gaishe ta “yauwa sannu Zeezee yawo ba d’an kwali ko? Bakisan bakin mutane kad’ai ya isa ya karya miki wannan sumar taki ba?” Shiru Zeezee tayi batace komi ba as tana nazarin wani k’aryan zata mata chan tace, “yauwa Mama na ne ta turoni wai in kinada N500 ki bata in ta samu zata miyar miki, batada cenji ne kuma tana son ta sallami wani.”
 
  “Ji Maman Zeezee de dawata zance meh d’ari biyar kuma?” Tayi maganan tana ciro d’ari biyar d’in daga lalitarta “gashi kai mata.”
  “Toh nagode” ta amsa tare da ficewa, kantin Ya Wakeel ta nufa ta kashe d’ari biyar d’in tas cikin sayayyan shirmen banza sannan tadawo gida Mama na ganinta bata ce mata komi ba ta wuce da ledar parlour. Bajewa tayi kan rug ta tab’a wannan ta tab’a wancan tana cikin haka Mama ta shigo, ko d’ago kai ta kalleta batai ba se shan chocolates nata take “ke ina kika samu kud’i kikayo wannan siyaya?” Shiru... “Dake fa nake magana! Am very sure babu kalan wad’annan chocolates cikin na school naki.”
  “Haaa’ah! Nikam ba kud’in ki na d’auka ba ina ruwanki?”
  “Kinsan Allah zan mauje ki, ina kika samu kud’i nace?”
  “Nima ban sani ba.” Ganin Mama tayo kanta da nufin bugin ta tasa ihu “zan fad’a zan fad’a.”
  Oyya speak up!”
  “Gidan Ummu Mufeeda naje nace kince ta ara miki d’ari biyar-”
  “Ni?!” Mama ta dafe k’irji.
  “Amman karki damu tace ta baki a kyauta kinga ba sekin biya taba.” Bata hankara ba Mama ta fisgota ta hau nad’a mata na jaki bayan ta mata lik’is ta tattara chocolates d’in tayi sadaka dasu wa almajirai. Kuka kenan! Kuka Zeezee tayi tayi tana jan Allah ya isa har bacci ya isketa a garriage koda yaran suka dawo daga islamiyya suka ganta kwance gun basuyi ta kanta ba dan sun san halinta sarai daga tambayarta meya faru seta hauka da rashin kunya kokuwa in Baba ya dawo tace kai ka tab’a ta.

  Cikin bacci Zeezee taji k’aran security’n motan Baba, firgit ta mik’e ta shiga rusa sabon kuka bayan yayi parking motar taje ta same sa tana hawaye “ya haka K’anwata keda waye?”
  “Maamaa!” Ta fad’a a shagwabance.
  “Me ta miki yau kuma?”
  “Duka na tayi haka kawai” d’aga ta yayi ya share mata hawayen sannan sukayi ciki “Hafsah! Hafsah! Wallahi muguntan naki ya soma yawa kullum sede ba’a barki da ‘yar nan ba se kiyi ta dukanta sekace ganga? Ina kike fito nace!” Da confidence nata ta fito “ai bakaji me tayi yau ba...” nan ta kwashe labarin komi ta bawa Baba hoping he’ll back her today, to her suprise bayan ya gama sauraronta yace, “toh laifin waye? Da kin bata kud’in da ta tambayekin da duk hakan ya faru ne?”
  “Lallai ma Alhj!” Mama ta fad’a short of words, “kana nufin tayi dai-dai kenan?”
  “Bance tayi dai-dai ba amman you are partially to blame kuma karki sake tab’a ta dan wallahi zan soma jan Allah ya isa.”
  “Wallahi sede kaja amman muddin ta sake tafka rashin hankali kaman na yau banga me hana ni dukanta ba abin kunya yarinya is 6 years old almost getting to 7 amma banda fatiha da nas, falaq and ikhlas ba abinda ta sani” tana kaiwa nan tayi ciki.
  “Kar ki jita kinji K’anwa ta zan nemo miki malami yana miki karatu a gida islamiyya nede bara kije ba.”
  “Toh Baba.”
  Alwalan Sallan Maghrib suka shiga yi kasancewar yau Baba ne ze jasu a gida kowa na alwala banda Zeezee datayi cross leg kan kujera tana game a ipad, fitowan Mama daga bayi ta galla mata harara “ke bazaki tashi kiyi alwalan bane?”
  “Barinyin ba!” daidai nan shigowan Baba d’akin kenan “ina yaran suke? Ku fito muyi sallah.”
  “Zeezeen fah? Baza tayi sallan bane?”
  “Ke ina ruwanki yarinyan nan is just 6 kuma ko a muslince ma cewa akayi se yaro yakai 7 a soma sasa.”
  “Meh laifi idan an fara sata yanzu?”
  “Kanki akeji Ibraheem ku fito.” Nan suka fiffito Baba yahau jansu bayan sun idar Baba yasa Zeezee ta d’auko school bag nata dan yin homework nata.

   “Zab’i wanda ze miki homework d’in amman banda Ibraheem kinga yana aikin project nasa” (Ibraheem is now a petrochemical engineering student at ATBU) yana 400 level.)
  “Ni shi nakeso.”
  “Yi hak’uri k’anwata gobe shi ze miki amman yau ki zab’i daya cikin sauran kinji? Maza jeki su miki kizo mu kwanta” ba tare da tace komi ba ta fice k’aramin parlour, su Mariam ta tarar ba Ibraheem. “Ya Omar kamin homework d’ina.”
  Omar dake jin dad’in chatting dayake ya d’ago kai tare da galla mata harara “bazanyi ba bakiga ina amfani da waya na bane.”
  “Kana chatting da budurwa de kuma sena fad’awa Baba kema Adda Mariam naji ranan keda Ya Ibraheem kuna magana wai wani friend d’inshi na sonki duk sena fad’a.”
  “Banza yanzu ma kije ki fad’a” cewar Mariam tare da watsa mata harara.
  “Zaka min ne ko sena je na gayawa Baba?” tayi maganan tana hararsa da manya-manyan idanunta.
  “Kawo in miki” yayi maganan full of sarcasm, wurga mai jakar nata tayi “Verbal Reasoning ne da Quantitative inka gama ka kaimin jaka na d’aki”  ta k’are maganan tana harararsa.
  “Kutcee! Ya Omar kana jinta take ma wannan rashin kunyan?” Cewar Yasmeen.
  “A’a’hah! Barta kekam” yadawo da kallonsa kan Zeezee, “in nagama zan kai miki suke nan homwork d’in?”
  “An bamu a handwriting ma shima kamin page 17.”
  “Lallai! yanzu handwriting d’inma bazakiyi ba?” Yaseen ta fad’a.
  “Ina ruwanki?” ta murgud’a mata baki “dan bance kimin ba kike da bakin magana koh?”
   “Ahh ahh! Kekam Yasmeen barta mana, jeki kwanta ‘YAR GATAN BABA.” Dad’i sosai taji taje tayi ta game nata a d’aki koda Baba ya tambayeta assignment infa? K’arya ta mai tace sun gama.
  “Omar I don’t trust you what are you planning on doing? Yau kai ne Zeezee ke ma rashin kunya haka baka ce komi ba” states Mariam.
  “Bar ni da ita Adda Mariam ita ba hegiya ba, kwab’a mata homework d’in zan ta kama zero yadda gobe za’ayi punishing nata da kyau.”
  “Pwhahhah!” Suka kwashe da dariya “wallahi amman ka burgeni da haka zamuna getting back at her fitsararriyar yarinya haka” Yasmin tayi maganan tana jin dad’i.

  DON’T BE A SILENT READER TELL ME HOW U ACTUALLY FEEL, THINK ABOUT MY NOVEL
 

MIEMIEBEE
👄👄👄👄
  www.beeenovels.blogspot.com

4 comments:

Kyller said...
This comment has been removed by the author.
Kyller said...

It's very interesting and educative, tun ba'ayi nisa bah...This shows us exactly what happens in the outer world! Keep up with the hard work dear, more grease to your elbows! Allah ya kara basira. Aameen

Unknown said...

Hmmmm er uwa kinyi kokari Allah ya kara basira.

Unknown said...

Sis dis ix just superb.....kip it up dearie