BY MIEMIEBEE
PAGE 44
"Ummi no, ba ita bace."
"Then wacece, Nazeefah?"
"Eh Nazeefah, Nazeefah ce Ummi."
"Ni yanzu ka rud'a min kai, Nazeefah ce tafi kwanciya maka a rai kokuwa ita zaka saka?"
"Ummi hankalina yafi kwanciya da Amal."
"Toh Alhamdulillah in shaa Allah hakan shi yafi alkhairi."
"Ummi Nazeefah kuma fah? Shikenan yanzu semu rabu?"
"Toh ya zamuyi Prince? Rabuwa da ita ya zamo dole se inde zaka bijire wa za6in da Allah yayi maka ka saki Amal wanda nima ba barinka zan ba tunda har Allah ya riga yayi ma za6i."
"I know Ummi kuma nima komin yaya bazan ta6a iya rabuwa da Amal ba but Nazeefah kuma fa? Na tabbata baza ta ta6a yafe mun ba, zan iya cewa soyayya na ne kad'ai ya bata wuya a rayuwa. Lokacinda ta soma jin dad'in aurena kuma na kama na k'ara aure nayi mata kishiya. Ban ta6a kyautata mata ba Ummi and now da abunda zan sak'a mata kenan bayan duk wannan wuya da ta sha? I need to treat her right one more time please ki taimakeni Ummi."
"Hak'urin nan de shi zan cigaba da baka Prince, nasan da wuya Nazeefah ta kar6i bak'on lamarin nan da hannu bibbiyu kaman yadda ka fad'a amma as time progresses zata gano cewa za6in Allah shine mafi alkhairi a gareku gabad'aya kuma ba kullum bane muke samun abinda muke so. Don yanzu koda ka bijirewa za6in da Allah yayi ma ka saki Amal kabar Nazeefah, ba alkhairin da ze biyo bayan hakan se ma sharri. Se ka ga ma rabon ya zame mata ajali, kuma zancen wai baka ta6a kyautata wa Nazeefah ba kaima kasan k'arya ne. Duk kulawan da ya kamata ace mace na samu daga gun mijinta kayi mata kuma itama ta sani, so just calm down and do what's right Allah na tare da kai."
"Thank you Ummi" da haka ya katse wayan yayinda kalamun Nazeefah suke ta yi masa yawo akai. Ji yayi gabad'aya baze iya sauwak'e mata ba. Dama seda ta fad'a mishi cewa tasan Amal ze d'auka akanta saboda baya sonta se Amal se gashi kuma Amal d'in ze d'auka yanzu. Sede ba don baya son ta bane kaman yadda ta fad'a se don Amal ce za6in da Allah yayi masa kaman yadda itama Yayi mata lokacin da zata aureshi. Tsoronsa d'aya kar wannan za6i ya sake 6ata tsakanin wannan 'yan uwa. Dan kaman yadda Nazeefah ta sanar da shi ya tabbata muddin idan taji Amal ya bari ya saketa seta tsani Amal fiye da yadda ta tsaneta yanzu. Oh Allah shin ya zeyi yanzu? Idan da ace ze iya rabuwa da dukansu biyu da yayi dan hakan shi zefi wa kowa kwanciyan hankali. Gara duka su rasa sa da ya d'au d'aya yabar d'aya amma yaya ya iya? Zuciyarsa bazata iya jure masa rashinsu duka ba barin ma Amal tasa da yake ganin idan har ya rasata baze iya sake samun mace mey kyawun halatayya irin tata ba. She's just different.
Mik'ewa yayi a hankali yabar d'akin ya nufi nasu inda Amal ke kwance a kan gado se tunani take. Har ya k'arisa kan gadon bataji shigowansa ba. Seda ya kira sunanta tukuna.
"Rania?" Da mamaki cike da tsoro ta mik'e zaune tana kallonsa. Bazata iya tuna when last ya kirata da wannan suna ba, probably tun da ya gano cewa ita da Nazeefah 'yan uwa ne. Ganin bata da niyyan amsasa seya mik'a mata hannunsa da nufin ta sa nata a ciki. Bayan dogon nazarin da tayi daga k'arshe seta mik'a hannunta ta sanya cikin nasa inda ya mik'ar da ita tsaye akan k'afafunta. Na matuk'a kanta ya d'aure yayinda zuciyarta ta shiga bugun tara-tara barin ma da Afzal ya rungumeta a jikinsa.
Shikenan ya tabbata ita zata tafi. Se bata kawai jikinta yake itace ze saka, tasani zamanta da shi ya k'are, ta sani Nazeefah ce tafi kwanciya masa a rai, ta sani Nazeefah ce za6in da Allah yayi mata. Tabbas tayi musu murna sedai kuma tayi k'arya idan tace bata ji zafin hakan ba because she loves him. No matter how hard she tried not to show how terrified she felt takasa saboda yadda take jin zafin rabuwa da shi. Kawai ji tayi hawaye na gangaro mata daga ido dai-dai wannan lokaci Afzal ya d'agota daga jikinsa da k'yar dan yadda ta kankamesa. Cike da mamaki ya tsaya kallon yadda take kuka sannan daga bisani ya shiga share mata hawayen nata "Please don't cry Rania."
"I should really start packing my clothes" ta sanar dashi tana mey hana k'wayoyin idanunta had'uwa da nasa. "I'm really happy for you two Yaya, Allah ya baku zaman lafiya mey d'aurewa."
"Mey kike cewa haka Rania? Zaman lafiya tsakani na da waye?"
"Da Nazeefah."
Murmushi ya saki kad'an "Meyasa kika ce haka? Why not you?"
"Saboda bani ce za6in da Allah yayi maka ba Yaya. I know I'll be the one to leave and even though nima hakan ne ze fiye mun kwanciyan hankali I just can't deny the fact that I still love you so very much and I'll miss you so damn much."
"But you don't have to miss me Rania because you're not going anywhere, this is your home anan kuma zaki cigaba da zama ba inda zaki."
"No ba sekayi hakan ba Yaya, zanje in samu Mami a gida, chan d'in ze fiye mun kwanciyan hankali yaso ko haya ne se kasa a nan d'in." Dariya sosai ta basa wanda ya kasa dannewa yayinda ta tsaya kallonsa cike da mamaki da takaici. Mey yake nufi da hakan?
"Rania listen to me, ba inda zakije nan ne gidanki kuma d'akin mijinki okay?"
"D'akin mijina? Nazeefah kuma fa? Karka bijire wa za6in Allah saboda son zuciya Yaya. Idan kuma tsoron abinda Papi da Mami zasuce kake then ka kwantar da hankalinka kasani duk zasuyi maka kyakkyawar fahimta kaman yadda nima nayi maka. We all know you love me Yaya, please don't bother yourself."
"Tsaya, kafin muyi aure mey kikayi? Kinyi Istikhara right?" Kai ta gyad'a masa a hankali cike da rashin fahimta sannan ya cigaba "Kuma bayan da kika gudanar se waye Allah ya za6a miki?"
"Kai Yaya" ta amsa a takaice.
"Kina ganin it is possible ace ni kuma nayi Istikharan yanzu se wata ta daban ta zame za6in da Allah zeyi mun bayan ke kuma ni Ya za6a miki?"
"But Yaya-"
"Ki sani Rania ko sau dubu mutum yayi Istikhara za6in Allah d'aya ne sedai idan shi yaso bijire wa hakan. Kaman yadda kikayi naki istikharan Allah ya za6a maki ni, nima haka ya za6a min ke yanzu. We two are meant to be Rania in shaa Allahu mutuwa ce kad'ai zata shiga tsakani na dake. Rania I love you so much kuma Allah kad'ai ne sheda game da irin son da nake yi miki, shi kad'ai yasan idan bake bazan iya rayuwa ba, shi kad'ai yasan muddin na rasaki bazan ta6a iya samun kamilar mace mey kyawawan d'abi'u da halatayya irin naki ba shiyasa ya za6an min ke ya sake bani daman da zan soki in kuma kula dake har ila k'arshen rayuwa na. I can't do without you Rania and I can't ask God for more da ya sake bani daman kasancewa mijinki, forgive me for all the times I've wronged you Rania, I'm terribly sorry please forgive me."
Kuka Amal ke sosai yayinda ta kasa amincewa da abubuwan daya fad'a mata. Se gani take kaman a mafarki komai ke faruwa tabbas itama bazata iya rayuwa idan ba shi ba. Gani take kaman duk yadda yake jin yana sonta ita tafi sonsa, don dai kawai ita bata nunawa ne. Daga k'arshe kuma bazata iya yima Allah godiya ba da ya sake bata daman kasancewa matarsa, sai dai kuma bazata iya duba irin rayuwan k'unci da tashin hankalin da Nazeefah zata fad'a ba a rashin Afzal. Se gani kawai take inda itace Afzal yace ze sauwak'e wa. Tasan duk kalan rashin tawakkalinta tana bayan Nazeefah. Tasan Nazeefah na iya yin k'aramin hauka akan wannan dalili, she knows this is not going to be easy on her shiyasa take tausaya mata sosai.
"Rania?" Ya kirata bayan shirun da tayi, jikinsa kawai ta fad' yayinda ta shiga yin kuka na sosai. "Bakayi mun komai ba Yaya don haka ka daina tambaya na yafiya I love you so very much." Ba k'aramin dad'i kalamanta suka sanyasa ba, matseta tsam ya sakeyi a jikinsa tamkar ana shirin k'watan masa ita yayinda wani irin sonta yake sake shiga zuciyansa. Sun dad'e a haka sannan daga bisani ya janyeta daga jikinsa sede har anan hawaye Amal ke.
"Please don't cry Rania."
"I wish I could stop Ya Omri."
"But there's no need to."
"There's every need to cry Ya Omri."
"Saboda ban barki kin tafi gida kaman yadda kikeso ba kike wannan kuka Rania? Saboda Allah ya za6an min ke? Ashe ba haka kika so ba, I thought you said you love me" Kai ta gyad'a mishi take tana murmushin takaici.
"Then meyasa kike kukan? A tunani na this is supposed to be the most happiest moment for us both."
"Yes it is Yaya kuma hawayen nan da kake gani, hawayen farin ciki ne gani nake kaman a mafarki komai ke faruwa, I can't believe that we're still going to remain married to each other after hope has been gone."
"I feel thesame way Rania, but tun farko tun kafin in gudanar da Istikharan nan nasan komin yaya akayi ni dake bamu rabuwa."
"Ko meyasa kace haka?" Tayi saurin tambayansa cike da mamaki.
"Saboda Istikharan da kikayi kafin mukayi aure Rania, idan da har ace akwai sharri a auran mu da Allah baze za6a miki ni akan Abdul daya kasance masoyinki ba. Idan har na rabu dake kinga kenan babu amfanin istikharan da kikayi. Ko ce miki akayi shi istikhara temporal decision ne na d'an lokaci? Hankali na ya tashi ne gabad'aya saboda Nazeefah. Ina matuk'an tausayawa halin da zata shiga idan har ta gano cewa I chose you over her, shiyasa nayi coming up da plan na cewa zanyi Istikhara kinga idan har nayi ita da iyayenta bazasuyi mun mumunar fahimta ba, zasuga za6in Allah nabi ba wai na zuciya na ba. Sedai kuma yanzu bayan dana gudanar da hakan nakega still Nazeefah bazata amince ta kar6i wannan bak'on lamarin da hannu bibbiyu ba. Nasan komin tayaya bazata ta6a fahimtar cewa Allah ne ya had'ani dake ba, bazata ta6a gane cewa ba komi mutum yake so a duniyan nan yake samu ba, gani take komai laifinki ne Rania and that is what hurts me the more knowing who you really are. Bana son a sanadin hakan ta sake tsanarki, ita gani take komai laifinki ne, ke kika janyo bayan ba haka bane. I wish Nazeefah could see this kind and selfless side of you. Har yau kalaman ki na yinin ranan da na sanar dake cewa Nazefah k'anwarki ce suna kaina. Har yau na kasa mancewa dasu kuma bazan ta6a mancewa da su ba. Yadda kika cire son kai kikace kin yafe ni wa Nazeefah even though kina so na bawai bakiya sona ba se don cewa da Annabi yayi "La yu'minu ahadukum hatta yuhibbu li akhihi ma yuhibbu li nafsihi" [imanin d'ayanku baya cika har seya so wa d'an uwansa abinda ya so wa kansa] I get that you love me but you're willing to let your sister have me and ba kowa keda irin imanin nan naki ba Rania ko ni nan bazan iya aikata abinda kikayi ba ranan saboda haka kuma naji respect naki ya k'aru a idona yayinda sonki ya sake k'aruwa a zuciya na."
Murmushin jin dad'i ta sakar masa tana mey share hawayenta "Ka sani ko da nace maka hawayen nan na jin dad'i ne k'arya nayi because zuciyata tausayawa Nazeefah take, I can't imagine the kind of hell she'll go through Yaya don haka har nakejin kaman mu hak'ura da juna sedai kuma bazamu iya yin jayayya da za6in Allah ba."
"Hakane Rania, let just pray for her in shaa Allah as time progresses zata fahimci komai ta kuma nemi gafararki ayi zaman lafiya gabad'aya."
"Da kuwa ba abinda zefi mun hakan farin ciki da jin dad'i Yaya. Inspite of how Nazeefah disperses me wallahi I still love her kuma zan cigaba da sonta ina yi mata uzuri har zuwa lokacinda zata gane gaskiya."
"Allah yayi miki albarka Amal ya baki yaran da zasu kula dake ranan da buk'atan hakan ya taso Rania, I'll forever love, cherish and adore you."
"Ameen Ya Omri I love you too."
"Let's eat out ai zaki iya fita ko?"
"Why not? Bari in shirya."
***
Washegari...
Dai-dai gaban gidansu Nazeefah yayi parking sannan ya zaro wayansa ya kira Daddy a karo na farko ya d'aga.
"Halo Afzal ka iso ne?"
"Eh Daddy."
"Toh bismillah mana ka shigo." Harga Allah beyi niyan shiga ciki ba amma yaya ya iya? Gyara packing nasa yayi ya k'arisa ciki inda ya samesa a parlour ya gaishesa. Bayan sun gaisa ya zaro takardan daya ninke daga aljihunsa ya mik'awa Daddy "Kaman yadda nayi muku alk'awari cewa zanyi Istikhara, duk kuma wacce Allah ya za6ar mun ita zan d'au in sauwak'e wa d'ayan. Toh game da sakamakon dana samu bayan na gudanar da Istikharan na yanke wannan hukunci ba don son kai ko son zuciya ko makamancin haka ba, da fatan kai da iyalanka zakuyi mun kyakkyawar fahimta. Ga takarda nan na sakin Nazeefah, dafatan ze isa gareta zaka kuma bata hak'uri a madadi na ni zan wuce."
"Dakata Afzal kar kayi saurin tafiya. Kayi hak'uri ka bani dama in baka hak'uri na jefaka da iyalinka cikin wannan rud'ani da tashin hankali da nayi. Kuma ka sani wannan hukunci daka yanke shine dai-dai koda ma ace bakayi istikhara ba bazan bari ka saki Amal ba saboda abinda nayi mata da mahaifiyarta kad'ai ya ishesu takaici da jarabawa. Dole nima in gir6e abinda na shuk'a. Da fari na d'au zan iya yi wa Allah wayo, na d'au idan har na aurar da Nazeefah shikenan bani da wani tsoro kuma ashe ba haka abun yake ba, ashe ita zina bashi ce idan har ka cita dole komin ta yaya ne ka biya. Kuma muddin ba a kaina ze ramawa Jameela abinda nayi mata ba dole se akan wanda nakeso. Dukda cewan Amal da Nazeefah 'ya'yana ne amma kaman yadda zanfi jin zafin sakin nan akan Nazeefah ba haka zanji ba idan da akan Amal ne saboda babu shak'uwan nan na uba da 'ya a tsakani na da ita. Allah ya za6an maka Amal ne saboda ya koya mun da 'yata darasi kuma saboda itama koda sau d'aya ne taji dad'in rayuwa. Ka sani wannan hukunci da ka yanke dai-dai ne kuma zanyi k'ok'ari in fahimtar da iyalai na, Allah ya baku zaman lafiya mey d'aurewa da Amal ya albarkaci rayuwanku in shaa Allah zan isar wa Nazeefah sak'onka."
"Nagode sosai Daddy."
"Ba komai, se kuma batun Jameela bazan gaji da rok'an kanka ba da kayi mun kwatance injeni gidansu in nemi tubarsu, idan ban samu sun yafe mun ba alhak'insu ya cigaba da bi na kenan, ka tausaya mun da iyalai na please Afzal."
"In shaa Allah zanyi ma Papi magana karka damu."
"Toh nagode sena ji daga gareka."
"Ba komai ni zan wuce" ya fad'a had'e da mik'ewa "Ka gaishe da Amal ina da niyyan shigowa inzo in dubata nima in nemi tubarta amma ina son in d'an bata lokaci saboda nasan yadda zata ji ta tsaneni yanzu."
"Zataji Daddy se anjima" yana kaiwa nan ya fice ya koma office har a yau idan ya gwada kiran layin Nazeefah bata d'agawa. Ba komai yasa yake son ya kirata ba se don so da yake ya bata hak'uri, baya son taga kaman baya sonta ne, har yau har gobe ze cigaba da sonta saboda akwai gur6in da ita kad'ai ce ta mamaye a zuciyansa. Ita ce macen da ya fara sani a rayuwansa, itace macen da ya fara sumbata itace macen da ya fara sharing wani abu nashi da ita. Shin har ze iya mancewa da ita a rayuwansa? He don't think so.
****
Daddy be samu ya kaiwa Nazeefah takardan nata a ranan ba se a washegari. Bayan ya dawo daga sallan Azahar ya d'au wayansa ya kira Mummy sedai kaman yadda ta saba ignoring call nasa hakan ma tayi yau don haka ya tura mata sak'o.
_Hjy Surayya kiyi hak'uri ki d'au wayan nan muyi magana. This is not about me it's about our daughter Nazeefah, thank you._
Sak'on ya shiga bada dad'ewa ba Mummy ta karanta se contemplating take ta kirasa taji lafiya ne ko ta bari. Chan k'arshe de ta kira wanda ya d'aga a karo na farko. Bata basa daman yin magana ba tace, "Meya samu Nazeefan?"
"Hjy Surayya wannan ba maganan waya bane gani nan tahowa yanzu."
"Karka 6ata lokacinka bana nan na fita."
"We both know k'arya kikeyi zanzo yanzu please" bata sake ce meshi komai ba ta katse wayan. Cikin mintuna da basu kai ashirin da biyar ba sega shi nan ya iso. Waya yayi mata akan ta fito nan da nan ta sanya hijabinta ta fice.
Ba yadda Daddy beyi ba da su k'arisa koda reception ne su zauna suyi magana tak'i, tace ita idan har baze fad'i abinda yake tafe dashi ba zata koma ciki. Toh suje cikin mota su zauna nan ma tak'i. Yasan sam bey kyauta mata ba amma ba wai yayi hakan dan ya raina ta bane ko makamancin hakan, shi tsoron sanar da ita yake gudun kada ta gujesa kaman yadda takeyi yanzu.
Hannu yasa a aljihunsa ya fito da takardan had'e da mik'a mata.
"Mey wannan?" ta tambaya ba tare da nuna yunk'urin amsa ba.
"Kedai bud'e ki gani." Kaman wacce bazata kar6a ba ta amsa ta bud'e had'e da karancewa.
_A ranan Laraba, goma ga watan Juneru shekara dubu biyu da goma sha takwas na saki matata Nazeefah, saki d'aya, biyu, uku saboda haramta mana zama da shari'a tayi a sanadin ta na kasancewa 'yar uwar matata Amal na jini._
Ajiyar zuciya Mummy ta sauk'e dama tasan za'ayi haka. Dama tasan Nazeefah ce Afzal ze saka kawai bata so ta nuna mata bane don kar ta tayar mata da hanaki amma tasan haka za'ayi dama kodan ma Allah ya kama Daddy yasa shima yaji zafin da mahaifiyar Amal taji sanda yayi mata fyad'e. Tasani dole ne wannan k'addara ya fad'a akan Nazeefah saboda itama Amal ta samu farin ciki koda sau d'aya ne a rayuwarta. Idan harda ace wannan saki akan Amal ya fad'a da Daddy baze ji zafi kaman yadda ace zeji yanzu da ya fad'a akan Nazeefah. Ta hakan ne kawai Allah ze sanyasa gir6e abinda ya shuk'a, ta hanyar mayar masa da 'ya bazawara kaman yadda ya k'wace wa 'yar mutane budurci.
"Shikenan ka huta ai yanzu Alhj, amma kasani nida 'ya'yana bazamu ta6a yafe maka wannan abun kunya daka aikata ba." Be bari ta shiga takawa ba yayi sauri ya rik'e k'asan hijabinta "Hjy Surayya bazan ma fara tambayan gafararki ba saboda nasan abinda nayi miki da 'ya'yanki is unforgivable but atleast give me a chance to apologize and tell you sorry. I'm gravely sorry for hiding the truth away from you, wallahi bawai don bana sonki bane kokuwa don bana mutuntaki yasa na 6oye miki wannan al'amari, sonki da nakeyi ne ya rufe min ido, bana son abinda ze shiga tsakani na dake Hjy Surayya, bana son in rasa ki. Dan son zuciya irin nawa se naga idan har na sanar dake gaskiya zaki gujeni kik'i aurena shiyasa na rik'e komai wa kaina. I love you so much Hjy Surayya and I'll never stop loving you, I'll wait. Zan jiraki koda kuwa zuwa k'arshen rayuwana ne amma bazan gaji da baki hak'uri ba dan Allah kiyi hak'uri ku dawo gida."
"Babu wani abinda zaka sake fad'amun da zaisa in canza ra'ayina. Idan 'ya'yanka kake so kana iya shiga ciki yanzu ka ebosu amma nikam takarda na nikeso. Kaman yadda ka shiga tsakanin auren yaran nan kasa Afzal ya saki Nazeefah saki ba d'aya ba, ba biyu ba har uku nima haka nake so ka rubuta mun nawa. Idan har 'yata zata shiga k'uncin rayuwa ka tabbata kai m seka shiga ninki ba ninkin nata don haka ka rubuta min takarda na yanzun nan anan. Tunda rayuwan zawarci ka za6a wa 'yarka tayi nima mahaifiyarta shi zanyi."
"Dan Allah kiyi hak'uri Hjy Surayya nasan nayi miki laifi, laifi babba amma dan Allah kiyi hak'uri ki gafirceni. Idan kika tafi kika barni ya kikeson in rayu?"
"Bakayi tunanin hakan ba kafin ka danne 'yar mutane kayi mata fyad'e? Se kaje chan ku k'arasa da ita mahaifiyar Amal d'in that is idan har zata iya yafe ma zaluntar ta da kayi."
"Kema kinsan bazan iya rayuwa da kowa ba bayan ke Hjy Surayya, kinfi kowa sanin yadda nake sonki tun ba yau ba."
"Sam ba haka bane, I was a fool to believe you love me Alhj, yaci ace tun a lokacin chan na gane kud'in mahaifina kawai kake so ba ni ba. Wallahi Allah ne kad'ai ze sak'a mun. Duk kalan halaccin danayi maka na sa mahaifina yayi maka duk baka ga hakan ba you still chose to lie and cheat on me."
"Dan Allah kiyi hak'uri bazan ta6a gajiya da baki hak'uri ba saboda nasan ban kyuata ba amma wallahi I love you Hjy Surayya I really do."
"Shin anya ma kuwa labarin daka tsara min da iyayena na cewa kai maraya ne gaskiya ne kuwa? Shin anya kuwa ba k'arya ka shirya mana ba saboda ka samu kaci arzikin mahaifina Alhj?"
Shiru Daddy yayi gun ya kasa cewa komai. Tabbas yayi mata da mahaifinta daya kasance hanshak'in mai kud'i bahaushe daga Kano k'arya lokacinda yazo aurenta. Saboda gudun da yake kar a nemi iyayensa kowani d'an uwansa a garin hakan asirinsa ya tonu na cewa yayi ma wata fyad'e a k'auye Mummy ta fasa aurensa ko iyayenta su hanata. Tun bayan da abin ya faru ya samu ya dawo makaranta be sake d'aga wayan iyayensa ba, duk lokacinda yaga kiransu baya d'agawa har ta tsinke saboda yasan akan mey zasuyi masa magana shi kuwa bayida abin cewa. Daga k'arshe ma da yaga kiran ya soma isansa se kawai ya sauya lamban wayansa gabad'aya, tun daga nan be kuma sake ji daga garesu ba se...
"K'arya kayi mana ko? Why aren't you saying anything Alhj?"
"Hjy Surayya yes, yes nayi miki da Abba k'arya batun iyayena amma wallahi ba don bana respecting naki bane se don tsoro da nake kar a garin hakan gaskiya ya fito in rasaki."
"Wani gaskiya?" tayi saurin katsesa.
"Batun abinda ya faru tsakani na da mahaifiyar Amal."
"Wane irin mak'aryaci ne kai Alhj? Mey nayi maka a rayuwa da ka za6i ka gina duk wani abinda mukayi accomplishing tare akan k'arya?" Ta tambayesa hawaye na saurin ciko mata a ido. "All I did was to love you Alhj I'm so disappointed in you na tabbata da Abba yana raye a yau da shima baze ta6a yafe maka ba."
"I'm truly sorry Hjy Surayya amma abinda ya faru ya riga ya faru idan da zan iya mayar da lokaci baya da nayi dan in gyara komai amma bazan iya ba please give me a second chance idan kika tafi kika barni taya kikeson in rayu? Tabbas idan ba ke su Nazeefah bazasu amince su dawo gida a gareni ba please kiyi hak'uri."
"Bayan k'aryan nan se kuma wani k'arya ka sakeyi mun?"
"Hjy Surayya a shirye nake da in sanar dake duk wani abinda kike buk'atan ki sani amma zaki galabaita tsaye a nan saboda labarina nada tsawo kiyi hak'uri mu shiga mota kokuwa mu k'arisa cikin reception." Bata ce da shi komai ba kawai ta shiga takawa yayinda yake biye a bayanta, a VIP reception suka zauna sannan Daddy yayi gyaran murya ya soma kaman haka.
"A shekaran da na dawo hutun second year d'ina ne muka had'u da mahaifiyar Amal wato Jameela wacce nake kira da Jamee na. Jameela ta kasance itace mace ta farko da Allah ya fara sanya min soyayyarta a zuciya na, so kuma na aure bana lalata ba. We started off as friends amma cikin k'ank'anin lokaci soyayya mey k'arfi ya shiga tsakaninmu. Jameela was simply everything I could ever ask for, lokacin da muka fara soyayya kwata-kwata shekarunta goma sha shida ne, she was so beautiful, young and innocent. Tsaftacacciyar soyayya muka gudanar nida ita as ko zance naje wajenta iyaka muyi hira ba wani ta6e-ta6e bale makamancin hakan saboda Jameela yarinya ce kamila wacce take san addininta sosai take kuma k'ok'arin bin dokokin da ya kafa mata. Ahaka ne har nazo na koma makaranta wanda bada dad'ewa ba Jameela tayi mun waya cewa mahaifiyarta na shirin had'ata aure da d'an chairman na garinmu idan har ban hanzarta turo magabata na ba ana iya aura mata shi d'an chairman d'in. Hankalina ne ya matuk'an tashi se Allah-Allah nake session d'in ya k'are in dawo gida. Kasancewar a scholarship na samu karatun seya zammana banida gatan dawowa gida kowani hutu se shekara-shekara. Addu'a muka tsayar sosai nida Jameela cikin ikon Allah kuwa se har wata shekarar ta zagayo shi wannan yaro be turo ba. Na dawo bada dad'ewa ba na samu mahaifina nayi mishi maganan Jameela akan ina son a tura tambaya gidansu sede sam Abba yak'i amincewa akan cewa da baki na ne zan ajiye mata idan nayi aure yanzu ina karatu. Duk yadda naso fahimtar dashi cewa Jameela bata da matsala da hakan besides ma ina d'an yin business, makaranta kuma shekara d'aya ne ya rage sedai hakan ya gagara Abba yak'i ya amince ya bani goyin baya. A sanadin haka nida Jameela muka shiga tashin hankali sedai bamu cire rai ba, muka mik'a komai ga ubangiji. Ban san ya akayi ba de amma wataran mahaifiyar Jameela ta jiyota muna waya bayan kuma ita ta riga tayi mata miji a sanadin haka tayi ma Jameela duka tayi seizing wayarta sannan ta horeta da kada ta sake kulani. Kwana biyu na daina ji daga gun Jameela ko na kira layinta baya shiga gashi sun k'are makaranta lokacin bale inje mu had'u a chan d'in. Rana d'aya kawai na jajirce na jeni gidansu dan yadda shirun yayi yawa, dukda cewan ta haneni da taka bakin k'ofan gidnasu saboda yadda ta nuna mun mahaifiyarta bata sona. A farko da naje mahaifiyar ta kar6eni da fara'a kasancewar bata gane waye niba a lokacin da nayi mata bayanin kaina kawai ranta ya 6aci ta sauk'e duk wani haushin da takeji a kaina tayi mun koran kare harda muciyan tuwo ta bini waje. Hakan ba k'aramin 6ata mun rai yayi ba dan dole na hak'ura da Jameelah saboda a rayuwa na washi walak'anci na kuma d'au alwashin sena rama cin mutuncin nan da tayi mun ko ta yaya ne. Rana d'aya ina zaune kawai sega kiran Jameelah ban 6ata lokaci ba na d'aga inda take sanar dani tana son mu had'u. Chan na kaita bayan gari da siyasan cewa abu nake so in nuna mata, ina son Jameelah amma abinda mahaifiyarta tayi mun ya tsaya mun a wuya ko kallonta nayi se na tuna da abin. Haka kawai shaid'an ya soma raya mun in d'au fansa akanta sedai kuma sonta da nake yana rik'eni. Amma haka shaid'an ya rinjayi zuciyana ta hanyan raya mun ai tunda mahaifiyarta tana sonta idan na ta6a lafiyarta kaman na ta6a na mahaifiyar ne don haka idan na lalata mata rayuwa abun seya fi wa mahaifiyar zafi. Ana cikin haka ne sega abokai na guda biyu dana basu labarin abinda mahaifiyar Amal tayi mun nan suka sake k'arfafamun guiwa suka bani had'in kai nayi ma Jameela fyad'e ba tare da d'igon imani ba."
"Koda mahaifinta ya kai k'arana dana mahaifina gurin mey unguwa k'aryata komai nayi na samu abokaina suka rufa mun asiri shima Abba ya goya mun baya saboda baze ta6a kawowa a ransa zan iya aikata abinda nayi ba. Acikin satin ko na gaba na samu na koma makaranta ban sake ji daga garesu ba. A karon chan ne na had'u dake Surayya, kika yi mun erasing duk wani bad memory'n dana bari da a k'auyen Askira. Tunda na sameki komai ya canza Surayya, soyayyar da kika nuna min ta dabance. Banida komai, Baki sanni ba, baki san wani nawa ba amma kika so ni kika kuma amince dani regardless. Ko a mafarki ban ta6a tsammanin cewa wataran zan iya mallakan 'yar babbar gida kamar ki ba mey hankali da tausayi. Lokacin da kika ce mun muyi aure ne nashiga tashin hankali badon bana sonki ba se don banason hakan ya tono mun labarina dana bari a garin Askira. Ban san da wani idon zan sake kallon iyayena da na shafesu a doron k'asa saboda selfish interest d'ina ba na kusan shekara. Rud'ani na matuk'a na shiga yayin da na rasa ya zanyi gashi bana son in rasaki saboda da in rasa ki gara na rasa komi nawa koda kuwa raina ne. Don haka nayi miki da Abba k'aryan cewa ni maraya ne. A tunani na hakan ne kad'ai zaisa Abba ya amince ya aura min ke Surayya. Ba abinda Abba beyi mun ba bayan dana aureki, abinda ya kama kayan da zansa, gidan da zamu zauna, motan da zan hau harta sadakin ki shi ya biya mun, komai da na sani na mallaka a lokacin na Abba ne. Harta aiki shi ya samo mun bayan da ya biya mun kud'i na gama masters d'ina muka dawo gida nan Nigeria idan ban manta ba kina da cikin Khaleefah."
"A lokacin da muka dawo ne bayan na tafi yin service d'ina na koma k'auyen Askira dan d'auko su Abba in nemi tubansu in basu hak'uri ake tabbatar min da cewa sunyi hatsari shekaru biyu da suka wuce a hanyansu na zuwa k'auyen Dambuwa. Shi Abba a take ya cika ita kuwa Umma tayi jinyan wata shida sannan mutuwa yayi halinsa. I felt hopeless and useless Surayya, iyayena sun mutu amma seda shekara biyu nake sani. Ji nayi kaman in soka wuk'a wa kaina in mutu wani irin d'a ne ni? Na sosai nayi nadaman abinda na aikata na d'au alk'awarin yin sadak'atul jariya da sunayensu Allah ya kai musu ladan kabari. Nasan rashin kyautatawan da nayi wa iyayena yasa nima Allah ya jarabce ni da gagararriyar 'ya kaman Nazeefah.l
"Daga gida na wuce gidansu Jameelah inda ake sanar dani suma sun tashi sun k'aura sun bar garin gabad'aya. Ba wanda ya sanar dani cewan rabo ya shiga tsakani na da ita bayan faruwan abun shiyasa ban ta6a sanin Amal 'yata bace se recently. Wallahi ba k'arya nake yi miki ba Surayya please believe me, taya zan so in had'a 'ya'yan cikina kishi Surayya bayan na san yin hakan haramun ne?"
"Yanzu ina ita mahaifiyar Amal d'in take Jameelah?" Mummy data amince da duk wani abinda ya fad'a ta soma da tambayansa.
"Tana cikin garin nan da zama amma bansan inda take ba, rannan Afzal ya taho da ita da mahaifinta gidan Nazeefah inda mukayi magana duka akan yadda za'a 6ullowa al'amarin nan nasu."
"Baka san inda take ba kace?"
"Wallahi ban sani ba Hjy Surayya ai kinsan bazan miki k'arya ba."
"Bawai ina k'aryata ka bane Alhj I just want to be certain, tana da aure?"
"Wallahi banda masaniya akan hakan amma base on abinda Amal ta ta6a fad'amun kaman mahaifiyar nata bata da aure."
"Ka aureta Alhj" ta sanar dashi. Da mamaki ya tsaya yana kallonta yayinda ya kasa amincewa da abinda tace.
"Eh?" Ya tambaya.
"Nace idan har Jameelah bata da aure kuma bata niyyan yin wani auran anan kusa ka aureta."
"Hjy Surayya kin ko san abinda kike cewa?"
"This's the only way zamu iya samu mu had'a kan yaran nan Nazeefah da Amal mu gyara zuri'ar mu. Ka fini sanin halin Nazeefah, yanzu da Afzal ya d'au Amal a kanta ba k'aramin tsanar yarinyar nan zatayi ba dama already ta riga ta tsaneta."
"Toh mey auro Jameelah zeyi ya gyara wannan lamari Hjy Surayya?"
"Tabbas auro Jameelah zaisa Nazeefah ta shiga hankalinta ta nutsu ta sani cewa mu dasu mun riga mun zamo abu d'aya yanzu ta kuma sani cewa shi kishiya na akan kowa ne idan har da tanayin kwatance dani tagani toh yau nima gashi anyi mun kishiya."
"Tabbas kinyi gaskiya Hjy Surayya amma bana son in had'a soyayyarki da kowa ke kad'ai nakeso."
"Karka damu dani kuma ma ai nasan kana son Jameelar taka har yau ko ba haka ba?"
"Amma ba kaman yadda nake sonki ba Hjy Surayya ni tausayin Jameelah kawai nake yanzu."
"Karka damu ai ni nace ka aurota."
"Hjy Surayya nifa banga amfanin yin hakan ba. Ba sena auro Jameelah ba."
"Ka aurota Alhj ni na baka dama karka damu."
"Surayya-" hannunta ta aza akan nasa cutting him off "Don't worry nima ai zama ni d'aya tal d'innan ya isheni ka kawo mun abokiyar zama tana tayani hira na tabbata kaman yadda Amal bata da matsala itama mahaifiyar tata haka ne."
"Wannan ba sekin fad'a ba Hjy Surayya Jameelah sam batada hayaniya."
"Toh kaga komi ya zo mana da sauk'i kenan, ka auro ta kaji?"
Hjy Surayya what can I say? You're the reason behind who I am today and everything I've achieved, banida bakin yi miki da Abba godiya. Allah saka da alkhairi ya cigaba da sanya miki albarka a rayuwarki ya kuma ci gaba da kai rahama kabarin Abba."
"Ameen Alhj tare da iyayenka kai ma."
"Kin hak'ura zaki biyoni gida?"
"Har sena amsa tukuna zaka tabbatar da hakan?"
"Gani nake kaman mafarki nake Hjy Surayya, Allah yabar min ke tabbas irinku acikin mata d'ad'd'aiku ne."
RANA D'AYA!💕
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
14 comments:
Wawu wawu😁😁😁👏👏👏! I'm extremely happy tonight, this chappy is a bomb💣🔥🔥🔥, rili did enjoyed it nakasa rufe baki... Thank you so very much miemie Allah ya miki albarka ya kara basira kuma #onelove
Wawu wawu😁😁😁👏👏👏! I'm extremely happy tonight, this chappy is a bomb💣🔥🔥🔥, rili did enjoyed it nakasa rufe baki... Thank you so very much miemie Allah ya miki albarka ya kara basira kuma #onelove
Thank you so much mimiebiee.
Godiya sosai, irin wannan basira hk ,Miemie Allah ya kr kaefin
Godiya sosai, irin wannan basira hk ,Miemie Allah ya kr karfin ido, guiywa da kuma basira. We luv u miemie,
Osheey Miemiebee! Allah ya kara basira
Miemie go dhey mak person dhey check dis page every minute 3days after posting 😂 wushe mama.. Can't wait 4 d next update 💋♥️
Thanks dear. Amman a ringa mana posting after two days kaman yanda a keyi da
Anya kuwa lfy ,shiru2 Allah yasa lfy.we care much about u.tnx
Miemie hope dai everything is fine??Luv yah
This page is awesome Allah ya kara basira
Walhy kuwa
Shiru haka
I pray allizwell
Water Hack Burns 2lb of Fat OVERNIGHT
Over 160,000 men and women are utilizing a easy and SECRET "liquids hack" to lose 1-2lbs each and every night while they sleep.
It is very simple and works all the time.
Here's how to do it yourself:
1) Take a glass and fill it half glass
2) And now learn this proven HACK
and you'll become 1-2lbs thinner as soon as tomorrow!
Post a Comment