Page 02
And this page goes to *ANEELURV* thanks for everything dear #OneLove
“Yauwa Hafsah ta barinje in siyo miki gashin koh?”
“Alhaji ni banga amfanin gashin nan ba kawai madara da milo nake buqatan k’ari sabida insamu k’arin ruwan nono ma Zeezee.”
“Toh angama Hafsah ta ina dawowa.”
“Toh Allah ya kare Baban Zeezee.” Dad’i sosai yaji ya miqe kan gadon tare da kissing Zeezee a hanci sannan ya d’ago kai ya galla ma Ibraheem da bakinsa kan ya tab’a bango dan turi harara “sauran kuma in na fita kai da qaninka kufita kujira kuga abinda zan muku” yana kaiwa nan ya fice zuwa garrage achan yasamu Yasmeen tana wasa “Baba ina zakaje?”
“Zanje siyowa Mamanku da sabon baby kayan tea ne.” Tanajin sabon baby ta had’e rai har Baba ya gano kishi take “zo nan” ya kirata bayan ta iso yace, “baraki bar wannan banzan kishin naki da bansan daga ina yasamo asali bako? Yanzu da k’anwar nakin kike gaba? Iyyeh? Kicigaba.”
“Baba kacewa Mama wai karta sake cemaka Baban Yasmeen se Baban Zeezee ni banason Zeezee.” ta turo baki.
“Karki sotan maras kunya kawai, zamuga me siya miki chocolate a gidan nan ai.” Da gudu ta ruga ciki tana kuka taje ta samu Mama.
*~ * ~ *~
Daidai nan Baba yadawo daga d’an siyayyan dayayi ma Hafsah bayan yayi parking mota yaciro tsire da kazan daya siya mata a hannu sannan ya danna wa Mariam kira. “Na’am Baba” ta amsa.
“Zo nan kicire kayakin daga mota kikai d’akin Mamanku.” Daga kitchen tafito tayi mai sannu dazuwa kafin ya amsa yaji wani erin kukan jaririya wane ana cire mata rai cike da tashin hankali ya kalli Mariam “meke faruwa? Kukan waye wancan bade na Zeezee ba?”
“Nata ne” ta fad’a wane tana enjoying kukan Zeezeen.
“Me akeyi mata?”
“Wankan gargajiya Baaba A’ee ke mata tana miqar mata da joints.”
“Meneh?” Daga nan yayi d’akin Hafsah a 360, Mariam tace, “daidai kenan” sannan taje ta soma ciro manyan gongonin madara da ovaltine number 1 da Baba ya siyo wanda barata iya tuna when last ya siya musu kalan suba.
Yana shiga ciki yaci karo da A’ee zaune kan kujera da bahon wanka gabanta ta juya hannun Zeezee a baya tana matsawa ayayinda Zeezee keta ihu kan ba gobe “Subhanallahi! Ya haka me kike mata A’ee?” yayi maganan yana k’ok’arin ajiye ledan tsiran kan kujera a yayinda Mama ke zaune kan kujerar, kafin Baaba ta amsa Mama tace, “sannu dazuwa Alhj, wankan gargajiya A’ee ke mata.”
“Wanka ko azabar da yarinya?” Be jira me zasuce both ba ya k’wace Zeezee daga hannun A’ee.
“Alhj ya da haka?” Mama tayi maganan baki bud’e haka ma A’ee.
“Banason wankan in baza kuyi mata asalin wanka ba se abar wankan gabad’ai haba me haka?” Ya kwantar da Zeezee a jikinsa yana bubbugata ko zatayi shiru amman ina se kuka take. “Daga yau kada a sake yimata wannan wankan, ke Hafsah kinada matsala wallahi d’iyarki na kuka amman ko a jikinki wad’ancan sakararru biyun kuma” ya dawo da kallonsa kan su Ibraheem da suke da shirin dariya. “Kaman ma kukan nata dad’i yake masu.”
“Amman Alhj fa kasani wankan nan dole ne shi ze miqar mata da kasusuwa ya hana kasala ko Yasmeen ma anyi mata kuma da chan bakayi magana ba.” A’ee ta gwada masa bayani.
“Naga ai wannan Zeezee ce ba Yasmeen ba, bana so nide na fad’a muku aka sakeyi ko a bayan ido na ban yafe ba.”
“Toh munji kawota a gama mata wankan.” Mama ta miqa hannu tana jiran ya dire mata Zeezee.
“Eh kafin nan kibata mama tasha tayi shiru.”
“Toh ai naga seda ruwan nonon zan iya shayar da ita kokuwa? Kuma babu.”
“Wannan ba matsala bane ina Mariam kawo madaran nan” dai-dai nan Mariam ke shigowa da gongonayen madara da ovaltine, baki Mama ta bud’e in suprise “Alhj wannan fah?”
“Madaran ki saboda Zeezee tasamu ruwan nono itama.” Hannu ta tafe, “lallai Baban Zeezee dagaske kake!”
“Niba wannan ba yanzu had’a kisha kibata mama tasha.”
“Kawota bara’a rasa na bata ba.” Nan da nan Mama ta amsheta ta shayar da ita sannan aka gama yima Zeezee wanka aka shafa mata mai anzo sa kaya tasoma kuka.
“Kekuwa A’ee kiyi mata a hankali mana bafa Yasmeen bace kina wani sa mata kaya da k’arfi da kuma hanzari haka seki b’alla mata hannu ai. K’asusuwanta ba k’wari garesu ba.” cewar Baba.
Mama kanma kasa cewa komi tayi dan mamakin sabon halin Baba da take. A’ee ne ta tab’e baki tace, “yanzu Alhj sa kayan ma koya min za kayi? Ko ka manta ungozoma ceni?”
“Chan miki nide kimata a hankali in kuwa bara kiyi ba zan mata da kaina.”
“Yi hak’uri zan mata.” Nan tabi Zeezee a hankali ta gama shiryata tsaf cikin baby pink rigan sanyi da shawul, amsheta yayi daga hannun ta ya nufi bakin k’ofa da niyyan fita, yana kaiwa bakin k’ofar Mama ta dakatar dashi ta hanyan kiran sunansa.
“Baban Zeezee ya haka? Ina zaka kaita?”
“Ina kuwa? D’aki na mu zauna.”
“Toh Alhj in ‘yan barka suka zo ganin baby fah, se in ce masu meh?”
“Se kice masu babyn na gun Babanta meson ganinta yazo d’akina, kuma ki tabbata kinsha tea da kyau kar Zeezee tasoma jin yunwa kice ba ruwan nono.” Yana kaiwa nan ya fice cike da mamaki Mama ta kalli A’ee dake kallonta itama sannan ta tab’e baki tajawo cup ta had’a tea tana kurb’a a hankali. Koda ‘yan barka suka fara zuwa Mama taje d’aki ta samu Baba kan yabata Zeezee haka yaqi ya sake nanata abinda ya gaya mata akan duk meson ganin *_‘YAR GATA_* yazo d’akinsa.
*~ *~ *~
Bayan Sallan Isha Baba na a zaune a d’akinsa da Zeezee kwance kan cinyarsa se buga budget na bikin suna yake, Zeezee ta soma ‘yar kuka take yayi gefe da abinda yake ya nufa d’akin Hafsah inda ya tarar da ita tana bayi tana wanka. K’ofan ya k’wank’wasa daga ciki tace, “waye?”
“Baban Zeezee ne me kike kifito.”
“Alhj wanka nake.”
“Nasani ai shine nace kifito.”
“Inbar wankan kenan?”
“Eh kibari.”
“Toh Alhj kumfan dake jikina kuma fah?” Nan Zeezee ta dad’a kuka. “Kifito nace Hafsah karki bari na sake nanata kaina tam!” Haka nan dan dole ta watsa ruwa ta goge jikinta da sauri tafito tana tura mai baki. Hannunta yaja izuwa gado ya ajiye mata Zeezee kan cinya “gashi yi ki shayar da ita yunwa takeji.”
“Wai Alhj kana magana se kace kasan meke damunta halan kukan bacci ko k’ishin ruwa fa take ba na abinci ba, kuma na cigaba da shayar da ita minti minti haka ai seta ramar dani.”
“Karki damu za kina cin abinci bata mana da sauri ba kijin kukanta ne?” Seda ta k’are masa kallo sannan ta shayar da Zeezee har seda tayi bacci, duk anan albarka Baba keta sa mata.
“Yanzu da tayi bacci ka yarda in zare abuna?”
“Abinta de ba naki ba Hafsah zare ai tayi bacci.” A hankali Hafsah ta zare mamanta daga bakin Zeezee ta kwantar da ita. “Yanzu kuma se a barni inyi wanka aiko?”
“Sosai ma Hafsah kiyi kifito akwai tsaraban dana tanadar miki.”
“Again akan dubu hamsin d’in?”
“Sosai ma kuwa jeki, kika gama kizo ki sameni a d’akina.” Cike da jin dad’i ta miqe tare da fad’in “toh” ta fad’a bayi.
D’akinsu Ibraheem Baba yayi inda ya sami duka yaran zaune suna assignments nasu, yana shiga suka yi masa ‘sannu’ banda Yasmeen datak’i koda kallonsa, ‘yar murmushi ya saki yasa hannu a aljihu yaciro chocolate na bounty guda biyu ya miqa mata “zo ki karb’a Mamana na kaina” ba yabo ba fallasa taje ta amsa tare da yin godiya. “Yauwa Ibraheem wuce kaida Omar kuje ku tsaya kan Zeezee tana bacci.” Cike da mamaki Ibraheem ya d’ago kai yana kallon Baba totally speechless, wai shin Baba bega yana assignment bane da zesa sa yima Zeezee gadi? Tambayan dayayi ma kansa kenan.
“Da kaifa nake magana d’an fari ka kuma jini koh?” Baba ya sake magana. “Kai Omar miqe! Kabar abinda kakeyi ka dawo seka cigaba.”
“Ayyii Baba assignment fa nakeyi” cewar Ibraheem.
“Ai nagani ba makaho ne ba ni, kuje kuyi gadinta in nagama abinda nake zan karb’e ku.” Ibraheem ze sake magana Baba ya daka mai tsawa “wuce nace!” A sanyaye shida Omar suka bi gefensa suka fice se gunguni suke.
*~ *~ Bayan Mama tagama kimtsa kanta ta kalli su Ibraheem da suke tsaye kan Zeezee se harararta suke ayayinda take bacci peacefully. D’an murmushi ta saki tace, “dade kunbar wanan kumbure kumburen koni mahaifiyar ku ban tsira ba inde akan Zeezee ne kuma ku hak’ura kawai wataran se labari.”
“Toh shikenan Mama wai in wannan abar zatayi bacci se an tsaya a na gadinta mschw!”
“Katayi kaji? Bari yazo ya jika ni ba ruwana, Omar d’ina karka kulasa kaji ko? Yanzu zanje in dawo seku tafi.” Daga nan ta wuce d’akin Baba dake chan babban parlour, Sallama tayi sannan ta shiga, zaune ta tarar dashi kan gado da paper akan cinyansa se budget list yake bugawa. Bayan ta zauna gefensa tace, “Alhj gani” tayi maganan tana leqa abinda yakeyi nan taga budget yake had’awa kona meh oho?
“Yauwa ina zuwa, Hafsah” yana kai wani point ya ajiye biron ya miqe ya nufa wardrobe nasa tare da ciro wasu manya-manyan shopping bags guda biyu ya dire mata a gaba “wannan nakine, wannan kuma na Zeezee.” ya nuna mata da yatsa. Baki ta sake in shock.
_Bade kayaki bane cike ciki?_ tambayar data iya tama kanta kenan aiko tana bud’ewa ta tabbatar da zaton datake, d’ayan cike yake da zannuwa manya dakuma laces sekuma d’ayan kayan babies had’ad’d’u qualitative ones.
“Alhaji duka wad’annan?!” Abinda bakinta ya iya furtawa kenan.
“Ai ba yawa Hafsah, farin cikinki yafiye mani komai a duniya, kalamu barasu iya kwatanta irin farin cikin da kika sanya ni ciki ba yau kinga ko dole insan taya zanyi in kwatanta miki, komi anan naki ne dana Zeezee.”
“Wayyo! Baban Zeezee you are too much duka wad’annan?!” Ta zazzago kayakin k’asa tana bi da kallo kap ciki ba k’arami zani. “Nagode sosai Baban Zeezee Allah ya qara bud’i yabarmin kai.”
“Ameen Hafsah ta ai ni naki ne ke kad’an ki.”
“Ba kishiya koh?” Ta gwada jin bakinsa.
“Haba! Ai alk’awarin nan dana d’au miki tun kafin muyi aure yana nan har yau kuma har gobe.”
_“Kafin ke ba kowa Hafsah, haka zalika bayan ke ma ba kowa, kece first and last I’m all yours”_ Hafsah ta nanata alk’warain da Baba yayi mata tun kafin suyi aure.
“Exactly! Kinga ko ba zancen kishiya duk abinda nake so nake buk’ata kina dashi kina yimin dan meh zan miki kishiya?”
“Gaskia ne Alhj Allah yabar soyayya I love you.”
“I love you too” ya yi maganan tare da zama a gefenta.
“Alhj na kayakin nan sunyi yawa! Karka biye min da Zeezee ka tsiyaye kana mana siyayya wallahi koba kayakin nan ma ni am satisfied and happy...”Ta nisanta “amman fa kace bakada kud’i kwana biyun nan ina kasamu kud’in wannan siyayya?”
“Ai na gaya miki inde akanki da Zeezee ne toh inada millions.” Baki ta tab’e ba tare da tace komai ba se bin kayakin take da kallo chan ya miqo mata dubu hamsin “as promised, wannan kuma sekiyi d’inki dashi koh?”
“Alhj!! Karkasa in kasa bacci mana yau.”
“Aikuwa dana ji dad'i kinga sekita gadin Zeezee.”
“Toh nikam ba abinda zance banda Allah ya qara bud’i barin je in samu Zeezee su Ibraheem su samu su gama homework nasu.”
“Toh toh ba abinda kike buqata again koh? In akwai speak up.”
“Ba komai Baban Zeezee... Yauwa nace me kakeyi shigowa na? Naga kaman budget kake had’awa kona meh?” ‘yar murmushi ya saki “karki damu you’ll find out soon My Dear.” Bayan d’an nazarin datayi ta juyo tana kallon sa kamar yadda shima ke kallonta “Alhj bade taron suna kake planning yiba koh?”
“Me kike fad’i wai? Jeki samu Zeezee kibar suaratan banza” daidai ze miqe ta riqe hannunsa “Alhj gayamun gaskia taron suna kake shirin yi?”
“Toh haramun neh? Kuma naga yaran nan duk kowa anyi taro a sunansa se ana *_YAR GATA_* ne zakice bara ayi ba?”
“Alhj ni bafa abinda nake nufi ba kenan, kaifa kace min kwana biyun nan baka samu sosai kuma ni banga amfanin kashe kud’i ba dalili ba, taron sunan nan de ba dole bane ‘yar ragon suna aka yanka walillahil hamdh.”
“Maki kenan amman nikam senayi taron sunan nan aci asha a tayani murnan samun Zainab.”
“Yanzu Alhj murnan da mukayi nan du be isheka ba?”
“Be isheni ba Hafsah se kap ‘yan unguwa, ‘yan uwa da mutan arziki sun min congratulations zanji dad’i so tun wuri ki fara tura gayyan suna.” Baki ta tab’e tace, “toh duk abinda kace amman wallahi kasani in kazo daga baya kana min complaining cewa bakada kud’i barin saurareka ba.”
“Karki sauraran” nan ta miqe tare da ledojin a hannunta “seda safe toh.”
“A huta gajiya Hafsah ta, Allah yabamu alkhairi.”
“Ameen” har ta kai bakin k’ofa Baba ya dakatar da ita, “Hafsah please kar kiyi ignoring kukan Zeezee koda da daddare ta tashi buk’atan nono kibata.”
“Toh Baban Zeezee naji” daga nan ta fice su Ibraheem suka samu daman k’arisa assignment nasu suka yi kwanciya kasancewar da akwai school gobe.
*~ *~ ~RANAR SUNA* ~* ~*
Mama and Zeezee |
Gidan Alhj Isma’il Yusouf cike yake da ‘yan uwa da abokan arziki se hidima ake ana ci ana sha ana d’aukan hoto, wato yadda Alhj ya tsara bikin sunan Zainab ya wuce tunanin kowa daga kan iyalansa har ‘yan unguwa. Bikin suna amman sekace na aure, komai is in abundant supply, Mama data d’au ko zob’o za’ayi serving guest dashi ta mugun shan mamaki ganin ana sauk’e canned and bottled drinks ga snacks, ba abinda babu, uwa uba ga kaji nan barkace. Babu kaman su Ibraheem da suka ringa satan drinks suna kaiwa fridge na d’akinsu, tunda yake be tab’a ganin anyi suna akayi bushasha haka kamar na Zeezee ba, ba shakka Zeezee *_‘YAR GATA CE!_*
Bikin suna de ba abinda za’a ce banda Allah shi raya Zainab dan kuwa abin se wanda yagani!
_6:50PM_
Yawancin mutane sun watse kad’an daga ciki ne suka rage wanda yawancin su ma dangi ne, Hafsah da Zeezee sunci kyauta sosai na sosai zannuwa da kayan baby har neman wajen sasu ake, kan gado cike yake dam da kayaki. Kwance Zeezee take bisa kan gado agefe guda tana ta zuba bacci ita kad’ai a d’akin. Daga bisani tasoma kuka alokacin Mama na bayi tana watsa ruwa se sauri sauri take tafito ta d’auketa, ai kaman alarm Baba keda yajiyo kukan Zeezee ya shigo da hanzari ya tarar da ita se kuka take. Da hanzari ya d’agata yashiga danna wa Hafsah kira.
“Na’am Alhj gani fitowa ” nan da nan tafito.
“Kinajin Zeezee na kuka bara ki bar duk abinda kike ba ki d’auketa? Ina yaran suke?”
“Sun shiga nan mak’ota, Alhj da Allah riqe min ita in samu in sa kaya.”
“Har kisa kaya tana jirar ki kenan? Amsheta ki shayar da ita.”
“Wai-” katseta yayi, “bana son jin wani zance amsheta nace” haka ba yadda Mama ta iya ta karb’eta ta shayar da ita har seda ta koma bacci Baba ya yarda ta zare maman.
Da misalin k’arfe 9:34PM Mariam dake taya Mama kwana tun haihuwan Zeezee tashigo cikin shirin baccinta ta dire bargonta gefen Zeezee tare da k’are mata kallo. Lallai kuwa gaskian jama’ah kap cikinmu ba me kyan wannan ‘yar jaraban tayi maganan a zuci tare da sakar da tsaki a fili ba tare da tasan tayi hakan ba, tas taji an buga mata k’eya har ribbon nata na neman fad’i a hanzarce cike da rikicewa ta juya tana kallon direction dataji sauk’an marin, Baba taga tsaye akanta.
“Baba nikuma menayi?” Ta tambayesa tana shafa k’eyar tata.
“Zeezeen kike kalla haka harda jan tsaki?” Daidai nan Mama tafito daga bayi itama da shirin kwanciya.
“Baban Zeezee ya haka? Baka kwanta ba?”
“Ina kuwa zan kwanta bayan jikina na bani keda wannan muguwan” ya nuna Mariam da yatsa “kuna ignoring Zeezee da daddare saboda haka anan zan kwana yau. ”
“Anan kuma?” ta tambayesa fuskarta d’auke da neman k’arin bayani.
“Eh anan Hafsah ai na gaya miki jiki na na bani da daddare kuna barin yarinyan nan tai ta kuka da wannan muguwan yartan” ya galla wa Mariam harara yanzu kuma.
“Yo Alhj ba sena gama arba’in ba tukunah?”
“Ke kika sani, nide anan zan kwana Mariam fice kije ki d’ago Yasmeen daga d’akina ki kaita d’akinku achan zata kwana yau.”
“Toh” ta fad’i tana jin dad’i dama harga Allah ta gaji da tashi kullum da daddare tana yawo da Zeezee a hannu har seta koma bacci, “seda safe Mama, seda safe Baba” tace dasu tare da ficewa.
Bayan Mama taja comforter ta kwanta ta kalli Baba dake zaune gefen gadon yana ma Zeezee addu’a tana turo baki tace, “ni wallahi Alhj nasan yau hanani bacci zakayi in kasa wannan Zeezee agaba.”
“Ai dama nasani ignoring nata kike da daddare kuma daga yau hakan bare sake faruwa ba” nan ya miqe ya kashe masu wuta suka kwanta da Zeezee rigingine a jikinsa.
_2:47AM_
Cikin bacci Baba ya soma jin kukan Zeezee, take ya tashi tare da kunna wutan d’akin ya d’agata yana jijjiqata ganin tak’i yin shiru ya maido da kallonsa kan Mama da tayi kamar bataji kukan Zeezee ba tana ta bacci.
“Hafsah!” yayi whispering sunanta, shiru bata amsa ba.
“Hafsah tashi nasan kina jina tashi nace ko ba kijin kukan Zeezee ne?”
“Alhj dan girman Allah ka barni in huta, ka fa san irin hidiman da na sha jiya.”
“Meaning baraki bata mama ba kenan komeh? Tashi nace!” yasa hannu yana jijjiqata da k’yar ta miqe ta zauna tana galla mai harara har a nan Zeezee bata bar kuka ba. Chan ta miqa hannu ta d’ago feeder’n Zainab ta mik’a mai, “gashi bata ruwan tasha k’ishi takeji” kallonta kawai Baba ya tsaya yi totally speechless mah.
*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
2 comments:
thanks a lot
Tnx
Post a Comment