Friday, 30 September 2016

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 91
BY MIEMIEBEE









       
    Cike da so da qaunan juna suka shirya suka fita chin lunch a restaurant Manhattan kamar yadda Fannah ta buqata, bayan Anas ya kawo musu order’nsu suka soma ci cike da jin dad’i, sosai Fannah ta zage ta gabza abincin se kewaye kewaye take ko zata ga Ummimi daga bisani k’ofar restaurant d’in ya bud’u atare Fannah da Anas suka miyar da kallonsu wajen Ummimi sukaga tsaye wajen tana rik’e da leda da alama shopping tayi sanye take da rigan cleaners, mamaki ne fal kwance kan fuskokinsu musamman ma Anas _bade Ummimi aiki take anan as a cleaner ba?_ ya tambayi kansa disbelievingly. Sun d’au tsawon minti biyu suna kallon juna sannan daga bisani Anas ya kawar da kallonsa daga gareta ganin hawaye sun soma ambaliya mata a fuska.

    “Flower tashi mutafi.” Dagangan tace, “Habeebi ban gama chi bafa.”
   “Nasani zanje in siya miki wani lets leave now” yayi maganar tare da miqewa, kafin Fannah ta sake samun daman magana Anas ya d’agata badan tanaso ba tasoma binsa sunzo daidai bakin k’ofan kenan zasu wuce Ummimi tasa hannu ta tare Anas ta hanyan rik’o hannunsa chak! ya tsaya ba tare da ya juya ya kalleta ba.
    “Anas dan Allah karka min haka nasan banida iko akanka nasan banida daman tambayar yafiyanka amman dan Allah kabani daman baka hak’uri dan Allah Anas” ta k’are maganar cikin sautin kuka. Shiru Anad yayi totally speechless ayayinda zuciyarsa ke raya masa kar ya kuskura yabata wannan dama zuciyan nasa kuwa yabi ya fisge hannunsa daga nata yakama tafiya, dawani erin force Fannah taja kanta baya tare da k’wace hannunta dake a nasa cike da tashin hankali ya juyo yana kallonta.
   “Flower lets go!” Yayi demanding.
   “No Habeebi I’m not going anywhere with you se inhar ka tsaya ka saurari Ummimi, haba mana Habeebi wannan fa mahaifiyarka ce ita ta tsuguna ta haife ka bekamata kana wulaqantata kamar kashi ba, Habeebi nasan kanason Ummimi please give her this one chance to explain herself please for Hanan.”

    Alokaci d’aya Ummimi taji tana son Fannah dan yadda ta burgeta, “nagode ‘yata, Anas dan Allah kaji maganar matarka kabani daman baka hak’uri dan Allah Anas.” Hannunsa Fannah ta rik’o a hankali tana mirzawa “kaji Habeebi? Zaka iya bawa mahaifiyarka daman baka hak’uri, can you? Please...” Kallonsa ya miyar kan Ummimi daba abinda take banda kuka yana ganinta kawai se last incident daya faru tsakaninsu ya soma masa yawo a k’wak’walwa seyaji he can’t give her the chance she is asking for, gabad’aya ya riga ya dawo daga rakiyarta da ace 15years back ta dawo da yayi accepting nata amman banda yanzu. “No I can’t Flower I can’t mutafi nace!” Yayi maganar a tsawace.
    “Habeebi is okay calm down okay? Calm down” tayi maganar cikin salon dake kwantar masa da hankali.  _*“INA TARE DA KAI Hanan NA TARE DA KAI*_do this for me please just listen to her” badan yanaso ba ya gyad’a mata kai.

   ****
      Zaune Anas da Fannah ke kan wani d’an dogon kujera a yayinda Ummimi ke zaune opposite them fuskarta jik’ap da hawaye. Cikin kuka ta soma magana;
    “Anas nagode daka bani wannan dama nagode sosai Allah maka albarka” ko kallon direction nata baiyi balle yace ameen.
    “Nasan banida izinin da zan fara rok’ar gafararka saboda abinda na muku, bansan ta ina zan fara baka hak’uri ba wallahi barin ku danayi shine babban kuskuren dana tafka a rayuwata Anas, kuskuren da har a yau ina nadamar sa kuma har in mutu zan cigaba dayi, wallahi sharrin shed’an ne it wasn’t my intention to leave you guys my family.” Ta tsaya ta share hawayenta tare da jan hanci “Anas I love you, wallahi ina sonka fiye da yadda nakeson kaina, tun tafiya na a kullum da tunaninka dana mahaifinku dakuma na k’annenka nake kwana nake kuma tashi dashi, da abinda na muku tun aduniya na fara ganin sakamakon sa ina ace na tafi lahira ban nemi gafararku ba? Anas dan Allah kayi hak’uri, baka bani dama ba amman ni na baiwa kaina kayi hak’uri ka yafemin please na tuba Anas ka tausaya min mahaifiyarka dan Allah d’ana barin iya samun kwanciyan hankali ba har se in ka yafemin ka tausaya min please.” Ta rushe da kuka miqewa Fannah tayi takoma gefenta ta tsaya tana shafa bayanta cike fa tausayi idanunta itama sunyi jazir. “Ummimi please kibar kukan haka nan ya isa dan Allah.”

      ‘‘Yata dan Allah kimasa magana ya tausaya min ya yafemin.”
   “Anas Habeebi ka tausayawa mahaifiyarka please.”Kai ya girgiza cike da takaici “mahaifiya? Yanzu ke Ummimi bakiji kunya ba da kike kwatanta kanki da mahaifiyata nikuma da d’anki? Bakiji kunya ba? As far as I’m concerned Ummie itace mahaifiyata. D’an da kika tunkud’esa kamar kashi 15 years ago, d’anda kika k’yamata d’an da kika masa permanent tabo a hannu” ya yi rolling hannun shirt nasa ya nuna mata tabon tabbas ta tuna itace taji mai ciwon danko kafin ta fice daga gidan taga yadda hannunsa ke yoyon jini amman saboda yadda shaid’an yafi k’arfinta alokacin ta fice ta barsa. Wani sabon kukan ta rusheda.


     “Kin tuna ciwon?” Ya tsamota daga duniyar tunanin data fad’a. “You think you still have the right to call me your son? Kinsan kalan k’uncin rayuwan da mukayi witnessing bayan tafiyarki? Kinsan ya akayi aka girmar damu aka girmar da Amal jaririyan da kika turo bayan tafiyarki precisely? Kinsan ya aka tarbiyyattar damu?” Zuciyanta taji yawani buga tare da sarin da kanta ke mata tana me k’ara tsanan kanta.
    “Kinsan ya akayi muka taso ba gatan uwa har muka fara mancewa da labarinki? Kinsan dare nawa muka kasa bacci saboda tunanin ki? Kinsan kwana nawa na d’iba inayi a waje ina tunanin ko zaki dawo mana? Kinsan what hell you made Abuu went through? The answer is No baki sani ba saboda alokacin kina chan da sabon mijinki kina more rayuwa. Its all over Ummimi I’ve loved you, we’ve loved you so dearly bu not anymore banida gurbin da zan sake ajiye soyayyan ki a zuciya na saboda na dawo daga rakiyarki, ke kika haifeni I can’t change that amman abinda nakeson kisani shine ki sa a mind naki baki tab’a haifan d’a me suna Anas ba, so nake ki mance dani kamar yadda na manta dake a rayuwa na cause I can‘t forgive you I will NEVER forgive you.” Yana kaiwa nan ya miqe da sauri tare da juyawa gudun kar hawayen dayake maqewa su fito seda ya shanyesu sannan ya juyo alokacin kuka sosai Ummimi ke wane zata cire ranta ayayinda Fannah ke bata hak’uri.

     “Anas tabbas ba k’arya cikin kalamunka tabbas nasan namuku laifi, laifin da yayi babban tabo duka a zuqatanku wallahi nayi nadama Anas kabani dama in biyaka 15years that passed, let me make it up for the past 15years da mukayi ba tare ba please kar ka hanani performing obligation d’ina as your mother.”
     “You are not my mother so you don’t have to saboda I don’t need you ko ayau akace Ummie wacce ta girmar dani wacce nake regarding nata as my mother ta rasu zan cigaba da rayuwa na balle ke, because I’m a grown up now as you can see I’m married saboda haka I don’t need you na yafe miki tsawon 15 years da mukayi ba a tare ba, ba sekin biyani ba, kitafi ki koma inda kika fito banasonki a rayuwa. Flower lets go” yaja hannunta suka soma tafiya, k’ok’arin jan hannunta daga nasa take amman takasa har seda suka isa mota tana kuka tana mai magana “haba Habeebi ban tab’a sanin your heart is as cold ba se yau, mahaifiyarka ce fa your own mother koda laifin kisan kai tayi be kamata ka mata haka ba, ka duba yadda tayi nadama mana kodan haka baraka saurara mata ba?”
   “Yes Flower barin saurara mata because I don’t need her 15years danayi ba ita yasa na mutu ne? No saboda haka bana buk’atar ta taje tasamu family’nta we don’t need her.”

   “Hab-” katsesa yayi “enough okay?!” Yayi maganar cikin sautin tsawa ganin yadda ta firgita sekuma yaji ba dad’i hannayensa ya aza kan shoulders nata “Flower I’m sorry banason ina miki tsawa, banason muna musu banason Ummimi ta zama sanadin samu fad’an da bama yi please stop crossing me kibarta let her be kinfi kowa sanin kalan k’uncin data jefa mu especially me, data tafi ta barmu without turning back. Ko kin manta saboda ita nasoma shaye shaye har ya kaiga nayi raping naki Flower duk kin manta? It because of her you suffered itace silan komai Ummimi batada advantage se disadvantages.”
     “Tabbas ba k’arya cikin maganganunka Anas” cewar Ummimi dake tsaye some inches away from them da alamun ta saurari dukkannin abinda Anas ya fad’a. “Tabbas duk wani abin haramun da ka aikata nima me laifi ce kuma nice sila saboda da ace ina nan da na hanaka aikata hakan, kayi gaskia da kace banida advantage se disadvantages all am asking for is kabani dama to be a mother to you again Anas koda baraka yafemin ba kabani dama insake rik’eka a hannayena in dafa maka abinci this is all I ask Anas please.”
   
    “You should hace thought about this 15years ago kafin kika tafi, alokacin ne wad’annan kalamu naki zasuyi tasiri akaina amma banda yanzu da kika riga kika karya min zuciya in baki sani ba kisani I’m not the Anas you left 15 years ago wannan Anas bayida tausayi saboda tafiyar mahaifiyar sa yakoya masa rashin tausayi da imani, my heart is as cold as stone dan haka kibar b’ata yawun bakinki kina bani hak’uri barin tab’a hak’ura ba  Flower lets go.”
    “Okay Habeebi zan bika amman please kabani koda minti biyu ne inma Ummimi magana kaji?”
    “Flower me zakice mata? Kibarta please.”
    “Habeebi dan Allah fa nace please minti biyu kad’ai.¢ Kai kawai ya gyad’a mata “thank you so much my Lion.” Wajen Ummimi ta nufa taja hannunta suka b’ace daga kallon Anas bisa wani bench suka zauna Fannah na sharewa Ummimi hawaye. “Please kibar kukan hakanan ya isa dan Allah.” A raunane ta d’ago idanunta tana kallon Fannah “ ‘yata ya sunanki?”
    “Fannah, Fannah suna na.”
  “Masha Allah Fannah nagode da kulawarki a gareni Allah sak’a miki da alheri yakuma sauk’eki lafiya” (agarin share mata hawaye da Fannah ke hijabinta ya d’agu anan ne Ummimi taga cikin nata.) Mamaki ne ya mamaye fuskan Fannah taya Ummimi tasan tana da ciki? Cike da kunya tace, “ameen Ummimi please kibar kukan haka nasan Anas haka yake yanada taurin kai ne kuma sonki da yake yasa yake treating naki haka amman in shaa Allah wataran se labari Anas ze yafemiki nan bada jimawa.”

    “Haka kike gani ‘yata Anas ze iya yafemin abinda na masa?”
   “Allah ma muka mai laifi ya yafe mana balle d’an da kika haifa? Trust me ze yafe miki kidage da addu’a kawai nima zan saki cikin nawa.”
   “Nagode sosai ya Shettima yake dan Allah?”
   “Shettima nanan girmansa kusan d’aya da Anas yana kan karatu.”
   “Masha Allah nasan da kunya ma in tambayeki ya baby’n dana turo musu da ita bayan tafiya na wanda ko halittan fuskarta ban k’arewa kallo ba.”
   “Amal? Amal sunanta she is 15 years now itama ta na nan lafiya tana ss2 kinsan wani abu?” Kai Ummimi ta kad’a “sautin muryanku d’aya dakika fara min magana na zata ma Amal ce.” Murmushin takaici ta saki “Allah sarki Amal Allah yi mata albarka”
    “Ameen barikiga pictures nasu” nan taciro wayarta tana gwada wa Ummimi, hawaye sosai Ummimi ke kamar ba gobe tana me sake tsanan kanta abinda ta ma family’nta. “Amal da Anas sak kaman ni na, Shettima ma ba laifi, ‘ya‘yan Albarka Allah ya cigaba da raya min su yamusu albarka, yamuku albarka gabad’aya” tafad’a tana share hawayenta. “Ameen Ummimi.”
    “Ya Babansu yake? Wace Ummie da Anas yake fad’a kuma?”
   “Babansu na nan k’alau, Ummie k’anwar mahaifinsu ce.”
     “Ohhh Allah sarki nako ganeta itace ta girmar dasu?”
   “Eh itace.”
    “Allah sarki Allah ya saka mata da alheri, Babansu be sake aure ba?”
    “Gaskia be sake ba”
   “Allah sarki Ya Ibraheem, Fannah awani gari kuke yanzu da zama?”
   “Dukan mu a Maiduguri muke.”
   “Okay kunzo nan shaqatawa ne?”
  “Eh munma kusa komawa zaman nan ya ishemu gida yafi dad’i.”
   “Hakane ‘yata no place like home, dan Allah kitayani ma Anas magana nasan yana jin magananki koda bare yafemin ba yabani izinin zama mahaifiyarsa again, I want to make up for the past 15 years da mukayi ba a tare ba.”
    “In shaa Allah Ummimi karki damu sede wani gudu ba hanzari ba am sorry to ask mesa kikesa uniform na cleaners?” Murmushin takaici ta saki tare da share hawayenta. “Anan nake aiki Fannah as a cleaner.”
    “Subhanallahi cleaner kuma Ummimi? Meya faru? Meyasa?”
   “Long story ‘yata da wannan aikin kad’ai na dogara.”
   “Ummimi ina mijniki da ‘ya‘yanki? A yadda Anas yabani labari aure kikayi bayan tafiyanki.”
   “Tabbas aure nayi, Fannah mijin dana aura d’an cult ne nagudu nabarsa har a yau nemana yake.”
    “Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un to ‘ya‘yanki fa ko babu?”
   “Akwai har uku nafarin mata ne twins Basmah da Barrah sekuma autan Aleeyu wanda yake nan sak Anas har blue eyes nasu wanda sukayi inheritting dagu gun mahaifin kakana iri d’aya.” Hannu tasa a aljihunta taciro picturen ta nuna wa Fannah.

    “Woww masha Allah kyawawa dasu.”
    “Barrah da Basmah are 13 years, Aleeyu kuma 10 daganan ban sake haihuwa ba.”
     “Ayyah, wallahi Aleeyu sak Anas inda bansani bama cewa zanyi Anas ne haske kawai Anas ya d’ara sa kad’an but Ummimi a ina suke su yanzu? Suna wajenki ne ko wajen mahaifinsu?”
   “Ko d’aya ‘yata suna wajen mahalicinsu.” Tasa hannu tana share hawayenta.
   “Ban fahimce kiba Ummimi.”
   “Babansu yayi kud’i dasu Fannah, ya siyar da ‘ya‘yan cikinsa wa k’ungiyansu.”
    “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!” take itama Fannar tasoma kuka. “Ummimi I’m so sorry kiyi hak’uri dan Allah, Allah sa k’arshen wahalansu kenan Allah sarki kiyi hak’uri dan Allah.”
   “Bakomai nima abinda yasa na gudo na barsa kenan saboda nice next target nasa jini na ne next abinda k’ungiyansu suke buk’ata dana gano hakan na gudu na barsa.”

    “I’m so sorry Ummimi shi rayuwa haka yake kowa da kalan jarabawarsa, ki cigaba da musu addu’a bale ma yara ne dukansu Allah sa masu cetoh ne.”
   “Ameen ya rabb-” bata samu daman k’are maganan ba ganin Anas datayi.
    “Flower lets go.” yayi i terrupting nata.
   “Toh Anas ina zuwa yanzun nan” bayan daya koma ta dawo da kallonta kan Ummimi.
    “Ummimi yanzu a ina kike kwana?”
  “Anan a d’akin da aka tanadarwa cleaners.”
   “Subhanallah mesa baki fad’a min ba? Bari zanyi wa Anas magana inshaa Allah zaki biyomu gida.” Hannunta Ummimi ta rik’o da sauri “a’a Fannah karki ma b’ata yawun bakinki please I don’t want to be a burden ni abinda nakso kimin d’aya ne hanyan da zesa Anas yayi accepting d’ina as his mother.”
   “Duka biyu zanyi Ummimi bareyi kina kwana agidan cleaners ba bayan da gatanki ina zuwa” nan ta fice taje tasamu Anas dake tsaye gefen motansu yana jiranta seda ta iso gab dashi ya saki mata murmushi wanda itama ta miyar masa “lets go?” Kai ta gyad’a masa tare da ajiye masa picture’n su Basmah akan bayan motar.

   “Meshi?” Ya tambayeta.
   “Ka duba kaga” ba gardama ya d’aga hoton yana kallo. Be sansu ba amman seji yake kamar yasansu gakuma me kamanninsa dayake gani cikin hoton harda blue eyes d’inma, tunaninsa ne ya jagule alokaci guda he seems puzzled. “Flower suwaye wannan? Waye wannan yaron?”
    “Kaga kuna kama koh?”
   “Sosai kuwa the eyes the face everything please suwaye ne?”
    “Your siblings Habeebi, k’annenka ne.”
   “K’annena?” Ya d’ago kai yana kallonta cike da mamaki. “Inada k’annen da sukafi Shettima da Amal ne?”
   “Yes step siblings naka ne.”
   “You mean yaran Ummimi?” Seta gyad’a kai pucture’n ya miyar mata “gashi banason ganinsu.”
   “Ayyah Habeebi basu maraye bale kace haka.”
   “What do you mean?”
   “Dukan su nan Allah yayi musu rasuwa, babansu your step-father d’an cult ne ya siyar da yaransa wa k’ungiyansu bayan nan yadawo kan Ummimi dalilin dayasa ta gudo tabarsa kenan har kaga take aiki anan ayanzu haka batada wajen kwanciya, Habeebi ka tausaya mata please...”



*© MIEMIEBEE*

 beeenovels.blogspot.co.ke

Wednesday, 28 September 2016

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 90
BY MIEMIEBEE








 
     
       “Flower mesa kike kuka? Do you want to talk about it?” A nitse ta d’ago kanta daga k’irjinsa ta share hawayenta sannan ta masa nuni da ward d’in. Cike da rashin fahimta yace, “what about it Flower?”
    “Habeebi baka ga yadda matan suke kuka bane? Yadda haihuwan ke basu wahala Habeebi I’m afraid” tasake rushewa da kuka. Kallonta ya tsaya yi Fannah barata ishesa da kallo ba. Sake kwanto da ita yayi a jikinsa yana bubbuga bayanta “is okay kinji bar kukan ya isa, you will have a safe and easy delivery in shaa Allah zamu cigaba da miki addu’a bar kukan haka ya isa.”
    “Habeebi ina tsoro kasan wasu matan daga labour room se lahira suke wucewa Habeebi banason in mutu ban rik’e Hanan ba.”
    “Flower kibar magana haka wayace zaki mutu baraki riqe Hanan ba? In shaa Allah zaki shiga labour room kuma kifito fine and good banason irin maganan nan kinji? Stop crying ya isa.” D’agota yayi sannan ya share mata hawaye “lets go and eat.”

    Ba musu ta miqe tana manne a jikinsa har suka isa gun motansu. Yana cikin driving ya juyo ya kalleta tayi lamo jikin kujeran tana kallon window.
    “Flower kinsan you are funny koh.” Ba tare da ra juyo ba ta amsa shi, “menayi kuma yanzu?”
   “Kukan da kikayi mana, gaskiya banason Hanan ta d’auko kukanki abu kad’an kuka.”
    “Sekayi ai kai dama in baka nemi tsokana naba bakajin dad’i.”
   “Oh common Mom Hanan chill please wasa nake miki.” daga nan bata sake che masa k’ala ba.
    A Restaurant Manhattan Anas yayi parking bayan ya fito da ita daga motan sukayi ciki, table dake kusa da bakin k’ofar ya zaunar da ita a yayinda ya yi ciki dan yimusu order kasancewar traditional restaurant ne. Fannah na zaune ita kad’ai kan kujerar tayi jugum har a yanzu hankalinta be kwanta ba regarding mata masu nak’uda data gani d’azu daga bisani ta d’ago kai tana kallon k’ofar seji take kamar ana binta da kallo data dudduba kuwa se bataga kowa ba.

     Kamar daga sama taji hannu dafe kan kafad’ar ta a razane ta d’ago kai acewarta ma kidnapping nata za’ayi harta bud’e baki zata sa ihu setaga mace ce ‘yar uwarta anan ne hankalinta yad’an kwanta. Bata tab’a sa matan a ido ba amman kuma she is sure ba a yau ta fara ganinta ba zuciyarta se rad’a mata take she’ve met this woman before amman ta rasa a ina.
    “Sannu Sister yi hak’uri in na razanar dake please.” matar tayi magana cikin muryarta wanda sosai yayi kama da wata wanda Fannah tasani amman ta rasa gane a ina, no matter how tayi ta tuna a’ina tasan muryar ta kasa.
   “A’ah ba komai Aunty” cewar Fannah har a yanzu se kallon wannan babbar mace me k’imanin shekaru 45 take tana me tunanin a’ina ta tab’a ganinta.
    “Toh nagode nace dan Allah wancan da kuka shigo dashi just a while ago mijnki ne?” Shiru Fannah tayi tana  nazarin ko ta bata amsa kokuwa kar ta bata saboda question d’in is too private. Shirunta ya sake bawa matar damar magana. “I’m sorry please karkiji tsoro ba abinda zan miki suna na AYSHA kuma ‘yar Nigeria ce nima kamar ku kawai I want to know ne please ki fad’amin.”
    “Eh mijina ne.” tayi maganan idanunta cikin na Aysha, hawaye ne suka soma gangarowa kan kumatun Aysha wanda yamugun bawa Fannah mamaki toh kode son Anas nata wannan Aysha ke da har zatayi kuka da ga jin ance yanada aure.

    “Aunty Aysha mesa kike kuka?”
  “Babu, babu ba komai sunan mijin naki A... A... Anas koh?” cike da mamaki Fannah ke kallonta har taya tasan sunan Anas? Ta bud’e baki zatayi magana kenan Anas yakira ta from far behind.
   “Flower!” Da sauri ta juya izuwa direction nasa, drinks biyu ne riqe a hannunsa “wannan ko wannan kikeso.” Murmushi ta saki sannan tayi nuni dana hannun daman nasa, ido ya kashe mata sannan ya koma anan ta juyo dan cigaba da magana da Aysha sede ta duba gabas da yamma kudu da arewa bataga Aysha ba. A nitse ta miqe ta fito waje tana kewaye kewaye ko zata ganta amman ko alamarta babu, badan tanaso ba ta dawo ciki ta zauna shima Anas bada dad’ewa ba yadawo da plates nasu a hannunsa nata ya ajiye mata a gabanta. “Thank you Habeebi amman basu da waiters ne sekai zaka kawo mana da kanka?”
    “Ninaso Flower, kinsan white people d’innan da shegen son mata banason su kalla min ke.” Dariya sosai take “over possessive ba” tace cikin dariya.
    “Na yarda whatever lets eat.” Cike da jin dad’i suka soma chin abincin daga bisani Fannah tace, “yauwa Habeebi bakasan meba.”
  “Meneh?” Ya tambayeta tare da kai spoon baki yanacin abincin.
   “Shiganka ciki wata mata ‘yar babba haka tazo ta sameni take tambayana wai ko kai miji na ne dana tabbatar mata mijina ne kai sekuma tasoma min kuka wai sunan ta Aysha kuma abinda yafi ban mamaki ma yadda tasan sunanka, nayi nayi intuna a ina na tab’a ganin ta amman na kasa ‘cause her face seems familiar.”

    Spoon daya kai bakinsa ya maido shi plate d’in tare da d’ago blue eyes nasa yana kallon Fannah. Anan data kuma k’are masa kallo itama se ta tuna a ina tasan kamannin fuskan Aysha, anan tagane a’ina ta tab’a ganin fuskar Aysha ashe cikin family photon su Anas ne wanda ya goge fuskarta, anan ta gane Anas nata ke kama da Aysha, muryar Amal kuwa sak na Aysha ce. Aysha itace Ummimin su Anas. Ummimi na raye bata mutu ba.

    “Kikace meh?” Cewar Anas alokaci d’aya yaji lisafin k’wak’walwarsa na gushewa jin an ambaci Aysha sunan mahaifiyarsa da ya tsaneta fiye da komai a duniya.
    “Habeebi Ummimi nagani, wallahi ita nagani just a while ago.”
    “Whaattt?!” Ya tambayeta cike da k’in yarda.
   “Habeebi itace wallahi itace, Ummimi ce tana raye tashi mu neme ta I know she is somewhere close to us” kafin ta miqe Anas ya zaunar da ita har a yanzu besan meyake ciki ba tunaninsa duk ya jagule kayinsa na juyawa. K’arfin hali yayi yace, “ba ita bace Flower, Ummimi ta mutu inma bata mutu ba tana chan bangon duniya da mijinta da yaranta saboda haka ba ita kika gani ba lets eat and leave this place.”
   “Hab-” katse ta yayi a tsawace “I said enough ba ita bace!” Ta mugun firgita barata iya tuna when last Anas ya mata tsawa haka ba ‘yar k’ollan dake ciko mata a ido tayi sauri ta shanyesu bata sake ce masa komai ba.
    Sunfi minti biyu zaune ahaka ba tare da sunce da juna ko uffan ba, abincin gabansu ma duk sun kasa chi as Fannah ta zura wa Anas daya zurfafa cikin tunani ido.

      _What if abinda Fannah ke fad’i gaskia ne dan kuwa be tab’a fad’a mata asalin sunan Ummimi ba how comes zata sani inhar bawai taga Ummimin bane dagaske. Amman kuma is it possible? Meze kawo Ummimi New York? Dakansa ya amsa wannan tambaya._
     _Ai koda tazo tafiya ce mana tayi wanda ze aureta yace ze kaita k’asar waje meaning k’asar waje nan New York ya kawota kenan?_

    Kai ya girgiza a sauri “No it can’t be!” yayi maganar a fili. Hankalin Fannah yayi matuqar tashi ganin hankalin Habeebinta ba’a kwance ba.
     “Habeebi is okay kaji? Ya isa haka Abu Hanan.” tasa hanky ta share masa zafaffun gumin dake k’eto masa. “Lets go” yace da ita tare da miqewa ya riqo hannunta suka fito suka kama hanyan lot kamar ance Fannah juya ta juya idanunta basu sauk’a ako ina ba sekan Ummimi dake tsaye daga bakin k’ofan Restor d’in, sanye take da hijabi bak’i iyaka guiwa fuskarta duk alamun hawaye, kallo d’aya za’a mata agano tsantsan rashin kwanciyan hankali da wahala tattare da ita amman duk da hakan kyawun halittan fuskarta wanda su Anas suka d’auko be gushe ba.

     “Habeebi” Fannah takira sunansa tare da dakatar da tafiyarta badan yanaso ba yatsaya shima batare da ya raba hannayensu ba. “What is it Flower? Lets go!” Yayi maganar cikin wani erin murya. “Habeebi ka juya ka ganta gata chan” a hankali yake karkato da kansa har ya juya gabad’aya sannan ya d’ogo blue eyes nasa ya miqar basu sauqa ko ina ba se akan Ummimi. Kallonta yake cike da rashin yarda, sam yakasa yarda Ummimi ce yau a gabansa shekaru nawa rabuwansa da yasata a ido? 15 good years, memories na incident daya faru lokacin tafiyar Ummimi ne suka soma masa yawo a k’wak’walwa.

      “Anas” yaji muryar Ummimi dake nan kamar na Amal na tsamo sa daga duniyar tunanin daya wula, a gabanshi yaga Ummimi tsaye idanunta cike dam da hawaye tana kallon cikin idanunsa. “Anas... My.. My... My son... Anas my son” tasa hannu akan kumatunsa tana shafawa a hankali ayayinda k’arfin kukanta ya dad’u, shi kansa Anas idanuwansa sun kad’a sunyi jazir, he don’t even know what he is feeling fatansa kad’ai Allah sa dukkannin wannan mafarki ne.
     “Anas my son kamin magana dan Allah.” Hannunta ya sauk’e daga fuskarsa cike da k’in yardan itance a gabansa. “Ummimi?” Ya kira sunanta. “Kece?”
    “Nice Anas, Ummimi ce mahaifiyarka, Ummimi ce your own very real mother, Anas nice.” Duk yadda yayi dan shanye kukan yakasa besan a lokacinda yasoma zubar da hawaye ba, Fannah dake tsaye a gefensu tayi shiru ta k’ure musu ido tana kallon yadda suke zubar da hawaye.
     “Anas kayi min magana please” yunk’urin hugging nasa tayi wanda sakamakon haka yaja baya da wuri. Hannun Fannah ya rik’o “lets go Flower” nan ya juya.
   
    “Anas!... Anas! dan Allah ka tsaya.” Cewar Ummimi cikin sautin kuka. “Habeebi please ka tsaya ka saurareta kaji please” Fannah tayi maganar tana k’ok’arin tsayar dashi amman sam yak’i saurarenta. Murfin motan ya bud’e mata “get in!”
   “No Habeebi I’m not getting in, taya zaka bar mahaifiyarka haka?”
    “Fannah kinga banason abinda ze had’ani dake just get in” zata sake magana ya daka mata tsawa “I said get in!” Shi da kansa yasata cikin motar sannan ya zagaya ya shiga shima ya kunna motar. Ta window Fannah ke kallon Ummimi dake kuka sosai tana bin motar nasu da kallo amman Anas kota kanta beyi ba.

  **** _Some hours later..._
     Zaune Anas ke akan wresting chair yayi shiru, tun dawowansu bema Fannah magana ba itama haka bata huce da masifan daya mata ba d’azu ba, zaune take kan gado tana kallon sa a nitse ta miqe taje ta samesa tana tsaye akansa amman ko kewayowa ya kalleta beyi ba. “Habeebi” ta kira sunansa tare da zama kan cinyansa.
    “Yes Flower” yayi maganar not paying attention to her, hannunsa ta d’aga ta had’a da nata. “Habeebi I’m sorry for crossing you earlier.”
   “Is okay Flower ni yakamata in baki hak’uri for shouting at you I’m sorry kinji?”
    “Ba komai ya wuce muje mu huta.” Kai ya kad’a mata “banajin bacci just go, nap well Baby Hanan” yayi maganar hannunsa kan cikin Fannah.
   “Mesa baraka kwanta ba Habeebi ba haka na sanka ba tunanin Ummimi kake?”
    “I don’t want to talk about her Flower jeki huta.”
   “Habeebi yakamata ka cire son zuciya kayi facing reality, duk abinda Ummimi ta maka kamata yayi kayi hak’uri ka yafe mata, uwa uwa ce yanzu zakaso ace Hanan ta min kalan abinda ka ma Ummimi?”
    “For God’s sake Flower kidena kwatanta Hanan da Ummimi, Allah raba Hanan da halin Ummimi banason maganan ta karki sake d’auko min maganar ta.” Zata sake magana ya katse ta “am I clear?” Badan tanaso ba ta gyad’a masa kai ta sauk’a kan cinyansa ta koma gado ta miqe. Batasan a lokacin da bacci yayi awon gaba da ita ba.

     A hankali ya miqe ya nufa wardrobe tare da ciro wallet nasa family picture’nsu ya bud’e yana kallon fuskar Ummimi. “Why do you have to show up Ummimi? Why? Bayan duk mun mance dake munyi moving on mesa zaki dawo ki sake hargitsa mana rayuwa as you did before, why? Mesa bakida tausayi ne?” Ganin bayida amsoshi ga wannan tambayoyi ya haye gadon ya kwanta a gefen Fannah tare da kwantar da ita jikinsa hannunsa na akan cikinta.

   “Hanan in shaa Allah baraki d’au halin Ummimi ba, baraki ma yaranki abinda Ummimi tama Daddy’nki ba.” Daidai nan Hanan dake ciki tayi kicking take Fannah ta tashi “Habeebi Hanan ta motsa yanzu” murmushi ya k’irk’iro mata “yes Flower nima naji” hannunsu duka suka kai kan cikin nan Hanan tasake motsawa. Dad’i kamar ya cinyesu both suna feeling baby Hanan insu.

    ****
     _Washegari 1:30PM_
   Anas na tsaye a gaban mirror a bathroom fuskansa shaving cream ne da alama shaving zeyi danko riqe yake da shaving stick a hannu amman sam ya kasa yi, gabad’aya hankalinsa bayya a jikinsa ko bacci yakasa jiya se tunanin Ummimi yake, duk yadda yasan ze iyabi dan hana tunaninta yayi amman ya kasa the more yana hana kansa the more yake tunanin nata, Fannah ma takasa bacci ta zauna awake with him ko kad’an bayason maganan Ummimi koda Fannah ta taso da maganar masifa yake mata sosai wanda shima ba a son ransa yakeyi ba, he just can’t take it.

    Ya zurfafa cikin tunaninsa next abinda yaji shine hannun Fannah akan nasa tana amsar shaving stick d’in kwata kwata besan lokacin da ta shigo ba. Sanye take dawani silky dogon riga me spaghetti hands. “Habeebi take it easy please banason ina ganinka cikin damuwa.” Juyo da fuskarsa tayi ta soma yimasa shaving d’in lightly kamar yadda take ganin yanayi. Bece mata komai ba har seda ta gama masa ta wanke mai fuskar tare da share ruwan da towel. Kallon kansa yayi a mirron, sosai shaving d’in yamasa kyau saboda bata kwashe gashin duka ba, tabar sajen da kuma beard nasa wanda suka had’e kad’an very light irin na larabawan nan sosai yayi kyau.
   “Flower kin ma fini iya shaving d’in ban tab’a leveling haka ba” yayi maganar yana shafa kan gashin fuskar nasan. “Thank you sweetheart.”
   “No big deal Habeebi” Hannayenta ya had’a gu d’aya tare da pecking nasu, “Flower ko baki fad’a ba nasani you are mad at me saboda abubuwan dana riga miki jiya, I’m sorry kinji? I’m sorry for shouting at you and Hanan”
     “Na sani Abu Hanan you don’t have to be sorry komi ya wuce muje muci abinci amman yau ba anan nakeson chin abinci ba.”

    “Fad’i duk inda ke da Hanan kukeso muje muchi.”
  “A Restaurant Manhattan mukeso” (inda sukaga Ummimi jiya) kai ya girgiza mata “no Flower baramu je chan ba choose any other place amman banda chan.”
    “Ayya Habeebi chan nakeso.”
   “Flower NO! And that stays that bara muje chan ba.” Ba tare da tace komai ba ta k’wace hannayenta daga nasa ta fice zuwa d’akinsu tare da kwanciya kan gado tana jin footsteps nasa ta soma rera kukan qarya.
    “Flower yanzu kuka kike saboda nace bara muje chan ba?” Yayi maganar yana k’ok’arin d’agota. Shuresa ta shiga yi “ka sakeni nikam bana so stop touching me.”
    “Haba Mom Hanan I’m sorry kinji?”
  “Banji ba ni ka sakeni.” Kunnuwansa ya riqe both “Flower I’m sorry kiyi hak’uri.” Da hanzari ta suk’e hannayen nasa “ni bance kabani hak’uri ka ka kaini Restaurant Manhattan kokuma karka sake min ko Hanan magana.”

   “Flower kiyi hak’uri mana ki zab’i wani restor daban.” Banza dashi tayi tare da juya masa baya. “Mom Hanan magana fa nake miki...” Nanma shiru “Mom Hanan” still shiru “toh naji tashi muje Restaurant Manhattan d’in” a ransa yana me addu’an Allah yasa kada su had’u da Ummimi. Cike da ji dad’i ta miqe tare da brushing masa ligjt kiss a lips “thats my Abu Hanan! Lets go” kallonta kawai yake cike da adoration.


*© MIEMIEBEE*

 beeenovels.blogspot.co.ke

Tuesday, 27 September 2016

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 89
BY MIEMIEBEE







      Daidai tashiwan Anas daga bacci kenan, da k’yar ya iya ya raba jikin Fannah da nasa dan wani sabon salon baccin da ta koya bata bacci se in akansa. Bayan ya tura ta gefe yasake lullub’eta da bargo sannan yayi pecking nata a goshi. Bayi ya nufa yayi wanka agurguje yasa mint blue shirt da farin ¾ wando. Kitchen ya nufa yasoma had’a musu Chocolate-chip cookies for breakfast, in less than an hour yagama komai se coffee daya had’a musu, dining table ya shirya tsab sannan ya koma d’aki dan tayar da ita, zaune ya tarar da ita se murza idanunta take. “Good morning Flower har kin tash-” besamu daman k’arisa maganan ba dan yanayin daya tsince ta ciki kamar kuka take, daya gama k’arisowa kusa da ita kuwa seya tabbatar da hakan zama yayi a gefenta.
   Cike da tashin hankali yake maganar. “Omg! Flower why are you crying?” Kasa amsa shi tayi kawai tayi hugging nasa a yayinda kukanta ya tsananta. Bayanta yake bubbugawa a hankali, “shhh! Kibar kuka kinji I’m here stop crying Flower” seda ya tabbata tayi shiru ya d’agota. “Meya faru?”
    “Habeebi promise me baraka tab’a barina ba, promise me please.” Ta sake matsesa ajikinta tana meh cigaba da kuka.
    “Shhh! I will never leave you Fannah, never ki kwantar da hankalinki *_INA TARE DA KE_* forever.” Hannu yasa ya share mata hawayen ”meya kawo wannan zance? Kinyi mafarki ne?” Kai ta gyad’a masa. “You want to talk about it?” Nan kuma ta kad’a mai kai “I’m afraid Habeebi.”
    “Toh shikenan is okay, tashi kiyi wanka yanzu.” Ba musu ta miqe ta amshi towel dayake miqa mata bayan ta cire kayan jikinta ta d’aura towel d’in “Habeebi ka rakani bathroom d’in wallahi tsoro nake wai Ya Farouq na ciki.”
     “Mafarkin Farouq kikayi dama?” Cike da tsoro ta gyad’a kai. “Karki damu Farouq is gone foever.”
   “Nasani Habeebi still ina tsoro ka rakani please” hannunta ya riqe yakaita har bathroom d’in tabarsa yafito tak’i labule taja ta tare kanta shiko yana zaune akan hand basin bayan data gama suka fito tare man shafawanta ta nema kap kan mirron babu. “Habeebi kaga lotion d’ina?” Se ayanzu ya tuna ya had’a cikin akwati d’azu. “Bangani ba Flower, babu akan mirron?” yayi qarya.
   “Babu” tayi maganar tana nufan wardrobe dan ciro sabo.
   “Wait wait!” yayi sauri ya dakatar da ita, “babu achan ga vaseline chan ki shafa.”
  “Habeebi wai me kake b’oyewa cikin wardrobe d’innan ne?”
   “Kan Farouq ne aciki kika kuskura kik-” be samu daman k’arisa maganan ba sanadiyar tsallen da Fannah ta daka se a jikinsa ta tsaya chak! hannu yasa ya tare ta kafin ta fad’i. “Na tuba wallahi barin bud’e ba, dan Allah kabari ina vaseline d’in zan shafa.” Dariya sosai ya tsaya yi “toh muje mu shafa miki amman sauk’a tukuna.” ya gwada cire hannyenta dake rataye a wuyansa, kafad’a ta buga nufin barata sauk’a ba tare da sake kankamesa, haka tana zaune kan cinyarsa ta shafa manta. Kayan ta daya cire mata wani baqin abaya ya miqa mata, “gashi sa.”

     “Habeebi abaya nefah.”
   “Ina sane ai” ya gyad’a mata kai.
   “Toh ina zamuje da zan sa abaya?”
  “Ikon Allah! Mom Hanan ko d’an bincike seya baki hanya wani irin bincike ne haka?! Allah kika sake questioning d’ina zan bud’e wardrobe d’in Farouq yafito.”
   “Nabari nabari please kabar fad’in sunansa Hanan zatayi kuka.”
   “Toh Mom Hanan na dena” yayi managar hannunsa na akan cikinta. “Flower yaushe Hanan zata soma motsi I want to feel her.”
    “Dr tace se pregnancy’n yakai zuwa 16 weeks and Hanan is just 8 weeks yanzu kaga da saura.”
    “Ohh kice min se cikin ki yayi k’aaaatoo Hanan zata fara motsi.” Hannunsa ta d’aga daga kan cikin nata “nifa na fad’a maka bawai wasan nan na sani dariya bane banaso.”
    “Toh I’m sorry yi sauri kisa kayanki.”
  “In nasa ina zam-” bata k’arisa maganan ba tayi tsit dan ta tuna da abinda Anas yace mata akan ta sake masa tambaya ze ciro kan Ya Farouq cikin wardrobe. Kamar baby ya riqota a hannu zuwa dining table yasan ta da kewaye kewaye kar idanunta sukai kan akwatinan nasu.

    “Habeebi harda breakfast kamana yau wow!” Yana bud’e flask d’in k’amshin abincin ya mamaye wajen gabad’aya se shaqa Fannah ke tana d’igan miyau. “Baby hurry up and serve me yunwa nakeji.”
   “Kwad’ayi kike ji de.” K’aramar tsuka taja ta bugesa gefe ta amshi flask d’in taja gabanta ta soma chi. Tsayuwa yayi yana kallon ta cike da mamaki ganin takusa cinyewa ba shi yayi magana “Flower nifa ban chiba karki cinye duka.”
    “Ayyah Habeebi, Hanan kuma fah? Kayi hak’uri kabarmu mu cinye mana.”
    “Bawani Hanan d’innan glutton (meh shegen cin abinci) kawai.”
   “Kafad’i koma meh mu cinye?” Kai ya gyad’a mata yana murmushi yadda takecin abinci na bala’in kashesa. Bayan da ta gama yaje yayi frying sausages ya karya dashi shima. Bayan da suka gama ya tattara dining table d’in “Flower jekisa mayafin abayan naki we are going somewhere.”
   
     “Ina kenan Habeebi?”
   “Aww! inje inciro kan Farouq ko?”
   “A’a please nayi shiru.”
  “Better jeki shirya ina jiranki and karki bud’e wardrobe d’in ni na fad’a miki.”
   “Toh Habeebi kazo muje tare wallahi tsoro nakeji” seda yayi ta mata tsiya sannan ya rakata yana ganinta tana shiryawa har tagama tayi arabian rolling mekyau me amsarta sannan ta feffesehe da turare d’ayan da kad’ai tagani kan mirron ta tambayi Anas ina sauran turarukanta kuma tana tsoron kar yaciro kan Farouq daga cikin wardrobe. “Kingama?” Ya k’are maganar hannunsa k’ark’ashin hab’anta yana kallon fuskarta datasha light makeup.
    “Eh nagama semeh kuma yanzu?”
  “Se...” Yakai bakinsa kan nata “Habeeb-” be sake mata baki ba seda ya tand’e maroon strawberry flavor jan bakin data shafa tas.
    “Haba! Habeebi” tayi maganar lokacin da ta juyo tana kallon bakin nata a mirror. “Mena sharemin jan bakin yanzu?” Tayi pouting lips nata.
   “Saboda yamiki kyau sosai and banason in mun fita mutane suna kalla min ke, because you are mine Flower, as from today banason ki sake yin makeup in zamu fita okay?”
   “Nikam wannan Habeebin” tayi maganar chan k’asa k’asa tana zumbure zumbure.
   “Yes Flower kajol da nude lipstick kawai na yarda kina sawa kinji?” Shiruu “nace kinji?”
   “Naji-” katsesa yayi “good, agida kawai na yarda kina kwalya.”
   “Habeebi gaskia akwai ka da son kai amma kaika iya d’aukan wanka kamar me zuwa gidan biki idan zaka fita.”
    “Toh mijinki neni ai” be jira ta sake magana ba yajata waje zuwa mota sannan ya dawo ya kai boxes nasu mota dake se game nata take ta  bugawa ko kad’an bata ga me yake ba seda ya shigo mota ya tambayeta “Mom Hanan are you ready?”
   “Do I have a choice bayan baka sanar dani ina zaka kaini ba.”
   “Karki damu you’ll find out soon.” Seda ta bari sukayi nisa da tafiya ta yadda barasu iya komawa gida ba, balle yace ze ciro kan Farouq tasoma jero masa tambayoyi wanda duk ciki ba wanda ya bata straight answer.

     Wani tambayan ma seda ta ga sun dosa hanyan airport “Habeebi wai me zamuyi anan?†
    “Flower inda zaki d’an k’ara hak’uri everything will turn out cool.” Badan tanaso ba tayi shiru waje yanema yayi parking sannan ya fito da ita a yayinda wani security ya cicciro musu luggages nasu “Habeebi wannan fa akwatina ne a hannun mutumin nan” tayi maganar tana bin mutimin da kallo.
  “Yes ina sane Flower” ya jawota jikinsa.
   “Toh a ina ya samu?”
   “Acikin booth kayakin mune aciki.” Cike da mamaki da rashin yarda tsantsan mamaki ta d’ago kai tana kallonsa. “Kayan mu aciki? Kana nufin tafiya zamuyi?” Gira ya d’aga mata.
    “What?! Habeebi-” yatsansa ya aza a lips nata “shhhh! Nasan me zakice ban fad’a miki ba you are not ready barakije ba but please don’t say so kinji? Don’t ruin this I’ve worked hard for it.”

    Hugging nashi tayi abinda beyi tsammani ba a tunaninsa she will freak out tace masa barata jeba. Cikin sauti cike da jin dad’i tayi maganar, “Taya zance barinje ba Habeebi bayan nasan you worked hard for it I just hope we will enjoy inda zaka kaimu. Me, you and our Hanan Habeebi.” Dad’in kalamunta yaji sosai yayi hugging nata back “we will in shaa Allah Flower, I love you dearly.” Bayan tayi breaking hug d’in ta ciro wayarta daga jakarta “me zakiyi Mom Hanan?”
   “Zan kira Mami in sanar da ita.” Wayar ya amsa “don’t worry na riga na sanar da ita lets just go, hope you are ready to go fly to Abuja?”
   “Abuja? Okay I am ready.” Wajen private jet nasa wanda be tab’a tafiya dashi ba yau ne karo na farko suka nufa se admiring jirgin Fannah ke bata tab’a ganin kalan jirgin ba se a TV.
    “Habeebi mu kad’ai zamuyi tafiyan ne?”
    “Yes Flower this is my private jet ba public jirgi bane.”
   “Ohhh wow! Its amazing baka tab’a fad’a min ba.”
   “Sorry nima ban tab’a using nashi ba seyau tun kafin muyi aure na saya I mean tun lokacin dana fara sonki Flower I was hoping Allah ze kawo min ranan da zan shiga ciki dake that is when we’ve accept each others love just as we did a very long time ago now, I love you Flower” Kyakkyawar fuskarsa ta shafa “I love you too Abu Hanan.” Hannunta ya riqe suka shiga ciki bayan angama komai da komai sauran tashiwar jirgi Fannah tasa suka karanto add’o’in kariya. Tun anan Anas yagano ta soma jin tsoro dan kuwa this is her first time shiga jirgi.

    Seatbelts Anas yamusu tighting aiko ta riqo hannunsa gagam “Habeebi na fasa tafiyan ina jin tsoro please su tsaya.” Dariya yakeson yi amman ya b’ata rai. “Flower just keep calm muna tashi everything will be normal.”
    “No Habeebi ni kawai kace musu su tsaya” a hankali jirgin ya fara tafiya bata wani ji tsoro ba seda jirgin ya fara tashi anan ta fara kuka harda hawaye hannunta Anas ya matse cikin nasa yana fad’a mata dad’ad’d’un kalamu ahaka har suka tashi da suka fara flying kuwa seta bar jin tsoron. A hankali ta bud’e idonta d’aya sannan d’ayan. “Kin dena jin tsoron?” Kai ta gyad’a a hankali “are we flying already?”
   “Yes Flower we are kiduba window kiga.”
   “A’a tsoro nakeji.”
   “Ki leqa ba abinda ze sameki am here.” Cike da tsoro ta leqa kad’an da wuri ta dawo da kanta ciki “calm down Mom Hanan ki kwanatar da hanakalinki ko kinason Hanan ma taji tsoro ne?” Kai ta kad’a masa “good” yace tare da pecking nata, headphone ya ciro yasamata akai tare da kunna mata qira’a. Cikin ‘yan mintuna suka iso Abuja nan ma da suka zo landing kad’an ya rage Fannah batayi kuka ba.

   Transcorp Hilton Hotel Abuja suka sauk’a zuwa Azahar bayan sunchi abinci sun sake wanka suka wuce embassy’n USA  kasancewar a New York Anas yakeson suyi rainon Baby Hanan. Dad’i sosai Fannah taji daya sanar da ita plans nasa, sun gaji iya gajiya wai haka ma dan da sanin ido kenan aka samu aka gama musu abubuwan on time zuwa jibi everything will be ready seya rage sauran tafiya. Koda suka dawo gida Fannah takasa fitowa daga mota dan gajiya Anas ne ya cirota da kansa yakaita har zuwa d’akinsu. Akan gado ya direta kafin ya juya ta riqo kolan rigarsa tajasa jikinta kafin yayi wani k’wararren motsi ta kifa bayansa da gadon ita kuma ta haye kansa. “Habeebi bacci nakeji.”
    “Flower bamuyi Sallan isha bafa.”
   “I know Habeebi mubari zuwa 10-11 haka se muyi please.” Shiru yayi tare da aza hannunsa kan bayanta yana shafawa a hankali. In the next 5 minites Fannah tayi bacci. “Flower!” ya kira ta shiru ba amsa.
    “Flower har kinyi bacci?”
   “Uhmm” tayi groaning cikin baccin. D’an murmushi ya saki tare da pecking kanta. A haka shima ya samu yayi bacci se 11:27PM Anas ya tashi anan sukayi Sallah suka chi abinci sannan suka watsa ruwa suka sake komawa bacci.

     Kwanan su biyu a Abuja Anas ya sama masu visa. Washegari around 8:00AM suka d’au flight zuwa New York kamar sabon shiga haka tata jin tsoro ma yau.

     _10 hours later... Exactly 6:00PM a Nigeria 1:00PM a kuma New York_
 
     Su Anas suka shigo NY gajiya kam ansha sosai, musamman Fannah kusan duk a kwance kan gadon dake jet d’in ta yini amman hakan be hana k’afafunta kumbura dam ba.
    A MANDERIAN ORIENTAL HOTEL NY suka sauk’a. Fannah de takasa b’oye k’auyancinta inwhich Anas found so adorable and cute komai tagani seta tambaya. Warming jikinsu sukayi cikin had’ad’d’en jacuzzin dake bathroom d’in sannan suka yi ordering abinci sukaci.

     Baccin sauk’e gajiya suka yini sunayi ranan da daddare bayan sun idar da Sallan isha sunci dinner Anas yahau massaging wa Fannah k’afafunta da suka kumbura bayan daya gama mata kuma suka kwanta.
     Washegari basu fita ko inaba a d’akinsu suka wuni ba abinda suka tsinana wa kansu banda romancing juna da suka yini sunayi se the next day suka fita ganin gari leisure points da dama erinsu 911 Memorial Guided Tour with Museum, Disney on Broadway Exclusive, Magic Walking Tour, NBC studio, central park, Brooklyn bridge, 9/11 Memorial and Museum, da sauran su suka jejje se killing selfies suke Fannah nawa Afrah da kishi kamar ya kasheta sending. They had alot of fun se Maghrib suka dawo masauk’insu all tired. Sallah kawai sukayi suka miqe kan gado se bacci.

      Haka fa rayuwa ta cigaba da kasancewa Mr. And Mrs. Fauzi cikin so da k’aunan juna, zamansu a New York ba shiyasa Anas hana Fannah sa hijabi ba dukda kuwa in aka gansu se an tsaya ana kallonta amman kamar yaddda bata damu ba haka shima Anas d’in, sosai yake kishin Flowersa. Baby Hanan nasu kuwa se girma take a yanzu haka cikin Fannah nada 5 months da anganta anga me ciki dan ko har ya b’ullo kai tun anan Anas ya fara neman tsokananta dan haka tama bar zama da vest inya nan se baggi kayakin da zasu b’oye mata‘yar cikin nata, ga yadda taciko dam iya cikowa Anas baya iya hak’ura da ita yanzu aduk lokacin da ya kalleta se sha’awan ta ya taso masa kullum suna cikin yin abu d’aya.

   ****
      Yau ranar ta kasance Tuesday ayau ne Mr. and Mrs Fauzi zasuje duban gender’n Baby’nsu tunda cikin yayi k’wari, dukansu bugawa zuqatansu ke barin ma Anas dakeson ‘ya mace kamar hauka.

****
     Murna gun Anas da Fannah baya misantuwa da aka tabbatar musu mace ce baby’nsu. Sabon siyayya Anas yace zasu soma yiwa Baby Hanan yanzu da aka tabbata Hanan d’ince a hanya, inbawani ikon Allah ba.
     Ta ward d’in karb’an haihuwa suka fito aiko Fannah na ganin yadda mata masu ciki ke nak’uda yadda suke shan azaba ta rushe wa Anas da kuka. Kuka na sosai seda suka nemi waje suka zauna hankalinsa duk yabi ya tashi ya rasa meya sata kuka haka, just a while ago she was happy jin sex na baby’nta yanzu kuma tana kuka to meh dalili? Ko ta dena san ‘ya mace sena miji ne?

    “Flower is okay kinji stop crying please ya isa” ya cusa ta ajikinsa yana bubbuga bayanta har izuwa lokacin da tayi shiru.

*© MIEMIEBEE*

  beeenovels.blogspot.co.ke

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 88
BY MIEMIEBEE










 
     
      Kuka ne kawai Mami batayi ba kafin securities na wajen suka barsu suka shigo har take cewa aranta barata sake zuwa gidan Fannah ba ko Villa albarka. Bayan Anas ya bud’e musu k’ofan yamusu sannu dazuwa da Mami tayi oberseving fuskarsa kuwa setaga kamar shi d’inma baida lafiya, batasan saboda yadda ya damu da rashin lafiyar Fannah neba harshima yake affecting nasa.
    “Anas kaima bakada lafiyan ne?” Murmushin dole ya k’irk’iro.
   “A’a Mami mushiga daga ciki, she is inside.” Bayansa sukabi zuwa d’akin.
    “Mami” cewar Fannah cikin wani erin murya. “Subhanallahi Habibti” tayi maganan tana tab’a tempreture’nta. “Sannu kinji? Sannu, Anas meke damunta haka?” Shiru yayi yana nazarin taya ze fara sanar da ita face-to-face. Ganin baida na cewa Fannah ta amsa ta “Mami munje asibiti aka tabbatarmana juna biyu ne tattare dani.”
    “Kai toh Alhamdulilah, Alhamdulilah Anas shine baka sanar dani jika nane yakusa ko ta kusa isowa ba?” K’eyansa yashafa cike da kunya. “Toh Habibti Allah raba lafiya, sannu kinji? Wannan daman ai is normal nan da ‘yan satuka zaki dawo kanki na da se hak’uri.”
   “Sannu Ya Fannah, Allah raba lafiya” cewar Afrah tana yimata wani shu’umin kallo. Kai kawai Fannah ta kad’a mata. “Kina iya cin abinci?” Kafin ta amsa Anas ya amsa “a’a Mami tun jiya ba abinda tasha banda black tea.”

    “Toh ya kikeso d’an naki yay k’wari in bakiya chin abinci iyyeh Fannah?! Afrah zaki koma gida yanzun nan ki taho min da gauta dakuma zogale mu had’a mata miya ta samu taci.” Anas da bashi akace zechi ba shine yakai hannu bakinsa ya rufe kan wanda zeyi amai. “Mami is it necessary? Flower zaki iya chin miyan gauta koh? Zaki iya chi?” Kai ta girgiza masa.
    Kan gadon yanufa ta d’ayan side d’in ya zauna “zakici louisiana ko bufalo wings?”
   “Habeebi black tea nakeso.”
   “Toh ai kinji Mami tace baby’nmu will not be healthy in bakiya chin abinci, ko in miki frying sausage?”
    “Ni black tea nakeso” Kallonsu kawai Mami take “kun gama?” ta tambayesu. Shiru sukayi suna kallon ta. “Nace kun gama? Afrah wuce gida ki d’ibo min gautan.”
   “A’a Mami please abin beyi zafi haka ba” cewar Anas yana dakatar da Afrah daga tafiyar. “Akwai ragowar glorified rice na jiya zan mata reheating tachi.”
   
    “Shi glorified rice d’in kenan? Anas kaga fa duk wannan abubuwa na shirmeh ba taimakanta zasuyi ba kabari taci tuwo d’anku yasamu lafiya maza jeki Afrah.” Anas kan yayi kuka. Nan da nan Afrah taje ta dawo, Mami tashiga had’a miya bayan ta gama ta kawo d’akin da tuwon semovita. Take warin miyan gautan ya mamaye d’akin. “Habibti tashi kichi, kinji? sannu.” Hanci Anas ya toshe dan warin da miyan ke masa he can’t believe Mami zatasa masa Flower cin wannan abu shi dayasan haka ne ze faru da be kira taba in the first place. Da kanta ta zaunar da Fannah ta soma bata, loma biyu Fannah tayi tajawo bowl tayi amai ciki hakan ba shi ya hana Mami sake d’ura mata ba.
    “Mami please ya isa haka nan karta sake hararwa.” cewar Anas cike da tausayin Fkowersa.
    “Anas kasan me nakeso dakai?” Kai ya kad’a mata hankalinsa na akan Flowersa ganin yadda batason chin abincin hankalinsa ya sake tashi. “Kaja Afrah ku fice kubani gu in bata abincin nan, nasan tsayunwanka nan ke hanata ci, in baka nan ita da kanta zata zage taci tashi kufita.”
    “Habeebi please karka tafi kace mata banaso” Fannah tayi maganar kamar wacce zatayi kuka.
   “Fannnah banason shagwab’a fa tuwon nan da kike gani shi ze baki k’arfi ba wannan ruwan da ake ta d’ura miki wanda banda kumburi ba abinda ze saki ba” tayi maganar tana bin ledan ruwan da aka sawa Fannah da kallo. “Anas jiranka fa nake.” ta miyar da kallonta a garesa. “Da k’yar ya miqe amman yakasa barin d’akin. “Mami please kibita a hankali kinga batada lafiya.”
   “Naji zan bita a hankali fita ina jiranka.” Badan yansaso ba yafice Afrah tabi bayansa.

     Haka Mami tasa Fannah agaba ta riga d’ura mata miyan gautan kamar ba gobe tun tana hararwa har tadaina yazauna acikinta. “Good anjima kad’an kuma zakici miyan zogalen shima yana da amfani sosai, sannu koh?”
    “Mami kasheni kikeson yine? Dan Allah ya isa ni kitafi ma.”
    “Ai ina nan Fannah kinga yadda kika zube kuwa? Ace mahaifiyarki na raye amman kikayi wannan rama? Wannan abu da keda Anas kuka raina shi zai taimaka miki bawani bufalo wings ne komeh abin ban ma san shiba.”

****
    Tun kamin Azahar Mami ta tura Afrah gida gudun kar Aiman ta dawo ba kowa gida itako se bayan La’asr Anas yayi dropping nata bayan tabawa Fannah miyan zogalen kuma alhamdulillah bata harar ba, kunne sosai tajawa Anas da yadaina biye wa Fannah yana barinta tana kwana da yunwa, sauran ragowar tuwon kuma ya tabbata yabata zuwa dare in bahaka zata dawo gobe tabata da kanta.

    Kafin Anas ya dawo gida Fannah tariga tayi bacci, wani sabon ruwa yasa mata kamar yadda Dr. Mansoor ya koya masa sannan ya rage kayan jikinsa ya haye gadon shima tare da aza kanta a k’irjinsa yana me shafa bayanta a hankali anan shima yasamu yayi bacci se Maghrib ya tashi yayi alwala ya tayata tayi itama sannan yajasu Sallah, jikin nata alhamdulillah tunda har tasamu tayi Sallah duka a tsaye.
   Tana manne a jikinsa jiki ba k’arfi tace, “Habeebi zansha black tea.” Kai ya girgiza mata “Flower kinga Mami tace kar inbarki kina shan tea zallah tace se in kinci tuwon d’azu inbarki kisha tea.”
     “Habeebi wallahi tuwon ba dad’i please ka had’amin tea.”
    “Mom Hanan I know” yayi pecking goshinta “kinason Hanan koba haka ba?” Kai ta gyad’a “good then eat well se Hanan namu tafito healthy, kinji Mom Hanan?” Shiru tayi bata ce komai. “Yawwa Mom Hanan tashi inje in d’ebo miki toh.”
    Koda ya kawo abincin k’inci tayi da k’yar cike da dabara yasata ta soma ci har ya gama bata bata harar ba anan ne ya had’o mata black tea ya bata. Bayan sun idda Isha yasa mata last drip nata suka kwanta.

      Washegari ma da zazzab’i ta tashi sede ba kaman na jiya ba nayau da d’a  sauk’i, kamar yadda Mami ta buk’acesa ya mata reheating tuwon jiyan yau harda ‘yar kukanta dak’yar yasamu taci sam batason ci gashi kuwa shi kad’ai ne in taci bata hararwa bayan shi duk wani abinda takai baki seta fito dashi waje. Da rana Mami ta turo Afrah da miyan ayayo da d’anyen kub’ewa duka a had’e. Fannah kamar ta k’urma ihu shikansa Anas dayake bata amai abincin ke sasa amma haka ze dage yabata.
   
  ★★★
     Mami bata fasa kawo wa Fannah miyar gargajiya ba, acikin ikon Allah Fannah ta fara samu sauk’i in two weeks time tadawo old self nata sede sometimes da take tashi da morning sickness, jiri dakuma k’warnafi bayan nan bawani ciwo again. Babynsu da suka bata ko shi suna Hanan kuwa  nan cikin k’oshin lafiya.
     Yau ranar ta kasance Sunday Fannah na zaune akan dining table ba abinda babu shi agabanta inde kayan k’walama ne sauran ma ba iya cinsu ta iya ba amman tasa Anas ya siya mata ta tab’a wannan ta tab’a wancan ayayinda Anas ke a parlour se famana latsa wayansa yake da alama abu very important yake dan yadda yayi focussing akai. Chan data gaji da ciye ciyen nata ta tattara ragowar tasa cikin leda sanna ta miqe, sanye take da baggi T shirt da befi tsakiyan cinyarta a tsayi ba da hannunsa d’aya an jefar, gashinta kuwa takamasa gud’aya chan a saman kanta, zare zaren ragowan da basu samu shiga packing d’inba na akan fuskarta kasancewar sakwa-sakwa tayi packing d’in. Parlourn ta iso ta baje kan cinyansa ko uffan bece mata ba se harkar gabansa yake.
   “Habeebi” ta kira sunansa tana kallonsa.
   “Uhm Mom Hanan what is it? Har kingama shanye duk tarukuchan dake kan table d’inne?”
     “A’a.” Ta basa takaicaccen amsa.
   “Toh me kikeso?” Har a yanzu be d’ago kai ya kalleta ba hakan ya d’an b’ata mata rai. “Habeebi wai me kake haka da ko kallona baraka d’ago wannan blue eyes nakan barakayi ka kalleni ba.” Seda ya sake latsa wayan na kusan seconds talatin sannan ya d’ago blue eyes nasa “yes Baby machine me zan miki?”
   “Bansani ba seda ka gama replying nata kasan ina a raye ka cigaba da abinda kake” kafin tace zata tashi ya zagaye hannayensa a ‘yar kunkuminta ya dakatar da ita.

     “Wani irin magana kuma kike Flower? Yanzu har kina tsammanin akwai macen da zata iya snatching maki ni a duniya? (ko Fans albarka😜) i’m not replying any gurl kiduba wayana kigani.”
   “Eh daka yi deleting chat d’inba ai nasan baka sonmu da Hanan yanzu.”
    “Flower wai mena miki yaune kam? Naga alaman ba abinda ke miki dad’i kamar kiga kin k’untatamin, niko meh kikamin it will never change the love I have for you” daidai zeyi kissing nata kenan tasa hannu ta riqo lips nasa “kad’au yau ma wannan magic kiss nakan zeyi tasiri akaina neh? Toh bareyi ba sakeni nikam.” Sake matso da ita jikinsa yayi “tell me Mom Hanan why are you mad?”
     “Aww ma tambayana kake koh? Bayan tun d’azu kake ta danne dannen ka a wayanka baka damu ko *_INA TARE DA KAI_* ko bana *_TARE DA KAI_* ba, your phone is more important than me.”
    “Inji waye Mom Hanan? Kinason kisan me nakeyi a wayan neh?”
    “Banaso ai na riga na san-” bata k’are maganan ba yayi shutting nata dawani hot kiss sam tak’i basa had’inkai a farko dan tasan sa sarai he is such a bad kisser nan danan zesa ta mance da dukkannin problems nata ta yafe masa ba tare da tasan tayi hakan ba, sam yak’i sake ta, ya d’au alwashin se ya kashe mata jiki liqis tukuna, yana meh bin duk wani saqo a jikinta da hannayensa yana meh mata sending electric sparks. Ai duk yadda tayi dan k’in basa had’in kai ta kasa daga k’arshe seda tayi giving in wa kiss nasa, ta sa hannayenta duka cikin gashin kansa pulling him closer, se kissing juna suke so deeply, sun d’au tsawon lokaci suna abu d’aya sannan da hanzari suka hau romacing junansu ganin abin bana tsayawa bane na bugo legediz benz d’ina na rufo musu k’ofar parlourn harda cin tuntub’e na.

   ****_An hour later..._
     “Nikam kabar kallo na da wannan mayun blue eyes naka haka bad boy kawai.” Fannah tayi maganar tana mayar da T-shirt nata jiki. Anas kuwa na a kishingid’e jikin 3 seater da nickers zallah a jikinsa, ya yi crossing arms nasa a kan chest da wani killer smile a fuskarsa yana mata wani mayen kallo next abinda yaji shine shirt nasa da Fannah ta wurga masa a fuska, hannu yasa ya cire har a yanzu bebar murmushin ba. “Flower menayi kike cemin bad boy?”
    “Ai kafi kowa sani” daidai tazo wucewa ta gefensa kenan yajata ta fad’a jikinsa ya saketa sam yak’i.
    “Bansani ba tell me” yayi maganar numfashinsu na had’ewa dan yadda fuskokinsu ke kusa kusa.
    “Gashi kuwa I can’t resist you koda nace barin baka had’in kai ba at last senayi because you got it all Abu Hanan.” Pecking nata yayi a kumatu “so do you Mom Hanan.” Kanta tayi adjusting a jikinsa sannan tace, “Habeebi meh kakeyi amman d’azu a wayan?”
     “Baby Mamah bakiyi trusting d’ina bane?”
   “Nayi mana Habeebi kawai ina son sani ne.”
   “Okay kinsan yau Baba yacika 1 year 10 months da rasuwa koh?”
    “Ya Salam! Habeebi wallahi na mance I’m so sorry kaji?”
    “Is okay nasan bada gangan kika manta ba, ban tab’a fad’a miki bane saboda aikin lada ba’a son ana yad’awa, so kowani 2-2 months nake sa akai kud’i da kaya gidan marayu in memory of Baba.”

     “Owww! Kayi tunani me kyau Habeebi, Allah tura masa ladan kabarinsa kaikuma Allah cigaba da bud’i dakuma kare mana kai, Hanan and I love you so much.” Tayi pecking  nasa shima a kumatu.****

     _3 weeks later..._
   Daidai cikin Fannah nada 8weeks (2 months) kenan alhamdulillah jikinta da sauk’i sosai. Yau ranar ta kasance Monday as early as possible k’arfe 4:30AM Anas ya tashi shikad’ansa yahau shirya musu akwatinsu shida Fannah, suprise yakeson mata. Duk wani abinda zasu buk’ata be bari a baya ba seda yagama had’a komai sannan ya d’au ‘yar k’aramar hand luggage ya cika da kayan wasa da teddies na Baby Hanan kafin Asubah yagama had’a komai ya ajiye boxes d’in a parlour yadda Fannah barata gani ba.

    ****
     Fitowan Fannah daga bayi kenan tayi alwala, ta d’au hanyan wardrobe nasu dan ciro hijabinta Anas yayi sauri ya dakatar da ita “Mom Hanan wait hijabi kike nema koh?” Kai ta gyad’a masa. “Good gashi.”
     “Thanks amman banason wannan yanada nauyi nafison d’ayan barin d’auko yana cikin wardrobe d’in ai.” Gabanta yasha sabida kuwa duk hijabanta masu laushi yasa su cikin akwatin bayason ta bud’e wardrobe d’in tayi ruining suprise daya tanadar.
     “Habeebi wai me haka? Muna chin lokaci fah, kamatsa in d’auko hijabi na muyi Sallah.”
   “Ga wannan kisa.” Ya miqa mata  k’in amsa tayi “banason wannan yanada nauyi.”
   “Toh nikuma nace kisa wannan.”
   Haba manah! Habeebi so kake in jik’e kafin mu idar da Sallan ne?”

     “Flower ai sanyi ake karb’i kisa mana.” Kafad’a ta buga “ni banaji, matsa min.” AC’n d’akin ya k’ure “kinji sanyi ake karb’a kisa.” Seda ta galla masa harara sannan ta amsa tasa bayan da suka idar da Sallan ta nad’e hijabin as always zata miyar cikin wardrobe d’in, takai hannunta kan handle d’in kafin ta bud’e Anas ya dakatar da ita ta hanyan sa hannunsa akai seda ta firgita. K’irji ta dafe “Habeebi kasan ka ban tsoro please kadaina what if wani abu yasamu Hanan fah?”
    “I’m sorry in shaa Allah ma ba abinda ze sameta kawo in ajiye miki jeki kwanta.” Kallonsa tayi na ‘yan lokuta. “Habeebi wallahi you are hiding something from me, meh abun? Kuma mesa bakason in bud’e wardrobe d’in dakaina?”

    “Saboda Dr. Yace in hanaki yin any form of labour kuma ai bud’e wardrobe ma aiki ne, prince charming naki ze miki jeki kwanta.” Har a yanzu bata yarda ba. “Sekuma meh? There is still something you are not telling me.”
   “Oh! Mom Hanan kin cika bincike sekace wani spy” Turata gefe yayi ya sa hijabin sannan yaja hannunta suka koma suka kwanta. Daman tun jiya ya sanar da ita bareje office ba yau dan haka tasamu takwanta peacefully.

    _8:07AM_

 

*© MIEMIEBEE*

   beeenovels.blogspot.co.ke

Monday, 26 September 2016

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 87
BY MIEMIEBEE










       
     “Yauwa Habeebi nace ya labarin Moosa ne? Har yanzu shiru ba’a samesa ba?” yatsunsu yayi interwining;
    “D’azu munyi magana da police sunce suna kan investigating har yanzu, kinsan Farouq shege ne Allah kad’ai yasan inda yakaisa.”
    “Allah sa a samesa a raye Habeebi nasan danni Ya Farouq ya masa duka haka saboda yak’i shigo dashi ciki.”
    “You are right Flower in shaa Allah zamu sam-” besamu daman k’arisa maganan ba sakamakon ringing da wayar sa yasoma ganin number’n Inspector General yayi saurin d’agawa.
    “Hello Inspector.”
   “Yes Mr. Fauzi I will like to congratulate you.”
   “Yes... About what Sir?” Yayi maganar cike da neman k’arin bayani.
     “Mun samu Moosa your driver achan Mongunu wai gidan Bad Boy achan Farouq ya kaisa ya b’oyesa.”
    “Alhamdulillah, Alhamdulillah this is indeed a great news.”
    “It is kuma shima Bad Boy d’in yana a hannu yanzu according to record babban drug dealer ne partner in crime na Farouq kuma dan da miliyan biyar nasa akayi bailing Farouq a prison 2 weeks ago.”
    “Okay... Thank you Sir ina Moosan yake yanzu?”
    “An kaishi asibiti dan duba lafiyarsa I guarantee you ba abinda suka masa.”
    “Ina godia Sir zamuyi magana anjima.” Nan ya katse wayar tare da juyo da kallonsa kan Fannah dake kallonsa fuskarta d’auke da tambaya. Kafin tayi magana ya aza yatsansa kan lips nata “nasan me kikeson tambaya, an samu Moosa? Ko ba haka ba?”
    “LOL eh haka please an samesa?”
    “Yes sweetheart an sami Moosa yana asibiti yanzu as we speak yakamata inje in duba sa, I will be right back.” peck ya manna mata a goshi kafin ya miqe ta riqo shirt nasa. “Habeebi nima zanje.”
    “Zakije ina?” ya tambayeta disbelievingly.
    “Asibitin mana nima in duba sa kasan fa nice sila.” Kai ya kad’a mata “inaaa! you are going nowhere ko kin manta kema yau aka sallamoki? Bafa kida lafiya ki zauna ki huta barin d’au lokaci ba zan dawo kinji Flower?”
    “O’o” ta shakwab’e fuska.
   “Flower please kiyi hak’uri ki zauna zan isar masa da saqon gaisuwanki bareyi ki bini ba.” Badan tana so ba ta gyad’a kai wearing a sad face.
   
     “Flower ba goodluck kiss?”
   “Eh babu” ta fad’a ba tare da ta kallesa ba.
   “Oh common! Flower.” Alokaci d’aya ta d’ago fuskarta tana mai murmushi “Habeebi na gabad’aya ze fita barin basa goodluck kiss ba? Impossible!” a hankali ta had’a musu lips tare da kissing nasa a passionately. “Off you go take care okay?”
    “I will and you too Flower, in shiga dake ciki ko zaki iya?”
    “Don’t bother zan iya I love you”
   “I love you too Flower.” har ya soma tafiya ta tsayar dashi “wait wait tsaya in d’aukemu selfie so I can be starring at my husband’s handsome face kafin ka dawo.” Murmushin jin dad’i ya saki tare da dawowa baya ta d’aukesu sannan ya fice, anan yashiga ya fito da key’nsa ya fice itama bada jimawa ba tashiga ciki.

   *****_3:10PM_
      Daidai nan Anas ya dawo gida rashin ganinta a parlour ya tabbatar masa a d’aki take aiko yana shiga d’akinsu ya sameta zaune kan dressing mirror se sosa cikin gashinta take da comb tsantsan k’aik’ayi.
    “Flower” ya kira sunanta anan ne tasan da shigowarsa ta juyo tana kallonsa cike da so da k’auna “sannu dazuwa Habeebi.”
    “Thank you, me kikeyi haka?”
   “Wallahi kaina k’aik’ayi na kwana biyu ban wanke ba, ya jikin Moosa’n?”
   “He is okay alhamdulillah.” Yayi maganan yana dosowa gabanta.
    “Toh masha Allah, aha! Mami ma ta kira tana gaisheka” tacigaba da sosa cikin gashintan.
    “Ina amsawa” yace tare da karb’e comb d’in daga hannunta. “Habeebi bani please k’aik’ayi” ajiyewa yayi kan mirron tare da rik’o hannunta “muje in wanke miki kan Flower.” Dariya sosai ta tsaya yi wanda sakamakon haka Anas ya tsaya kallonta yana admiring nata, dariyan sa na mugun kashesa.
   “Habeebi baraka isheni da kayan dariya ba, yaushe kazamo hair dresser da zaka wanke min kai?”
    “Aww bakisani ba Flower? I can be anything fo you, Dr, hair dresser, cooku, servant komi da komi ma, muje.”
    “A’a please kabari.”
    “Flower banason dogon surutu” hannunta ya sake ya shiga cikin wardrobe ya ciro mata vest tare da miqa mata “sa muje in wanke miki” anan shima ya rage kayan jikinsa ya ragar da singlet se ¾ wando zallah.

     Ba musu ta cire T- shirt d’in tasa vest daya kawo mata acikin jacuzzi ta zauna ya karkato da kanta direction guda. “Welcome to FAHNAS beauty salon how can I help you Mrs. Fauzi?” Dariya sosai take “thank you, wash and set nakeso.”
    “You are at our service.” Daga farko seda yayi combing dogon sumanta sannan ya wanke thoroughly da ruwa sekuma da shampoo, a hankali yake mata massaging kan wanda ke mata dad’i sosai cikin d’ank’ank’anin lokaci ta nemi k’aik’ayin ta rasa. Bayan daya gama wanke mata ya d’aure mata kan da towel sannan ya miqa mata babban towel ta nannad’e jikinta dashi. Gaban dressing mirror ya ajiyeta ya ciro hand drier ya kunna sannan yasoma drying mata gashin bayan ya gama ya mata oiling sannan yayi mata packing gu d’aya harda style na donurt.
 
    “Wow! Habeebi you are amazing!” tayi maganan tana duban kanta cikin mirron. “Wai nikam ya akayi ka iya komai neh?”
   “LOL!” yasoma feeling. “Kin manta inada sister ne?”
     “Thank you so much for making my hair.”
   “Always Flower.” Yayi maganar yana mata murmushi miqewa tayi tare da pecking nasa a both kunatunsa, sekuma tip na hancinsa kafin ta kai kan lips nasa ya dakatar da ita. “Uhn-uhn Flower I know where this is going.” Murmushi cike da kunya ta saki “then let it happen.”
     “A’a Flower kin tuna meh Dr. Yace? Cemana yayi kina buk’atan atleast 3 months na hutu before you can get pregnant again.”
    “Toh ai hutun d’aukan ciki yake nufi bawai totally mubar yin...” Sekuma tayi shiru “ai ka gane me nake nufi.” light red lips nasa yayi pouting “ban gane ba” yayi maganar da gira d’aya a d’age. Bugi cike da shakwab’a takai masa a hannu “wallahi qarya kake ka gane.”
    Dariya yake sosai “toh naji na gane but even still Flower muyi hak’uri.”
   “Toh baby ba semuyi using protection ba.” Kai ya girgiza mata “I don’t trust in that, saboda sometimes suna bursting kuma kinga zaki iya samun ciki if that happens which is very harmful to your condition” ya tab’a tip na hancinta. Baki ta murgud’a masa “ina ni kayi rejecting yau Mr. Fauzi nima sena rama.” Hannayenta ya gwada rik’ewa da wuri ta fisge ita a dole tayi zuciya. Daidai zata juya masa baya kenan ya zagaye hannayensa a waist na tare da pulling nata closer to him. “Haba Mrs. Fauzi matar Anas, the mother to my awesome kids in shaa Allah. Taya zanyi rejecting the perfect woman I’m lucky to call my wife? Kema kinsan hakan k’arya ne, Flower ni kaina ina missing naki like hell I miss us on bed amman kinga lafiyarki ya fiye min komai, koda na shekara da shekaru akace inyi avoiding naki zanyi inhar hakan ne ze sama miki lafiya balle ma na d’an months, bawai nayi rejecting naki bane understand kinji? I’m sorry my sugar lips”
   
   Kafad’a ta buga uwar zuciyar har yanzu bata sauk’o ba. “Flower meh kikeso in miki ki hak’ura?”
    “Muje mu kwanta.”
   “Zamu kwanta amman ba abinda ze shiga tsakaninmu its a deal.”
    “O’o toh na fasa hak’uran.”
    “Sena sauk’a akan knees d’ina zakiyi?” Ganin yasoma sauk’a tayi sauri ta hanasa. “A’a please baby don’t na hak’ura but can I kiss you atleast Mr. Fauzi?” Murmushi yamata “ofcourse Mrs. Fauzi” sannan yayi owning lips nata da kansa yasoma kissing nata.***

     ****
      Tun daga ranan rayuwan masoya biyu ya cigaba da kasancewa kamar yadda ya saba da a baya ko inche fiye dana da ma, ba fad’a kullum cikin farintawa juna rai suke, ga uban lovely suprises da Anas yake cikin bawa Flowersa a kullum. A kullum wutan soyayyan junansu dad’a ruruwa ya ke a birnin zuqatansu.
 
   ★★★★
    _6 months later..._
_Monday, 6:20AM_

       Tsaye Fannah ke a kitchen da shiganta kusan minti uku kenan yanzu amman takasa tsinana komi ciki dan wani irin zazzab’in da takeji wanda ya fara mata tun jiya da daddare amman sam tak’i nuna wa Anas saboda batasan sasa cikin damuwa ‘cause ta lura aduk lokacinda batada lafiya Anas yafita damuwa. Tsugune take gefen sink takasa koda miqewa, tafi minti biyar ahaka sannan da k’yar ta miqe sanadiyar amai da yazo mata, cikin sink d’in ta riga kwararo amai wane zata harar da hanjinta seda tayi emptying cikinta kap sannan ta wanko bakinta, wane k’adangare tabi jikin bango har izuwa d’akinsu.

      A kasalance ta miqe agefen Anas dake ta bacci hankali a kwance.
    “Habeebi” ta kira sunansa ko motsawa beyi ba se a karo na uku yayi groaning “uhmmm Flower.”
   “Habeebi ka tashi kaji? Yau Monday akwai office.” A hankali ya bud’e idanunsa kallo d’aya yama Fannah yagano batada lafiya she is looking so pale. Cike da tashin hankali ya shafa fuskarta “Flower are you okay?” Kai ta girgiza masa “Habeebi I’m sick ko breakfast na kasa had’a maka, I’m sorry.”
    “Subhanallah, shhhh! Haqurin me kike bani?” body tempreture’nta ya tab’a yaji ya hau sosai yayi zafi. “Omg! Flower kinji tempreture naki kuwa? Ya kikeji?”
    “Zazzab’i Habeebi sau biyu nake amai yau ko miyau ban iya had’iye.”
   “Omg! Flower mesa baki fad’amin ba?” I’m sorry kinji?” Kai kawai ta girgiza masa dan batajin ma zata iya magana.
      “Arghhh!” Ta saki wani irin k’ara hannunta rik’e da gefen cikinta, cike da tashin hankali yakai yana dubanta “Flower wani abu ne?”
    “Habeebi ciki na tanan, wayyo!”
   “Sannu Flower ina zuwa” bayi ya fad’a a gurguje yayi wanka sannan ya had’o mata black tea tare da b’allo mata meds. Duk’unk’une cikin bargo ya tarar da ita “Flower tashi ki zauna kisha magani kinji?” Da k’yar ya miqar da ita tare da jinginata jikin gadon, magunan ya miqa mata sam tak’i karb’a.
    “Flower kiyi hak’uri kisha if not baraki warke ba.” Kai ta kad’a masa nufin barata sha ba.
   “Why?” Ya tamabayeta.
    “Habeebi kasan meh?”
  “A’a meh?” yayi maganar ba alaman kwanciyar hankali tattare dashi.
   “I think I’m pregnant gani nake kamar ciki ne dani” Bright blue eyes nasa ya zaro waje “Flower you are what?!” Yayi exclaiming cike da k’in yarda dan yadda jin dad’i ya mamaye masa fuska da zuciya.
    “I’m pregnant again Habeebi kaga ko bareyi insha kowani irin magani ba it may harm our baby.” Tsantsan jin dad’i har a yanzu Anas yakasa believing. Besan a lokacin da ya ajiye tean a gefe ya rungumo Fannah ba.

      “Flower we are soon going to be Daddy and Mammy again, I love you!” Hugging nasa back tayi dukda ba dad’in jikinta takeji ba. “Yes Habeebi” breaking hug d’in yayi tare da riqe hannayenta biyu cikin nasa “Flower dagaske kike you are pregnant?! Omg! Akwai little Fauzi achan? Ko inche akwai HANAN namu a chan?” murmushi tamasa tana gyad’a kai, hot kisses yahau peppering mata a fuska yana sauqowa kan wuyanta tasa hannu da k’yar ta iya ta shuresa “Habeebi please kadaina, kabari banaso.” Cike da mamaki yake kallonta “bakiya son sugar lips naki yau?” Kai ta gyad’a tana turo baki.
     D’an murmushi ya saki another symptom yace a ransa “I know this attitude cikin nema dake amman your last pregnancy ai bakiya hanani kissing naki wannan kuma ko kiss d’inma bakiya so?” Nanma kai ta gyad’a.
   “Humm! Akwai babban aiki Flower ‘cauae I can’t stop kissing you, yanzu kisha black tea d’in seki kwanta zuwa 10 haka se muje asibiti.” Kai kawai ta gyad’a masa shida kansa yabata tean bayan data gama sha ya kwantar da ita. “Habeebi kaifa baraka je office ba?”
    “Mom Hanan bata da lafiya inje office inyi meh? barinje ba zan sanar da Kacallah.” Kai kawai ta gyad’a masa “thank you.”
  “Always Baby Machine” yayi pecking nata a kumatu. Hannu tasa ta goge “Habeebi banaso.” D’an murmushi ya saki sannan ya koma d’ayan side d’in ya kwanta tare da janyota zuwa chest nasa ahaka suka koma bacci.

     10:30AM Anas ya tashi banda Fannah data kasa bacci tun d’azu se juyi take ajikinsa. Jikinta yayi zafi tamkar wuta shi kansa Anas seda ya razana. “Flower” ya kira sunanta cike da tausayi. “Na’am Habeebi” tayi maganan tana kakkarwa. Kodaya gwada d’gata daga cikinsa sake kankamesa tayi not letting go.
     “Flower sannu kinji? D’agani mu shiryaki muje asibiti.”
    “Habeebi mubari anjima ban tsammanin zan iya tashi.”
    “Sorry kinji? Yi hak’uri” da k’yar ya d’agata ya kaita bayi cikin 30 minutes suka shirya zuwa asibiti achan aka duba Fannah aka tabbatar wa lovely couple cikin sati uku ne d’auke da ita. Murna gun Mr and Mrs Fauzi kam baya misantuwa Anas promised to protect his child with his life wannan karan.

   ****
     Tun isowarsu gida Fannah keta tufar da miyau, ga kuma amai a asibiti ma seda tayi dawowansu ma haka, Anas is so worried ko kad’an bara’a had’a laulayin cikinta na farko da wannan ba, bata iya cikakken minti biyu a tsaye se jiri ya kwasheta. Sede bataji k’amshin turare ba in bahaka ba setayi amai na turaren wutan daya mamaye mata gida ma haushinsa takeji. Sallan Azahar ma sauran a zaune ta k’arisa, lunch da Anas yayi musu ma kad’an ta iya tachi shima ta harar.
     Hankalin Anas yayi matuqar tashi zaune yake akan kujera a gefenta, damuwa ne karara a fuskarsa, ayayinda take kan gado lullub’e da bargo se zufa takeyi. Hannunsa dake akan bayanta ya d’aga dan irin zafin da jikin nata yayi sannan ya share mata zufan.
     “Sannu Flower, you’ll be fine in shaa Allah I’m here for you.” Moderate cold water ya nemo da towel yana mammatse mata jikin ko ze d’an sauqar mata da body tempreture cikin ikon Allah kuwa zafin jikin nata ya ragu sede bada jimawa ba ya sake rising. Tausayin Fannah duk yabi ya mamaye Anas sam bayason ganinta ba lafiya haka fa suka kwana cikin wannan zazzab’i ba wanda yayi bacci cikinsu se jinyarta Anas yake gabad’aya hankalinsa yabi ya tashi wani irin pegnancy sickness ne haka?

      _Washegari..._
    Rashin lafiyar yau yama fi na jiya ko meh taci seta harar banda black tea tun Anas na iya jurewa har ya kasa Dr. Mansoor ya kira yazo ya sake duba Fannah har ruwa seda aka sa mata, cikin kwana biyu Fannah tazamo abinda tazama ko k’wararren motsi batta iya yi. Maminta Anas yakira ya sanar da ita halin da ake ciki aiko ba tare da b’ata lokaci ba taje tasamu Afrah dake miqe kan gado se hirarta take sha da dearheart nata.

    “Ke katse wayar” cewar Mami dake tsaye akan Afrah dako noticing shigowar Mami batayi ba. A firgice ta katse wayar, hannunta dafe kan k’irjinta “kai Mami dan Allah yaushe kika shigo? Kinfa bani tsoro.”
    “Bansani ba kinsa soyayya agaba ina zaki sani dama, mschw! Yarki ba lafiya amman ko a colar rigarki.”
    “Fannah?!” Tayi maganam ido a waje.
   “Eh mana yanzu Anas yakirani yake sanar dani. Maza maza tashi muje mu dubata wai har ruwa aka sa mata.”
   “Oh! Allah sarki Ya Fannah kode wani cikin ne Mami?”
   “Mukaje ma sani oya tashi kishirya.”****


*_GWS FLOWER, MOM HANAN😔_*

*Ina me baku hak’uri and inason ku k’ara hak’uri da irregular posting kwana biyu, somethings came up so se harkoki suka min yawa*

*© MIEMIEBEE*

  beeenovels.blogspot.co.ke

Saturday, 24 September 2016

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 86
BY MIEMIEBEE







 
        Take idanun d’an banza da sukaji rauni suka kad’a sukayi wani irin jaaa, hannayensa biyu na akan hannun Mr. Fauzi dake wuyansa yanata k’ok’arin cire hannayen amman ko kad’an yakasa dan bayida k’arfi ko kad’an Anas ya riga ya masa liqis. “An.. An... Anas ple...” Tari yafi k’arfinsa har anan Anas yak’i sakesa as ya d’au alwashin seya kashesa. Wani irin nishi Farouq yasoma ja da k’arfin bala’i.
      “ANAASSSSS!!!!” yajiyo muryan Abuu from far. “Anas don’t kill him ka sakeshi” yayi maganar yana gudu har seda ya iso wajen, k’ok’arin jan Anas daga kan Farouq yake amman ya kasa, “Anas ka sakeshi karka kashesa” seda wasu police guda biyu suka sa hannu sannan aka samu aka d’aga Anas daga kan Farouq.

     “Noo kubarni in kashe bastard d’innan, he dsereves nothing than to die. Let me go! Ku sakeni!” turesu gabad’aya yayi harda Abuu sannan ya sake komawa kan Farouq yakuma shaqure masa wuyan again, tsantsan azaba k’afafun Farouq se dancing suke, sake binsa su Abuu sukayi sunata k’ok’arin d’ago Anas har a yanzu Abuu bega Fannah ba se da ya juya kansa yaganta kwance so lifeless a k’asa gakuma jinin dake ta fitowa daga jikinta har yanzu.
     “Fannah!!” Ya kira sunanta da k’arfi hakan yasa Anas dawo da kallonsa wajen shima. “Anas ka sake Farouq its Fannah you need to focus on Anas matarka!” Da k’yar suka d’aga shi, da gudu yayi kan Fannah ya tattara ta a hannunsa se cikin motarsa a yayinda Abuu ya tsaya da police d’in ana carrying investigations, jakan kud’i da komai da komai duk aka sa cikin motar police daga k’arshe Farouq aka d’aga shima aka kaisa asibiti dan ko bara a iya hukuntasa a haka ba dole se ya samu sauk’i.

      _An hour later..._
       Baba, Mami, Afrah, Aiman, Abuu, Anas, Ummie, Shettima dakuma Amal duk zaune suke a harabar d’akin Fannah dukkaninsu fuskokinsu cike da damuwa, daga masu kuka se wanda suka had’a tagumi babu kaman Anas da ya kasa zama gu d’aya se pacing yake. Abuu ne ya miqe ya nufa inda Anas keta jeka ka kadawo tare da dafe kafad’ansa. “Anas you need to calm down in shaa Allah Fannah zata samu sauk’i muna nan muna mata addu’a taho muje ka zauna.”
     “Abuu I can’t wallahi in wani abu ya sami Fannah ko abinda ke cikinta I must kill Farouq with my own hands.”
    “Kabar magana haka in shaa Allah ma ba abinda ze samu Fannah” ya kwanto da Anas jikinsa yana bubbuga bayansa a sannu sannu yaja Anas suka koma suka zauna. Hannu yasa ya share hawayensa “Abuu mesa za’a kawo wancan son of a b*tch d’in nan asibitin? Mesa basu kaisa wani asibitin ba? Abuu why? Infact bekamata ma akawosa asibiti ba compared to abinda yama Fannah.”
      “Anas muyi focussing akan Fannah yanzu Farouq will follow afterwards.”

   _5 minutes later..._
      Red globe dake a saman k’ofan d’akin da Fannah ke ciki ne ya d’auke in some seconds k’ofan ya bud’u atare duka families d’in sukayi wajen Anas ne a gaba. Cike da tashin hankali yake maganar “D... Dr... Dr how is she? How is my wife?” Ganin yadda Anas ke cikin tashin hankali Dr’n ya dafesa a kafad’a “Mr. Fauzi calm down karka damu your wife’s condition is stable zaka iya shiga ganinta bayan nan duka family zasu iya shiga ganinta also.”
    “Alhamdulillah!  Dr. What of the baby? Shima ya rayu? Were you able to save my baby?” Kai kawai ya iya ya girgiza masa.
     “No Dr dan Allah karkace kun kasa saving babyna please...” ya k’are maganar cikin sautin kuka. “I’m so sorry Mr. Fauzi there is nothing we could do saboda anriga anyi terminating cikin ba yadda za’a iya saving baby’n it was destroyed already tun kafin kuzo nan, maganin Misoprostol da aka bata yagama aiki, maganin nada k’arfi sosai and yana leading to hard and painfull miscarriage we should be thankful ma maganin be b’ata mata hanji ba saboda overdose da aka bata.”
      “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un” kad’ai ke tashi awajen se kuma sautin kukan da yabiyo baya Mami nayi Baba bata hak’uri haka Ummie da Amal ma, Afrah kuwa Shettima ne ke condoling nata.
     “I’m sorry excuse me please” yana kaiwa nan ya fice. Anas kuwa kasa riqesa k’afafun sa sukayi suuul ya sulale k’asa da wuri Abuu ya sake Ummie ya tarosa.
     “Ya kashe min baby Abuu he murdered my child.”
     “Shhh! Anas kayi hak’uri” A fusace ya miqe Abuu da Shettima suka soma kiran sunansa suna binsa, gudu yasa be tsaya ko ina ba se a d’akin Farouq. Banging k’ofar yayi take Ya Khaleel dake zaune gefen Farouq da kayinsa duk bandage hannunsa kuwa handcuff ne had’e da gadon dayake kwance akai. Kamar a kyaftawan ido Anas ya had’e Ya Khaleel da jikin bango tare da shaqure masa wuya Abuu da Shettima ne suka shigo da wuri suna k’ok’arin karb’e Ya Khaleel amman sun kasa dan yadda Anas ya rik’esa.
   
     “Ina kaga abinda shegen d’anka yayi wa Fannah? Kagani koh? And you are the one responsible irresponsible father kawai, wallahi both of you must pay.” da k’yar Ya Khaleel ke maganan “Anas dan Allah ka sakemin wuya dan-” tari ne yafi k’arfinsa da k’yar da taimakon wasu doctors biyu aka k’wata Ya Khaleel se shafa wuyansa daidai inda Anas ya kama yake idanunsa sunyi wuru-wuru.
     Kamar me aljanu Anas yayi kan Farouq da rai ke a hanun Allah ya shaqe masa wuya shima da wuri aka k’wato sa. “Anas get your senses kowa yasan abinda suka maka da zafi amman in ka kashe Farouq yanzu babban matsala ne a garemu, kotu ne zasu hukunta Farouq bamu ba.”
      “Nasani sede kafin nan inason inbawa d’an banza kashi” nan yasake yin kan Farouq sede kafin yamasa wani abun aka taresa. Cikin wani irin sauti Farouq ya soma magana “duk kaine Baba wallahi duk kaine barin bari akaini prison ni kad’ai ba.”
     “Meh kake cewa haka Farouq?” Cewar Ya Khaleel cikin rud’ani yana matsowa kusa da Farouq gudun kar ya tona masa asiri.
     “Aikasan me nake nufi, da tun farko baka fiddoni daga prison d’inba daduk haka be faru ba.”
     “So its true!” Cewar Anas “I knew it dama ai na fad’a maka Abuu wannan” ya nuna Ya Khaleel da yatsa “munafiki ne, zakusan no one messes with Mr. Fauzi or his property, musamman kai Farouq” yanuna sa da yatsa “Shariah Court zankai ka su yanke maka hukuncin kisan kai kamar yadda kayi murdering min baby kaikuma uban banza sena tabbata an yanke maka shekaru da dama a gidan yari anan ne zan iya samun peace of mind.” Wani wawan dariya Farouq ya b’arke da, “ko a babu nasan na rabaka da source of happiness naka.” Daidai Anas zeyi kansa dan kai masa punch su Abuu suka riqesa “lets go Anas mu fita kaje ka duba Fannah kabar nan” da k’yar aka samu aka fiddo shi daga d’akin.

       ****
    A hankali ya bud’e k’ofan d’akin da Fannah ke ciki. Kwance yaganta bisa gado abin tausayi, besan a lokacinda idanunsa suka cike da hawaye ba if only ze iya amsan rashin lafiyan da yayi, ina ma ace ze iya karb’an duk wani pain da takeji right now da yayi. Kujera ya matso dashi kusa da gadon nata tare da zama. Ko hannunta yakasa riqewa dan tausayi, hawaye yake sosai a hankali ya d’aga hannunta ya had’a da nasa tare da pecking hannun. Da alama bacci take dan kuwa bata bud’e ido ba har a yanzu. D’ayan hannunsa yakai kanta yana shafa uban gashin dake kwancd akan goshinta, ya d’au tsawan minti uku yana ahaka sannan a hankali Fannah tasoma bud’e idanunta har ta bud’esu duka.

      “Habeebi” tace cikin dashasshiyar muryarta duk yadda yayi dan stopping hawayen nasa ya kasa kai ya miqa yayi pecking nata a goshi. “Flower welcome back” yayi maganar yana mata murmushi itama murmushin ta miyar masa a wahalance. Data gwada zama kuwa sam takasa dan zafin da takeji daga k’asan mararta, wani irin wahalallen k’ara ta saki da sauri ya sake kwantar da ita. “Not yet Flower don’t move kinji? am here sweetheart” ya sake pecking nata a goshi.
    “Habeebi mesa kake kuka?” Tayi maganar idanunta na cikowa.
     “Babu, am just happy you are back baki tafi kin barni ba, Flower I love you so very much” ya matse hannunta cikin nasa.
     “I love you so much more Habeebi barin tab’a barinka in shaa Allah.”
    “I know Flower nasan baraki barni ba I was just scared.” Yasa hannu ya share mata hawayenta “karkiyi kuka kinji? Its bad for your condition.”

     Kai ta gyad’a mai, “Habeebi what of our baby? Yana nan?” Ta tab’a kan cikin nata tana shafawa a hankali. Shiruu Anas yayi danko besan ta ina ze fara mata bayani ba. “Habeebi mesa kayi shiru? please tell me baby na nanan kokuwa ya tafi?” Nanma shiru kuka ta soma sosai “Habeebi kafad’amin please, tell me my baby is still with me, tell me burin Ya Farouq na rabani da baby na be cika ba please Habeebi.”
    “Shhhh!” Ya aza yatsansa kan lips nata “bar kuka kinji?” Ya share mata hawaye. “Habeebi please tell me” seda yayi kissing forehead nata sannan yace, “Flower ki kwantar da hankalinki kinji? I’m so sorry nayi delaying time, da a lokacin da kika turo min da saqon nazo dana hana aukuwan wannan abu, am sorry please.” Maganansa ya tabbatar mata ta rasa babynta. “Habeebi so the baby is gone?” Ta tambayesa. “Ka fad’a min please.” Cikin wani erin salo ya gyad’a mata kai “baby ya tafi ya barmu Flower, we’ve lost our baby all because of me, I’m sorry.”

       “Habeebi ba laifinka bane laifi na ne, da ban had’iye maganin ba da babynmu be tafi ya barmu ba, ni na kashe babynmu da kaina...” ta rushe da kuka. “Shhh!” yasa hannu yana share mata hawaye “don’t ever talk like that Flower ba laifinki bane, mugodewa Allah you are back, mugodewa Allah Farouq be samu ya kaiki wani wajenba in shaa Allah, Allah ze kawo mana wani baby kinji? Kibar kuka and I promise you Farouq will come nowhere near you again ko fuskarki bare sake kalla ba.” Kai ta gyad’a masa cikin kuka yana share mata hawaye seda ya tabbata tayi shiru ya kirawo su Abuu da su Baba duk suka shigo suka gaishe da Fannah.

   ★★★★
      Tun daga nan aka soma jinyan Fannah, sosai take samun kulawa gun Maminta, Ummie ma kusan a asibitin take yini se dare take tafiya haka Anas ma kullum yana gefen Fannarsa yana bata iya kulawan daze iya, office gabad’aya yabar zuwa yabar Kacallah in charge. Kamar yadda yayi promising kuwa seda ya cika, Shariah court yakai Farouq inda achan aka yanke masa hukuncin rataya na kisan kai dayayi, kafin nan Abuu yace inhar Farouq ze bawa Anas hak’uri yanemi gafararsa za’a janye zancen amman ina Farouq taurin kai wane tsohon k’adangare yace ya gommaci ya mutu daya bawa Anas hak’uri haka a idan mutane aka mai rataya ya wuce lahira. Ya Khaleel kuwa 10 years imprisonment aka basa na bada goyin bayan kisan kai da yayi, daga nan aka rufe chapter’n Farouq da Ya Khaleel.

    *(NOTE: ga masu fad’in kar a hukunta Farouq kusani hukunci ne me tsauri wato kisan kai ya dace dashi saboda yayi aborting baby wanda yake daidai da committing murder, inkuma har wai ba kashesa akayi ba aka yanka masa wasu shekaru a gidan yari toh definately wata rana ze fito kuma ze cigaba da hunting Fannah)*

***** _1:05PM_
    A yau aka sallami Fannah daga asibiti sosai Dr yabasu shawarwari ciki harda hutun ‘yan watanni da Fannah ke nema kafin ta sake d’aukan wani cikin.
      Bayan isowansu gida Fannah taga security men as in k’warraru designed security men guda biyar bakin k’ofar. “Habeebi wannan mutane fah?”
    “Your security men Flower in shaa Allah from now no harm will come to you.”
    “Habeebi ai dama enemy d’in d’aya ne Farouq kuma he is gone yanzu ba me sake tak’ura mana.”
   “Even still Flower I want to keep you safe, ban tunanin zan iya yafe wa kaina in wani abu ya sake samunki, you are a like Flower da ba’ason abinda ze tab’a sa” murmushi ta saki masa, bayan yashigo yayi parking motar sannan ya ciro luggages natan yayi ciki dasu, da kansa ya cirota daga motar yakaita har d’akinsu. “Thank you Habeebi.”
    “Always Flower” yayi maganar yana ciro mata towel nata daga wardrobe “gashi kiyi wanka semuci abinci I cooked your favorite.”
    “Favorite wanne kenan? louisiana?”
    “Yes sweetheart kishiga kiyi wanka ko in miki?” Towel d’in ta fisga daga riqonsa “haka kawai seka haumin wanka?”
    “Barin iya bane?”
   “Eh” ta fad’a tare da murgud’a mai baki. Gabanta yasha tare da d’agata sama chak! be direta ko inaba se cikin jacuzzi sannan yasoma raba ta da kayan jikinta. “A’a Habeebi wallahi zaka iya kayi hak’uri kabari please.”
   “LOL shegen kunyan kinnan bansan ranan barinsa ba, ina jiranki” nan ya manna mata peck a kumatu sannan ya fice. Cikin kwanciyan hankali ta samu tayi wankanta ta fito zaune ta tarar da Anas gefensa wani baggi T shirt ne baby pink in color da hoton birds da flowers akai. “Come here” ya buk’ace ta, ba gardama taje ta zauna gefensa, akan cinyansa ya azata sannan yaciro lotion nata ya soma shafa mata sam bata hanasa ba bayan da yagama takallesa cike da so da k’auna tana murmushi sannan tace, “thank you Habeebi.”
    “Its my job Flower in tayaki sa kayan?”
    “A’a karka damu” a hankali tasa kayan daya cire mata wanda tsayin yamata daidai tsakiyar cinya. “Toh Habeebi ba leggings da zan sa taciki?”
    “Babu I missed your sexy legs so yau inason inta kallonsu.”
    “LOL” ta murmusa “baraka kasheni da kayan dariya ba Habeebi toh muje muci abincin” tayi maganan tana bin jikinta da turare bayan tagama ya rik’o hannunta suka fice daidai gaban d’akin babynsu ta tsaya hakan yasa Anas tambayarta ko lafiya.
   
      “Flower wani abu ne?”
   “Habeebi kawai na tuna da babynmu ne, I miss him/her” ta k’are maganar tare da aza hannunta kan cikin nata. Ganin zata fara masa kuka yayi sauri yayi hugging nata yana bubbuga bayanta. “Is okay Flower Allah ze kawo mana wasu in shaa Allah bar kuka kinji?” Hannayenta ta zagaye a bayansa a hankali tana gyad’a kai “I pray so Habeebi.” Sun d’au minti biyu suna manne da juna sannan Anas ya raba jikinsa da nata “muje muci abincin ko? Se kisha meds naki”
    “Yes amman inason inshiga d’akin first.”
    “A’a Flower banason kiyi kuka kuma nasan definately kika shiga zakiyi.”
   “Please Habeebi” badan yanaso ba yabud’e masu k’ofan suka shiga. Daidai gaban babban gadon ta tsaya tare da sunkuyawa ta ciro d’aya daga cikin cute pink teddy bears d’in tana murmusawa, hawaye kawai tasoma zubarwa, kafin tasa hannu ta share Anas ya riga ya ganta.

    “Flower kinga shiyasa nace banason kishigo.”
    “Habeebi ka tuna lokacin da nace mu sayi blue ones kace a’a pink kafiso saboda jikinka na baka mace zamu haifa? Kasan wani name ya fad’o min alokacin?”
    “No Flower tell me” ya juyo da ita gabansa tare da kwantar da kanta a chest nasa yana shafa bayanta. Kanta ta d’ago tana kallonsa *“HANAN* Habeebi. Kasancewar kanason baby girl nima na soma ji ajikina mace zan haifa and *HANAN* zanso muna kiranta dashi amman not anymore Habeebi...” sekuma ta rushe da kuka. Face nata yayi cupping yana share mata hawayen “kibar kuka kinji sweetheart? We will have another baby and many more kuma aduk lokacinda muka samu baby girl I promise you ke da kanki zakiyi naming nata *HANAN* kinji? Bar kuka.” Kai ta gyad’a a hankali tare da hugging nasa gagam a jikinta.
   
     “I love you Habeebi, I love you so much.”
    “I love you too Flower muje muci abinci.” Teddyn ya amsa ya ajiye sannan ya jata har a yanzu bata bar kukan ba, shida kansa yake bata abincin har ta k’oshi sannan ya b’allo mata meds nata ya bata bayan sun idar da Sallah suka fita waje garden dan shaqatawa kan wani dogon kujera suka zauna ya kwantar da ita ajikinsa me bala’in sata mance da dukkannin damuwanta.
      Hannu yasa cikin ¾ wandonsa yaciro wani heart-shaped pack tare da miqa mata. “Habeebi meh wannan?”
   “Its yours bud’e kiga.” Excitedly ta amsa ta bud’e had’ad’d’en silver bracelet taga aciki meh chain d’an dogo seda toliyar heart a k’arshen wanda yake nan d’an babba. “Wowww its a beauty!” tayi exclaiming.
    “Do you like it?”
    “I love it Habeebi.” Hannu yasa ya ciro daga pack d’in tare da d’ago siririn hannunta ya sa mata chas ya zauna. “Just as I imagined it” ya fad’a tare da kissing hannun nata.

    “Tsaya kiga wani abu.” Toliyan heart d’in ya bud’e mata _“FAHNAS”_ taga rubuce ciki in italics. “Habeebi this is way beautiful” fuskarsa ta riqo tayi pressing masa appreciating kiss daya kashe masa jiki lokaci guda, koda ta gwada sakesa kuwa holding lips natan yayi ya cigaba da kissing nata seda suka ji kansu problem free sannan ya saketa, murmushi ta sakar masa “I love you my sugar lips.” Murmushin shima ya miyar mata “sugar lips?” Yayi maganar da gira d’aya a d’age “ofcourse Habeebi I missed your lips and your body” kafin ya hankara ta sake pressing masa another hot kiss, se kissing juna suke passionately and hungrily tamkar yau suka fara tasting juna****

     _some minutes afterwards..._
         “I love you Flower.” yace da ita yana shafa dogon sumarta. Sake shigewa jikinsa tayi;
    “And I love you too Habeebi like bohot bohot!” ta sakar masa da best smile nata me mugun amsar ta dakuma birkita wa Anas lisafi.

*© MIEMIEBEE*

  beeenovels.blogspot.co.ke

Friday, 23 September 2016

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 85
BY MIEMIEBEE





       Asuban fari ta tashi tayi Sallah da nafilfilunta bata damu da tada Farouq ba danko tasan bayi zeyi ba, bayan ta kammala addu’o’inta takoma kan kujera ta zauna tata Azhkar har garin Allah ya waye. K’arfe 8:30AM ta shiga bayi tayi wanka wani highwaist skirt da karinat blue tasa sannan ta lullub’e jikinta da mayafi babba se 9:30AM Farouq ya tashi ”good morning Ya Farouq” ta gaidashi.
     “Morning wifey how was your night?”
    “Alhamdulillah I hope yours too, na had’a maka ruwan wanka kashiga kayi semu karya” ba musu ya miqe yashiga anan ta ciro masa wani sky blue jampa ta ajiye kan gadon. Wajen bayin ta nufa ta kasa kunnenta jin bulbulan ruwa ta tabbata wanka yake dan haka ta nufa wajen side drawer’n kansa, kwalin baby nokia sabi tagani har guda biyar wanda taga alamun kamar an bud’e ta k’arisa bud’ewa tacire se juya baya take gudun kar Farouq yafito. Abin takaici taga ba sim ciki ta duba sauran drawers d’inma babu. “Mschww! Ya Salam!” Cikin wardrobe nasa ta nufa tasoma neman sim card one by one take bin kayakin nasa achan counter’n k’arshe taga sim packs kusan goma hamdala ta saki daidai tasa hannu zata zari d’aya kenan Farouq ya murd’a handle na k’ofan, a gigice ta miyar da su ciki. Da towel d’aure a k’ugunsa ya doso inda take “me kikeyi wifey?” Ya tambayeta ba wasa a fuskarsa. B’arin baki ta soma ganin bata gama miyar da kayan nasa yadda ya bari ba.

     “Uhmm... Ermm. Ya Farouq har ka fito?”
    “Eh meh kikemin cikin kaya?”
   “Bbb.. Babu kaga kaya nake nema maka na cire wancan” tayi nuni da jampan dake kan gadon “sekuma bemin ba nafison kasa farin jampa.”
    “Hakane wifey?”
    “Eh Ya Farouq fari zefi maka kyau.” Dad’i sosai sokon yaji “toh ai ga inda nake ajiye fararen kayaki na” nan ta matsa masa ya zaro wani farin half jampa “good kayi ka shirya muje mu karya am hungry.”
    “Okay wifey” cikin d’an k’ank’anin lokaci ya shirya suka fice zuwa dining room achan aka had’a musu had’ad’d’en breakfast suna hira suna chi Fannah na iya k’ok’arinta dan sakewa da Farouq tanason yayi trusting nata sosai.

           *ANAS* _10:36AM_
     Zaune yake a d’akinsa ya had’a uwa uba tagumi gabad’aya ya fita daga hayyacinsa ba aikinsa banda tunanin Fannah rabuwansa da bacci tun da Farouq ya d’auke Fannah.
      “Anas!” Cewar Abuu yana buga k’ofar d’akinsa. “Kafito mu karya kaji already police d’in suna jiran mu.” Shiruuu... “Anas in shigo?” Nanma shiruu dan haka ya sa kai kawai. Hannu ya dafe a kafad’ar d’ansa. “Anas take it easy wallahi da abinda kakeyi zaka kamu da ciwon zuciya zamu sameta in shaa Allah. Ba kanada bank details nasa ba? Nayi magana da bank d’in za’ayi freezing account nasa.” Cike da tashin hankali ya juyo yana girgiza wa Abuu kai.

     “A’a Abuu please kar muyi haka wallahi zamu sake worsening situation d’in karmuyi dan Allah banason yayi ma Fannah wani abu.”
    “Anas wani erin magana kake?”
   “Abuu please dan Allah kar ayi freezing account nasa ni nasan Farouq.”
     “Shikenan zan musu magana abari kamar yadda kace yanzu tashi muje mu karya semu fita.”
    “Abuu fitan nan baida amfani we can’t ever find her hanyan sauk’i shine mu kama Ya Khaleel. yaji an kama Babansa a hannu ze sake min Fannah.”
    “Anas hakan bame yuwu wa bane we don’t have any evidence da ze nuna Ya Khaleel na aiki da d’ansa.”
    “Akwai Baba muje mu duba record na Farouq wa yayi bailing nasa am sure Ya Khaleel ne.”
     “Toh naji yanzu de katashi muje mu karya” Anas ya bud’e baki zeyi magana Abuu ya dakatar dashi “a’a karka cemin bakajin yunwa tashi muje” shida kansa ya miqar da Anas suka nufa dining.

★★★★ *FANNAH*
    _1:15PM..._
     Zaune Fannah da Farouq suke akan dining table daidai zasu fara chin lunch kenan aka k’wank’wasa k’ofa “MB get the door” cewar Farouq kamar yadda ya buk’ata haka MB yayi.
    “Wayene?” Farouq ya tambayui MB. Kafin MB ya amsa yaron yayi magana;
     “Bad boy ne ya turoni wai abasa kud’insa.”
     “Ba yayi tafiya?” Yayi maganar yana barin kan kujerarsa dad’i sosai Fannah taji dataga be d’aga wayar saba, yanzu zata iya texting Anas. Har ya kusan bakin k’ofar sekuma ya dawo ya d’au wayar batasan lokacinda tayi tsaki a fili ba.
    “Wifey lafiya?” ya tambayeta.
   “Uhmm lafiya, banji dad’in d’aga kan da akayi bane daidai zamu fara chin abinci.”
    “Karki damu I will be right back” kai kawai ta gyad’a masa ya fice ya rage daga ita se MB a d’akin, abincinta ta nutsu taci se tunanin ya za’ayi tayi texting Anas location d’inta take. Abu kamar wasa fa Farouq be dawo d’akinba.
 
      _32 minutes later..._
     K’ofan akayi banging dalilin firgitan da Fannah tayi seda ta yasar da apple dake hannunta tare da juyowa a kid’ime Farouq tagani idanunsa suna wani juyawa kallo d’aya tayi masa tagano abige yake. MB ne ya taimaka ya k’ariso dashi kan kujera ya zaunar dashi.
    “Omg! Farouq meya sameka haka?”
    “He had too much to drink” cewar MB.
    “Okay excuse us zaka iya fita I will take care of him.” Ba musu MB yayi excusing nasu, anitse ta baro kujerarta ta nufa wajensa. “Ya Farouq meya faru? Me kasha haka?”
     “Karki damu wifey wannan shegen bad boy d’inne yakeson rusa min plans ya dawo kuma yana buqatan kud’insa”.
    “Toh ka basa mana.”
    “Wifey kikace miliyan shabiyar kikeso in na basa kud’insa goma ne ze rage.”
   “Semu sake tambayan Anas ai karka damu kasan me nakeso dakai? Ka huta yanzu kaji?” Kai ya gyad’a mata. Gabansa tayi clearing ta kwantar da kansa a hankali idanunsa suka soma kafewa har bacci yayi gaba dashi. Side pockets na jampan sa ta dudduba bata ga wayarsa ciki ba data leqa setagansa cikin aljihun chest na rigan tunanin ya zatayi ta ciro take seta kai hannunta se tsoro ya hanata danko tana da tabbacin baccin sa beyi nisa ba at any moment ze iya tashi yakamata red handed. Zama tayi gefensa tana tunani chan ta kira sunansa “Ya Farouq!” Shiru ba amsa “Ya Farouq” tad’an buga table d’in.
   “Urghmmm” yayi groaning cikin bacci.
    “Ya Farouq ka tashi muje d’aki ka kwanta kaji? Nan is uncomfortable.”
   “Bari karki damu.”
   “Dole in damu mana Ya Farouq d’ina na kwance a tak’ure tashi muje d’aki kaji?” A kasalance ya miqe dan yadda ya bugu ko bud’e idanunsa bai iyawa dan bata da wani hali ne kawai tasa hannu ta taresa ganin yakusa fad’i a k’asa. “Astaghfirullah” ta rigayi har seda ta jibgesa kan gadon d’akinsu. Kamar mamaci ya soma sabon bacci wajen.

     Bad to worse tace a ranta “yanzu ya zanyi inciro wayar yadda yayi ruf da cikin nan?” dabara ce ta fad’o mata. “Ya Farouq ka cire kayan mana zaka fi jin dad’in baccin...” Shiruuu
    “Kaji Ya Farouq tashi ka cire kayan se ka kwanta” da k’yar ya tashi ya cire kayan ya wurga mata hamdala ta saki. “Rataya min akan drawer” yayi maganan a bige. Yadda ya buk’aceta tayi a hankali ta juyo ta kallesa ganin idanunsa a rufe tasoma lalimo aljihun nasa dan ciro wayar har takai kai sauran cirewa kawaibFarouq ya miqe, da wuri tabar wajen ta k’ariso wajen gadon “mene ne Ya Farouq?” Bakinsa kawai ya toshe agurguje ya ruga bayi amai ya riga kwararowa hakan yabata daman ciro wayar, b’ari duk wani sassan jikinta ke har tasamu tayi texting Anas kamar haka;

     _Anas Habeebi its me Fannah, Mobil filling station Yobe by pass come ASAP and save me please PS don’t call._
     Bayan tayi sending tayi deleting a take, kafin tace zata miyar da wayan Ya Farouq ya fito daga bayin idanunsa basu sauk’a ako ina ba se Fannah dake riqe da wayansa seda ya k’ariso gabanta ya tambayeta “meh kike min da waya?” Gabaki d’aya ta tsure kasa koda furta ‘A’ tayi se rawa jikinta ke.
    “Magana nake miki meh kikemin da waya?”
   “Bbb... Babbu..” Hannu yasa ya fisge wayar, call logs ya shiga ya duba sannan messages nanma bega wani abu ba sede jikinsa na basa ba lafiya ba.
     “Baki amsani ba nace me kikemin da waya?”
    “Bb... Babu Ya Farouq wayar ne ya fad’i garin rataya maka kayan naka shine na d’ago.” Tayi magana cikin murya me rawa.
      “K’arya kike Fannah meh kika min da waya?”
   “Allah babu Ya Farouq ka duba kaga.”
    “Fannah kinsan in na gano wasamin da hankali kike zan mugun sab’a miki.”
    “Ya Farouq ya kake magana haka ne? Kaima kasan wannan ba trick bane inasonka Ya Farouq.”
     “Barin ga ko dagaske ne kinaso na.” GPS radio yayi turning off sannan ya kira Anas***

         *ANAS*
       Yana cikin motarsa acikin gari yanzu barinsa police station an yarda da yamma za’a je a duba record na Farouq. Driving yake a hankali koda yaji wayansa yayi k’aran shigowan new message a while ago be damu yaduba ba acewarsa seya isa gida ya duban. Ganin kiransa kuma ake yanzu ya d’ago wayar ya duba sabon layi yagani kafin ya nemi waje yayi parking ya d’aga wayar ya tsinke. Daidai zeyi calling back kenan yace bari ya duba saqon tukunah. K’wararo idanunsa waje yayi bayan daya karanta. “Flower! Its Flower!” Har ya danna numban ze kira sekuma yatuna tace kar ya kirata take yayi mastering numban kar incase zata kirasa. Yakai kan numban Abuu kenan yaga exact numban da Fannah ta turo masa message dashi na kira, ba tare da b’ata lokaci ba ya d’aga “hello Flower??”
      Wani shu’umin murmushi Farouq ya saki yana kallon Fannah “so its true you called him with my number koh?” kafin ta hankara ya shaqure mata wuya hannunsa tahau bugi “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri ka sak.” Kasa k’arisa maganan tayi dan yadda ya shaqe mata wuya.
      “Hello Farouq?! Me kake mata please ka saketa. Flower kina jina?”
    “Anas Habeebi please help me ze kasheni.” tayi maganar da k’yar.
    “Farouq me kake mata? Ka saketa please dan Allah don’t hurt her.”
   “Kasheta zanyi ni zata raina ma wayo kasani kayi ban kwana da matarka dakuma d’anka” yana kaiwa nan ya katse wayar. Koda Anas ya sake gwada kira kuwa bai shiga Abuu ya kira da sauri ya fad’a masa location da Fannah ke, shima Abuu ba tare da b’ata lokaci ba ya sanar da police koda ya cewa Anas ya jira sutafi duka a tare k’i Anas yayi he can’t wait to save his Flower.
     ****
       “Kiransa kikayi ko meh? Munafukar Allah kawai ni zaki raina ma wayo kiyi tricking d’ina? Me kika yi da wayan nache?”
     “Aahh..hahhh” ta soma wani erin nishi. “Yya.. Farouq dan-” sama sama nishinta ya soma ganin zata mutu masa ya saketa tari ta hau yi idanunta sun kad’a sunyi jazir suna tsiyayar hawaye. “Wait what do you mean da kikace Anas yazo ya taimakeki, texting masa location d’innan kikayi? Magana nake miki!” Nanma shiru se tari take tayi. “Kin fad’a masa location da muke koh? Hohoho! Smart girl zakiyi bayani.” Akwati ya ciro yasoma had’a musu kayakinsu har a yanxu Fannah bata yi recovering ba daga shaqentan da Farouq yayi bayan yagama had’a musu kayakin ya tattara abubuwan daze buk’ata “tashi mutafi.”

       “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri karka kaini wani wajen.”
    “Maganan banza ina ni zaki raina ma wayo? Semuga ya Anas nakin ze cetoh ki” bejira ta sake cewa wani abu b ya fisgota sannan ya soma janta se rok’onsa take amman ko a kwalan rigarsa. Daidai wajen staircase ta durk’ushe ta kankame k‘arafun “meh haka?! Ki tashi mutafi.”
      “Wallahi barin bika ba mugu kawai ka sakeni.”
   “Ina wasa dake ne?! Nace ki tashi!” sam tak’i motsawa ganin ba mahalicci se Allah ya sauk’a ya ajiye jakan nasu  sannan ya sake haurowa nan suka shiga dambe sam tak’i sake k’arafun gagam ta rik’e ita barata bisa ba seda yayi dagaske sannan ya samu ya sauk’o da ita se fad’anshi take. Wani syrup ya ciro daga cikin jakar. “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri karka sani shan wannan abun, na tuba dan Allah kayi hak’uri...” Ko sauraranta beyi ba yaja hannunta ya danne ta a k’asa tare da had’a hannayenta biyu gu  d’aya, kwalban yakai mata baki sede sam tak’i bud’ewa “ki bud’e nace!”

      Se hawaye take abin tausayi tana girgiza masa kai, “nace ki bud’e” goshi ya gara musu wanda sanadin haka ta  bud’e bakinta tare da sakar dawani irin azabartacciyar k’ara, hakan yabasa daman sa mata kwalban a baki seda ya juye mata tas sannan Ya cire, tarawa tayi a bakin nata tak’i had’iyewa “ki had’iye nace!” ganin tak’i had’iyewan kuma tana cinye masa lokaci ya matse mata hanci tun tana iya jurewa har numfashinta ya soma yankewa idanunta sunkad’a sunyi wani irin jaa bayan riqe numfashinta data tayi daga k’arshe kawai ta had’iye ganin zata iya mutuwa ga mugun yak’i sake mata hanci kuma.

      Daidai nan aka hankad’o entrance door d’in da wani irin force da seda ya k’ofar ya fad’i a k’asa da hanzari Farouq da Fannah ke kwance bisa cinyansa idanunta suna wani kakkafewa ya miyar da kallonsa bakin k’ofar. Fannah kuwa da k’yar idanunta suka iya comprehending mutumin dake tsaye bakin k’ofar. “Anas! Habeebi” kad’ai bakinta ya iya furtawa. “FANNAAAHHH!!!” Ya kira sunanta cikin tattausar murya me uban sauti. Sandarewa Farouq yayi wajen yarasa taya Anas ya samu ya shigo bayan uban securities daya zuba awaje be k’arisa wannan nazari ba yaji an cukumo mai collar riga. Kafin ya hankara Anas yakai masa wani erin mumunar punch da hannunsa me zobuna uku, take hancin Farouq ya fashe ya soma zuban jini. Wani punch d’in ya sake kai masa aciki tare da miqar dashi ko ta kan Fannah beyi ba, nishi yake tamkar zaki. Dogayen k‘afafunsa ya d’aga d’aya ya tunkud’e Farouq dashi seda yayi tumbling a k’asa Anas be barsa ba ba har yanzu. Sleeves nasa ya sake rolling yabi kan Farouq tareda hayewa kansa yasoma kai masa punches tako ina afuska ko wani spot a fuskan Farouq zuban jini yake har yanzu Anas be barsa ba seda yaji muryar Fannah tana kiransa. “Anassss!!!” Da ihu, alokaci guda ya bar abinda yake tare da kewayo wa. “Anas please help me, wayyo Allah !!” ta k’are maganan hannunta dafe kan cikinta se juyi take a k’asan ga wani erin azaban da ita kad’ai tasan yadda takeji acikinta. Hawaye take me tsuma zuciya. A gurguje Anas yayi kanta tare da aza kanta kan cinyansa. Hannunsu ya had’e “shhh! Flower am here, your Habeebi is here kinji stop crying.” A kasalance ta d’ago idanunta ta azasu kan  fuskarsa daba abinda ke kwance akai banda tsantsan damuwa da tashin hankali a raunane. “Habeebi I’m sorry, I‘m sorry plea-” bata k’are maganar ba ta sakar dawai irin wahalallen k’ara;
     “Arghhh! wayyyooo Alllahh cikina Anas help me please zan mutu wayyyooo Allah!!” ta k’are maganar hannunta dafe kan cikinta.
      “Flower me Farouq ya miki? Meya miki?” Yayi maganar cike da tashin hankali.

    Da k’yar ta iya nuna masa kwalban da yatsanta, a hanzarce ya miqa hannu ya d’aga “Nooo!! Nooo!! Nooo!! please” abinda yake ta furtawa kenan bayan ya karance jikin kwalban, wani irin k’ara Fannah ta sake sakarwa tuni ya jefar da kwalban tare da d’aga skirt nata jini yaga yana bin k’afafunta unstoppingly.
      “Noo!! please NOOO! Fannah please noo Flower.”
    “Anas I’m sorry ple-” bata samu daman k’arisa maganan ba idanunta suka ruhu ta bar motsi kwata kwata. “Flower I can’t lose you please wake up dan Allah kitashi please Flower I can’t leave without you, don’t leave me please” jinin dake bin k’afafunta se dad’a yawa yake. Rungumota yayi a jikinsa gagam tare da had’a musu goshi se kuka yake yana sunbatu. Daga bisani ya mik’e a fusace ya nufi kan Farouq da har ayanzu ya kasa koda motsa k‘afa dan yadda ya bugu kansa Anas ya haye tare da shaqure masa wuya da k’arfin da Allah ya basa, zuciyansa se tafasa yake yana saqa masa ya kashe Farouq kar yayi sparing nasa. “You must die you filthy son of b*tch you are going straight to hell...”



*© MIEMIEBEE*

beeenovels.blogspot.co.ke