Saturday, 21 July 2018

RANA D'AYA!

BY MIEMIEBEE
PAGE 22


    Har cikin ransa yaji dad'in kalamunta dukda cewan ya san ta fad'i komai ne don kawai yaji dad'i bawai don har cikin zuciyanta tana nufin hakan ba, yasani tausayinsa kawai takeji bawai sonsa take ba.
  "Yaya why are you not saying anything?" Ta tambayesa a sanadin shirun da yayi. "Dan Allah kayi hak'uri."

  "It's okay Lily you should get going thank you."

  "Yaya fushi kake dani har yanzu?"

  "Sanin kanki ne komin mey kikayi mun bazan ta6a iya yin fushi dake ba Lily."

  "Shine ko kallona bazaka juya kayi kace ka hak'ura ba?"

  "Will it change anything?"

"Please Yaya kayi hak'uri Wallahi bazan iya jure fushinka ba."

  "Toh na hak'ura" ya fad'a had'e da juyowa yana kallonta kaman yadda ta buk'ata. "Bar kukan haka toh" hannu tasa ta shiga share hawayenta.

  "Thank you so very much, barin koma toh Allah k'ara sauk'i."

  "Ameen thanks too bari inyi ma Sultan magana ya kaiki gida."

  "A'a no need daga school nake zan koma I still have one lecture to attend" tayi maganan tana duban agogon hannunta.

  "Are you sure?"

  "Yes Yaya" ta amsa had'e da sakar masa k'aramin murmushi.
 
  "Alright you take care" a waje ta tarar da Sultan tayi masa sallama sannan ta fice.
  Bada dad'ewa ba Nazeefah ta kawowa Afzal abincin, bayan ta basa ya ci ya buk'aci Dr'n da ya sallamesa.

****
   Ta fannin Abdul kam k'aramin hauka ne kawai beyi ba, yau ko fita office ya kasa, banda tunanin Amal ba abinda yakeyi, gabad'aya ya rasa mey ke masa dad'i yau kwana nawa amma a rasa wanda zeje ya duba masa lafiyar Amal? itama Amal d'in kwana nawa yau amma bazata nemesa ba? Anya kuwa lafiya? Tunani de ba wanda beyi ba. Toh kode su Mami sunyi mata miji ne a gida suka hanata yin waya dashi suka amshe mata wayan ma gabad'aya? But ai bazasu ci amanar sa haka ba bayan seda ya tura su Baba da su sanar dasu shi yayi kamu then what could be the problem? Kwana yayi yana nazari, washegari da yamma ya kira Maamah. Har tsoron picking call d'in take amman haka ta d'aga don ba yadda ta iya.
   
   "Maamah what is going on?"

  "Game da mey Ya Abdul?" Ta tambayesa tamkar bata fahimci inda ya dosa ba.

  "Please tell me meke faruwa meyasa line na Amal baya shiga?"

  "Ya Abdul ban san-"

  "Maamah we both know you're lying sarai kinsan meyasa, dan Allah nace please tell me it's been over a week bana samunta har Mama nasa aje aji mun ya take amma shiru. I can smell it something is not alright."

  "Ya Abdul-"

  "Ki fad'a mun kinji?" Ya katse ta "Idan ma abu ne yasamu Amal d'in kuke 6oye mun just tell me I promise bazanyi reacting ba."

  "Ya Abdul ba abinda ya samu Amal, lafiyarta k'alau."

  "Then meya faru? Meyasa bata picking call d'ina?"

  "Ya Abdul I'm sorry."

  "Fad'a mun kinji? Kar kiji komai."

  "Kayi hak'uri amma bazan iya ba."

  "Meyasa?"

  "Na d'au alk'awarin komin yaya baza aji mutuwan sarki daga bakina ba, kayi hak'uri."

   "Aure Amal zatayi ko?" Ya tambayeta a hankali daga yadda yake magana mutum zesan zuciyarsa a karye take, sosai ta sha mamakin yadda ya gano hakan ba tare da wani ya sanar da shi ba.

  "Ya Abd-"

  "Aure zatayi ko?" Yayi saurin katse ta "Just answer me."

 "Ya Abdul I'm sorry."

  "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" taji ya furta. "Meyasa baki fad'a mun ba Maamah?"

  "Nima labarin be dad'e da iske ni ba."

  "Ban yarda ba Maamah, dalilin da yasa Baba suka turoni nan dan Amal zatayi aure ne ko?"

  "Ya Abd-"

   "Just tell me yes or no kar kiyi mun k'arya" ya buk'aceta.

  "Yes" ta furta a hankali "Amm-" be bata daman yin magana ba ya katse wayan. Nan take ta shiga kiransa sede tuni ya kashe wayan gabad'aya. Wajen Mama ta ruga aguje tana mata kuka "Mama Ya Abdul ya gano gaskiyan al'amarin he knows everything."

  "Kaman ya? Ban fahimceki ba." Nan ta kwashe duk yadda sukayi da Abdul ta zuba mata. "Jeki ki d'auko mun waya a d'aki yi sauri." Nan da nan taje ta d'auko ta kawo mata, layin Abdul ta shiga kira duka biyu amma switched off kukeji. Tirk'ashi idan hankalinta yayi dubu be tashi ba. Baba ta kira a office take sanar dashi halin da ake ciki, dama ya sani komin jimawa wataran Abdul ze gano gaskiya don haka ya buk'aceta da ta kwantar da hankalinta zeyi ma abokinsa dake chan wanda ya samowa Abdul aikin da yaje ya dubasa. Har anan hankalin Mama be kwanta ba, Maamah kam se kuka takeyi.

  Tunda ya kashe wayan nasa ya shiga aikin kuka, kuka yake sosai kaman d'an yaro yayinda zuviyarsa keyi masa k'ona, ji yayi komi ya fita masa a rai, ina ma ba a k'addaro masa da wannan rana ba. Shikenan shi kuma tasa jarabawar kenan? Akan 'yan matan da yakeso? Until when ze samu sanyin idanunsa tunda gashi Amal da yake sa ran kasancewa da ita har k'arshen rayuwansa ma ta tafi ta barsa. Wai shin meyasa be gane gaskiyan al'amarin bama tun a farko? Ai da abun tambaya yadda duk cikin fad'in gun aikin nasu aka d'aukesa k'walli d'aya tal aka basa appointment letter'n. Da akwai abin tambaya game da yadda su Baba da ita kanta Amal d'in suka nace cewan lalle-lalle seya kar6i aikin. Meyasa be gane cewa aure Amal zatayi ba tun daga kan lokacin da ta soma yi masa kuka a waya haka kawai ba dalili har izuwa ranan daya tafi, kukan da ta keyi yafi k'arfin ace wai kawai na rabuwa da masoyi ne, ashe na zafin rabuwa dashi gabad'aya ne. Meyasa? Meyasa bata sanar da shi ba? Meyasa su Baba suka yita zolayarsa suka k'i sanar da shi gaskiyan al'amarin? Mey yayi zafi da har se sun turosa Canada? Gabad'aya he felt used and abandoned. Ganin kukan baze amfanar dashi da komai ba ya mik'e a raunane ya shige bayi inda ya bud'e shower akansa ruwan na zuba wala Allah hakan zey sanya sa mancewa da d'umbin matsalolinsa.

   Ranan Abdul beyi bacci ba, se tunanin yadda Amal taci amanansa kawai yake. Saidai kuma da ya nutsu ya zauna yayi tunani yaga haka kawai fa Amal bazata rabu da shi ba, ba tare da wata k'wak'k'warar dalili ba, yana da tabbacin cewa ba a son ranta ta aikata koma mey tayi ba, ze iya rantsewa akan irin soyayyan da Amal takeyi masa, shi kansa yasan Amal na sonsa so kuma na tsakani da Allah ba yadda za'ayi ta amince zata auri wani ba don wani k'wak'k'waran dalili ba, what could be the reason? He need answers.

*****
   Kaman yadda ta saba yi idan ta tashi kullum da safe hakan yau ma tayi, hotunan Abdul tasa a gaba tana kalla tana kuka, duk yadda takeson mancewa da shi abun ya gagara. Ba abinda takeso sama da ta saurari muryansa, she misses him so much, she wants to know how he's doing, what he's doing and all. Bata tsammanin zata iya cigaba da rayuwa ba shi badan tanaso ba ta share hawayenta ta mik'e. Kitchen ta zarce inda ta had'awa Afzal kunun aya da aldeb ta d'ura cikin silver flasks da ta saya da sunansa sannan ta wuce bayi tayi wanka ta shirya zuwa school. A office na Sultan ta tsaya ta mik'a masa sak'on Afzal sannan ta basa nasa shima take rok'ansa idan ya samu dama ya kaiwa Afzal kuma tana gaishe sa da jiki.
 
  Bayan Sultan ya idar da sallan Azahar ya zarce gidan Afzal inda ya tarar da Afzal d'in kad'ai a gida kasancewar Nazeefah ta tafi school. Bayan sun gaisa ya mik'a masa sak'on Amal. Sosai Afzal yaji dad'i baze iya tuna when last yayi tasting hand made smoothies na ta ba, he really misses it alot. A fridge ya ajiye, se bayan La'asr Sultan ya tafi. Da Maghrib bayan Nazeefah ta idar da sallah ta wuce dining space dan d'auko ruwa kawai taci karo da flasks har biyu cikin fridge d'in wanda take da tabbacin ba nata bane. Sa idon da zatayi ta tabbatar da cewa ba yau ta soma sa flasks d'in a ido ba sanda take amarya sau dayawa Afzal yakan taho da flasks d'in har akwai lokacinda ta gwada d'aukan d'aya zata sha ya k'wace yake cewa ai wacce ta basa batace ta bata ba. Toh fa wata sabuwa! Shin flasks d'in waye ne wannan d'in? Kode na budurwarsan ce? Amma kuma ai kwana biyu bata jinsa yana waya har yaushe yayi wata sabuwa da zata fara kawo masa drinks? But she's sure wannan flasks d'in sune na budurwarsa ta da yau ya zatayi? Ina zata sa kanta? A rayuwa in akwai abinda ta tsana shine taga ko kuwa taji Afzal na kula wata. Zata iya jure komai amma banda kishiya, flasks d'in ta zaro ta ajiye akan table tana jiran dawowan Afzal. Be dad'e ba se gashi ya shigo, zuciyarta ta danne tayi mai sannu da zuwa sosai gabansa ya fad'i ganin flasks d'in da yayi a gabanta shin wai meya hanasa sanyasu cikin fridge na d'akinsa yasa key? Tashin hankali. Takawa yayi a nitse ya k'arisa dining table d'in "Zaki sha ne?" Ya tambayeta. Kai zalla ta kad'a.

  "Then meyasa kika fito dasu? Naga acikin fridge d'in zasu fi yin sanyi."

  "Afzal?" Ta kirasa "Flasks na waye ne wannan d'in?"

  "Kaman ya na waye kuma?" Mik'ewa tayi ta tsaya "Ba wannan ne ba karo na farko da nake tarar da flasks d'innan a gidan nan am very sure na mutum d'aya ne tambayata itace ta wace ce?"

  "Nazeefah-"

  "Ta budurwarka ce ko?" Tayi saurin katse sa.

  "Budurwa kuma Nazeefah?"

"Tun da nake amarya ina ganin flask d'innan tana kawo maka smoothies aciki yanzu ma taji batun rashin lafiyanka ne ta kawo maka kenan ko?"

  "Wani irin magana kike haka Nazeefah? Dan kinga flask shikenan seki ce na wata?"

  "Toh na waye ne?"

 "Na Umman Sultan ne" ya had'e mata k'arya nan take.

  "Umman Sultan?"

  "Baki yarda bane? Ki tambayi Danladi d'azu Sultan ya kawo mun."

    "Taya tasan baka da lafiya bayan kace kar a sanar da kowa?"

  "Well Sultan told her before I could stop him."

  "Kana nufin tun fari itake kawo maka smoothies d'innan?"

  "Nazeefah zan miki k'arya ne? Come here" hannunta ya kama ya jata jikinsa had'e da rik'e k'aramin k'wank'wasonta.

  "Ba k'arya kake mun ba ko?"

  "Haba in miki k'arya." Kanta ta kwantar bisa k'irjinsa had'e da kewaye hannayenta a bayansa "I love you so much Afzal, ban tunanin zan iya sharing d'inka da wata, ina kishinka sosai please promise me bakada wata budurwar a waje." A hankali ya d'agota had'e da rik'o fuskanta cikin hannayensa "What does it matter koda ina da wata budurwar a waje Nazeefah? You'll always remain the Queen ke bakisan kece uwar gida ba?"

   "Yanzu kana nufin akwai wata a waje kenan?"

  "Ni bance ba" yayi saurin cewa.

  "Afzal ba k'arya kake mun bako?" Matso da fuskansa yayi kusa da nata had'e da sauk'ar mata da gentle kiss a goshi "Stop bothering yourself okay? In kawo mana cup? Ko bakison ta6a aldeb na Umman Sultan?"

  "Bari in kawo mana" a nitse ya saketa ta zarce kitchen ta d'auko musu cups d'in. Har suka gama cin abincin Afzal se tunanin kalaman Nazeefah yake, ya santa ya san d'anyen aikinta ta ina ze soma sanar da ita batun Amal yanzu after making it clear ita akan kishiya zata iya aikata komai. Hmm!

***
   Kwana biyu iyayen Abdul suka jera suna nemansa amma wayoyinsa duk switched off kaman yasan Baba na iya turo abokinsa yazo ya dubasa ya tattara kayakinsa ya gudu hotel inda yake kwana. Ko fita office baya yi haka ze yini a d'aki yana tunanin Amal tamkar wani zararre ya koma. Se a daren na uku ne ya kunna wayansan, yana kunnawa kiran Mama na shiga kaman wanda baze d'auka ba yayi answering.

   "Abdul! Alhj Abdul ya d'au wayan" ta sanar da Baba dake gefenta. "Abdul Baba na dan Allah kayi hak'uri."

  "Mik'o mun wayan" cewan Baba sede tak'i ita se taji muryan Abdul tukuna.

  "Abdul yi hak'uri kayi mun magana, Mama is sorry."

  "Mama why?" Abinda ya fara tambayarta kenan. Matuk'a ya bata tausayi har takeji da ma tun farko ta sanar da shi gaskiyan kawai da war haka zuciyarsa ma ta warke.

  "Abdul kayi hak'uri ka sani we only want the best for you."

  "Best for me Mama? A ganinku 6oyemun gaskiyan al'amari da turoni Canada shine abinda yadace?"

  "Abdul kayi hak'uri daga ni har mahaifinka ba wanda yake da zuciyan fad'a maka wannan abu, bamu san ta ina zamu fara sanar da kai ba amma kayi hak'uri."

   "Yaushe ne auran nata?"

  "Muma bamu sani ba Abdul but anytime soon."

  "Wa zata aura?"

  "Abdul ba amfani."

  "Just tell me."

  "Afzal."

  "Afzal??" Ya nanata da mamaki "Afzal??" Ya sake tambaya.

  "Eh shi."

  "How???"

  "Abdul its a long story amma inason ka sani Amal masoyiyarka ce ta hak'ik'a, kuma ko da wasa kar kawo a ranka cewa taci amanar ka."

  "What happened Mama?" Gyaran murya tayi sannan ta kwashe labarin duk abinda ya faru ta basa bata bar komai ba. Gabad'aya se ya dena tausayawa kansa ya shiga tausayawa Amal. Tabbas Amal ta cika masoyiyarsa ta hak'ik'a kaman yadda Mama ta fad'a. Inde haka ne toh Allah sa hakan shi yafi alkhairi a garesu duka, ya kuma bawa Afzal ikon rik'e ta da amana sede bai tsammanin ze iya daina son Amal. Sam beso hakan ya faru ba, yaso ace shine mijin da ze kula da Amal, mijin da ze zauna da ita har ila k'arshen rayuwarta, yaso ace shine mijin da zata haifan masa yara rabi masu kama da shi rabi masu kama da ita sede kana naka Allah na nasa.

  "Ga Babanka nason yi maka magana."

  "Toh ki bashi."

  "Baba na?" Baba ya kirasa.

  "Na'am Baba ina yini?"

  "Ya kake?"

  "Lafiya" ya amsa sama-sama.
   Hak'uri sosai Baba ya shiga basa amma ya nuna masa shi fa ba komai, abinda Allah ya riga ya k'addara bashida makawa and everything happens for a reason he's sure Allah nada dalilin shiga tsakaninsa da Amal da yayi, abu d'aya kawai yakeso a taya shi da addu'a Allah yasa rabuwa da Amal d'in shi yafi mashi alkhairi. Sosai Baba yaji dad'in kalamunsa daman yasan d'ansa da tawakkali, albarka yayita sa masa k'arshe yake tambayansa ko ze dawo gida ne? Yaso se a saya masa sabon aiki koma wani iri yakeso.

  "A'a Baba nagode zan cigaba da zama nan d'in kawai."

  "Are you sure?"

  "Yes Baba ba amfanin dawowa na, gara inyi zama na anan ko wala Allah a hankali Allah ze yaye min son Amal."

  "Toh shikenan zamu tayaka da addu'a, so se yaushe zaka zo mana kenan?"

  "After a year or two in shaa Allah nan d'in yafi mun kwanciyan hankali."

  "Toh Allah yima albarka Baba na, Allah ya mayar maka da wacce tafi Amal kuma, addu'an mu na tare da kai a kullum."

  "Nagode Baba."

 "Toh ga Mamanka tana son yima magana." Itama Mama addu'a tayita masa tana sa masa albarka bayan nan sukayi sallama. Washegari Maamah da Amal suna zaune a makaranta tana bata labarin yadda suka k'aya da Ya Abdul jiya se kwatsam gashi yana kira bata 6ata lokaci ba ta d'aga bayan sun gaisa yake tambayarta ko tana gida ne.

   "A'a ina school" ta amsa.

  "Kuna tare da Amal kenan" kafin tayi tunanin yi masa k'arya yace, "Bata kinji? I just want a word with her" batayi gardama ba ta juyo gefen Amal. "Ya Abdul na son yi miki magana" ta sanar da ita. Kai Amal ta shiga kad'awa "I can't speak with him Maamah bazan iya ba ki basa hak'uri."

  "Sabida mey?"

  "Maamah naci amanan Ya Abdul , har abada bana tsammanin zan iya sake yi masa magana, kunya baze barni ba. "

  "Ya Abdul tak'i amsa" ta sanar da shi.

  "Dalili?"

  "Wai she can't spek to you ever again kunyan abinda tayi maka take."

  "Sa a handsfree" ba musu ta sanya "Amal?" Ya kirata sede ta kasa amsawa.

  "Amsa kinji? Kar ki damu" se kad'a kai take yayinda hawaye ya shiga ciko mata a ido amma ta kasa amsan wayan. "I'm not hanging up unless kinyi magana" hakan ko yak'i kashe wayan kud'insa se tafiya yake a iska ganin asaran ya soma yin yawa kawai ta amshe wayan daga hannun Maamah ba don taba so ba tare da miyarwa a headset "Ya Abdul" ta kirasa cikin sauti me rawa.

  "Amal shikenan idan ban nemeki ba bazaki sake nema na ba? Haka akeyi?"

  "Ya Abdul ba haka bane amma dan Allah kayi hak'uri."

 "Bade kuka kike ba?"

  "I'm not cryi-" kukan ne yaci k'arfinta tama kasa k'arisa zance nata. Hak'uri yayi ta bata har seda ya samu kukan nata ya d'an lafa.

  "Meyasa baki fad'a mun ba Amal?"

  "Ya Abdul ta ina kake tsammanin zan soma sanar da kai wannan labari mara dad'i mey uban d'aci? Dan Allah ka gafirceni nasan naci amanarka, naci amanar soyayyarka but I'm so sorry wallahi ba a son raina na rabu da kai ba. Yaya was dying and soyayyata kad'ai ce zata iya ceto da ransa, bazan iya barinsa ya mutu ba inspite of all the good fortunes da yayi mun dan Allah kayi mun kyakkyawan fahimta" ta k'are maganan cikin kuka.

  "Amal I know ba'a son ranki kika rabu dani ba and I do understand everything, nasani Allah ne ya rabamu and am sure yana da dalilinsa na yin hakan I'm just hurt and broken saboda baki sanar dani ba kikayi ta zolayata for all these while."

  "Please forgive me amma zolayarkan ce kad'ai mafitar da nake da, banason a sanadin sanar dakai gaskiyan al'amarin wani abu ya samu kafiyarka Ya Abdul I value your life morethan I do value my own, idan har abu ya sameka ban tsammanin zan iya yafewa kaina shiyasa na buk'aci iyayenka da nawa kar su sanar da kai, I'm terribly sorry."

  "A tunaninki canza layi da kuma daina nema na shine baze cutar dani ba Amal? If only kin sanar dani ko kuwa kin bari an sanar dani da zuciya na baza ta min k'una da ciwon da takeyi mun yanzu ba, I felt used and abandoned."

  "I'm so sorry Ya Abdul bana son ka d'au naci amananka ne, please forgive me."

  "Na sani Amal bazaki ta6a cin amana na haka kazai ba. Kuma ba k'aramin lada kike dashi ba na yafe farin cikinki dan ceto ran Afzal ba, only God shall repay you."

  "But I never wished for it Ya Abdul, gabad'aya rayuwa na da kai nake planning. Na gama sa ran da kai zan raya sunnan manzo, I never wished to be separated from you, please believe me."

   "Shhh! Na yarda dake Amal kuma nasani Komai na faruwa ne bisa dalili Allah nada dalilin raba mu da yayi fatanmu kawai Allah sa hakan yafi alkhairi."

  "Please forgive me."

  "Baki yi mun komai ba Amal, ina iya rantsewa akan soyayyan da kika nuna min and har in mutu bazan ta6a mancewa da hakan ba, ina alfahari da ke Amal, tabbas kin cika masoyiyata na hak'ik'a and I shall never forget that just keep praying kinji?"

  "Ya Abdul I miss you, I terribly miss you" ta sanar dashi cikin tsananin kuka.

 "I miss you even more my Princess, bazan iya kwatanta zafin rabuwa dake da nake ji ba but God's plan is the best, Allah tabbatar da alkhairi tsakaninki da Afzal ya sa ya kula mun dake kaman yadda ya saba da a baya."

  "Ameen" ta amsa a hankali. Kai kuma fa Ya Abdul? Wa ze kula mun da kai? Wa ze baka dukkan farin cikin da ka cancanta?"

  "Allah, Allah ze ban dukkan ababen da kika k'irga Amal just pray for me."

  "Ya Abdul you're one of a kind, kafin a samu irinka se an tona. Allah ya baka mace wacce ta fini da komai wacce zata soka fiye da yadda na ta6a sonka, wacce zata sa kamance da ni a rayuwarka gabad'aya."

  "Ameen Amal amma bazan ta6a mancewa dake ba, bana tsammanin akwai macen da zata sanya ni in mance da kalan tsaftcacciyar soyayyar da kika nuna mun. Amal kin riga kin zamo 6angare a jikina, I'll forever cherish our relationship, I'll forever love you."

  "I'll forever love you too Ya Abdul or even more, thank you for understanding me."

  "My pleasure bar kukan haka kinji? Kinga nima kina sani" yayi maganan yana tare hawayen dake shirin zubo masa.

  "Na daina please don't cry" ta amsa tana share hawayenta.

  "Toh se wataran kuma Amal, take care of yourself-" Katse wayan kawai tayi, ta ma kasa barinsa ya k'arisa abinda yayi niyya yayinda ta rushe da wani irin masifaffen kuka. Shi kansa Abdul hawaye yake da ya sauk'e wayan he still can't believe sun rabu da Amal, matar da yake sanyata cikin duk wani plan na rayuwarsa aciki, matar da baya iya d'aukan minti biyu beyi tunaninta ba, "oh Allah you know what is best for me" ya furta a hankali yayinda yake share hawayensa.

   Har zuwa Azahar Amal bata bar kukan da takeyi ba, Maamah se hak'uri take bata amma abun ya gagara. Suna zaune a masallci bayan sun idar da sallah sega wayanta yana ruri. Maamah ce ta ciro daga cikin jakar had'e da duban wake kira.

  "Waye ne?" Amal ta tambayeta tana duban yadda fuskanta ya kumbura timm acikin madubi.

   "Yaya ne" ta amsa. Kaman tace mata ta kashe saidai kuma ta d'au alk'awarin bazata kuma wulak'antansa ba, bata son abu ya sake samun lafiyansa. Haka ba don tana so ba ta d'aga. "Yaya" ta fara da cewa.

  "Na'am Lily" ya amsa.

  "Ina yini?" Ta gaishesa.

  "Lafiya k'alau ya kike ya school?"

  "Alhamdulillah ya jikin naka?"

  "Na warware Alhamdulillah."

  "Toh Allah k'ara sauk'i."

  "Ameen inzo muje muci lunch?" Shiru tayi tana nazari har ga Allah bata da niyyan fita dashi yau ba don komai ba kuma se don kukan nan da tayita yi fuskanta ya kumbura, tabbas tasan yana ganin yadda fuskanta yayi timm d'innan ze hau tambayarta dalili. Tsoronta d'aya ne kar ya gane gaskiyan al'amarin k'rashe kuma ciwonsa ya sake tashi. "Lily?"

  "Na'am Yaya."

  "Inzo? Or are you busy? In baze yuwu ba just tell me kinji?"

  "A'a kazo Yaya I'm free." Sanyi yaji sosai "Alright I'm on my way."

   "Toh sekazo" nan ta katse.

  "Maamah nakega kiyi joining su Aisha kawai Yaya yace zezo muje muci abinci."

  "Ayyah toh ba matsala adawo lafiya."

  "Thank you" nan ta mik'e ta bi su Aisha. Yayinda da Amal ta zaro kwalli daga jakarta taja a idonta sannan ta shafa powder duk wai don ta d'an 6oye kumburin fuskan nata amma ina da anganta ansan ta sha kuka, kukan ma mey wuya. Bada dad'ewa ba sega Afzal ya k'ariso kasancewar Nazeefah bata fita school ba yau se yayi tunanin suci abincin a cikin makaranta kawai. Unimaid garden suka k'arisa se anan yake tambayarta meya faru.

  "Babu" ta amsa sama-sama tana kare fuskarta. Hijabin nata ya janye "Taya zakice babu bayan gashi fuskanki duk a kumbure Lily, meya faru?"

   "K'anwar coursemate d'ita ce ta rasu muka je ta'aziya" tayi mai k'arya saidai take waien ya gano k'arya take. Kukanta baya wuce akan Abdul, tunanin hakan ba k'aramin k'ona masa zuciya yayi ba. Danne zuciyan nasa yayi ya mata ta'aziyya, hira sama-sama sukayi bayan sun gama ci ya d'an zagaya da ita cikin school sannan ya mayar da ita lecture hall nasu ya koma office.

   Nazeefah na kitchen tana had'a girkin yamma taji ringing na wayanta akan dining table. Da wuri ta fito ta d'auka ganin k'awarta Khadijah ke kira.

  "Halo Khadijah?"

  "Na'am Nazeefah ya kike?"

  "K'alau."

  Shiru yau baki fito school ba."

  "Wallahi cramps ne ya rik'e ni d'azu amma da sauk'i yanzun."

  "Ayyah Allah k'ara sauk'i toh."

  "Ameen yane toh?"

 "Nace ba wani mota ne kam mijinki yake hawa?"

   "AMG C43 lafiya?"

  "Chab! Wallahi shine! 'Yan mata shine!" Ta sanar da k'awayenta dake gefenta.

  "Shine wa?" Nazeefah ta tambaya curiously.
   
   "Babe mijinki muka ga tare da wata some minutes ago nan cikin unimaid garden." Wani irin mumunan fad'i gaban Nazeefah yayi.

  "Afzal d'in?" Ta tambaya cike da k'in yarda.

  "Wallahi shine shi da wata suka zo suka ci abinci suka fice duk a idonmu."

  "Kai k'arya ne ban yarda ba, bade Afzal ba sede ko me kama da shi."

  "Ki tsaya achan, ana fad'a miki abu kina musu wallahi shi muka ga ni bansan ma mey ya hanani d'aukansu a waya ba da na tura miki an kashe musun."

  "Khadeejah, Afzal fa kikace? Afzal kika gani da wata?"

  "Tabbas."

  "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Nashiga uku na lalace! Tun ba yau ba nake zarginsa ashe de gaskiya ne, amma ko! Yanzu rashin kunyansa har ya kai yana d'aukan 'yan mata yana kaisu cin abinci a idanun jama'ah?"

  "Hmm ai na miji ba d'an goyo bane Nazeefah komin dad'inki da shi seya cimiki amana."

  "Oh Allah nagode sena shigo gobe."

  "Allah kaimu." Tana ajiye wayan ta shiga sintiri a dining space d'in har miya ya soma k'onewa bata sani ba. A takaice girkin ranan sam ba hankali a jikinta tayi. Koda Afzal ya dawo bata mai maganan ba duda cewan ji take kaman ta rufesa da duka don zafin kishi. Lafiya k'alau tayi welcoming nasa bayan sallan Maghrib suna zaune a dining zasu fara cin abinci Afzal ya lura da kallon da Nazeefah ke tayi masa kusan tun dawowansa daga office.

  "Nazeefah are you sure you're okay? " ya tambayeta. Kai tayi saurin gyad'a mai had'e da kawar da kanta. Nan da nan tayi serving nasu spoon d'aya Afzal ya kai baki ya harar da abincin waje.

  "Subhanallahi!" Yayi exclaiming.

  "Lafiya?" Tayi saurin tambaya.

  "Ai na fad'a dama ba lafiya ba shin meke faruwa? Kinji uban gishirin dake cikin abincin nan kuwa? Bayan nan ga warin k'una what's really going on? Jikin naki ne har yanzu? Ai da kin bar girkin" Ji take tamkar ta d'aukesa da mari dan haushi. Bak'in cikin da yakeji yanzu kad'an ne dangane da wanda ya cusa mata.

  "Mey kajeyi a makaranta yau?" Ta tambayesa. Sosai tambayan nata ya basa tsoro taya ma tasan ya shiga school yau bayan bata fita ba? Allah ya taimakesa bawai munafukan k'awayenta bane suka gansa tare da Amal suka kirata suka yi mata gulma. Shima tun farko mey ya kaisa cin abinci a cikin school? Ai don Nazeefah bata fita school ba that doesn't mean k'awayenta ma basu fita ba, yayi sakarci. Tabbas su suka had'a komai.

  "Kayi shiru" ta sake da cewa.

  "Naje ganin friend d'ina dake lecturing achan ne" ya shirya mata k'arya dukda cewa yasan ba zama zatayi akai ba. Kallon da takeyi masa zalla ma amsa ne game da tambayan da yake yi wa kansa.

   "Wani abu ne?" Ya tambaya da kallon ya soma yi masa yawa.

  "Babu kawai dama ance mun anganka a school ne yau."

  "Ohhh like I told you naje ganin friend d'ina ne" ya amsa saidai yasan k'arya take masa, kaman yadda shima yayi mata k'aryar. Tabbas an gansa da Amal ne aka kira aka gaya mata.

  "Ya cikin naki ya daina ciwo?" Ya tambayeta yana neman canza topic d'in gudun kar fad'a ya 6arke musu.

  "Da sauk'i" ta amsa sama-sama.

 
  ***
   Tun kan wayan da Amal tayi da Abdul se gabad'aya halinta ya sake sauyawa ya koma na da, no matter how hard she tried ta kasa mancewa da shi, da tunaninsa take tashi da kuma shi take yini. Shima ta 6angarensa hakan ne. Kullum cikin tunaninta yake ba makawa.

    Haka zata yini d'aki tana kuka. Kwana biyu kenan bata fita school ba ta fake da cewa wai period cramps ke damunta. Shiko Afzal da zaran yaji bataje school ba yasan batun Abdul ne. Hak'urinsa ya k'are, bai jin ze iya jure hakan again he wants Amal to be his alone gashi a gida be san ta ina ze fara sanar da Nazeefah cewan yana shirin k'ara aure ba tabbas yasan baza ta ta6a amincewa da hakan ba, a cikin d'an k'ank'anin lokaci ya gano irin zazzafan kishin da take da shi. Lallai se yayi taka tsan-tsan da d'aukan Amal a mota anyhow tunda yanzu har an soma kawo mata gulma gida.

   Washegari ya shirya tsaf abinsa ya je gida gun Abba. Bayan sun gaisa yake ce mai shi yana son a tura gaisuwa gidansu Amal a shirye yake ya k'ara aure. Sosai Abba ya taya sa murna had'e da masa nasiha sosai akan yin adalci inda daga k'arshe kuma yake tambayansa ko ya sanar da Nazeefah batun auren ko kuwa tukuna.

  "A'a tukuna amman ina da niyya nafison idan ku manya kun gama komai sena sameta in fad'a mata abinda ake ciki, kar taga kaman ba neman aure nake ba kawai ina flirting ne a waje."

  "Kana da point kam amma kana ganin k'in sanar da ita har se idan an sa rana ko makamancin hakan shine dai-dai?"

  "I suppose it is Abba" ya amsa sa.

  "Toh shikenan Allah shige ma gaba zanyi magana da kawunanka cikin satin da za'a shiga se muje gidansu Amal d'in."

  "Toh Abba nagode sosai Allah saka da alkhairi."

  "Ba komai Allah yayi ma albarka."

  "Ameen bari in lek'a Ummi."

  "Ai bata gida baka sani bane?"

  "Wallahi no dake ina shigowa site naka na zarce."

  "Ayya ai ta fita suna wai."

  "Toh ba matsala ni zan wuce." Da haka sukayi sallama. Gidansu Amal direct ya wuce yayi mata waya kan ta fito gashi nan bakin k'ofa. Hijabinta ta ja ta sanya ta feshe jikinta da turare sannan ta fice taje ta samesa inda suka gaisa. Bayan nan ya kira sunanta a nitse.

  "Na'am" ta amsa.

  "Nace ba izun naki nawa ne yanzun? It's been long ban ji kina mun zancen islamiyya ba Lily."

  "I'm sorry kasan jami'a da islamiyyan ne se a hankali idan ba hutu akayi ba bana samun time na karatun kaman yadda nakeso."

  "Hakane kam, kina ma k'ok'ari ai am very proud of you tunda kika fara karatu baki samu carry over ba."

  "Thank you Yaya."

  "So izib nawa kika had'a so far?"

  "Saura goman k'asa in gama had'awa gabad'aya kuma dama chan tun da na ta6ayin biyar d'in k'asan a takaice de izu biyar ya rage mun idan na zauna nayi tilawa."

  "Masha Allah so ina da Hafizah as a wife to be kenan?" Kai ta gyad'a masa a hankali cike da kunya. "Zaki iya tuna alk'awarin dana d'aukan miki anytime kika gama haddanki?"

  "Eh toh not vividly amma de kace akwai special kyautan da zaka mun idan na had'a."

  "Very good Umarah nakeson mu tafi tare."

  "Saudi?" Ta tambayesa cike da k'in yarda.

  "Eh Lily Saudi."

   "Yaya are you serious?" Ashe de Allah ze nuna mata ranan da zata kai wa d'akinsa ziyara. Oh Alhamdulillah!

  "I'm damn serious, I would want us two to go together."

   "Toh Allah nuna mana I really can't wait."

  "Ameen but kinsan bazeyi muyi tafiya mu biyu kad'ai ba ko? Tunda ni ba muharraminki bane."

  Dank'ari se yanzu hankalinta ya buga ta kuma fahimci inda ya dosa a takaice de so yake yace mata aurensu ya kusa. Oh Allah ita bawai auren neba matsalarta, tunanin yadda zata fara zaman aure da Afzal take wai ma zancen kishiya a gefe. Mutumin da duk rayuwarta ta d'aukesa a matsayin yayanta kuma rana d'aya seta fara kallonsa a matsayin mijinta? How is that even possible?




RANA D'AYA!
#RD

Love... king Miemiebee👄✨

6 comments:

Fatima said...

Thanks dear Allah ya Kara baseera... Mutuniyata an iya ki shi @nazeefa

Unknown said...

Ameen you're welcome dear

Unknown said...

Job weldone dear,can't wait to go 2ru page23....jzkhair

Unknown said...

Continuer

Unknown said...

Published

Unknown said...

Pls kinada soft copy din wannan littafin.,idan kinadashi Dan Allah kiyi man forwarding dinshi ta what's app: 09035076144