BY MIEMIEBEE
PAGE 23
"Lily kinyi shiru" ya fad'a yana kallonta.
Kanta tayi saurin kawarwa tare da ambatan sunansa a hankali se kuma tayi shiru.
"Lily I'm sorry but I can't wait any longer, I've waited for so long to be with you and to make you mine and now is the perfect time, please kar kice a'a nasan kina iya had'a haddan naki acikin watanni biyu zuwa uku masu zuwa. Idan har kika samu kika had'a kinga se ayi bikin sauk'an naki dana auran mu at once bayan nan kuma se mu wuce Saudi for our honeymoon, don't say no please."
Excuse ta shiga nema amma gabad'aya ta rasa ta mey zata ce masa. Bata san mey ba amma anytime Afzal yakeyi mata zancen aure gabanta yake tsinkewa yana fad'i, har wani tsoro-tsoronsa ma takeji. K'arshe de ta samu ta 6ullowa zancen ta hanyan sak'alo sunan Nazeefah. "Toh Yaya Nazeefah fah? Ita baza mu tafi da ita ba?"
"Lily I want you to believe in me, ki sani cewa zanyi iya k'ok'arina don ganin nayi adalci tsakaninki da 'yar uwarki. Nasan auran mey mata a zamanin yanzu isn't something easy but I need you to believe in me, ni da Nazeefah cikin kwanakin nan zamu tafi in shaa Allah so that idan munzo tafiya dake bazata ga kaman anyi mata rashin adalci ba. But kafin mu tafi da ita I need your approval please ki amince zaki aureni, I've spoken with Abba already a shirye yake suzo su sami su Papi ayi maganan, amincewan ki kawai nake nema Lily."
"Yaya I do believe in you, tsoro na d'aya ne" ta sanar da shi a nitse.
"What is it? Tell me" ya amsa take.
"Nazeefah, Yaya tsoron zama da kishiya nake bansan mey Nazeefah zata iya aikatawa ba, ban san irin kishin da take da shi ba, bansan ko zata amince dani kokuwa a'a ba, banason in zame d'aya daga cikin jeri matan da kishiyoyinsu suke yi musu illa kaman yadda banida niyyan cutar da ita bazan so nima ta cutar dani ba."
"You're safe with me Lily, I'll do everything in my power to keep you save and kar kiyi tunanin Naeefah is that evil nasani kishi kam dole ne but she'll never hurt you, I'll make sure of that and besides banida niyyan had'aku gida d'aya, unguwa ma ba had'aku zanyi ba ni kawai ki amince."
"Toh shikenan Yaya na amince da k'udurinka, kana iya turo su Abba but I have one favor to ask."
"Ask me anything Lily."
"Please kayi hak'uri semun kammala first semester d'in yaso se ayi auren cikin hutu, bana son hidiman bikin ya raba mun hankali."
"I'll do only as you wish Lily se abari idan kin kammalan ba second semester kuke ba?"
"Eh" ta amsa had'e da gyad'a kai.
"Allah taimaka toh."
"Ameen."
"So will you agree to marry me?"
"Yaya ba nace eh ba."
"I want to hear it again, Lily am head over hills for you, please tell me again will you marry me?"
"Yes Yaya" ta amsa cike da kunya ko kallon gefensa ta kasa bale cikin idansa.
"Thank you Lily ji nake kaman duk duniya ba wanda ya kaini farin ciki, Lily a yau kin cika mun buri da kuma mafarki. I've been looking forward to this day and now I shall be looking forward to the day I'll make you mine, the day you'll start answering my name and the day I can call you my wife. Lily you don't have to worry because I've promised to take care of you, to love and protect you with my life, I've promised to never leave your side. In shaa Allah bazakiyi nadaman aurena ba."
"I know Yaya Allah and I'm very grateful Allah ya baka ikon yin adalci tsakani na da Nazeefah."
"Ameen Lily kinsan wani abu?"
Kai tayi saurin kad'awa da nufin a'a .
"Guess!"
"But I can't ka fad'a mun kawai."
"I love you" ya sanar da ita. Har cikin ranta taji nauyin kalamun nasa yayinda kunya me tsanani ya rufeta fuskanta ta shiga karewa. "Kin san wani abu again?" Nan ma kai zalla ta iya kad'awa.
"I love you" ya kuma sanar da ita. By now kam Amal ji take kaman zata lume k'asa don kunya, bata san mey ba amma kunyansa takeji kunyan ma me tsananin tsiya bata tsammanin zata ta6a iya sakewa dashi. Wani sa'in tana missing relationship nasu na da dasuke a matsayin Yaya da Lily zallah ba wani abun ba.
"Can't I get an 'I love you' back?" Ya tanbayeta tare da had'e girarsa.
"Yaya..." se kuma tayi shiru.
"Lily I know you're not comfortable with me, nasan kina tsananin jin kunya na and I respect that alot but please give me the chance to love and make you happy."
"Yaya I'm already yours ka daina damun kanka haka."
"I feel honored then" ya amsa "Can I ask of a favor?"
"Ina sauraronka."
"Can you please tell me you love me too? I need to hear these words so badly."
"Yaya-"
"Lily I know it you don't love me-" ya katseta.
"Yaya ya kake magana haka?" Itama tayi saurin katse sa.
"Na sani Lily, nasani har yanzu Abdul ne a zuciyarki kuma shi kikeso and bawai ina kishi da hakan bane kokuwa ina jin haushi, nasan zafin rabuwa da masoyi nasan ze d'au lokaci kafin ki iya mancewa dashi ki bud'e mun zuciyarki. I just want you to know that no matter what I'll stand by your side. I'll provide support and love you regardless, I'll be here Lily even if you don't need me."
"But Yaya I need you also-"
"Shhh!" ya katse ta "And also bana son kiyi tunanin cewa banida godiya ne nake tinziraki haka ina gaggawa, ki sani it's just because I love you so damn much. Bayan nan I'm very grateful for all the sacrifices you've made to save my life, I'll forever remain grateful to you Lily I just need to hear these words koda kuwa you don't mean them just tell me."
"Yaya I-" seta bud'e baki zata sanar da shi kalamun seta kasa ji tayi bakinta yayi nauyi, banda sunansa ba abinda take iya furtawa.
"Please try" ya rok'eta. Sede ina duk yadda taso sanar dashi hakan abun ya gagara se gani take kaman Ya Abdul na tsaye a gefen windon yana kallonta.
"I'm sorry then" yace k'arshe feeling so sad.
"Yaya ni ya kamata in baka hak'uri dan Allah kayi hak'uri Wallahi I'm trying, I really want to forget about Ya Abdul abun ne yafi k'arfina please forgive me" ta sanar da shi cikin sautin kuka.
"Its okay Lily ba se kinyi kuka ba, forgive me but ba laifi na bane don hak'uri na ya gaza, you're just like a drug, so addicting. Ji nake kaman in ban same ki ba ina iya rasa rayuwana."
"Yaya dan Allah kabar magana haka I'll always and forever be yours, kasa a ranka na riga na zama taka bana son inji kana maganan rasa rayuwanka, ya kakeson in rayu in ba kai?" Tunda suka fara hirar se yanzu ne ta juyo tana kallonsa idonta cike da k'walla.
"Forgive me, but bakiya sona ya kikeson inyi idan ba mutuwa ba?"
"Yaya I care about you, I care about your existence morethan anything dan Allah kabar cewa haka."
"Anything for My Lily."
"Thank you" ta amsa had'e da sakar masa k'aramin murmushi tana share hawayen nata. Murmushin shima ya miyar mata yayinda ta shiga duban lokaci a cikin wayanta. "Maghrib ya kusa ko?" Ya tambayeta. Kai ta gyad'a a hankali "Ya kamata mu soma yin niyyah."
"Sure" ya amsa tare da mik'a hannunsa ta back seat ya janyo wata leda. "Here wannan naki ne."
"Yaya baka gajiya da bani gifts ne kam kullum?"
"Bazan ta6a gajiya da farinta miki ba Lily."
"Amma Yaya-"
"Not a word please" ya katseta. Bata k'ara musu ba ta mik'a hannu ta amsa had'e da yimai godiya. Seda taga ficewansa ta k'arisa ciki. D'akinta ta nufa inda ta zazzage kayakin gabad'aya designer turaruka ne da man shafawa aciki seda su gel da sauran kayan shafe-shafe. Oh! Idan ta tuna da irin kashe kashen kud'in da Afzal yakeyi akanta setaji kaman ta samu Ummi tace ayi mishi fad'a ya daina. Bata son a sanadinta ya samu kariyar arziki ko makamancin hakan gashi ya dage kullum idan zezo se yayi mata gaggarumun shopping.
***A nitse Afzal ya k'arisa gida sede tun da ya hau kan hanya yake tunanin kalamun Amal da kuma yadda ta kasa furta masa kalaman da kunnensa suke kwad'ayin ji. Be san kuma mey zey sakeyi Amal ta bud'e masa zuciyarta ba ta koyi sonsa, he misses her alot. He misses her smiles and laughter, everything about her he mise. Duk abinda yasan ya kamata yayi ya yi amma ina har yau ta kasa sakewa da shi. Yana isa gida Nazeefah ta taso tayi masa sannu da zuwa jawo hannunta kawai yayi ya rungumeta feeling so lonely.
Ta kai kusan minti d'aya tsaye ko motsi babu sannan a kid'ime ta zagaye hannayenta a bayansa hugging him back cike da rashin fahimta. "Afzal is everything okay with you?" Ta tambayesa a hankali har anan be saketa ba yayinda kuma ya kasa amsa ta. "Afzal?" Se anan ya raba jikin nasu.
"Nazeefah I feel so alone, shin bayan su Ummi akwai mey sona kuwa?"
"Wani irin magana kuma kake haka? Meya faru?"
"Just answer me, akwai?"
"Akwai mana Afzal, and ina d'aya daga cikinsu. I love you Afzal no matter what, kar ka ta6a tsammanin bakada masoya bayan su Ummi. I'm here and I love you kaji?"
Kai ya gyad'a a hankali "Thank you Nazeefah."
"You shouldn't mention food is ready taho muje inyi serving naka ko seka dawo daga masallaci? Naga Maghrib ya kusa" Ta tambayesa. Bata kai da juyawa ba ya rik'o hannunta kafin ta fahimci abinda yake shirin yi kawai taji moist lips nasa akan nata, mutuwan tsaye tayi a wajen yayinda ta kasa koda kyafta ido. A hankali taji large arms nasa yana rufe bayanta yayinda yake matso da ita kusa da shi, deepening the kiss in the process. Wani irin electrification taji yana bin jikinta yayinda taji numfashinta na neman d'auke mata, bata san a lokacin da ta shiga mayar masa da martani ba. A hankali a hankali suke tafiya manne da juna har seda Afzal ya turata jikin bango. Mutum na iya cewa sun mance da duniyan da suke ciki don zafin kiss kawai, gabad'aya sun fita daga hayyacinsu. Chan Afzal ya saketa a hankali yana k'ok'arin kama numfashinsa kaman yadda itama takeyi, goshinta ta sauk'e dai-dai saitin ha6arsa yayinda wani irin zazzafan sonsa yake shiga jikinta. Ji take gabad'aya duniya ba wanda ya kaita murna, ashe de Allah ze k'addaro mata da wannan rana? Oh she can't get over how sweet, soft and moist his lips were, bata k'i ya sake kissing nata over and over again ba.
"I'm sorry" taji ya furta a hankali yayin da minty breath nasa yake fifita hancinta. Shi kansa ya rasa gane meke faruwa.
"It's okay" ta mayar masa har anan ba wanda ya motsa acikinsu.
"I'm sorry" ya sake fad'a had'e da sauk'e hannayensa da suke rik'e da kunkuminta "I'm really sorry ban san meke shirin faruwa da ni ba please forgive me" kafin tace wani abun ya wuceta da hanzari inda ya zarce d'akinsa. Key ya sa had'e da manna bayansa jikin k'ofan. Idonsa ya rufe gam amma ya kasa daina tunanin kiss da sukayi sharing da Nazeefah shin meke faruwa? Gabad'aya ji yayi Amal yake kissing, mey soyayyar Amal ke shirin yi masa? Taya zeyi kissing Nazeefah ya d'au Amal yake kissing? Anya kuwa soyayarta ba shi ze halaka sa ba? Yanzu da wani ido ze sake kallon Nazeefah? Oh Allah! Yau yana cikin wani yanayi. Sallan Maghrib da be fita ba kenan ranan wane sabuwan amarya haka ya la6e a d'akin. Tun Nazeefah na jiransa da ya fito suci abinci har bacci yayi gaba da ita zaune akan dining d'in. Chan wajajen goma ya lek'o waje a sanadin yunwan daya fafarosa. Sid'ak-sid'ak yake tafiya wai kar tajiyo motsinsa ta fito, ba k'aramin tsinkewa zuciyansa yayi ba ganinta da yayi zaune akan dining ta kafa kanta akan dining table d'in. A farko niyyan juyawa ya koma d'akinsa yayi tunda de bata gansa ba amma kuma ya fasa sanadin kukan da cikinsa yayi don yunwa. Matse idonsa yayi ya k'arisa wajen had'e da yin gyaran murya se kuma yaga bata motsa ba.
"Nazeefah?" Ya kira sunanta nan ma shiru lek'a fuskanta da zeyi kawai ya tarar bacci takeyi. Allah sarki bade bacci ne ya d'auketa anan ba tun tana jiransa ya fito suci abincin tare? Shin ta ma yi sallah kuwa? A hankali ya shiga tada ita har ta bud'e idonta.
"Kinyi sallah?" Ya soma da tambayarta. Kai zalla ta gyad'a masa yayinda idanunta suke neman kafewa.
"Abinci fa kinci?"
"Ba tun d'azu ina jiranka ka fito muci ba kak'i."
"Ba wai nak'i bane Nazeefah..." se kuma yayi shiru a bisa rashin sanin abinda ze sake cewa.
"Are you ashamed because you kissed me? Are you Afzal?" Ta tambayesa da mamaki.
"Ko kad'an ba haka bane."
"Toh yaya ne? Afzal I know you don't love me but I'll never surrender, zan cigaba da hak'uri ina farinta maka har izuwa ranan da Allah ze sa a ranka kaji zaka iya yafe mun abubuwan da nayi maka da a baya, I really am sorry" ta k'are maganan idanunta na neman cikowa da hawaye.
Zama yayi a gefenta a hankali had'e da rik'o hannunta cikin nasa. "Kibar cewa haka please ni baki yimun komai ba."
"Ban yi maka komai ba?" Ta tambayesa da d'umbun mamaki.
"Ban yi maka komai ba amma auran mu sama da shekara biyu kenan yau baka ta6a tunanin sauk'e mun hak'k'ina da Allah ya d'aura maka ba? Baka ta6a damuwa da wani halin nake ciki ba Afzal. Kana ganin ka kyauta mun kenan?"
"Nazeefah-"
"Amma kar ka damu har ga Allah ni na yafe ma komai saboda bana son Allah ya tsayar da kai ranan qiyama akai na" ta sanar da shi had'e da katse sa sannan ta cigaba. "Nasani ni na bud'e k'ofan duk wani tashin hankali da wulak'anci daga gareka, da tun farko na rik'e mutunci na nayi respecting naka da duk hakan be faru ba I just hope it's not too late to say sorry." Sosai kalamunta suka shigesa ya kuma tausaya mata. Ya sani tauye hak'k'in bawa ba abu bane me kyau musamman ma na tsakanin mata da miji but shima ai ba a son ransa yake hakan ba.
"A tunanin ki a son raina ne nake tauye miki hak'k'in ki? A tunanin ki nid'in zama haka dad'i yake mun ne? Kokuwa kina tunanin ni banida sha'awa ne? As much as you need me as your husband know that I need you as much amma-" se kuma yayi shiru.
"Amma mey? Please talk to me Afzal I can't do this anymore."
"I can't Nazeefah, bazan ta6a iya had'a kwanciya dake ba.l Har cikin ranta taji zafin kalamun nasa ba shiri hawaye ya shiga tsiyaya daga idanunta.
"Afzal meyasa? Me nayi da zaka hukunta ni haka? Dan Allah kayi hak'uri, Afzal bazan iya rayuwa ba kai ba, wallahi da in rasa ka gara na rasa komai ciki harda rayuwa na. I love you Afzal I can't stop saying it no matter what."
"Nazeefah I'm sorry."
"Ni ba hak'urinka nakeso ba Afzal, ka gayamun dalilin da yasa bazaka iya had'a kwanciya dani ba idan wani laifin nayi in baka hak'uri."
"Forget it, just forget it" kafin ya kai ga mik'ewa ta jawo hannunsa tana hawaye sosai "Please tell me Afzal a shirye nake da inyi ta baka hak'uri har se Allah ya huce ma zuciya dan Allah ka fad'a mun." A da ya d'au alk'awarin komin yaya baze ta6a sanar da ita laifin nan da tayi masa ba amma kukan da takeyi ba k'aramin karya masa zuciya yayi ba.
"Please tell me Afzal I can't do this anymore."
"Remember the first day aka kawo ki gidan nan?" Kai tayi saurin gyad'a "Mey kikace wa k'awarki da ta kiraki?" Ya tambayeta, sede ta duba ta duba tayi tunanin gaba da baya amma ta kasa tuna komai. "Afzal wallahi bazan iya tunawa ba dan Allah ka fad'a mun."
"I can't tell you, bazan iya ba Nazeefah saboda kalamun basuda dad'in sauraro zan baki nan da duk lokacin da kike buk'ata ki zauna kiyi tunani idan har kin tuna da kanki then I'm willing to forgive you."
"Afzal please tell me I'm so sorry."
"I'm sorry as well but I can't." Yana fad'in haka ya kuma mik'ewa da niyyan ficewa hannunsa ta sake rik'owa "Nasan kana jin yunwa please ka zauna kaci abinci."
"Karki damu."
"Please Afzal."
"Kefa? Kinci?"
"Ni idan har zaka ci ma hakan ya isa ya k'osar dani don't worry about me."
"I'm not eating unless with you."
"Toh ka zauna please kar ka tafi."
"Toh kibar kukan haka" badan tana so ba ta shiga share hawayen nata seda ta bar kukan ya amince ya zauna nan tayi serving nasu suka ci bayan sun gama ta tattara plates d'in takai kitchen. D'akinta ta wuce dan watsa ruwa shima haka, chan yana shirin kwanciya se gata ta shigo daman ita yake jira. Bayan ta kwanta ya kashe musu wutan. Kan pillonta ta bari ta matso kusa da shi had'e da sauk'e kanta a birnin k'irjinsa tana mey zagaye hannunta akan cikinsa. A hankali taji hannayensa yana kewaye bayanta "Goodnight Nazeefah" ya sanar da ita had'e da sauk'e mata peck a kai.
"Goodnight Afzal I love you." Bada dad'ewa ba yayi bacci itako ta kasa, se tunanin maganansu na d'azu take. Shin mey ta fad'a da ya 6ata masa rai haka har ya gommaci ya tauye wa kansa hak'k'i ya sha wuya da ya kusance ta? Se kusan k'arfe biyu bacci ya d'auketa. Washegari wajajen k'arfe hud'u bayan Afzal ya dawo daga office tayi masa sannu da zuwa had'e da amshe jakansa. Har d'aki ta rakasa ta ajiye jakan nasa a mazauninsa sannan ta shiga bayi ta had'a masa ruwa ya shiga ya watsa bayan ya fito ya sanya shorts da singlet sannan suka fito dining inda suka ci abinci. Bayan sun gama ta tattare wajen tsaf. Har Afzal ya shiga takawa zuwa d'akinsa yaji muryan Nazeefah na kiransa, chak ya tsaya had'e da kewayowa. Mik'ewa tayi ta k'arisa ta samesa.
"Afzal I'm sorry I'm really sorry."
"Why? What for?" Yyi saurin tambaya.
"Bayan tunanin da na yini inayi na tuna abinda na fad'a a daren auren mu dan Allah ka gafirceni, I was young and stupid then, yarinta na yawo a kaina bansan ciwon kai na but tuba nake please forgive me for hurting you like I did, wallahi I didn't mean a word."
"It's okay Nazeefah ya wuce."
"Dan Allah ka yafemun."
"Na yafe miki komai Nazeefah forgive me also."
"You have nothing to be sorry for."
"Toh hawayen ya isa haka" ya fad'a had'e da sa hannunsa yana share mata hawayen nata. Hugging nasa kawai tayi yayinda kukan nata ya tsananta "Thank you for forgiving me Afzal, I love you so much." A hankali ya zagaye hannayensa a bayanta hugging her back.
"Its okay" ya sanar da ita yana shafa bayanta a hankali. Be barta ba seda kukan nata ya lafa hannunta ya ja izuwa parlourn inda suka zauna akan kujera.
"Yaushe zakuyi exams naku?"
"Da d'an saura se nan da two months in shaa Allah."
"Masha Allah shikenan an zama graduate kuma ko?"
Ka manta ne? First semester muke ai? Se mun gama second tukuna."
"Yesh haka My computer scientist" yayi complimenting nata.
"Thank you" ta amsa tana murmushin jin dad'i, har cikin ranta taji dad'in yadda ya kira ta 'his computer scientist.'
"I'm so proud of you Nazeefah Allah sanya albarka acikin karatun."
"Ameen Afzal thank you."
"Ina son mu tafi Umarah tare."
"Umarah?" Tayi exclaiming cike da mamaki.
"Yes just me and you."
"OMG!" Tsalle tayi tare da hugging nasa. "Are you serious?" ta sake tambaya bayan da ta sake sa. "Yes Nazeefah" ya amsa.
"Yaushe toh?"
"I guess se idan kun gama exams naku yanzu kinga ai kina school."
"But ba wani serious lectures ma muke ba."
"A'a Nazeefah bana son wasa da karatu ai 2 months d'in kaman gobe ne karki damu kinji?"
"Toh shikenan Allah kaimu I just can't wait."
****
Haka nan tun daga ranan Nazeefah da Afzal suka soma zaman lafiya a gidan. Kullum shi yake kaita school, idan lokacin lunch yayi kuma ya d'auketa suje su ci da ikon Allah basu ta6a had'uwa da Amal ba sannan duk sanda yake gida baya kiranta gudun kar Nazeefah ta gano wani abun. A satin da ya gabato ne su Abba suka turo gaisuwa gidansu Amal inda su Papi suka amince suka kuma bada Amal. Siyayya sosai su Abba suka yi fiye da wanda Baban Abdul sukayi, kayaki se de ace masha Allah. Kaman yadda Afzal ya buk'ata haka Abba ya sanar da iyayen Amal cewa baya son a d'au lokaci kafin ayi bikin so samu idan Amal ta kammala part three nata batun kayan d'aki da gara kuma yace ya d'auke masu nauyin su kawai su amince ayi bikin ba tare da an 6ata lokaci ba. Papi beyi jayayya da hakan ba shima dama bayi da ra'ayin jan bikin idan ma da akwai abinda ze sasu jan bikin shine shirin yima Amal kayan d'aki amma yanzu da Afzal ya nuna zeyi komai sede suyi musu fatan alkhairi.
Sati uku Papi ya basu a gaba da su dawo kafin nan Amal da mahaifiyarta sun gama yanke hukunci game da ranar da za'a sanya na auren. Sosai su Abba sukayi godiya inda suka sauk'e dubu ashirin da suka tashi tafiya.
****
Haka tafiyan ta cigaba duk da kalan halatayya irin na Amal, Afzal be kariya ba, be fasa kirarta da kuma zuwa gidansu dubanta ba. Gashi duk abinda ya gani me kyau se ya sai mata ita da Nazeefah sosai yake kwatanta yin adalci a tsakaninsu. Nazeefah kuwa har yau bata san meye ake ciki ba.
Ta fannin Abdul kuwa sosai yake kewar Amal, rana baya ta6a wucewa beyi tunaninta ba sede kuma bai fasa tashi cikin dare yana rok'an Allah ya kawo masa sauk'i ba.
****
Yau bayan sallan Isha Afzal da Nazeefah suka shirya tsaf inda suke je sukaci abinci bayan nan ya wuce da ita 3G gallery inda ta sassayi jakukkuna da dama. Bayan ya biya komai sun dawo mota ya sake fita da sunan yayi mantuwa inda ua sai wa Amal tasa itama jakukkunan ya bayar aka sa masa a booth suka k'arisa gida. Project nata ta d'auko suka cigaba da yi mata daga inda suka tsaya jiya, wajajen goma tace su bari haka su kwanta yaso su cigaba gobe. Yau wankan ma a bayin d'akinsa tayi, bayan ta fito shima ya shiga yayi zuwa k'arfe sha d'aya de suka samu suka kwanta. Kaman kullum ta gangara jikinsa sede yau Afzal ya d'au niyyan mayar da Nazeefarsa cikakkiyar mace. Yau fiye da sati biyu kenan tunda ta nemi tubansa amma ba abinda ya shiga tsakaninsu. Tun Nazeefah na sa ran ze nemeta har ta dena saidai ko da wasa bata sake yi masa maganar ba ita de bata fasa da yin addu'an Allah shirya tsakaninsu ba. Kaman acikin mafarki taji ana yi mata wani irin shafa, a firgice ta bud'e ido sede kafin tace zata mik'e zaune ya rik'ota gam a jikinsa.
"Shhh!" Ya buk'aceta se anan hankalinta ya d'an kwanta. A hankali cike da dabara ya shiga sarrafata yayin da take basa had'in kai har yaci nasaran raba ta da kayan jikinta. Wannan dare de da Nazeefah ta dad'e tana jira finally Allah ya kawo mata shi, anci kuka anji dad'i duk a lokaci d'aya. A hankali har bacci me nauyi yayi gaba dasu duka sede duk lokacin da Nazeefah ta tuna yadda Afzal ya riga tarerayarta se ta murmusa acikin baccin. Wani irin gobaran sonsa ne yake ruruwa a zuciyarta ji take idan ba shi bazata iya rayuwa ba.
Kiran sallan Asuban fari Afzal ya tashi, a hankali idanunsa suka sauk'a akan Nazeefah datake manne a jikinsa se bacci take bayan da ya kunna wutan d'akin. Murmusawa yayi a hankali yayinda events na last night suka soma dawo masa ashe de raguwa take se kurun bakin tsiya. Cike da dabara ya raba jikinsa daga nata had'e da lullu6e jikinta da bargo. Bayi ya fad'a yayi wanka sannan ya d'aura alwala ya had'a mata ruwan d'umi tukuna ya fito. Bayan ya sanya jallabiyansa ya nufi kan gadon inda take bacci har yanzun.
Sunanta ya shiga kira a hankali har seda ta bud'e idonta, da sauri ta sake kullesu bayan da suka had'a ido hakan ba k'aramin murmushi ya sanya sa ba, wai kam dama Nazeefah na da kunya? Wai toh idan tana irin wannan kunyan? Amal tasa fah? Amal da ko kalamun soyayya ya fad'a mata bata sake iya kallon cikin idansa. Lallai akwai k'ura a gaba.
Gyaran murya yayi yace, "Tashi haka toh kiyi wanka muyi sallah baccin ya isa."
"Toh ka daina kallo na" tayi maganan idanta rufe gam.
"Yau kuma? Tashi kinga lokaci na k'urewa."
"Toh Ya Afzal ka tashi ni idan da hali ma ka fita idan na kimtsa zanyi maka magana" ta sanar da shi. Murmusawa yayi sosai "Yau kuma nine Yaya saboda kinji wuya jiya?"
"Ya Afzal mana" ta fad'a had'e da jawo pillow tana kare fuskanta.
"Toh naji naji, zan jiraki a parlour."
"Toh ka tafi" mik'awa yayi ya janye pillon a hankali had'e da sanya mata light peck a goshi sannan ya mik'e ya fice. Seda taji k'aran kulluwan k'ofa sannan ta shiga bud'e idon nata a hankali. Haka kawai ta tsinci kanta cikin tsananin farin ciki, se murmushi wa kanta take barin ma idan ta tuna abubuwan da Afzal ya rink'a yi mata daren jiya, yadda ya rink'a binta a hankali yana kashe mata jiki. She felt like a princess, like a baby and all. Aww she's madly in love with him, a hankali ta mik'e ta nufi bayin. Shiganta ba da jimawa ba Afzal ya dawo d'akin, bedsheet d'in ya tattara yayi disposing. Kafin ta fito har ya shimfid'a sabo ya zauna bakin gadon yana jirarta.
"Ya Afzal" ta kirasa lokacinda ta fito tana tsaye bakin k'ofar d'aure da d'an guntun towel. Kafin yayi magana har idonta ya kai ga sabon bedsheet daya shimfid'a kan gadon. "Awwn Ya Afzal ai ko ni ma zan iya canzawa it doesn't have to be you."
"Don't worry sanya kayanki muyi sallah" ya amsa. Nan da nan ta shirya ya jasu bayan sun kammala azkhar nasu suka shiga shirin office da school. Yau ma kaman kullum shi yayi dropping nata. Nazeefah fa ji take tamkar duniyan ma tayi kad'an ta d'auke ta dan murna da farin ciki kawai. Tuni ta sanya hoton Afzal a home and lock screen nata, idan ta isa gida ma zata canza na laptop nata ta sanya hoton nasa.
Da Azahar lectures nasu ya k'are saidai Afzal baze samu daman zuwa d'aukanta ba don haka ya tura driver'n Ummi da ya d'aukota kasancewar yana da meeting. Bayan da ya d'auketa se tayi tunanin ya wuce da ita gida gun Ummi ya kwana biyu basu lek'a juna ba. Sosai Ummi tayi murnan ganinta daman tana da anniyar kai masu visit this weekend saboda shirun yayi yawa. Hira suka sha sosai sekace ba surikai ba, suna cikin cin abinci ne Nazeefah tayi gyaran murya "Ummi?" Ta kirata.
"Na'am Nazeefar Mummy."
"Kai Ummi wai yaushe zaki sauk'e sunan nan ne kam?"
"Ko Nazeefar Afzal ce?"
"Toh ko kefa? Ai hakan ma yafi dad'i" nan suka k'yalk'yale da dariya.
"Ahh lallai soyayya manya wannan kumatu da kika k'ara anya kuwa ba abu a k'asa?"
"Laaa ji Ummi dan Allah ni kinga har zaki sa in mance abinda nakeson tambayarki ma wallahi."
"A'a yi hak'uri tambayan ina jinki."
"Shin mey yafi burge Ya Afzal game da mace?"
"Addini" Ummi ta amsa nan take. "Yana bala'in son mace mey addini."
"Allah Ummi?"
"Sosai ma kuwa."
"Ai kuwa ya zama dole in koma islamiyya kodan shi ma."
"Toh fa mey Prince yayi har ake neman farinta masa rai haka."
Hmm Ummi kenan ai komai ma Ya Afzal na mun jiyan nan ya kaini 3G gallery bakiga jakukkunan dana d'iba ba kuma duk ya biya makaranta yanzu kullum shi yake kaini sede idan banida lectures na safe please ki cigaba da sanyasa a addu'a keda kike mahaifiyarsa, nima inayi masa amman naki daban ne. Allah ya taimakesa ya k'ara masa bud'i."
Masha Allahu sosai Ummi taji dad'in kalamun Nazeefah ashe in de haka ne Afzal yaji fad'an da ita da Abba su kayi masa kenan. Madallah gaskiya tayi wa Nazeefah murna sede kuma alokacin da ta fara jin dad'in aurenta a lokacin Afzal yake shirin k'aro mata kishiya. Oh kowa de da tasa k'addarar, Allah de ya sa ta d'au hakan a matsayin k'addararta ta kar6a hannu bibbiyu.
"A gaskiya naji dad'in kalamanki matuk'a Nazeefah, naji dad'i yanzu da ke da Afzal kuke zaman lafiya Allah yasa hakan ya d'aure ya kuma cigaba da had'a kawunanku."
"Ameen Ummi so bayan addini sey kuma mey yakeso?"
"Addini de itace babba, kika rik'e addini to kin kama k'afansa kenan, inda so samu wannan gyale ma ki daina sanyasu in ba a gida ba, yana son mace me sanya tufafin da ze rufe mata jiki bayan nan kuma mace mey tsafta, mey kunya. Ki zame mey kunya, mey kuma kamun kai ba kowani na miji zakina huld'a dashi a makaranta ba inba wanda ya zama dole ba." Se kai Nazeefah keta gyad'awa wane mey d'aukan lectures "Nake ga idan kika kiyaye wannan ababen da na k'irga miki toh fa kin riga kin mallake Prince kin zama uwar gidansa."
"Thank you very much Ummi in shaa Allah zakiga canji wallahi ina son Ya Afzal and doing just what he likes makes me happy. A shirye nake da in sadaukar da farin cikina saboda nasa, please ki rink'a samin shi acikin addu'a Allah cigaba da karemun shi."
RANA D'AYA
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
13 comments:
Awwn thanks sweetheart u really make my day....really appreciate .more ink to ur pen
Thanks dear. Allah ya qaro basira
Thanks dear! U r making us checking ur page always to c if there is a new update! We cant wait 2 hav more
Thanks dear! U r making us checking ur page always to c if there is a new update! We cant wait 2 hav more
Godia babu adadi, more ink to ur pen
Awwwn����...been offline 4 a while.tnx soo much dear waiting 4 more
Thank so much,more greese to ur elbow
Amen you're welcome 😊
You're welcome dear
You're most welcome
More coming soon dear 😘
Ameen you're welcome
Glad you're welcome 😊
Post a Comment