Saturday, 25 March 2017

‘YAR GATA CE!

BY MIEMIEBEE
Page 72
  March, 2017



   "Call daga wa kenan?"
  "Daga colleague d'ina regarding Boss."
  "Boss? Wani Boss kenan?"
  "Your in-law mijin Madam."
  "Kana nufin Ya Al'ameen? Meya samesa?" Tayi maganan cikin tsan-tsan tashin hankali.
  "Hajiya Boss is in a very critical condition, yanzu na gano dalilin dayasa Madam ta sume, a hanyan dawowansa yau daga Abuja 6arayi suka taresu suka gudu da motanshi suka kuma har6esa kusa da heart nashi Driver'nsa kuma suka mai d'ankaren duka yanzu duk haka suna nan a Teaching Hospital a emergency ward."
   "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, what?! Da wanne zanji yanzu? An shiga da Ya Al'ameen d'in OR ne?"
  "Eh Hajiya."
  "Innalillahi! Ka samu dama ka gansa kai?"
  "Yes Hajiya he is in a very critical condition he is bleeding through everywhere."
   "Subhanallah! Allah ya bashi lafiya Allah ya fito dashi yasa ayi a sa'a bari na leqa Zeezee mu koma chan d'in." Nan da nan ta shiga d'akin Zeezee inda ta tarar da ita se aikin kuka take. A gefenta ta zauna tare da had'a musu hannayensu. "Sannu Mama na sannu, ya jikin?" Kai zallah Zeezee ta gyad'a mata "Mama ina Ya Al'ameen? Please tell me its not true tell me ba a har6esa ba, and also my baby please tell me banyi miscarrying baby na ba. I can't afford to lose my family" tayi maganan cikin kuka sosai.

   "Zeezee ki kwantar da hankalin ki please kinga kema ba lafiya kike dashi ba, baby'n ki na nan lafiya ba abinda ya samesa."
  "That's not true Mama kawai kina fad'a min ne."
   "Am not lying to you Zainab ki ta6a cikinki kiji  your baby is fit." A hankali ta aza hannunta kan cikinta cike da fargaba, feeling bomb d'in yasa taji d'an sanyi a ranta "Ya Al'ameen fah? Please kar ki gaya min ya mutu Mama." Kuka take sosai, hugging nata Mama tayi "shhh! Its okay please anyi OR dashi in shaa Allah he is going to make it muyi mishi addu'a kawai."
   "A ina suka har6esa Mama?"
  "Zainab-"
  "Please answer me I need to know."
  "Zai-"
  "Mama please I beg you" ta k'ara rushewa da kuka.
  "A kusa da heart nasa ne Zainab."
      "Innalillahi! Mama I killed my Husband, na kashe Ya Al'ameen."
  "Kaman ya kin kashe sa Zeezee? Armed robbers su har6esa kice ke kika kashe sa."
  "Mama its all my fault, about 3 weeks now kullum ina cikin fushi dashi I failed to believe him daya cemin he wasn't cheating on me, I killed him also." Sake hugging nata Mama tayi "shhh! Ya Al'ameen be mutu ba kuma in shaa Allahu baze mutu ba kinji? Mu mushi addu'a kawai."
    "I can't afford to lose him Mama."
  "You won't in shaa Allah Zeezee, ina zuwa bari inje in duba shi."
   "Zan biki."
  "Kaman ya zaki bini Zeezee? Kema bakiga gado aka baki ba."
   "I don't care about myself Ya Al'ameen is all I care about."
 "No Zainab ba inda zakije kina nan so kike kije kiga condition da yake ciki abu ya samu lafiyan abinda ke cikin ki?"
  "Mama please karki hanani ganin Ya Al'ameen please."
  "Zainab-"
  "Please Mama." Hannu Mama tasa ta share mata hawayen nata sannan a nitse ta mik'ar da ita suka shiga takawa har suka isa izuwa ward d'in. Sadeeq na ganinsu ya miqe tare da basu waje don su zauna, "Sadeeq ina Ya Al'ameen?" Zeezee ta tambaya in a cracky voice. K'ofan d'akin kawai ya nuna musu "basu fito ba har yanzu?" Asked Mama.
  "Eh har yanzu."
   "Sadeeq how bad is his condition? Please karka min k'arya." Zeezee ta tambaya.
  "Critically bad, acikin jini suka wuce dashi he seemed so lifeless." Kwanciya kawai Zeezee tayi jikin Mama tana kuka sosai da k'yar suka zauna har anan Zeezee ta kasa barin kukan da take yi. Hajiya Babba ne ta kira Mama inda take tambayarta ya jikin Al'ameen nata, ana ruwa a KD bazeyi ta shigo ba please a kula mata da yaronta.
   "In shaa Allah Mama Babba kibar kukan haka please addu'ar mu kawai yake buk'ata."
  "Nagode Maman Zeezee Allah yabar zumunci."
  "Ameen ki gaida Hjy Sadeeyah."
  "In shaa Allah zataji, nima ki gaishemin Zeezee da jiki please ta kuma kwantar da hankalinta kar abu ya samu lafiyan d'an nata."
  "In shaa Allah zan gaya mata sannu."
  "Yauwa sannu se anjima."

   Few minutes more k'ofan d'akin da Al'ameen ke ciki ya bud'u. Kusan a tare suka dosa gun duk tashin hankali bayyane a fuskokinsu karara. "Dr how is he?" sukayi maganan dukansu uku in unisons.
   "Kune family'nshi?"
  "Eh" Mama ta amsa.
  "Am his wife and this is my mother" Zeezee tayi explaining "so tell me how is my husband doing inside there please, karku cemin ya mutu don Allah."
  "Zainab calm down please" cewar Mama.
   "Kuyi hak'uri amman bazan 6oye muku wannan lamari ba. Mijinki is in a very critical condition rai a hannun Allah yake, mude munyi abinda ya kamata bullet a cardiac walls ba abu ne ba na wasa. Mun samu mun cire bullet d'in amman har yanzu pulse nasa is not responding ya tsaya gu d'aya baya picking."
   "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Suka ambata a tare. Rushewa cikin wani irin kuka me tsuma zuciya Zeezee tayi tana sumbatu tana ta kashe mijinta a yayinda Mama ke calming nata down. "Kuyi hak'uri kuyi mishi addu'a wala Allah ko zuwa nan da gobe pulse nasa yana iya dawowa idan be dawo ba kuma... I'm sorry."
   "No! No! No! Please this can't be true it can't be. Ya Al'ameen can't die don Allah Dr do something baku iya aikinku bane da zaka cemin sorry? Kana nufin mutuwa zeyi kenan? Kasan ko waye shi? He is my husband the father to my unborn child, banason d'a na yayi witnessing a day without a father please you've got to do something and save him he can't die."
    "Kiyi hak'uri Ma'am I know how it feels amman ba abinda zamu iya ne, munyi duk abinda ya kamata sauran mun bar wa Allah."
   "No there is still something missing-" katse ta Mama tayi "thank you Dr mungode Allah ya biya."
  "Ameen excuse me please zaku iya shiga ganinsa." Har k'asa Zeezee ta sauk'a Mama na tarota tana kuka sosai. "He can't die Mama he can't yanzu shikenan baby na ya zama maraya kenan?"
   "Wayace miki ya zama maraya Zainab? Ce miki akayi Ya Al'ameen ya rasu? Yana nan da ransa fatan mu Allah tashi kafad'an shi, ki shiga ki gansa kinji?"
  "I can't Mama bazan iya kallonshi acikin wannan critical condition d'inba sanin ba abinda zan iya masa I can't."
  "You have to Zainab, Ya Al'ameen bayida kaman ki go inside kije ki gansa."
  "Please Mama."
  "Go Zainab jeki gansa." Jiki ba k'wari ta mik'e tsaye a hankali ta shiga takawa har ta isa cikin d'akin. Kasa juyawa ta kallesa tayi se hawaye kawai take unstoppingly. Da k'yar sannan ta iya ta juyan, sight nasa data gani dad'a mata volume na kukanta yayi, sosai guiwowinta suka shiga shaking har ta k'arasa kan gadon nasa. Oxygen supply nasan ta aza shaking hands nata akai sannan back to gashin kansa tana shafawa soothingly. Duk kalan treatement and bandage da kan ciwon nasa yasha be hana jini fita ba har yanzu, just how much have he suffered? In a cracking tune tayi stating "I'm so sorry Ya Al'ameen, I'm terribly sorry I should have believe you when you told me you weren't cheating on me, I'm terribly sorry please don't die kar ka tafi ka barni I need you, I love you our unborn child needs you please don't go." D'ayan hannunsa da babu connections jiki ta d'aga ta had'a da nata tana shafawa a hankali "please kar ka tafi Ya Al'ameen" a hankali ta aza hannun nasa akan cikinta, kaman baby'n nasu na jinsu se yayi kicking. Hakan ba kad'an yasa Zeezee kuka ba. "See? Our baby needs you, kar ka tafi ka barshi please you need to wake up." Kuka ta cigaba da yi wajen tana shafa gashin kansa a hankali. Chan ta d'ale gadon tare da kwanciya dage gefensa ta had'a musu hannu a haka har tafara bacci itama.

   Jin shiru Mama ta gwada lek'asu inda ta tarar da Zeezee kwance a gefensa tana bacci. Murmushi tayi at their site sannan tace "Allah baka lafiya Al'ameen Zainab loves you so much." A nitse ta miyar da k'ofan taje ta samu Sadeeq ya kaita gida inda ta taho masu da abinci tasan sarai Zeezee must be hungry.
    2 hours sleep Zeezee ta samu a gefen Al'ameen nata ta tashi. Se gani take as if idan ta kirashi da Sweetheart ze amsa ta cikin zazzak'ar muryansa yace mata My Princess, she is missing him over. Hawayen dake neman gangarowa kan cheeks nata ta tare da wuri "you've once told me to believe in our love, you promised to never give up on me Ya Al'ameen and I will be holding on to that promise nasan bazaka tafi ka barni ba please wake up." Ko motsawa beyi ba ga pulse nasa na nan yana hanging tun d'azu. "Sweetheart please wake up ko finger ne kamin shaking ko hankalina ze d'an kwanta wallahi idan ka tafi bazan iya rayuwa ba. I can't bear the thought that nice silar mutuwan Baba and now yours dan Allah karka min haka Ya Al'ameen I need you to wake up, wake up please." Suratan ta cigaba dayi tana kuka har Mama ta shigo d'akin ta tsinceta.
   "Yo! Zainab kin tashi kuma a maimakon kiyi sallah kike zaune gun har yanzu?"
  "Mama he is dying and I can't do anything to save him" ta fad'a cikin kuka sosai.
  "Ya Salam Zeezee" tayi maganan tana k'arisowa gefenta. "Kibar magana haka don Allah, waya ce miki mutuwa zeyi? In shaa Allahu ze tashi."
  "Mama da ze tashi da yayi, ba irin suratan da ban mishi ba he is not responding, duk ni ne, laifi nane. A kullum baya bin land se air amman nata tada mishi hankalinsa har seda ya gommaci yayi risking life nasa haka. Am very stupid to think that Ya Al'ameen will eve cheat on me, be kamata na sak'a mishi da haka ba despite all abubuwan da yayi min a baya. Da be biyemin ba ya cigaba da zamansa achan."
   "Bayan yadda kike tada mishi hankali Zainab? Sadeeq told me everything yakamata kina yima Maj-Gen uzuri kisani shima fa bawan Allan nan ba a son ransa yake tafiyan nan yake barinki ba, har ace ya kira Sadeeq yace ki amshi waya ki k'i Zainab? Haba mana! Dole hankalinsa ya tashi yace ko ta motan ne ze biya just to make you happy." Wani kukan Zeezee ta sake rushewa dashi "Mama please karki ga laifi na sonsa da nakeyi ne yasa bana iya juran rashinsa a kusa dani, kinfi ni sanin hakan tunda mutuwa ya d'auke miki Baba. But wallahi I hate myself right now koda missing nashin da nake be kamata ina nuna fushi na akanshi ba saboda be dawo min ba kamata yayi in rik'e aciki."
  "Exaclty Zainab."
  "We all learn from our mistakes in shaa Allahu zan gyara daga yau, Ya Al'ameen poor thing" tayi maganan tare da miyar da kallonta kan lifeless Al'ameen. "Mama I killed My Soldier."
  "Kika sake cewa kin kashe shi zan sa6a miki kina jina ko? Tashi kije kiyi alwala kiyi Sallah na kawo miki abinci."
  "Toh nagode." Bayan ta idar da Sallan Mama ta sata cin abincin dole ta gama sukayi zaman amsan gaisuwa ta waya, se kira mutane suke sunayi wa Al'ameen fatan samun waraka.

    Ko wani minti-minti idon Zeezee na akan Al'ameen tana son taga first move nasa amman har ta gaji da checking on him be motsa ba, hakan ba k'aramin sake karya mata zuciya yayi ba. Idan Al'ameen ya mutu ina zata sa kanta? Nowhere. Da misalin k'arfe tara Zeezee taje ta samu Mama a wajen corridor, "Mama bazaki tafi ba dare fa yayi, bari inma Sadeeq magana ya mai dake gida."
   "Are you sure Zainab zaki iya kula da kanki da kuma Ya Al'ameen kema fa kinsan bakida lafiya I was thinking I should spend the night with you."
   "Ayyah no need, I'll manage Mama you've done so much for me, please kije ki huta."
   "Toh shikenan duk abubuwan da zaki buk'ata akwai anan?"
  "Eh nasa Sadeeq ya kawo min d'azu."
  "Okay toh Allah bashi lafiya kuma kibar kukan haka nan kema ba ishasshen lafiya gareki ba."
  "In shaa Allah Mama thank you." Har wajen mota ta rakata sukayi sallama sannan ta dawo ciki ta canza kayanta zuwa na bacci sannan a hankali ta d'ale gadon ta kwanta gefen Al'ameen, hannunsa ta d'aga tare da azawa kan cikinta kamar yadda ya saba yi idan zasu kwanta. Tana hawaye tsilli-tsilli har bacci yayi awon gaba da ita.

    Abu fa kaman wasa har washegari pulse na Al'ameen be soma beating ba, kuka kam Zeezee ta shasa kaman ba gobe. Da misalin k'arfe 7pm Mama ta kira Zeezee wanda da k'yar ta iya picking saboda yadda kuka yafi k'arfinta. "Assalamu Alaikum Zainab?"
  "Wa alaikumus salam Mama" ta ansa da k'yar cikin kuka.
  "Subhanallah Zeezee meke damunki ne wai? Kuka kike har yanzu?"
  "Mama he is dying his pulse is not picking up har yanzu, please do something bazan iya rayuwa ba shi ba."
  "Lets have faith Zainab in shaa Allahu ze tashi. Kibar kukan haka please, kinji?"
  "Uhumm."
   "Ki turo Sadeeq ya amso miki breakfast."
  "Bana jin yunwa."
  "Idan ke bakiya ji d'an naki naji kice Sadeeq yazo ya kar6a miki kinji? Kuma ki dage kici koda kad'an ne."
  "Toh nagode."
  "Yauwa zuwa anjima zan shigo."
  "Sekin zo." Anan sukayi sallama. Kallonta ta miyar kan lifeless looking Al'ameen ji tayi tana sake tsanar kanta, yanzu saboda he just wanted to make it up to her shine yayi sacrificing life nasa? Why is he to good?

    Wajajen 9am Dr da kansa yazo ya duba Al'ameen yake sanar da ita ba any improvement tattare dashi his pulse isn't beating har yanzu. Kuka ta shiga yi musu a wajen tana had'asu da Allah da su ceto mata ran miji. Har Mama dasu Lubiee suka zo suka koma still Al'ameen be motsa ba KD har yau weather isn't clear su Mama Babba
basu samu tahowa ba.

***
    Bayan sallan La'asr Zeezee na zaune akan sallaya se faman addu'a take tana kuka taji pulse machine d'in yayi making sound da hanzari ta miyar da kallonta wajen to her biggest suprise taga daga 40 ya buga ya dawo 39. Meh hakan ke nufi? Mutuwa kenan Al'ameen nata zeyi? Abinda ya kamata yana gaba-gaba taya zeyi baya? "Nurse! Nurse!" Ta sa ihu da iya k'arfinta har seda tayi drawing attention nasu a lokacin pulse d'in har ya sauk'o zuwa 34.
   "Nurse what is wrong with him please? Meyasa pulse nasa yake decreasing instead yayi increasing? Don't tell me he is dying please."
   "Sister please take her out" cewar Nurse d'in wa 'yar uwarta. In a minute Dr ya iso yana sanya gloves a hannunsa.
   "Take her out please" ya buk'aci nurses d'in. "Ma'am we are sorry."
  "Ma'am please lets go." Cewar nurse d'in.
  "No I'm staying here tun jiya kuyi mishi abinda ya kamata kun k'i seda kuka ga ya kusa mutuwa zaku nemi basa taimako? What is wrong with y'all people ko bakusan aikin ku bane? Mijina ne fah."
  "We are sorry Ma'am lets go outside please." Da k'yar aka samu aka jata waje inda take leqe ta window tana kuka sosai. Se sauk'a pulse na Al'ameen yake har izuwa 17. Pulse Dr ya shiga basa sede inaa heart nasa yak'i beating se ma dad'a decreasing da pulse d'insa ke. Kusan sau uku sunayi ba improvement sukayi giving up finally. Ding-ding pulse machine yake bugawa 7.. 6.. 5.. 4.. 3... 2..1. Se ya d'auke. Wani irin ihu Zeezee ta k'urma seda ta jawo attention na kowa a arean gun.
   "Ya Al'ameeeennnnn!!!"
   "Time of death 4-" Dr be kaiga k'arisa karance time d'inba Al'ameen ya kad'a index finger'nsa kad'an wanda Zeezee tagani da idonta. Pulse nasa ne kuma ya shiga beating fast-fast ding-ding 1.. 5.. 9.. 10.. haka ya cigaba dayi to everyone's suprise. Zeezee na hawaye tana murmushi all at thessme time sanda ya kai 99 sannan yayi stopping. Wani hamdala ta saki tana murmushi, ta window'n Dr'n ya d'aga hannu yayi mata thumbs up. Drip suka sa mishi sannan suka cire oxygen supply d'in, nishi yake a hankali sede har yanzu be bud'e idonshi ba.

    "Am so happy for you Ma'am your husband's condition is now stable." Dr Ya sanar da ita yana cire gloves na hannunsa alokacin daya fito daga d'akin.
  "Thank you Dr, thank you so much I won't forget this."
   "You're welcome."
  "Zan iya shiga ganinsa?"
  "Why not excuse me please." Yana ficewa tasa kai cikin d'akin inda a hankali taja kujera ta zauna gefen Al'ameen tana k'are wa kyakkyawan fuskansa kallo. Fingers nasu tayi interwining a yayinda hawaye ke forming rapidly a idonta. Miqawa tayi tare da kissing forehead nasa.
   "Thank you for choosing not to leave me My Soldier, da ka tafi da bansan ina zansa kai na ba. Thank you for keeping your promise with me, I can't ever repay you. I love you so much please shake a finger for me again." Hannunsa ta tsaya gani amman ko motsawa beyi ba.
   "Sweetheart idan har KAN TARE DA NI please shake a finger again, just a finger kaji? Your Princess loves you so much, I'm here, I'll never leave your side because I love you so very much, just shake a finger for me its all I need now." Idanunsa taga sun d'an motsa kad'an kaman ze bud'e se ya sake miyar dasu, hakan ba k'aramin farin ciki ya sanyata ba. "I know you'll never fail me My Soldier" a hankali ta miqa ta sake kissing forehead nasa in the process drop na hawayenta ya d'iga akan idonsa kafin tasa hannu tace zata goge taga a hankali Al'ameen na bud'e idonsa har ya bud'esu gabad'aya yayi setting nasu akan fuskanta. Even though blurred images yake kalla hakan besa yayi noticing ramewan da Zeezee tayi ba in just a day.

   "My Soldier!" ta furta unbelievably tana hawaye sosai, "My Soldier you're back!" Kwantar da kanta tayi bisa chest nasa ta inda ba a har6esan ba tana kuka sosai. "I'm so sorry Sweetheart, I'm terribly sorry for making you pass through so much pain like this ka yafemin please." Cikin wani irin dishasshiyar murya kaman ba nasa ba ya furta "Princess" a hankali. A take ta taso tana kallonsa "I'm so sorry Sweetheart." Kai ya kad'a mata "cry nomore" hannunsa ta side dake da lafiya ya d'aga a hankali ya shiga share mata hawayen nata. Kallonsa kawai take amman ta kasa dena kuka.
  "Why did you do it Sweetheart? Mesa baka hak'ura ba se idan wheather ya gyaru ka taho ba? Why do you have to risk your life like this?"
   "Because I want to make it up to you Princess, banason inji kina cewa I am cheating on you, I'll never cheat on you Zainab ke kad'ai nakeso and no one else. Ranan da kika fara cemin I was cheating on you kasa bacci nayi ranan, I can't bear the thought that na baki room na zargi na, can you please believe me yanzu that am not cheati-" yatsan ta tayi sauri ta aza akan lips nasa shutting him. Cikin tsan-tsan hawaye tana me nadaman abubuwan da tayi wa Al'ameen tace, "I'm terribly sorry Ya Al'ameen, please ka gafirceni for acting childish to you. I should have believed you da kace min you weren't cheating on me I'm sorry I just couldn't help it, it's because I love you so much, se gani nake like kana min wasa da hankali ne da kake ta cemin zaka shigo amman baka shigowan."
   "I'll never do that to you Princess I love you eternally it just that na kasa bringing kaina in sanar dake halin da na tsinci kaina a ciki ne, meya sameki kika fad'a haka are you sick?"
  "Ya Al'ameen I thought mutuwa zakayi ka barni" tayi stating hawaye na forming a idonta. "Pulse naka gabad'aya yabar beating I couldn't help it bazan iya rayuwa ba kai ba."
  "I'll never leave your side in shaa Allah kibar kukan haka kinji? Am here for you and for our little Princess and more to come Baby machine." Murmushi kad'an ta mar;
   "Thank you for not leaving me." Murmushin dake fuskarsa taga ya gushe, da sauri ta tanbayesa "Ya Al'ameen is everything okay?"
  "Princess sun tafi da motan, I shopped for you and my Little Princess I thought I might suprise you sun tafi da kayakin, I'm sorry."





*MIEMIEBEE.      TEAM #YGC!🎀*
Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄

No comments: