*BY MIEMIEBEE*
Page 49
FEBRUARY, 2017
_Assalamu Alaikum Readers/Fans. I know kuna hak'uri but ku k'ara please. Am very occupied ne these days bana samun time na typing thats why kuka jini shiru two days and zaku cigaba da jina shirun for some days ahead now till everything gets back to normal. Thank you for your maxi support, care and love. I heart y'all to pieces. Team *'YAR GATA CE!๐* OneLove๐_
"Naji Mama."
"Zaka shiga ka ganta ko na soma ganintan?"
"No kishiga tukuna after you."
"Se hak'uri Allah kawo rayayye." Da nod daya mata ta shige d'akin inda ta tarar da Ruky banda kuka ba abinda takeyi.
"Haba kekuwa kukan me kuma? Fatanmu Allah sa me ceto ne kukan ya isa haka."
"Mama I didn't get the chance to hold my baby, banida burin dayafi in riqe d'ana in shayar dashi Mama ya koma baya sona."
"Yana sonki Ruky shiyasa ya koma saboda yana son ya ceceki ranan qiyamah. Na miji ne ko mace?"
"Na miji Mama" ta sake rushewa dawani kukan da k'yar Mama ta samu ta lalasheta sannan ta shigo da Adeel ita kuma ta basu waje. Seda ya k'are mata kallon bakwai saura kwata sannan yace;
"Kin sani ba a haka kad'ai Allah ya rabaki da d'anki bako? Be greatful ma be had'a da naki ran bama ya tsaya akan abinda kika haifan."
"Adeel wace erin magana kakeyi? Yanzu abinda zaka fad'amin kenan bayan abinda ya sameni?"
"Da ta'aziyya kikeson na miki? Kisani kin cuceni a rayuwa Ruky kuma I shall never forgive you for what you did. Haka kawai kika sa na saki Zeezee saki biyu bama d'aya ba gashi nan kema abinda nake expecting daga garekin shima na rasa."
"Ya kake magana kaman laifi na ne ni kad'ai? Kaima ai ka rasa d'anka kuma da alhaqinka kaima, da tun farko ka nunamin Zeezee nada mutunci a idonka da duk hakan be faru ba."
"Aww haka ma zakice?"
"Eh mana kai ka fara bani room ai saboda haka kadena blaming d'ina fault ne dukan mu munada laifi."
"Yayi kyau in kin gama abinda kikeyi anan seki koma gida ni zan wuce bikon Zeezee."
"Gidan Babana zan koma sena warke sannan na dawo, gidanka da ba komi aciki me kakeson inaci har in warke?" Be sake cewa da ita komi ba ya fice nan fa Ruky tasa sabon kuka.
Gidansu Zeezee direct Adeel ya nufa sarai yasan in ya shiga ciki direct there will be trouble, bama wannan ba yanzu how sure is he Zeezee na gida? Rashin wannan amsar yasa ya kira Lubiee don ji daga bakinta. Seda ta gama ja mishi class sannan a karo na biyu ta d'aga tare da jan tsaki sekuma ta katse. Da ace ba neman abu Adeel ke a gunta ba yau da sena lahira yafita jin dad'i. Shegen zuciyansa ya ajiye a gefe ya sake trying nata about 3 missed calls se ana hud'u ta d'aga tare da fad'in "Malam fa kana taqura min yada kira haka?"
"Lubiee mesa bakida mutunci ne?"
"LOL mutunci? dama kasan da zaman wannan kalma kayiwa Zeezee abinda kayi mata?"
"Lubiee please that aside we can't ammend the past ni just tell me aina zan samu Zeezee yanzu?"
"A kaina tunda kabani ajiyarta maci amana kawai."
"Wai meke damunki haka?"
"Rashin mutunci" ta amsa a takaice.
"Sena rok'eki zaki sanar dani? I will tunda am in need please ina zan samu Zeezee?"
"You'll be the last person to come to know where she is daga bakina don wallahi Adeel ko mutuwa zakayi I won't let you know, she's had enough finally Allah ya hutar da ita daga monster erinka sannn kace in gaya maka inda take, for what? Saboda kaje ka sake hargitsa mata rayuwa? You are sick you know."
"Kina da daman zagina the way you want tunda nayi hurting miki best friend but kisani I really want her back."
"Aww really? I should have guess, kana neman cooku, me shara da wanke-wanke harma dame wanki da kuma sex machine ai dole kace you want her back to kasani Zeezee tayi maka nisa wallahi ko a mafarki bazaku sake had'uwa ba nayi regretting had'aku tun farko."
"Are you telling me where she is or not?"
"I'd rather die" tace dashi tare da katse wayar. Kansa ya riqe gabad'aya out of idea yanzu aina ze sami Zeezee? Fita yayi daga motan tare da yin sallama dawasu 'yan unguwa koji daga bakinsu ko Zeezee na gida sede duk cemasa suke basu ganta ba da k'yar tana gida. Tambayan ya tayi don kansa ya gaji ya koma gida inda ya d'au wayansa don trying number'nta. Yamata about 10 missed calls amman taqi d'agawa bawai kuma bata kusa bane actually wayan na a gefenta d'agawan ne bazatayi ba cause she don't think akwai wani abinda ze sake shiga tsakaninta da Adeel. Chan da yamma Lubiee ta kirawota suka gaisa sede sam Lubiee bata nuna mata Adeel called her ba saboda bata son dawo mata da memory'nsa bayan she is now moving on.
A daren ranan Adeel ya kasa bacci, ko kiran Ruky yaji ya jikinta ma beyi ba, jana'izan d'an nasa kawai yaje ya dawo se trying line na Zeezee yake amman bata picking chan dabara ya fad'o masa. Landline ya d'aga ya kirata dashi and ba tare da takawo tunanin komi a ranta ba ta d'aga tare da yin sallama. Seda ya sake jin zazzaqar muryarta yasake sanin yayi missing nata. Ma kasa amsa sallaman yayi seda ta sakeyi for the second time. "Wa'alaikumus salam Zeezee."
Bazata ta6a mancewa da wannan murya ba, take jikinta yahau rawa "Adeel?" Ta furta tana shakka.
"Zeezee- " sekuma ta kashe wayar akanshi "hello Zeezee? Zeezee?" Trying nata ya shiga yi amman ina bata picking, daga k'arshe ma kashe wayar tayi still be haqura ba ya tura mata saqo kamar haka;
_Zeezee please stop shutting me down we need to talk I really need you back so badly, Ruky ta haihu yau, na miji but ba rai I know hak'k'in abubuwan dana miki bisa rashin sani ke bina har ma da ita Ruky'n, I came to know that k'azafi ta miki regarding that event please pick up my call I love you_
Bata samu daman karance message d'in ba se a washegari da Asubah bayan ta idar da Sallan Asuba ta gama azkhar nata. Tana gama karancewa ta goge bata son sake ji ko ganin abinda ze sa ta da Adeel in contact she've learnt her lesson suje chan su k'arasa da Ruky'nsa ta gwammaci tagama rayuwarta a haka data koma d'akin Adeel. Ganin fa Adeel ya dameta da kira ta cire sim d'in gabad'ai ta karya se anan ta samu shan iska.
Acikin sati biyun da Adeel yayi ba Ruky ba Zeezeee ba k'aramin damuwa ya shiga ba, abinci sede kullum yaje gida yaci. Tun rabuwansa da Ruky a asibiti kuwa kota kanta be sakeyi ba. Yau Asabar Mamanta tasata ta shirya kayakinta tsaf sannan tayi dropping nata da kanta. Layin Adeel ta kira kasancewar k'ofar a rufe take, seda yagama 6ata mata lokaci sannan ya fito ya bud'e mata ko sannu da zuwa beyi mata ba ya koma ciki a yayinda take binsa a baya. D'aki ta nufa ta ajiye akwatinta sannan ta fito parlour ta tarar dashi zaune kan kujera se faman tunani yake.
"From all seeing Zeezeen taka bata dawo ba, ashese tanada wayo." Banza da ita yayi hakan yasa ta cigaba "ai dama ba wawiya bace da zata dawo maka yanzu da bakada komi konima don yazama min dole ne."
"Kinsan me Ruky? In baki ja bakinki kin min shiru ba zaki kwashi hak'waranki a k'asa. Saboda kinga ina barinki a baya ne kisani that was because bakida lafiya amman yanzu da kike garau faffasa miki baki zanyi."
"LOL incredible! Nikuma ce maka ayi zan tsaya ina kallonka kamar yadda Zeezee keyi? Ai ba qarya nayi ba bakada komi yanzu se uban pride d'in banza." Har maqora ta kaisa a zuciye ya nufi gabanta tare da yi mata wani irin riqo a hannu wanda tuni tasa d'ayan hannunta tana k'ok'arin jan kanta. Kasancewar a k'oshe take tuni tasamu ta fincike hannunta daga riqon dayayi matan "koda wasa wallahi kada ka sake riqemin hannu haka ka kallen da kyau ba Zeezee bace Ruky Mama ce."
"Ignorant fool" yace da ita sannan ya d'au wayansa ya nufi d'akinsa shi inbanda Zeezee ba abinda yakeso. Da yamma me aiki ta kawo masa abinci as always kasancewar Mami batasan Ruky ta dawo ba. Alokacin yana zaune a waje yana shan iska yajiyo qaran bell da kansa yaje ya bud'e ya anso abincin sannan yayi ciki dashi.
Tsaye a gefen fridge tana shan ruwa ya tarar da ita ko k'ala be cemata ba ya sauqe abincin sannan ya d'iba duka bebar komi ciki ba "ina nawa nikuma?" ta tambaya.
"Naki? Bakida hankali ashe."
"Kamar yafa?"
"Ki dafa da kanki ai gaki ga kitchen."
"Lallai ko zaka sha mamaki" bece mata ko k'ala ba ya nufi d'aki. Kitchen d'in ta shiga tayi garnishing had'ad'd'en spaggetti amman rabin leda yadda ita kad'ai zata iya cinyewa. Koda Adeel yazo fita daya ganta be mata magana ba acewarsa dukansu ta girka musu harda kiran Mami ya sanar da ita ba seta sake kawo mishi meal ba Ruky ta dawo.
Se kusan to 8pm ya dawo gida all exhausted. Dining direct ya nufa ya bud'e flask se gani yake ba komi ciki an sud'e tas kaman ance d'ago kanka ya d'aga se ganin Ruky tayi tana picking hak'orinta da alama yanzu tagama cinyewa.
"Ina nawa?"
"Yana kitchen kaman yadda ka fad'i min d'azu nima" ta ansa ba tare da nuna damuwa ba.
"Ina nawa nace dont play games with me ba d'azu kinyi girki ba."
"Eh nayi ga flask nan ai a gabanka."
"Then ina nawa?"
"Ban girka ba." Ta miyar masa.
"As in how?"
"Eh toh nayi girki amman ma kaina kad'ai kai ba kanada uwar dake sonka tana kawo maka ba seta cigaba dayin hakan ta huta sheni nima."
"Ruky ki kiyaye ni wallahi karki ganki 'yar buskud'a kiga wai bazan iya baki kashi ba."
"Ai bazama ka iyan bane is better kabar cika baki."
"Mschww wuce ki dafa min koda indomie ne."
"Bazan girka ba wai a jinka na mance da kalan wulaqancin dakamin ne lokacinda na haihu? Ai wallahi seka bani haquri mukoma shiri."
"Lallai ko zaki bushe kaman k'anzo inde ni kike jiran na baki hak'uri."
"Shikenan kaima bushewan zakayi idan ni kake jira na dafa ma abinci" bata jira jin me zece ba tayi d'aki abinta. Ji yake kaman ya bita ya nad'a mata na jaki amman ina yasan hakan bame yuwu bane yadda take 'yar buskud'an nan yayi wasa seta zauna a ruwan cikinsa gasa d'an siriri. Haka da kanshi ya dafa indomie'n zuwa 10 haka ya gama abubuwan da zeyi ya je ya sameta a d'aki tana shirin kwanciya itama.
"Ke bakisan kibawa mutum haqqinsa bane?"
"Nifa bazaka lalatamin jiki ka mai dani sex machine ba, kabarni in huta tukuna."
"Ki huta ba sadakin ki na biya ba?"
"Semeh dan ka biya? A'a wallahi Mallam bazaka tsufar dani ba."
"Banza ma dake inba don a rashin Zeezee ba shan ma zan nemeki ne?"
"Eh ai komin rashin dad'i na nafi babu dai ko? Kuma haka zaka kwana da sha'awarka, don ni ba abinda zaka samu daga gareni" ji yake kaman ya danne ta yayi mata na qarfi amman wane shi? Yace ze biyemata har gadon asibiti ana iya kwantar dashi akai. Allah sarki se kawai ya tuna da Zeezee yadda koda she's not in the mood haka don ta farinta mai rai zata basa kanta yayi duk abinda yakeso ba tare da tace mai tagaji ba kokuwa bataso ba, amman wannan fitsararriyan da bata ma kai Zeezee d'and'ano ba se uban iskanci ai sa'arki d'aya wannan girman naki ya fad'i hakan a ransa ina ma ace a lokacinda take amarya ne. Amman yanzu tunda ta haihu tasake bud'uwa ta qara k'iba. Hakanan ranan ya kwana da zalamansa.
Rayuwarsu haka ta cigaba da kasancewa, Ruky yin abinda taga dama take Adeel ko be isa ya mata magana ba cause shikansa ma tsoronta yake. Girki ma idan tayi na safe dashi na rana seta k'i haka sede in ya biya gidan friends nasa yaci. Bayan nan kuma ga habaicin da zata zauna tayita yi tana zaginsa batun rashin aikinsa. Haka ma se lokacin da taga dama take basa kanta, Adeel can't tell just how much he is missing Zeezee. Ahaka ne har abun ya ishi Adeel don kuwa shi kansa be saba ba da zama ba kud'i don haka ya shiga neman aiki inda rabonsa ya ratse yasamu a NGO albashinsa a wata dubu d'ari biyu da hamsin. (250k)
Yana amsan first salary'nsa ya kashe almost all of it wa kansa akan kayan sawa saura kuma yayi cafenin abinci dashi, besani ba amman kallonsa kawai Ruky take. Bayan ya jibge kayakin akan gado ya nufi bayi ya watsa ruwa sannan yafito da full confidence nasa don za6an d'aya daga cikin kayakin yasa ya tarar da kan gadon wayan!
"Ke ina kayaki na?" Ya tambayeta in a serious tone.
"Tukun nan ka gyara kanka ba KE anan."
"Kinsan ba sa'anki neni bako? Karkiga don ina d'aga miki k'afa kid'au wai bazan iya zaneki bane."
"LOL harka ban dariya, I would love to see you try."
"Mschww ina kayakina?"
"Na 6oyesu." Ta fad'a confidently.
"Kin meneh?" Ya tambayeta not believing.
"Ka jini ai na 6oye nace."
"Kayan k'aninki ne da zaki 6oyen? Fito min da abuna."
"Nak'i." Ta buga kafad'a.
"Ruky kifa sani I am not your mate."
"Ai dama ba cewa nayi ba kai sa'a nane. Kayaki nede na 6oye bazan fito dasu ba."
"Dalili?" Ya tambayeta yana cike, ji yake kaman ya goga bakinta jikin bango."
"Aww har ma tambaya na kake? Rabonka dakamin d'inki since when? Kai kanka bazaka iya tunawa ba, yanzu kuma da arziki ya soma shigowa instead kayi mana siyayyan tare a'a kai anyi maka wahayin selfishness and greediness you can't ka kama kacika kusan akwati da sabin kayaki toh wallahi niba wawiya bace da zan yarda, konima ka bani kud'i inje in sai nawa kokuwa bazaka sake ganin sabin kayakinka ba."
Lallai ma ya furta a ransa cike da mamaki jibi yadda take mai magana kaman wani d'an cikinta. Fusata yayi besan a lokacinda ya damqota ba da hannu "ni kike gayawa magana?" Da k'arfin da Allah yabata ta waina hannun nata ai tuni Adeel ya sake danko idan Ruky batayi biyun Zeezee ba tayi kusan hakan.
"Kalleni da kyau idan banyi biyun Zeezee ba nakusan yin hakan bale kace zakayi maltreating dina kaman yadda ka saba mata. Koda wasa don't you dare try this again."
"Mschw! Kinyi asara wallahi bani kayakina."
"Nima kabani kud'i na sai sabo." Ba yadda Adeel beyi da itaba ta basa kayakinsa taqi if only ze iya dukanta dataci k'aniyanta. Haka don dolensa fa seda ya irga 20k ya watsa mata aikuwa taqi amsa seda ya qara goma akai nanma taqi wai seya biya ta kud'in cefanen data musu da a baya.
"Kaman ya kud'in cefane? Anniyan ina ce ke? Cafenin k'aniya! Bani keyin cefani ba?"
"Da ka samu aiki yanzu ba" tayi maganan tana irga kud'in daya batan incase yad'an zare saura. "Ka gayamin kafin ka samu aikin wakeyin cafenin gidan?"
"Girkin da ko kinyi sekin ga daman samin d'in kikeson na miyar miki da kud'in ki yanzu? Lallai ki sake tunani yarinya."
"Ai kaima ka sake tunani wallahi dan seka miyar min da kud'i na." Shareta yayi ya zaro jeans and shirt nasa sabi yasa duk anan kallonsa take seda ya gama feffeshe turarukansa sannan tasha gabansa "Malam my money."
"Ki matsa min" yayi stating in a serious tone.
"Nak'i" ta tanka ba tsoro. Tunkud'eta yayi sede kaman gunki tana tsaye wajen "ai wallahi ba inda zanje ina nan seka biyani kud'in cefanin danayi da a baya."
"Me k'iran yarabawa kawai" yace da ita disgustedly.
"Whatever kud'i nede se ka bayar kokuwa ba inda zaka." One more hiss ya mata sannan ya irga 5k ya watsa mata se anan ta matsa mai ya fice. Kaman kullum ma yau ya nufi unguwansu Zeezee yayi parking a dai-dai tsakar unguwan inda yana iya hango almost all of the activities taking place there. Shikansa besan dalilin sa na zuwa nan kullum ba all he is adamant of is that komin jimawa zega Zeezeensa wataran saboda jikinsa na basa anan d'in Zeezee take. Ba yadda beyi da Lubiee ba ta sanar dashi inda Zeezee take amman tak'i, bataga dalili ba. 5pm na bugawa yaja motarsa yakoma gida.
5:14pm Zeezee tafito kanti don siyan kati inda take a layin shagon taji wasu maza a bayanta suna gulmanta ko dagangan suke don taji ko basu san itan bace masani se Allah.
"Ina Zeezee'n gidan Alhj Isma'eel danake maka magana akai the other day d'innan?" Cewar d'ayan.
"Eh wacce kacemin yarinya ce sosai amman auranta biyu duk sun mutun nan ko?" D'an uwan nasa ya amsa sa. Hakan yasa ya cigaba;
"Exactly!" Yayi exclaiming "aitoh bakasan meh ba, jiya Mustapha yake cemin wai ya ganta a gidan matar Uncle nasa yana sonta."
"Kai haba deh! Yanzu har akwai mutumin da zaiso zaman aure da yarinyar nan? Lallai!"
"Tayani ji deh, wai ta masa kyau."
"Kyan banza kyan maciji, ace yarinya wai ko ashirin bata kai ba da aure biyu suma wai du sun mutu, haba mana!"
"Kuma ai bakasan wani abu ba uban nata ne silan komi shiya sagaltata ta 6aci hakan."
"Toh Allah shi kyauta ya raba 'ya'yanmu da iyayen banza." Kasa rik'e kukan nata tayi kawai ta juya a guje ta fice se anan d'ayan ya saki baki yana binta da kallo "kai! ba itace Zeezeen ba?" Nan wanda ya soma kawo maganan yace, "dafa? Ai sanin tana nan na d'auko zancen don taji tasani kyau ba komai bane inba hali."
**
Tana isa gidan Mrs Mukhtar inda ya zame mata tamkar gidansu ta nufi d'akin da aka bata, ashe Mrs Mukhtar taga shigewarta ciki ga dukkan alamu kuwa ba lafiya ba don haka ta bi sahunta. Zeezee najin motsin ta tayi sauri ta shiga share hawayenta amman sede ina takasa hanasu zuba.
"Subhanallah! Kukan me kike haka Zainab?"
"Babu" ta furta a hankali covering her face.
"Ya isa toh yi hak'uri kinji? Komi meh wucewa ne wataran se labari."
"Aunty na riga na 6ata rayuwa na ashe duk mutanen da muka ga sun d'auke k'afa daga nema na 'yan unguwa ke basu tarihi na."
"Inji waye Zeezee? Karkice haka."
"Aunty yanzun nan naji da kunne na, shikenan ni haka zan qare rayuwana cikin k'unci da bak'in ciki sam ban kyauta wa kaina ba wallahi."
"Karkice haka Zeezee always have in mind that Allah na tare dake."
"Nasani Aunty amman abinda nayin ne yayi yawa, if I'll be granted one wish right now it'll be na koma gidan Ya Al'ameen I miss him so much" sekuma ta rushe da kuka. Hugging nata Mrs Mukhtar tayi tana bubbuga bayanta "Zeezee is high time ki cire Ya Al'ameen daga zuciyarki, banason kizo kizama disappointed daga baya its been morethan a year yanzu bamu sani ba ko bawan Allan ya sake aure. Ke de ki dage da addu'a in Maj-gen rabonki ne still zaki koma d'akinsa amman kidena bi a rai kinji? Inko ba haka ba Allah ze kawo miki wani na garin da ze kula dake."
"Naji Aunty, amman ni bazan sake welcoming wani na miji a rayuwa na ba" Zeezee tayi maganan tana d'agowa daga jikin Mrs Mukhtar "nagode Aunty barin kar6eki girkin."
"A'a no kibari zan gama da kaina ki huta abinki kinji?"
"Toh nagode" nan Mrs Mukhtar ta fice nan Zeezee ta koma aikinta na kullum wato tunanin masoyinta na haqiqa Ya Al'ameen . If only tasan ina zata samesa da taje ta samesan ta fayyace mai abinda ke ranta takuma nemi gafarsa. She don't care koda fad'a mai tana sonsa ze rage mata self esteem and dignity saboda she loves him so much ba wanda takeson ta kasance dashi kaman Al'ameen bayan iyayenta. Tunanin Adeel kuwa koda wasa batayi roqon Allah tayita yi Allah ya yaye mata son da take mai gabad'aya saboda Adeel bashida wani amfani a rayuwarta yanzu koda shine autan maza ta yafe shi.
****
Sanin koda ya (Adeel) wuce gida yanzu, Ruky bata dafa abinci dashi ba saboda zatace tayi lunch bazata yi dinner ba yasa ya wuce gidan Maminsa kawai. Achan tayi serving nasa dinner suna cikin ci ta lura da yadda Adeel is lost in his thoughts. Gyaran murya tayi still be motsa ba.
"Auta?" Tayi patting shoulder nasa. Ad'an razane ya d'ago kai daga kan plate nasa yana kallonta.
"Yes Mami."
"Meke damunka Auta? Tunanin me kake? Meke damunka?"
"Babu" yayi mata k'arya.
"Kamar ya babu? Kai da matarka ne?" Kai zallah ya kad'a mata.
"Toh dawa?"
"Mami I miss Zeezee, I want her back."
*MIEMIEBEE. Team #YGC!*
Beeenovels.blogspot.com
๐๐๐๐๐๐๐?
15 comments:
Godia muke sis, Allah ya kara basira
Gogia dubu miemie
Enx sis Adeel dis ix just d beginning ooo! Xeexee we ar with u, ur pains shall never go in vain.... Break a leg dear, miemie we ar gonna wait nd support u nw nd always dearie
Wow am so happy for zeezee.... miemie we''ll be praying for you insha Allah.... hope you'll be back soon. Allah ya saka ki a aljannah
Thnks miemie
Ameen thank you so much Dear
Ameen ameen thank you ๐
Tnx miemie. More ink to your pen. Allah yasa talaucin adeel bai fara ba sai bayan zeezee tabar gidan. Da ya siyar da motan ta
As always Miemie,kina iya kokarin ki ta entertaining din mu. Mungode, and GoodJob��, u're amazing. Allah shi biya, kuma Ya taimake ki a cikin al'amuran da suke delaying dinki, wanda yasa turo mana da sauran labarun suke on traffic. Blessings to ur brain with more ideas. Ameen. Thank you
Hhhhh...Adeel na cigiyar ZeeZee, ZeeZee na cigiyar Mag-Gen. That's more like it. What goes around comes around. Who loses, and who wins... Allahu Hafiz.
yo ai hikenan tnx meebee
Amin thank you❤
Thanks miemie Allah kara basira
Thanks Mariam, Allah ya karo kwazo da basira
Thanks Mariam, Allah ya karo kwazo da basira
Thanks Mariam, Allah kara kwazo da basira
Post a Comment