Monday, 20 February 2017
‘YAR GATA CE!
*BY MIEMIEBEE*
*Febraury, 2017*
5️⃣0️⃣
_Yo! Assalamu Alaikum Beautiful ones, I know I've been keeping you guys in such a suspence and for that MIEMIEBEE is sorry. To those who think they know me, well I don't think you know know me if you don't know that *Aunty Sis* and *Lubabatu Maitafseer* are my buddies😻. You guys are just simply amazing, my life is a blast with you two. Know that I love you so much and that may ALLAH SWT guide us together and may we continue to prosper. I'm indebted to you two. This page is in you honors, TheThree❤#youKnowWhatIMean😂🤳🏻_
Tooohh" Ta saki baki cike da mamaki. "Auta kasan da haka ka buga mata saki biyu lokaci guda?"
"Mami wallahi sharrin shaitaan ne, I didn't mean it wallahi ina son Zeezee."
"Ruky fa?"
"Mschww!"Yaja k'aramar tsuka "ina miki maganan mutane kina kawomin na beyerabiyar can."
"Oh! Da Alama gida ba lafiya kenan, toh kaje kayo bikon Zeezeen mana."
"Bansan ina take ba naje gidansu bata nan da alama Dad nata be yafe mata ba har yanzu, bansan ina zan sameta ba her line is not going through."
"Tooh kuma... ka tambayi Lubiee mana." Tayi suggesting.
"She will not tell me tana ganin naci amanar best friend nata she'll never tell me."
"Ko na kirata ne?"
"Zaki 6ata lokacinki ne I know Lubiee batayin abu se in tayi niyyah."
"Toh Auta ka cireta daga ranka kawai ka rungumi k'addara."
"I can't Mami I love her." Ya fad'a a tsawace.
"Kai don Allah free me bafa ni nace ka sake taba, kunje kun samu misunderstanding da matarka zakazo kana sauqe min fushinka."
"Everywhere is just hell!" ya buga plate nasa kan table d'in "na tafi." Ko seda safe bata mai ba tana kallonsa har ya fice. Getting to 9 ya isa gida bayan yayi parking yafito instead ya zarce site nasa da Ruky seya nufi na Zeezee wanda tun tafiyar ta ko tako varendar be ta6ayi ba se yau, gun yayi k'ura putuk! Key'n k'ofar dake had'e da car key nasa yasa sannan ya juya ya bud'e tare da sa kai. K'ura ne da cobwebs ya mamaye ko ina. Yana tafiya guiwa ba k'arfi ya samu ya qarasa har cikin d'akinta. Wardrobe nata ya bud'e yaga wayam! Ba abinda tabari komi ta kwashe Allah sarki Zeezee ya furta a ransa.
Side drawers yashiga ja yana dubawa kozega wani abinta amman duk ba komai, kominta ta tattara. A na qarshen ne yaci karo da wedding albums nasu guda biyu ciki ba wanda Zeezee ta tafi dasu nufin bata sake buk'atansa a rayuwarta kenan. Wani heart break ya sake ji. Bakin gadon yad'an kakka6e sa'annan ya zauna ya shiga viewing lovely photos d'in. Even though a ranan hankalinta baya jikinta tana tunanin gida, hakan be hana photos nasun yin kyau ba. Kalla ya rigayi har seda ya jiyo k'walla. Gabad'aya yaji ya tsani kansa yanzu meyasa ya hanke hukunci ba tare da yin dogon bincike da nazari ba? Addini beyi qarya ba dayace kafin a yanke hukunci ya zamanto anyi dogon bincike ga irinsa ai yanzu. Missing d'inta bil adadin ya shiga yi har don haka ya kakka6e gadon ya gyara ya kwanta gun yana rungume da photo album d'in ahaka har ya samu yayi bacci, Ruky kuwa koda tajisa shiru setayi zaton ko yana parlour ko sauran d'akunan don haka tana gama kallon series nata tayi kwanciyarta itama.
*^*^*^
Haka rayuwa on both sides ta cigaba da kasancewa ba dad'i. A kullum Adeel da tunanin Zeezee yake tashi ya kuma yini, Ruky abinda taga daman yi shi take Adeel be isa ya mata magana ba har wani shakka-shakkanta ma yake yanzu. On Zeezee's side kuwa tama bar fita waje yanzu kwata-kwata koda kuwa don siyan kati ne ta gommaci ta aika almajirai saboda abinda 'yan unguawa keyi mata sede bata fita waje ba shikenan sun shiga habaici suna zaginta kenan, abinda yafi cimata rai shine harda zagin Baba ma da suke.
Shi kansa Baba basu barsa ba, basuyi a gaban idonsa amman a bayan idonsa dandalin hira da zaginsa suke bud'ewa. Yau kamar kullum Baba da Omar sukaje masallaci an idar da Sallah ana zaune ana tasbih wasu maza daga bayansu Baba wanda basu gane Baban bane zaune a gabansu suka bud'e dandalin hira suna zagin Zeezee suna aibanta Baba, kalamu ba dad'in ji duk anan Baba na jinsu se k'ona da rad'ad'i zuciyarsa keyi masa. Omar na sallame nafilarsa ya hau bayin Allan da masifa da k'yar aka samu aka sasantasu if not cewa yayi seya musu duka danko yafisu k'arfi ko kodaga mere look. Dama kullum ana gayawa Baba abubuwan da 'yan unguwa ke cewa akanshi be ta6a ji da kansa ba se yau, jikinsa ne yayi sanyi a lokaci guda da k'yar suka samu suka k'arisa gida da Omar as tafiya kad'an yayi se sun tsaya ya huta. Sun shiga gida Baba ya wuce d'akin Mama ko tanka Mama dake musu sannu da zuwa beyi ba, miqewa yayi bisa gado yana riqe da zuciyarsa dake masa ciwo sosai.
"Omar lafiya? Meya sami Baban naku? Ko kunyi fad'a ne?"
"A'a Mama kede go and calm him down kar ciwonsa ya tashi."
"Gayamin meya faru Omar?"
Be b'oyewa Mama komi ba ya fad'i mata abinda ya faru. Cike da tashin hankali Mama ta shiga d'akinsu inda ta tarar da Baba kwance akan gado sede meh? Baya motsi wani irin rikicaccen ihu ta saki sannan ta biyosa da "inna-lillahi-wa-inna-ilaihi-raji'un. Alhj!" Da gudu ta nufi kan gadon tana tapping nasa sede at all baya responding. Omar ta shiga kira seda ya fito a rikice jin yadda take ihu "Omar Babanku, don Allah kayi wani abu." Shima Omar d'in gabad'aya ya rikice ya nufi kansu yana kiran Baba sede baya amsawa. Bayan nan ga kuma yadda heart nasa ke beating a hankali. Seda sukayi dagaske suka samu suka d'aga Baba ba tare da 6ata lokaci ba sukayi dashi asibiti inda aka wuce dashi emergency ward.
Banda kuka ba abinda Mama keyi a corridor'n d'akin da lokitoci da Baba ke ciki suna aikin ceto ransa. Omar ne ke k'ok'arin calming nata don shima hankalinsa gabad'aya a tashe yake fatansu kar Baba ya tafi ya barsu don tun ba yau ba Mama take lura da yadda Baba kebin abin Zeezee a rai. Ya yafe mata komi ya wuce yaqi, ga irinta nan ai yanzu. Me za'ayi da gata a rayuwa? Dama-dama ma ace gatan da hankali ke d'aukawa ake bayarwa yaro ba erin wanda Baba ya riga bawa Zeezee ba.
****
"Zainab! Zainab!" Kirar Mrs Muktar ga Zeezee wanda tuni ta gudu izuwa bayi ta 6uya a zatonta ma tayi bak'o ne shine Mrs Mukhtar ke kirarta dan kuwa ta rantse bazata sake kula wani na miji ba face Ya Al'ameen nata wanda she is sure shima yanzu ya riga yayi aure ya mata nisa.
"Zeezee! Ina kike ne?" Mrs Mukhtar tasake kiranta a yayinda tashin hankali ke building a voice nata.
"Zeezee!" A yanzu kam ta shigota d'akin.
"Na'am" Zeezee ta amsa tare da fitowa daga bayin, tashin hankali ne kwance karara a fuskar Mrs Mukhtar wanda tun kafin ta fayyace wa Zeezee komi, tayi saurin tambaya "Aunty lafiya?" Kai zallah Mrs Mukhtar ke kad'a mata "Zeezee Babanki."
"Baba!" Tayi exclaiming "meya samu Baba Aunty? Please tell me."
"Ya sake samun heart failure Zeezee yanzu haka yana asibiti su Mama sun kaisa."
"Innalillahi-" kasa qarisa salatin tayi se kuka wane lalacaccen famfo.
"Zeezee ba kuka bane abinyi, ki sanya hijabin ki mu fice, yi hak'uri in shaa Allahu ze samu sauk'i."
Hakanan through out the drive Zeezee ke ta kuka. Suna isa asibitin suka nufi inda su Mama dasu Mariam suke already se kuka suke. Da gudu Zeezee ta nufi inda Mama ke, sede kafin ta k'arisa Mariam tayi mata katanga stopping her.
"Kin halaka Baba, Maman ma bazaki barta ba?" Tayi maganan idanunta na tsiyayar da hawaye sosai. Cikin kuka da tsan-tsan tashin hankali Zeezee ta soma da cewa; "Adda Mariam don Allah kiyi hak'uri and let me hug her I beg you please."
"No way ki koma daga inda kika fito, tunda aka haifeki you've been nothing but badluck to us Zainab, wallahi idan abu ya samu Baba kisani I won't ever forgive you."
"Adda Mariam ya isa please yanzu ba lokacin yin tashin hankali bane" cewar Omar a yayinda Zeezee tasake rushewa da kuka tana kiran sunan Mama amman itama Maman yau ta kanta take bata iya tacewa Zeezee komi ba. Mariam ta bari Zeezee ta zauna kusa dasu ma tak'i. Tana kuka Mrs Mukhtar tajata zuwa wani benchi dake chan gefe ta zaunar da ita tana lalashinta amman se kaman sake tunzirata Mrs Mukhtar ke.
Not long enough Dr ya fito inda ya kira Mama zallah ya buk'aceta data bisa office nasa. Tana kuka tabi bayansa inda ya bud'e k'ofar ta samu tashiga tare da jan kujera ta zauna tana shessheqa.
Tissue ya miqa mata tare da sanar da ita "please calm down mijinki na cikin critical condition bazan 6oye miki ba."
"Subhanallah!" Ta furta tana kuka sosai "Dr is he going to make it?"
"Agaskiya bazan 6oye miki ba, chances na rayuwansa is not upto 30% kunsan condition nasa be kamata ba kuna barinsa yana tunani haka. His heart is all damaged yaci ace zuciyar ma ta buga yabar aiki amman Allah be k'addara hakan ba. Ku sashi a addu'a bamu san me Allah ke ciki ba."
"Dr dan Allah ba abinda zaku iya masa? He can't die don Allah ka taimakeni da 'ya'yana." Ta k'are maganan cikin kuka sosai.
"I'm sorry Ma'am but we've done all we can sauran mun bar wa Allah kuyi hak'uri. Kuna iya shiga ganinsa amman please Karki kuyi abinda ze tayar mai da hankali Allah basa lafiya."
"Amin Dr" ta amsa tana share hawayenta.
***
Mama ya jikin Baban? Mariam tayi saurin tambaya. Kai zallah Mama ke kad'a musu, nan fa hankalin yaran ya sake tashi binta kawai sukeyi a yayinda take heading to d'akin Baba. Ganin haka Zeezee itama ta miqe zata bisu sede kafin takai da bakin k'ofan Omar yasa hannu yana kareta ayayinda Mama ta juyo in crying tone tayi stating "taya zakice zaki shiga Zeezee bayan kinsan kece silar rashin lafiyan nasa? Kiyi hak'uri ki tsaya anan kibari nida yayyunki mu shiga."
"Mama yanzu bazan iya ganin Baba ba? Don Allah kuyi hak'uri kubarni inga mahaifina na rok'eku please."
"Ya kike magana kaman baki gane abinda Mama ke nufi ba?" Cewar Mariam spitefully. "So kike mu barki ki shiga ki gama halaka mana shi?"
"Ya isa Mariam" Mama ta katse ta "mu shiga." Ba tare da ta sake cewa uffan ba suka shiga tare da shutting door a face na Zeezee. Nan fa baiwar Allah abin tausayi ta kuma sauk'a har k'asa tana kuka a yayinda Mrs Mukhtar keta bata hak'uri.
Kallo d'aya iyalan Baba suka iya suka mishi idanunsu ya cike dam da hawaye. Banda kuka ba abinda suke iya yi. Kallo d'aya za'ayi wa Baba asan da k'yar ya kwana yau Alhamis ya kwana da rai. Hakan ba k'aramin sake tayarwa family'nsa hankali yayi ba. Da gudu Mariam da Omar sukayi kansa, shi Omar na miji amman se kaman yama fi Mariam yin kuka musamman idan ya tuna fa just a while ago suke zaune a masallaci lafiya k'alau. Har Mama ta kasa barin kuka.
"Ya'yan albarka ina kuke?" cewar Baba in a low and cracky voice.
"Gamu nan Baba" cewar Mariam "sannu Allah ya baka lafiya."
"Ameen" Mama da Omar suka amsa in unison. Hannunsa dake ajiye a gefe yake son d'agawa amman ya kasa, da Mariam ta gano haka seta d'aga ta had'a da nasan, shima Omar ya miqo hannunsa duk suka had'a gu d'aya.
"Masha Allah suwa dawa ne anan?" Ya tambaya gashi de a zahirce idanunsa a bud'e ne sede ko bayi gani dasu ne masani se Allah.
"Mariam da Omar ne anan Baba" cewar Omar yana share hawayensa da d'ayan hannunsa.
"Sannu 'ya'yan albarka Allah yi muku albarka."
"Ameen Baba" Mariam ta amsa "sannu." Se kuka suke sosai saboda raya musu da zuk'atansu ke na cewa Baba baze kwana ba yau.
"Mariam" Baba ya kirata cikin dashasshiyar murya.
"Na'am Baba gani."
"Mariam 'yata ki yafemin rashin adalcin da nayi a tsakaninku tun kuna 'yan yara, ki gafirceni don Allah."
"Baba wace erin magana kake haka? You've never once offended me don Allah kabar seeking forgiveness d'ina, what we are after at is your health."
"Nasani Mariam amman inji da kunne na kin yafemin." Hannunsa ta sake matsewa gam cikin nata tana me sake kuka "Baba inhar abinda kakeson kaji kenan shikenan, ni Mariam 'yarka na yafe maka komi da 6oyayye da kuma bayyananne duniya wa lahira, Allah ya baka lafiya."
"Ameen masha Allah Mariam nagode, Omar Baba na kaima ka yafemin rashin ad-" be idar da maganan ba Omar ya katse sa in a crying tone yace, "na yafe maka Baba, na yafe maka komi Allah baka lafiya."
"Nagode 'ya'yan albarka, Allah ya albarkaci rayuwanku ya baku zuri'ah d'ayyiba, sannan kuma ya haneku dayin rashin adalci a tsakanin 'ya'yayenku kunga abinda hakan ya haifar min. Kumin alqawari ko akan layi kuka ga iyaye suna rashin adalci a tsakanin 'ya'yayensu zaku tsaya ku musu wa'azi."
"In shaa Allah Baba Allah baka lafiya." Mariam kije ki ibo su Hafsah daga islamiyya." Mama ta fad'a da k'yar.
"Mama bazan iya barin Baba haka ba."
"Karki damu nida Omar zamu kula dashi, tashi kije Mamana." Ba tare da tayi gardama ba ta share hawayenta, "toh Baba zanje in ibo su Ramlah daga islamiyya."
"Toh sannu Mariam d'ina."
"Yauwa Baba, zuwa anjima zan dawo Mama."
"A'a Mariam ki zauna da yaranki if not waze kula dasu mijinki bayi gari."
"Mama koda me aiki ne zan barsu."
"A'a ban goyi bayan hakan ba gani ga Omar duk abinda Babanku ke buk'ata ni da Omar zamuyi masa."
"Are you sure Mama?"
"Yes Mariam karki damu."
"Toh shikenan amman if something goes wrong please don't hesitate to call me."
"In shaa Allah ki shafa min kan takwara na."
"Toh Mama" nan ta juyo tana kallon Baba da hannunsa ke rik'e dana Omar har yanzu. "Baba gobe in shaa Allah zan dawo get well soon Allah baka lafiya." Kai zallah ya gyad'a mata, anan ne ta samu ta fita.
Zaune ta tarar da Zeezee kan bench tanata aikin kuka har yanzu, ko niyyan magana Mariam batayi mata ba hakan yasa Zeezee ta miqe tana kuka sosai takira sunan Mariam.
"Adda Mariam?" Banza da ita tayi tana me cigaba da tafiya.
"Adda Mariam don Allah kiyi hak'uri ki sanar dani halin da Baba yake ciki ba don hali na."
Kaman bazata amsata ba tace, "da sauk'i" sannan ta fice ba tare data sake sauraronta ba. Kasa daina kukan Zeezee tayi har seda Omar ya fito daga d'akin shima kasancewar aiken sa gida da Mama tayi domin ya ibo mata abubuwan dazata buk'ata don kwanan asibiti.
"Ya Omar" ta kirasa tana k'ok'arin miqewa daga kan benchin.
"Na'am Zeezee." Ya amsata ba yabo ba fallasa.
"Ya Omar ya jikin Baba?"
"Da sauk'i."
"Ya Omar ka fad'amin gaskiya please, I tried to talk to Adda Mariam but she is so mad at me."
"Da sauk'i Zeezee addu'ar mu kawai yake buk'ata."
"In shaa Allah Ya Omar, how I wish I can see him also and hold his hand." Tayi maganan k'walla na cikowa a idonta. "I miss my Dad Ya Omar, I miss him so much. I can't ever forgive myself for letting him suffer like this, nice sanadin rashin lafiyarsa." Ta rushe da kuka sosai. Shi kansa Omar tausayi ta basa dukda kuwa haushinta yakeji saboda ita ta fara haifarwa Baba da wannan rashin lafiyar. Dan irin kukan da Zeezee take me tsuma zuciya yasa Omar yajata jikinsa tare da hugging nata yana bubbuga bayanta. Hugging nasa back tayi tana me cigaba da kukan.
"Ya isa, he is going to be alright in shaa Allah." Kai ta gyad'a seda tad'an yi shiru ya saketa nan ta shiga share hawayenta. "Ki zauna ina zuwa."
"Gida zaka?"
"Eh."
"Zan bika."
"Are you sure?"
"Yes please."
"Okay toh muje." Anan suka fice, Zeezee ce ta had'awa Mama dukkannin abinda zata buk'ata.
*****
"Hafsah?"
"Na'am Alhj" ta furta tana k'ok'arin shanye kukan dake neman kub'uce mata.
"Kina ina?"
"Gani nan Alhj" nan ta sake matsowa kusa dashi tare da had'a musu hannayensu.
"Hafsah ta ki yafeni kinji?"
"Alhj kuma wani irin magana kake?"
"Nide ki yafeni don Allah nasan sau dayawa nakan miki abubuwan da bakiso kiyi hak'uri ki yafemin please."
"Alhj please ka dena, kabar magana haka. Ya kake ta neman yafiya sekace mutuwa akace maka zakayi? Please ka bari ya isa haka."
"Hafsah ta inaji a jikina today will mark my last day, zuciyana namin ciwo sosai." Hawaye ne suka soma tsiyayowa daga kumburarrun idanunta. Jin shiru yace, "baza ki iya yafemin ba Hafsah ta? Yi hak'uri ki yafemin kinji?"
"Alhj me kayi min da zaka nemi gafara na? Ni nace kayi offending d'ina ne? Please kabar maganan haka lafiyarka ce a gaban mu yanzu."
"Baki fad'a ba amman nasan da hakan."
"Alhj inhar jin yafiya na kakeson ji toh ni na yafe maka duniya wa lahira."
"Nagode Hafsah."
"Nima nagode Alhj Allah baka lafiya, Hjy (Maman shi) ta kira d'azu k'afafunta ke ciwo taso fitowa yau amman tace zata bari zuwa gobe."
"Toh ba matsala, Allah kaimu."
**^^**
Har dare around 9pm Zeezee tak'i barin asibitin, ba yadda Omar beyi da ita ba ta ya kaita gidan Mrs Mukhtar amman tak'i ita tanason taga Babanta.
9:30pm Mama ta fito waje don yima Zeezee magana. Alokacin Zeezee na miqe akan benchi tayi lamo "Zeezee" Mama ta kirata.
"Na'am" ta amsa tare da miqewa a kid'ime.
"Me kike har yanzu baki koma gida ba?"
"Mama ya jikin Baba?"
"Da sauk'i yana bacci ma."
"Allah ya bashi lafiya."
"Ameen tashi Omar yayi dropping naki Mrs Mukhtar nata kira."
"Mama zan kwana anan."
"Anan a ina Zeezee?"
"Ko akan benchin I want to be anywhere close to Baba."
"Zeezee kiyi hak'uri ki koma gida."
"Mama don Allah kimin hanya, ina son inga Baba in gani da ido na wani halin yake ciki please Mama don't refuse my offer, I cannot forgive myself for what I've done to him."
"Zeezee dama Allah ya riga ya k'addara wannan rashin lafiya wa Babanku sede kice ta sanadin ki hakan ya faru Wanda dama komi seta sanadin wani yake faruwa, so kibar blaming kanki ki taya shi da addu'a Allah shi basa lafiya."
"Ameen Mama yanzu don Allah ba yadda za'ayi na gansa kafin na tafi?"
"Zeezee kin fini sanin abinda hakan ze haifar."
"Mama kince fa yana bacci."
"Even still Zee-"
"Mama please I beg you don Allah, this is all I ask." Zeezee tayi pleading abin tausayi. Mama zata sake magana Zeezee ta sake had'ata da Allah, she can't say no now. Muje.
"Nagode Mama, thank you so much" a nitse tabi bayan Mama suka shiga d'akin inda ita Zeezee ta tsaya daga bakin k'ofar a yayinda Mama ta k'arisa ciki ta sake duba fuskan Baba don ta tabbatar da baccin yake. Hannu tayi wa Zeezee nan ta k'ariso ciki.
Kallo d'aya Zeezee tayi wa Baba ta rushe da kukan zuci se hawaye kawai take tsiyayarwa. Binsa kawai take da kallo tana me sake tsanar kanta na sanya mahaifinta cikin wannan hali, duk anan kallonta kawai Mama take. Hannu Zeezee ta d'aga a hankali ta d'aura akan na Baba a hankali. Har Mama ta bud'e baki zatayi magana, ganin Baba be farka ba ta barta.
"Baba I'm so sorry, Allah ya baka lafiya, your daughter loves you so much if only I can take away your pain." Tayi kusan minti biyu akansa sannan da k'yar Mama ta samu ta turata waje "kije gida Zeezee, Omar na jiranki a mota in shaa Allah gobe seki dawo."
"Toh Mama take care of Baba please Allah bashi lafiya."
"Ameen seda safe."
"Allah tashemu." Tana kaiwa nan ta juya ta fice. Ciki Mama ta koma ta idar da shafa'i da wutr nata, ta shiga canza kayan sawanta tana cikin haka ne taji Baba yaja doguwar nishi. Rabin kayan na jikinta rabi ta cire ta k'arisa kansa "Alhj?" Ta kirasa cike da tashin hankali. "Alhj?" Tayi tapping nasa "na'am Hafsah." Ya amsa at long last.
"Alhamdulillah! Ka tashi kenan?"
"Eh" ya amsa sama-sama.
"Ya jikin toh?"
"Alhamdulillah."
"Barin canza kaya na ina zuwa." Da nod daya mata ta koma ta canza kayan nata zuwa na bacci sannan ta dawo ta zauna a gefensa.
"Hafsah ina Ibraheem da... da... da Yasmeen?"
"Ibraheem na Abj Yasmeen kuma Kd amman gobe in shaa Allah zasu d'auko hanya don dubanka."
"Ina son ganinsu yanzu kiyi musu magana kice suzo."
"Alhj ba gari d'aya fa muke dasu ba, Mariam, Omar da Zeezee ne muke gari d'aya dasu."
"Ibraheem da Yasmeen fah?"
"Suna chan Abj da Kaduna Alhj karka damu gobe zasu shigo."
"Inason yi musu magana Hafsah."
"Toh in kira maka su a waya?"
"Zamu samu muyi magana?"
"Sosai ma."
"Toh kiramin Ibraheem shine babba aiko?"
*MIEMIEBEE. Team #YGC!*
Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
2 comments:
Wow Enx sis dis marks the third tym tears roll down my cheeks because of a novel.... Mhen dis baba's illness really made me go emotional Allah yasa ya yafe wa zeezee kuma Allah ya kara mai sauqi......Lol Ehen miemie u wil pay for my expensive tears ooo. Break a leg gal sky ix ur limit
luv ya
Tnx sis, Allah ya kara basira, baba Dan Allah kada ka mutu sai ka yafe ma zeezee tukun.
Post a Comment