Monday, 27 February 2017

‘YAR GATA CE!

   *BY MIEMIEBEE*
Page 55
 February, 2017




Yau ne kawai Adeel be jesa gidansu Zeezee ba, instead yaje sa gida gun Maminsa. Bayan sun k'are cin lunch take tambayarsa ya rayuwa. Kai zallah ya kad'a mata.
   "Wai kai da Ruky ne har yanzu?"
  "Mami in kinayi wa Allah ki dena d'auko min zancen Bayerabiyar chan anytime we are together."
  "Toh Allah baka hak'uri meke damunka?"
   "Zeezee, I want her back, for the past two weeks ina zuwa gidansu amman brother'nta yak'i hak'ura ya barni inyo bikonta."
   "Itan ta yarda zata dawo ma ne?"
  "Bata yarda ba but I know she'll eventually."
  "Uhm Auta nida zaka ji nawa da hak'ura da ita kawai-"
  "I can't" yayi saurin katse ta. "I love her way much, I can't sacrifice her love to anyone."
  "Toh me kakeso ayi?"
  "Kuje da Uncle kumin bikonta."
  "Wannan abin kunya har ina? Despite yadda ka wulak'anta yarinyan nan."
  "Kema haka zakice wato? Wai akwai wanda baya making mistake ne a duniyan nan? I miss Daddy wallahi nasan da yana nan in an eye blink yamin abinda nakeso, kar kujen zan cigaba da trying luck d'ina har sena samu na shawo kanta da family'nta."
   "Me yayi zafi kake magana haka Auta? Sanin kanka ne ina sonka sosai-"
  "Shine bazaki iya zuwa kiyi ma Mom na Zeezee magana ba?" Ya katse ta. "Ina love anan?"
   "Abinda kakeso kenan?" Gira ya d'age mata. "Toh shikenan Allah shi kaimu gobe zanyi ma Baffan naka magana."
 "Yauwa ko kefa Mami? Thank you kinji?"
  "Ba komai amman Allah ka dena min magana gatsau-gatsau haka, uwarka ce nifa ko dan bani dukan ka ne?"
  "LOL duka fa kikace Mami? Wuce nan ai yanzu." Yi tayi kaman zata maresa take ya miqe daga kan kujeran tare da jan baya, "toh ni zan koma gida se goben."
  "Toh Allah kaimu ka gaishe da Ruky."
  "Ki kirata ku gaisa ni bazan gaisheta ba."
  "Heh! Su Auta manya" yana murmushi ya fice se bayan Maghrib ya dawo gida a lokacin Ruky na gida tana shirye shiryen fita dinner.

   "Har ka dawo ne?" Tayi maganan tana jawo k'ofan d'akinta.  
  "A'a ina hanya ne" ya amsata ba tare da ya kalleta ba.
   "Toh ni na tafi" bece mata k'ala ba taja motarta ta fice. Chan getting to 10 Adeel ya shiga d'akinsa tare da d'auko suit dayake saving kud'ad'ensa. Zaro su duka yayi ya irga sede a maimakon yaga 100k se 90k yake gani, sau uku yake irgawa amman ba gomansa. Danqaree! Aiko ba 6era suke dashi ba bale ace su suka cinye goman, kuma he is adamant be zare ko d'ari ba daga cikin d'arin how comes?
   "Ruky! Ruky sata ta fara min? Kut! Allah dawo dake gida wallahi zaki yaba wa aya zak'inta." Bacci yakeji amman yak'iyi yana jiran dawowan Ruky. Se pass 11 ta dawo gida all exhausted so kawai take ta kwanta. Tana stepping foot nata a parlour Adeel ya jefa mata tambaya, "ina kud'i na? B'arauniya."
 
   "Kamar ya kuma kud'inka? Ka bani ajiya ne? Kuma ka dena cemin b'arauniya."
  "Na k'ara b'arauniya kawai! Zan k'arisa gun in goga wannan bakin naki a k'asa wallahi, ina kika kaimin 10k d'ina?"
  "Ni ban d'auka ba" ta fad'a tana cire goggoron dake kanta. "Se kinji na jaki sannan zakiyi magana? Ina yake? Ko sena gayawa Babanki kin fara min d'auke-d'auke tukun?"
   "Toh ai laifinka ne, I asked you nicely kak'i bani ba dole nayi following other alternative ba."
  "Ohh is that so? Nasan maganinki wallahi bake ba allowances daga nan zuwa next two months. Wani irin rayuwa ne wannan? Zeezee dako k'wandala bayi had'a ni da ita, she never once stole from me. What kind of a woman are you? Mark me, kinyi na farko kinyi na k'arshe kenan wallahi." Baki ta murgud'a mai "kada ka bayar d'in" ta fad'a a lokacin da ya shige d'akinsa. "Barka na d'an rage wasu canjin anan."

    _Washegari.  Gidan Lt Alhj Isma'eel Yusouf._
   Zaune Mama da Omar suke a tsakar gida inda suka jiyo sallaman babban mutum daga waje. Sauri Mama tayi ta koma ciki sannan Omar ya amsa, bak'in fuska ya tarar sede kallo d'aya yayi wa Mami yagano mahaifiyar Adeel ce, yana kan wannan nazari ne yaga Adeel biye a bayanta. Welcoming nasu yayi suka wuce parlour suka zazzauna bayan gaisuwa suka yimai ta'aziyya sannan suka fayyace mai purpose na zuwansu inda Mami ta buk'aci Omar daya kaita gun Mama tana son yimata magana. Se kallace-kallace Adeel ke ko zega Zeezee not knowing bata gida taje ta gidan Adda Mariam. Ba musu Omar ya kaita gun Mama sannan ya dawo ya samu Adeel da Baffansa. Hak'uri suka yita bawa Omar inda Baffan Adeel ke sake jaddada masa batun nadaman da Adeel yayi and how bad he wants Zeezee back, achan ciki ma abinda Mami keyi kenan. At last Mama da Omar suka ce musu hakan ba damuwa bane zasuyi wa Zeezee magana idan har ta amince she wants to go back so be it, if not kuma they can't force her. Godiya sosai Mami sukayi sannan Omar yayi musu rakiya kasancewar Mama bata gama zaman takabarta ba har yanzun.

   Ko cikakken minti d'aya da tafiyansu Adeel beyi ba Zeezee ta dawo, bayan tayi parking motarta ta fito ta k'arisa ciki tare da yima su Mama sannu inda sukeyi mata sannu da zuwa.
  "Suwa suka zo Mama? Naga wani mota yabar gidan nan just now." Kallon Omar Mama tayi sannan back to Zeezee "zoki zauna kinji." Ba gardama ta zaunan, "Adeel, Mom and Uncle nasa ne sukazo Zeezee."
   "Me suka zo yi?"
  "Sunzo bikon ki" nan Mama ta zana mata yadda komi ya faru "so mu duk abinda kikeso shi zamuyi miki, in har kinga zaki iya komawa Adeel fine if not kuma a yanzu Omar na kiran Uncle nasan ya sanar dashi." Shiru tayi a yayinda hawaye ke forming rapidly a idonta. "Ko kina neman time to think?" Kai ta kad'a "Mama I don't need to think bana buk'atan Adeel a rayuwa na again, I've had enough."
   "I know Sweetheart amman still zan baki daga nan zuwa gobe kiyi making up mind naki kinji? Tashi kije you are free."
  "Nagode Mama, nagode Ya Omar Adda Mariam tace in gaishe daku."
  "Toh muna amsawa" Mama ta amsa, nan Zeezee ta fice. D'akinta ta nufa tare da bajewa kan gado inda ta fad'a kogin tunani, gabad'aya she is lost bata san me zatayi ba. Lubiee her only adviser ta kira bayan gaisuwa take sanrar da ita halin da take ciki.
   "Haba Babe! Yanzu har sekin tambayen shawara regarding wannan matter? I thought you've had enough, me zaki sakeyi da Adeel? Although nasan abu me kyau ne a sasanta amman what Adeel did you is unforgettable, kodan yadda kika nuna kinfi sonsa fiye da parents naki kad'ai ya isa ace baze ta6a wulak'anta ki ba, but he did it anyway."
   "Yes Lubiee nima ba son in koma masa nake ba."
  "But you still love him don't you?"
  "I will be lying if to say no kema kinsan he was my first love."
  "I know Babe, but please karki koma masa in shaa Allahu Allah ze kawo miki wanda ya fisa kinji? Have faith in faith."
   "Yes Babe thank you."
  "Always barin gudu muna da exams gobe."
  "Toh success" anan ta katse. Wahsegari da Asubah bayan sallah Mama tashigo ta d'akin Zeezee, bayan sun gaisa take tambayar ta have she made up her mind.
   "Mama ku kirasu ku ce musu suyi hak'uri don ni bazan sake komawa Adeel ba."
  "Are you sure this is what your heart wants?"
  "Yes Mama."
  "Amman Zeezee ai Adeel ya tuba naga, kuma ke haka kikeso kiyita zama, mahaifiyarki na zaman zawarci kema haka?"
 "Mama please don't talk like that, I believe one day Ya Al'ameen ze dawo min."
  "Hmm idan beyi aure ba kenan."
  "Ko da matansa uku ne inhar he is willing ya cikata dani in zama ta hud'u I'll accept his marriage Mama because I love him so much."
 
   "Zeezee bana son kizo kiyi 2-0."
  "Mama please..."
  "Shikenan zan yima Omar magana ya sanar dasu final decision naki ko?" Kai ta gyad'a "good" cewar Mama. "Amman Zeezee just because you're holding on to the feeling that Ya Al'ameen ze sake dawo miki hakan baze sa kina shutting bak'in da suke zuwa miki ba, banason k'arama dake jikin ki ya saba da zaman haka, d'akinki shine k'ima da darajar ki kinji?"
  "Naji Mama."
  "Wanda keda nistuwa ya fara zuwa ta wajen yayanki Omar semu basa dama muga iya gudun ruwansa in ya dace a had'aku walillahil hamd ke bakison ki koma d'akinki ne?"
  "Ina so Mama."
  "Yauwa 'yar albarka tashi ki koma bacci."
  "No ban gama azkhar ina ba tukun. "
  "Toh se zuwa safen."

  A yau d'in bayan sallan Azahar Omar ya kira Baffan Adeel inda ya sanar dashi final decision da Zeezee ta yanke tare da basu hak'uri. Sosai Baffa ya fahimce shi ya kuma mai godiya sannan yayi hanging wayar. Mami ya soma kira ya sanar da ita, rasa yadda zata fara breaking wagga news wa Adeel tayi inda ta buk'aci Baffa da yayi hak'uri shi ya fad'a ma shi Adeel d'in. Adeel na zaune a office wayarsa ya shiga ruri ganin 'Uncle A' yayi saurin picking.
  "Hello Uncle?"
 "Na'am Adeel kana ina ne?"
  "Office." Ya amsa.
  "Toh ba dan komi na kiraka ba illa don in jaddada maka outcome da muka samu, kasani kowani musulmi da k'addararsa a rayuwa kuma idan Allah ya aza wa mutum so ake ya danne zuciyarsa yayi accepting ya kuma dage da addu'a Allah fito mai da alkhairi daga hakan kana jina?" Jikinsa ne yayi sanyi matuk'a, "Uncle just tell me tace she isn't coming back huh?"
   "Eh Adeel kayi hak'uri, we can't force her."
  "Shikenan nagode." Nan ya katse wayar, jakansa kawai ya d'aga ya fice. He can't bear the thought Zeezee is gone forever bazata sake dawo mishi ba, why didn't he ever appreciate her time da take nan seda ta tafi? its true indeed that we don't know the value of what we have until we loss them. Bar (gidan sai da giya) kawai ya nufa inda yaje ya bugu iya buguwa. Be tashi dawowa gida ba se quarter to 9pm. Alokacin Ruky na kallon series abinta. Se buga k'ofan Adeel ke gbam! Gbam! Gbam wane ze b'alla shi daga hinges nasa. "Ina zuwa mana Adeel ka tsaya mana ha'a! 6alla k'ofar zaka yi ne?" Bubbugawan ya cigaba dayi har seda ta bud'en. Bankad'eta yayi ya wuce inda tajiyo warin barasan dake tashi daga jikinsa.

   "Adeel!" Ta kira sunansa cike da mamaki. "Me nake shirin gani? Dama kana shaye-shaye ne?" Jajayen idanunsa ya d'ago yana kallonta nan fa ta shiga tsoro, "wallahi idan baki ja bakin ki kin rufe ba zan kashe ki this instant in huta, tunda na rasa Zeezee kowa ma yana iya mutuwa."
  Kum! taja bakinta tayi shiru sanin yaufa ba a cikin hankalinsa yake ba. Sid'ak sid'ak ta wuce d'akinta tasa lock kallon ma ta yafe, kwanciyarta tayi inda shima Adeel d'in a parlour bacci ya sacesa. Cikin bacci amman se name na Zeezee yake ta furtawa.
    Asuban fari ya tashi da wata masifaffiyar ciwon kai, lalla6awa yayi yayi Sallah sannan ya koma ya kwanta se 9:44am ya tashi ya karya ko k'ala be had'asa da Ruky ba. Seda yazo fita take tambayarsa ina zasa.
   "Ina ruwanki da inda zani? Ke kike ajiye ni ne?"
 "Mallam daga tambaya? I beg free me o,  just cause Zeezee tace bazata dawo gareka ba doesn't mean zaka na sauk'e min fushinka akaina, ehe!"
   "Kina magana ne?" Yayi snarling at her, shiru tayi seda taji ya bud'e k'ofa tace, "baka bada kud'in cefane ba in ka dawo baka tarar da girki ba don't blame me."
  "Karki girkan mschww." Yawonsa ya fice ranan instead of office, da yamma wajajen k'arfe 5:40pm ya nufi unuguwan su Zeezee one last time yaji daga bakinta bazata koma masa ba ko ze samu sukuni dan har yanzu ya kasa yarda.

   Yau wai acewarsu Mama tunda an riga an sanar dasu Adeel Zeezee aiint going back to them ai shima baze sake tako k'afansa nan ba, with this thought Omar beje d'auko Zeezee daga islamiyya ba ta tako da kanta. Achan wani corner Adeel yayi parking motarsa sannan ya tako zuwa kusa da gidan su Zeezee tare da yin tsaye, tun daga nesa yake hangenta se dab data kusa shiga gida ya fito da wuri tare da sa mata kira. Chak ta tsaya jin muryan Adeel kafin tace zata bud'e k'ofa ta gudu ciki kuma har ya sha gabanta. Hannunta yaja seda ta fad'a jikinsa. Sa'an su d'aya ba mutanen dake wucewa sosai, shuresa ta shiga yi, "Adeel let me go ka sakeni meh haka?" Sake matse ta yayi a jikinsa "Zeezee please stop fighting it and just listen to my heartbeat, just listen to how much it's beating for you. Wallahi I can't do without you, hit me all you can, slap me but please karki ce bazaki dawo gida na ba. I'm truly sorry for maltreating you, I shouldn't have done that kiyi hak'uri please ki dawo I love you so much."
   Kukan itama ta rushe dashi jin yadda shima yakeyi, bar kai masa bugin tayi. Tana kuka yana yi, there's no denying tasan tana son Adeel but that is still not enough reason for her to go back to him, she have to be strong for herself. Sun d'au tsawon lokaci ahaka sannan da k'yar ta samu ya saketa tare da d'ago face nata yana goge mata dangling tears nata. "I love you Zainab, I love you so much wallahi."
   "What do you want Adeel?" Ta furta tana sauk'e hannayensa daga kan fuskartan.
   "I want you back Zeezee, I really do."
  "Why?" ta sake tambayarsa.
   "Because I miss you, I miss being with my lady."
   "Mami bata sanar dakai decision d'ina bane?"
  "Uncle did, but ban yarda ba Zeezee, I know bazaki min haka ba cause you love me just as much as I do love you, we are meant to be Zeezee please don't say no and come back to me. In gidanki kikeso in canza miki so be it, I just want to make you happy one last time."
  "You know what will make me happy once more?" Kai ya kad'a "idan kadena bothering d'ina ka fita daga harkata gabad'aya."
  "Zeezee thats not possible because I love you, I can't."
   "Just stick it to your head and mind that am gone forever and not coming back to you Adeel." Kai ya shiga kad'awa continuously. "Please don't say that, I really do want you back, Zeezee wallahi nayi nadaman aikata duka abubuwan da na miki, if only 'I'm sorry' can bring us back the way we use to be, give me one last chance please to prove my love to you."

   "No Adeel please stop making this hard on ourselves. Idan har abinda ya kawo ka nan don kaji daga bakina final decision d'ina ne so be it, bana sonka anymore Adeel, bana buk'atarka a rayuwa na anymore, koda kai ne autan maza na yafe ka, da in koma gidanka na gommaci mutuwa na, I don't love you okay?" Kuka take sosai take wannan magana saboda how difficult it is for her to admit that bata son Adeel.
   "I've once loved you but not anymore, they say first love never dies and na yarda da hakan saboda har yanzu kana da gurbi a zuciya na Adeel, na maka son da ban ta6a yima wani mahaluk'i a duniyan nan ba, na fifita ka akan iyaye na, I could die for you but not anymore, I'm hoping that one day Allah ze had'a ni da true love da ze ya burying first love da nake maka. Inhar kana sona, zaka so yimin abinda nake so by simply staying away from me" Hanky yasa ya share hawayensa sannan a hankali yace "me kikeso Zeezee? Tell me and zan miki shi saboda ina son kisan just how much I love you."
   "I want you out of my life Adeel, bana son sake ganinka, I want you to forget that you've ever had Zeezee in your life and move on."
   "Shikenan Zeezee, I'll try as much to get out of your life dukda nasan hakan abu ne mai wuya but tunda abinda kikeso kenan zan miki. I just want you to know that no matter how distant you are away from me, your heart is always here with me." yayi nuni da zuciyanshi. "Kuma I want you to know that I'll die loving you. Farewell Zainab, I pray Allah ya had'aki da farin cikinki kema, nikuma ya bani ikon iya jure rashin ki, I love you so much and thank you for once loving me." Mugun uncontrollable kuka ne yafi k'arfinta da irin heart melting words d'innan. Kaman kayan wanki tayi tsaye wajen tana aikin kuka, the next abinda tayi noticing is how Adeel yajata da hannu tare da shigar da ita cikin gidan nasu, before tayi comprehending wani abu taji lips nasa akan nata. Kissing nata yake hungrily yet passionately, k'in basa access tayi se hawaye kawai take tana beating against his chest da duk wani k'arfin ta. Shiko ya kasa hak'ura abubuwa da dama yayita mata har seda tayi gasping anan yayi using opportunity'n yayi owning lips nata fully, tun tana k'in basa had'in kai daga baya daya gama kashe mata jiki lik'is ta soma moving in sync with his move. Sun d'au tsawon lokaci suna abu d'aya sannan a hankali ya saketa, lasan swollen lips nata tayi tare da miyar dasu ciki tana me cigaba da kukan.
   "I will forever love you Zainab" yace da ita yana kallonta. Gudu kawai tasa ta shige ciki se d'akinta ta nufa tasa lock tare da wurgi da kanta bisa gado tana kukan cire rai, hanneyenta rik'e da kanta se juyi akan gadon take. Shima Adeel tsaye yayi wajen yana tsiyayar da hawaye sannan daga bisani ya fita ya koma cikin motarsa guiwa ba k'wari. Kuka sosai ya shigayi cikin motar, ba Zeezee rayuwarsa bata da wata ma'ana again. What else does he have to live for? His advice to all mankind is to appreciate what they HAVE before life makes them appreciate what they HAD verily nothing last forever, after all the life itself is temporary.

****
  "Zeezee! Ki bud'e k'ofar mana sekin sa min hawan jini ne tukuna?" Har anan se sautin kukan Zeezee kawai takeji. "Zeezee please upon up."
  "Mama am sorry please go away I need to be alone, kiyi hak'uri don Allah."
   "Zeezee bazan iya barinki haka ba ki tashi ki bud'emin ko sena yi kuka tukuna."
   "No Mama I beg of you dan Allah kiyi hak'urri ki tafi." Ta k'are maganan tana jan hanci. K'in tafiya Mama tayi har seda Zeezee ta taso ta bud'e mata don dolenta. Fad'awa jikin Mama tayi tana kuka me tsuma zuciya. A sannu a sannu Mama ta k'arisa da ita cikin d'akin tare da zaunar da ita bisa kan gado.
   "I'm here for you, I've gotchu." Kuka tayita yi Mama na bata hak'uri tana soothing nata. Se chan ta tsagaita kukan. "Can you tell me what happened?" Kai zallah take kad'awa nufin no, "remember am here for you kinji? Tell me meya faru? Keda Mallamin islamiyyan ku ne?" Kai kawai ta kad'a mata. "Then who?"
   "Adeel Mama."
 "Again? Meya faru kuma? Kina son ki koma mishi ne?"
  "Mama he left just now, Adeel ya tuba kuma yana son in koma mishi he kept on crying like a baby yana gayamin how much he wants me back. Yadda yake kuka nima ya sani Mama."
   "Shhh! all shall be well kinji? Bar kukan haka."
  "Mama I love Adeel also."
  "I know Zeezee kiyi hak'uri ki danne zuciyarki ki koma mishi nasan yayi nadama tunda abinda zuciyarki keso kenan."
  "I can't Mama, d'akin Ya Al'ameen nakeso-" katse ta Mama tayi "Zeezee bamu san ko Al'ameen ya sake aure ba or not we don't even know either Mamanshi zata bari ki koma masa."
  "I still don't care Mama shi nakeso gareshi kuma zan koma."
  "Allah sa hakan yafi alkhairi toh."
  "Ameen Mama nagode."
  "Ki huta kinji? Kukan ya isa."




*MIEMIEBEE.        Team #YGC!πŸŽ€*
Beeenovels.blogspot.com
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„

Sunday, 26 February 2017

‘YAR GATA CE!

   
*BY MIEMIEBEE*
Page 54
  *FEBRUARY, 2017*




    "Zeezee please kiyi hak'uri ki saurareni, slap me, insult the hell out of me, hit me anywhere you want and how but please don't shut me out. Wallahi Zeezee tun rananda na sake ki na shiga wani gaggarimin yanayi, give your very own one last chance please I beg of you, its all I ask."
   "One last chance?" Ta d'ago kai tana kallonsa ta nik'af nata finally cike da mamaki. "One last chance so you can maltreat me again? One last chance so ka sake duka na? force me into bed? make me do yours and wife's laundry? cook for you? sweep-" katse ta yayi da wuri "no, no please-" ya fad'a wane zeyi kuka.
  "Then why? Saboda kana nunamin Ruky ta fini k'ima da daraja a idonka?"
  "No Zeezee enough of that please, I want you back because I love you and miss everything about you, your smile, fragrance, body, hair, everything about you. I miss it."
  "I should have guess, ko ka manta am of no use to you tunda bazan iya haihuwa ba yanzu."
   "I don't f*cking care Zeezee, all I want is you."
   "You should have thought about that earlier kafin ka dakeni ka kuma buga min saki biyu."
   "Zeezee please! Cut it out. Meh kikeson in miki kigane cewa I've regretted every single action of mine back then? In Ruky kikeson in saka I'll at this instant because I don't love her, ke nakeso Zeezee please pity your very own."
   "What I want? What I want is for you to f*cking stay away from me Adeel plus you are nomore my very own, you never were. Bana k'aunar ka anymore Adeel ka riga ka fitamin a rai na, bana sonka. You came to me jiya da sunan tuba na kake nema and I did forgave you don't make me change my mind please."
   "Zee-"
  "I said go away!" Ta katse sa a tsawace.
  "No Zeezee please listen to me, lets solve this out, Zeezee haka kikeson ki k'arisa rayuwarki as bazawara? Bana son ganinki haka, you are worth than this."
   "Am I? Baka son ganina a haka ka buga min saki biyu? Mschww! am running out of patience just go away and never come back I don't ever need you in my life again."
   "No, that's not true, you can't forget me this soon-"
  "I can't?" Ta tambayesa "I was never in love with you Adeel, ko a da inma ba sonka nake ba. I came to realise that I was just afraid of you, a monster. Ya Al'ameen is the one I love and not you."
   "That's not true Zeezee you still love me I know that please come back."
  "Never."
  "Haka kikeso ki cigaba da zama?"
  "Koda hakan zan cigaba da zama meya maka zafi? Besides am going back to my truest love Ya Al'ameen."

   "No Zeezee please don't, karki tafi ki barni I beg you please. Kimin komi amman karki koma gidan Maj- Gen."
   "Give me one reason not to. Gidanshi zan koma I've made up my mind." Tana kaiwa nan tabi gefensa zata fice da sauri ya rik'o hijabin ta stopping her. Chak ta tsaya, kuka kawai taji ya fara kaman d'an yaro wanda itama tuni ya karya mata zuciya ta soma kukan.
   "Zeezee please" yayi pleading in a crying tone. "Please don't leave me" ya k'arisa maganan yana sauk'a akan guiwowinsa a idanun jami'un da ke wucewa. "I beg you please karki koma gun Ya Al'ameen come back to me and let me prove my love to you one last chance, please Zeezee don't refuse my offer." Kuka ne sosai yaci k'arfinta yadda words na Adeel ke getting to her. Tanayi yana yi, "let me go, ka sakeni" kad'ai ta iya furta mai. Kai yake kad'awa still in the kneeling position. "Zeezee please." Fincike hijabin nata tayi ta ruga ciki a guje tana kuka sosai. As always Mama na kitchen taga wucewan Zeezee da gudu yau unlike always da zata tsaya tayi mata sannu. Barin duk abinda takeyi tayi taje ta samu Zeezee dake baje akan gado tana kuka me tsuma zuciya.
   "Subhanallah!" Tayi exclaiming. "Ya da kuka haka? Meya faru?" Tayi maganan hannunta manne akan bayan Zeezee data kasa koda d'ago kai har yanzu.
  "Zeezee? Yi hak'uri ki amsa ni kinji? Meya faru?" Da k'yar ta iya tsagaita kukan tace, "babu."
  "Kamar ya babu kuma? Kina nufin haka kawai yau kika d'auro niyyan dawo min gida da kuka?" Kanta ta d'ago finally tare da share rolling tears nata. "Babu an yi mana wa'azi ne me ratsa jiki a islamiyya akan mutuwa se kawai na tuna da Baba."
   "Allah sarki, in shaa Allah Babanku is in a better place kinji? Mu cigaba da yimai addu'a yi hak'uri kukan ya isa haka Mamana."
  "In shaa Allah Mama thank you."
 "Tashi ki tu6e uniform d'in toh." Da nod da tayi wa Mama, Mama ta fice. Duk yadda tayi don kawar da tunanin Adeel daga k'wak'walwarta ta kasa, haka ta kwana ranan da tunaninsa.
   Washegari kuwa ko zancen zuwa islamiyya Zeezee batayi wa Mama ba, pass 3pm Mama ta shigota d'akinta, miqe kan gado ta tarar da ita tayi dunk'um tana tunani.
   "Bade tunanin Baba kike ba yau ma?Zeezee shin wai sekin haifar wa kanki ciwon zuciya sannan zaki huta? Da rasuwan Babanku sati nawa but kin kasa ki daidaita rayuwarki, haba mana! Mutuwa da zafi amman ya zama dole ki hak'ura."
   Tasowa tayi ta zauna "nifa ba tunanin Baba nake ba, ai kince in dena kuma ina iya k'ok'ari na ganin na ragen."
   "Toh me kike zaune yi haka tun d'azu? Tun da kika gama ayyukan ki ban sake jin motsinki ba."

    "Babu." Ta amsa blankly.
  "Toh islamiyyan fa? Babu ne yau?"
   "Akwai Bazan jeba ne" ((dalili kuwa shine bata son yau ma su sake had'uwa da Adeel she is simply avoiding him.)
   "Lafiya dai ko?"
  "Lafiya" tayi faking smile.
   "A'a ban san ki da haka bafa, gayamin mene"
 "Allah babu Mama, bana jin dad'in jiki na ne."
  "Kinsa tunani a gaba ba dole ba, bale ma I don't trust this silly excuse, gayamin gaskian zancen meya hanaki zuwa islamiya yau? Keda baki ta6a fashi.l
  "Mama babu."
  "Zainab!"
  "Na'am" ta amsa.
  "Tell me, mene?"
  "Mama..." sekuma tayi shiru. Isowa kusa da ita Mama tayi ta zauna a gefenta tare da rik'o hannunta "gayamin kinji? Am here for you."
  "Mama its Adeel" ta fad'a hawaye na forming rapidly a idanunta.
  "Subhanallah! What about him?"
  "Mama shekaran jiya yazo har nan bakin gate on my way back home daga islamiyya na ganshi..." nan ta kwashe labarin komi tabawa Mama bata ragar da komi ba.
   Ajiyar zuciya Mama ta sauk'e "ikon Allah! Ke yanzu me zuciyar ki ke raya miki?"
  "Mama I don't know I've had enough of his torture, I don't need some more."
  "Bakiya sonshi yanzu?" Kai ta gyad'a a hankali.
   "Are you sure?" Sekuma ta kad'a kai da nufin a'a. "Mama its hard for me to admit that bana son Adeel saboda he was my first love, I loved him with all that I've got."
  "I know Zeezee you must not repeat it again. Kina ganin ke ya tuba, tuban gaske?"
  "He did Mama saboda he even knelt down in front of me, but it still isn't enough compared to abubuwan dayamin da nake gidansa, Mama ban ta6a fad'a miki bane but har forcing d'ina in to bed Adeel nayi, sometimes ma he'll be drunk and then sleep with me forcefully" ta k'are maganan cikin kuka sosai. Hugging nata sosai Mama tayi cike da tausayi. "Its okay Sweetheart baza ki komawa Adeel ba unless you want to kinji? Kibar kukan haka." Kai tayi nodding "thank you Mama."
   "Always dear, share hawayenki ki shirya islamiyya idan aka tashi zan sa Omar yaje ya d'auko ki kinga ta hakan Adeel baze iya sake tsayar dake ba."
  "Are you sure Mama?"
  "I'm definitely am."

  Ba tare da ta sake cewa uffan ba ta shirya tsaf ta wuce islamiyya. Sede yau ma kaman jiya, bayan Omar ya d'aukota daga islamiya suka tarar da maroon Genesis G80'n Adeel parked gaba da gidansu kad'an.
   ""Ya Omar gashi chan." Tayi stating ba nitsuwa a tattare da ita.
  "Waye Zeezee?"
  "Adeel, gashi chan don Allah do something." Tana idar da maganan sega Adeel yana fitowa daga motarsa, ita se yau ma ta lura da bak'in da Adeel yayi.
   "Go inside Omar" ya buk'aceta. Da sauri ta bud'e motan ta fita nan Adeel ya shiga k'walla mata kira sam tayi kaman ba ita yake kira ba, tana kaiwa ciki tasa lock. Juyawan da Adeel zeyi yaga Omar, although besan saba amman jikinsa na basa wan Zeezee ne.
   Hannu Adeel ya miqa masa sukayi sallama sannan Omar ya tambayesa purpose of being here inshi.
   "I know ba lallai bane ka sanni, I'm Adeel Zeezee's husband-"
  "Ex husband" Omar yayi correcting nashi. Baki na 6ari yace, "yes ex husband, Yaya please bikon Zeezee nake sonyi, ku yafemin ku dawo min da ita, I love her."
  "Kasan kana sonta shine ka wulak'an tata ka buga mata saki bama d'aya ba har biyu? Please Mallam pack your wahala and go bamu buk'atanka."
   "Yaya please karka min haka, idan ita Zeezee yarinya tamin haka, kai babba be kamata kamin haka ba kaima. Wallahi sharrin shaitaan ne I never meant to divorce Zeezee believe me."
  "Bazaka tafi ta ruwan sanyi bane sena sa an maka koran akuya?"
   "Yaya please..." ya sake pleading. Ganin Omar na neman tara masa jama'a yasa kawai ya tafi badon yana so.

   Adeel be fasa zuwa gidansu Zeezee a kullum ba, infact he decided to make it a hobby. A kullum kuwa idan yazo da Omar suke had'uwa dan kuwa Zeezee a mota Omar ke barinta shi ya fito ya zazzage wa Adeel buhu-buhun rashin mutunci amman ba hakan zaisa gobe yak'i zuwa ba. Akan Zeezee ya ajiye pride nasa a gefe, inhar ze sameta he is ready to loss everything like everything. Kusan sati biyu Adeel ya jera yana zuwa gidansu Zeezee kaman maye. Ruky Mama sede ta kallesa saboda ko maganan arziki bayi had'asu don Adeel ya fita harkarta gabad'aya. In sunyi magana toh Ruky money monger tazo kar6an kud'i ne, wanda da yak'i da ya so dole ya bata kokuwa ta b'oye key'n motarsa. Yau ma kaman kullum yajesa gidan su Zeezee, bayan Omar ya korasa ya dawo gida rai a dak'ule only to find the gate locked harda kwad'o. Danqaree! Ya furta a ransa sannan ya shiga bubbuga k'ofan yana me sauk'e haushinsa akai. "Ruky! Rukayya! Ina wannan bayerabiyar ta shiga? Mschww!" Ganin fa bata gida yasa ya zaro wayansa daga aljihu a fusace ya shiga nemanta. Several missed calls yayi mata wanda ciki ba wanda ta d'aga as tasa wayar a silent se bidirin biki suke sha.

   *^GIDAN BIKI^*
   Wak'an girgiza k'wank'waso ke tashi wane ze har6a zuciyan mutum. Ruky da friends nata ne ke tsaye se rawa sukeyi, chan wata friend nata ta buk'aceta da sanin time, anan ne Ruky ta zira hannu tare da zaro wayanta nan taci karo da 28 missed calls from Baby. Tsuka taja sannan ta sanar da k'awarta ta.
  "Toh ni nasan zaka dawo da wuri ne? Ina kullum se bayan Maghrib kake dawowa, mschww!" Fita tayi zuwa less crowded area ta shiga Calling nasa back wanda tuni ya d'aga kasancewar wayan na a hannunsa yana tsaye bakin gate d'in wane me maula.
   "Ke mahaukaciyar ina ce? Gidan naki ne da zaki kama ki rufeni a waje?"
   "Abeg Mallam free me oo, kai kanka ka fad'a ka ta6a dawowa gida at this time ne? Base bayan Maghrib kake dawowa ba?"
  "Aww! Ma abinda zaki ce kenan saboda bakida tarbiyya koh?"
  "Ai gaskiya ne."
  "Da izinin uban wa kika fita? Na baki izini ne?"
  "Kaman ya kabani izini, baka gida izinin wa kakeso in tambaya?"
  "Aww kuma bakisan ki kirani ki sanar dani a waya ba wato."
   "Banida kati" ta amsa a takaice.
  "Yanzu da bakinki kika kirani ai."
  "K'awata ce ta samin."
  "Whatever come back home this instant kizo ki bud'e min gidana."
  "Gidan biki fa nake."
  "Allah yasa gidan mutuwa kike ki dawo Ruky bana wasa dake."
   "Gaskia nikam da sakel wallahi."
  "Zan sa6a miki kina jina? Wallahi na baki 20 minutes." Ding yayi hanging. Doguwar tsuka taja wane zata cire bakinta. "Allah ya sawaqa wallahi." Dai-dai nan isowar friend inta kenan, "ahh! Ruky Mama ya ana bidiri ke kina anan?"
  "Kibari kawai Mamx, Adeel ne wai ya dawo gida."
  "Meaning?" Ta tambaya tana tauna chewing gum.
   "Meaning na koma gida."
  "Dalili?" Ta sake tanbaya.
 "Nayi locking gida kafin na fito kuma ba key a gunsa."
   "Yo! Bashida gidan friends da zasa kafin nan ne? Nifa banison tak'ura a rayuwa wallahi shiyasa bazan iya zaman aure ba, shikenan mutum bashida 'yancin kansa se abinda wani ya fad'a, mschw!"
  "Kibari kawai Mamx kuma fa be ta6a dawowa gida war haka ba."
  "Ke kinsan meh?" Kai Ruky ta kad'a "ki sharesa kawai, kibari se Maghrib ki koma gida by then an gama duk abinda za'ayi anan."
   "Ke bakisan Adeel da surutu bane wallahi."
  "Ce mai zakiyi key'n motarki ta 6ace da k'yar kika samu."
  "Amman fa kin kawo point wallahi, hakan za'ayi." Hi five sukayi sannan suka koma ciki suka cigaba da karya k'wank'waso.

   Adeel har ya gaji da kiran Ruky Mama, gashi har tak'ara 15mins kan 20'n daya bata amman bata dawo ba, wannan raini dame yayi kama? Cikin motansa ya koma yayi zaman jirarta. Se chan 7:45pm ya hango wutan motarta yana nan zaune a motar har yanzu. A nitse ta fito ta bud'e gate d'in sannan ta k'arisa gun motar nasa tayi knocking bisa window, ko d'aga kai ya kalleta beyi ba, yin hakan sau biyu yasa ta koma motar ta tashiga, tana cikin kunnawa Adeel yasa kai ya shige gidan sannan ya jirata tayi locking kwad'o ta iso ta bud'e musu entrance door. Seda ta shiga yabi bayanta, a parlour ya tarar da ita "sa'an wasanki ne niko?" Yayi snarling at her.
  "Kaman ya sa'an wasa na kuma Adeel?" Binsa takeyi a hankali gudun ya hanata kud'in kashewa.
  "Bansani ba, minti nawa na baki kuma mintuna nawa kika k'ara akai?"
   "Toh ka tsaya mana ka saurari dalili na. Key'n mota na ne ya 6ata a gidan bikin da k'yar na samu."
  "Da kin ganni sanye da pampers ne sekice min haka and expect me to believe you. wallahi Ruky ki sani ba tsoronki nakeji ba just because ina d'aga miki k'afa ina ganin bakida lafiya doesn't mean I can't beat you up, wallahi kinji na rantse idan kika sake taka waje bada izini na ba Allah ya isa na as your husband na kanki, idan kuma bakisan ma'anan hakan ba try it keda mahaliccinki." Yana kaiwa nan ya fice zuwa d'aki inda ya hau tunanin Zeezee.

  Doguwar tsuka ta bisa dashi, "wallahi k'aryanka ne" sekuma ta kad'a kai "ya zanyi yanzu don Allah? Gobe dinner I can't miss it for the world, shi wannan Adeel yanada problem wallahi, mazajen kowa na barinsu suyi yawo amman banda shi mschw wallahi sa'an ka d'aya kafini gaskiya anan dana zaune kan cikinka." D'ayan d'akin ta nufa ta canza kayan jikinta zuwa a light and simple one sannan ta fito ta nufa kitchen. Spaghetti me rai da lafiya ta dafa tare da had'a mai mango juice sanin its his favorite. A dining ta jera sannan ta koma d'akin data fito ta feffeshe jikinta da turare tare da sake seducing shirin dake jikinta. D'akin nasa ta nufa inda ta tarar da shi miqe bisa gado ya zura wa ceiling ido, ko bata tambaya ba tasan tunanin Zeezee yake, ita tun tana kishi ma har ya zame mata jiki, Zeezeen ma ta dawo ita batada case as long as zena bata kud'i ze kuma barta tana fita unguwa ba matsala. Kan gadon ta k'arisa tare da hayewa ta end d'in da yake ta zauna.
   "Baby" ta kirasa cikin wata tantiriyar murya. Ko kallonta ma beyi ba bale yasan tanayi. "Haba! Baby am sorry don Allah." Nan ma banza da ita yayi.
   "Baby yanzu bazaka d'ago ido ka kalleni bama? I said am sorry dagaske key'n mota na ne ya 6ata kaima kasan bazan shanya ka haka kawai a bakin gate ba ai ko? Yi hak'uri kaji I'm sorry."

     Se anan ya juyo yana kallonta, sake bank'aro mai da k'irjinta tayi "tashi muje kaci abinci dinner is ready."
  "Kije kici bana jin yunwa" yayi maganan yana kawar da kallonsa daga gareta cause he is not in the mood, tunanin ya ze dawo da Zeezee ne ke gabansa.
   "Babe kaci lunch ne da zakace baka jin yunwa? Yi hak'uri muje I'll be the one to feed you." Haka tayita lalla6asa seda ya tashin, bayan tayi serving nasa tace zatayi feeding nasa sam yak'i shiwai shi zeci da kansa. Zama tayi gefensa se daddad'un kalamu masu sanya sanyi a zuciya take tayi mai, chan da lokacin bacci yayi ta sake d'aukan wani wankan tasa wasu arnan sleeping dress nata gata daman ba kad'an ba. Shisshige mai ta rigayi daren ranan seda tayi turning nasa on. A ranan ba k'aramin pleasure ta bawa Adeel ba. Da Asuba ta tashesa sukayi wanka sukayi sallah and in the morning ta had'a mai breakfast tare da shiryasa for office. Suna cikin karyawan ta kirasa a hankali yet romantically "Baby." Kaman baze amsa ba yace, "meh?"
   "Baby baka hak'ura ba har yanzu?" Yi yayi kaman be jita ba. "Na fa san kana jina, me kakeso in sake maka domin ka hak'ura? Am sorry kaji?"
  "Naji ya wuce."
  "Meaning kayi hak'urin?" Nodding kai yayi mata "thank you Baby I love you." Nan ma kai ya mata nodding "toh Baby kaja baya da Allah ya isan kenan daga kaina?"
 
   "That's it" yayi exclaiming "ai dama nasan ba tsakani da Allah bane kike duka wannan abubuwan nan da kikeyi."
  "Allah tsakani da Allah ne please kaja baya da Allah ya isan yi hak'uri, bazan sake fita ba seda izinin ka amman incase of state of emergencies kaga ya zama dole, da Allah ya isanka a kaina kuma kaga ai da akwai matsala." Shiru yayi se cin abincinsa yake "Baby ba zaka ce ka yafe ba? Me kakeso for lunch yau?" Kai ya d'ago yana kallonta kaman bazeyi magana ba chan yace, "naji naja baya da batun Allah ya isan, you are free."
   "Yeyy! Thank you" nan da nan ta taimaka masa yagama breakfast, sa6anin kullum yau har gun mota ta rakasa "Baby zan samu 5k please?"
  "Again!" Yayi maganan yana tadda engine d'in motar. "Ke wai ATM machine kika maida nine ko meh? Kullum cikin tambayan kud'i naga ko shi ATM machine d'inma wani sa'in cewa yake ba kud'i."
  "Haba mana don Allah bikin k'awata fa ake shikenan se ana yimata manni ni se in tsaya ina kallonsu? Yi hak'uri please."
   "Ruky banida kud'i kiyi hak'uri yau, dubu nawa na kashe miki tunda muka shiga month d'innan?"
   "Ni ba dogon surutu na buk'ata ba, zaka bani ne kokuwa a'a?"
  "Kema kin amsa da kanki ai."
  "Yama kyau wallahi" tana kaiwa nan tabar mai wajen "sekace ATM machine kullum bani wannan bani wancan, bazan bada ba."
  Itama a ciki se gunguni take tana zaginsa "wallahi ba abincin ranan da zan girka da kai aikin banza kawai." Tuna tasan inda yake ajiye wasu kud'ad'ensa yasa ta saki murmushi sannan ta nufi d'akin. Cikin pocket na wani suit nasa tasa hannnu ta zaro d'imbin kud'ad'de, dubu goma ta zara ta miyar da sauran sannan nan da nan ta shirya gidan biki abinta, dinner'n da se dare za'a soma amman dan neman yawo tun yanzu zata ita.




   *MIEMIEBEE.          Team #YGC!πŸŽ€*
  Beeenovels.blogspot.com
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„

Saturday, 25 February 2017

‘YAR GATA CE!

   *BY MIEMIEBEE*
PAGE 53
  *FEBRUARY, 2017*



Sabuwar rayuwa kowa kuma ya soma living, as for Mama ta shiga zaman takabarta inda take kuma kula da Zeezee, kwana ma tare suke yanzu, don kuwa har yanzu ba wani progress da aka samu game da condition nata. Mama keyi mata komi, da yamma wajajen 5:00pm kuma bayan Omar ya huta from office seya kaita waje zuwa wajen shak'atawa susha iska inda zeyita karanta mata stories. Itama Mama anytime she is less busy tana k'ok'arin karantowa Zeezee stories.
   Anyi haka na kusan sati biyu da 'yan kwanaki Zeezee ta soma magana wanda da kalman 'Baba' ta bud'e bakinta. Mama ta ajiye ta kan couch a d'akinta tana shirya wardrobe nata ta tajiyo muryan Zeezee da she can't remember when last ta jisa. Da gudu ta nufi wurinta tare da riqo hannayenta sede Zeezee tayi saurin wabje su.
   "Baba" ta sake nanatawa.
  "Zeezee? Mama ce ba Baba ba kinji?" Bayan data k'are wa Mama kallo na kusan mintuna biyu se kuma ta miyar da kallonta kan hannunta da take gani jinin Baba ne akai.

   "Baba" ta sake furtawa. Hannun nata Mama ta rufe da nata, "ba Baba anan kinji? Hannunki ne wannan."
   "Kefa wacece ce? Leave me alone please, Baba! Baba!"
  "Mama ce Zeezee baki gane ni ba?"
  "Mama? Nasan kine? Ni Baba nakeso, ina yake?" Zuciyarta taji ya sake karyewa jin wannan kalamu daga bakin 'yarta, kamar ya Zeezee bata gane taba? How is that even possible? Danne zuciyarta tayi ta amsata;
  "Baba yayi tafiya kinji?" Tayi maganan kuka na neman ku6uce mata wanda da k'yar ta samu ta had'iye.
   "Ina yaje? Kice mishi ya dawo shi nakeso ba ke ba."
  "Inda ya tafi ba a dawowa Zeezee, duk wanda ya tafi ya tafi kenan ba dawowa."
   "Ina son in bisa nima ki kaini gunshi."
  "When your time comes zaki bisa kema kinji? In kaiki bayi kiyi alwala kiyi sallah?"
   "Sallah? Meshi kuma? Ni Baba nakeso." Sosai Mama tasake shan mamaki. Me hakan ke nufi? Zeezee ta mance da kowa da komai kenan? Omar ta kira ta gwada tambayan Zeezee waye shi inda ta nuna musu bata san shi bama at all shima. Cike da tashin hankali Mama ta kira Dr tayi mai bayanin komi, "calm down Ma'am I think she must have lost her memories-" katse sa tayi saurin yi da "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un Dr memories fa kace? Kana nufin bata san kowa ba kenan yanzu?"
   "Yes but fatan mu Allah yasa temporarily ne ba permanent ba."
   "Innalillahi! Yanzu in kuma permanent d'in ne fa?"
  "I'm sorry but it'll take morethan a year kafin ta sake ganeku but inhar temporary ne within months zata tuna komi. You can only make this possible by staying close to her always, karki ta6a barinta ita kad'ai. Kuma never give up from making her happy, duk abinda takeso kina yimata kina tuna mata da ko ke wacece, in shaa Allah as time passes by she'll get back her memory."
   "Toh Dr data ce ko Sallah bata sani bafa?"
  "Komi ai yanzu ta mance dashi, her memory is as fresh as that of a baby."
   "Ya Salam!" Ta furta a hankali.
   "Ku cigaba da sata a addu'a in shaa Allah she'll be back to normal."
  "I pray so Dr, thank you."
   "In 3 weeks time call me back muga in har akwai improvement."
   "I'll Dr thank you."
  "You're welcome." Kai zallah ta kad'awa Omar daya saurari wayan da sukayin. "In shaa Allah zata warke Mama don't give up hope." Ya fad'a soothingly.
  "I pray so Omar, dududu da rasuwan mahaifinku sati nawa ne wannan masifa ze sake afka mana."
  "Subhanallah! Mama kisani Allah baya d'aura wa bawansa musibar da baze iya d'aukawa, muyi tawakalli kawai."
  "In shaa Allah Omar thanks for the reminder." Nodding kai kawai ya mata sannan a tare suka dawo da kallonsu kan Zeezee dake ta faman kallon hannunta.
   "Zeezee?" Mama ta kirata soothingly amman ko d'aga kai ta kalleta Zeezee batayi ba se a karo na uku. "Zaki ci abinci Mama na?" Kallon Mama kawai take totally lost.
   "Abinci, zaki ci? Kina jin yunwa?" Har anan kallonta Zeezee kawai take. Suratai ba wanda Mama batayi ba wanda ciki ba wanda Zeezee ta amsa. Kuka ta soma without knowing how, "Omar tabar maganan kuma again.
 Ina zan sa kaina?" Hugging nata Omar yayi yana tapping bayanta. "Shhh! Have faith zata samu sauk'i bi izinillah." Da k'yar ya samu ya fito da Mama daga d'akin yaje ya tsuguna gaban Zeezee dake ta kallonsa shima, se gani take kaman ta sansa. Badon komi ba kuma illa don kaman da Omar da sauran yaran suke ne da Baba, dama chan Zeezee ce kad'ai me kamannin Mama. Hannunta ta aza a hankali akan fuskarsa tana shafawa a hankali. "Baba?" Ta kirashi.
   Kai ya kad'a mata yana murmushi, "Suna na Omar am your big brother ba Baba bane, Omar suna na."
  "Omar? Toh ina Baba?"
  "Yayi tafiya, mesa kika k'i yi wa Mama magana?"
  "Wace Mama?"
  "Farar matar data fita yanzu."
   "Ni ban santa ba."
  "Ni kin sanni? Kin gane ni?"
  "Ba kai bane Baba?"
  "I'm Omar, Ya Omar remember me?"
  "No kaine Baba, ashe ba jinin ka anan" ta nuna mai hannunta. "Babu" ya fad'a yana mata murmushi, "hannunki ne ba komai kinji?"
  "Naji Baba." Kaman ya sake ce mata shifa ba Baba bane sekuma yaga ba amfani.

   "Zaki ci abinci?" Kallonsa ta tsaya yi nufin bata fahimta ba. "Yunwa" yayi pointing cikinsa "zakici abinci?" Yayi tambayan yana immitating da body movement. Kai ta gyad'a masa nufin yes.
   "Toh bari inyi ma Mama magana ta kawo miki." Da wuri ta kama hannunsa ta rik'e "ni o'o kai nakeso."
    "Ga Mama zata sa miki." Kafad'a ta buga "yi hak'uri Baba ni kai nakeso."
  "Toh naji sakeni ina zuwa."
  "Zaka sake tafiya ka barni?"
  "Ai ban ta6a tafiya na barki ba Zeezee" ganin kalamunsa na neman dak'ula mata lisafi yace, "tashi toh muje" haka tana rik'e da kayansa suka k'arisa kitchen yasa mata abincin, tabari Mama tayi feeding nata ma bataso, sam in taga Mama se tayi as if bata magana. Bayan ta gama cin abincin yace da ita "sauran Sallah ko?"
  "Me ma Sallan nanne?"
  "Kin manta Sallah Zeezee?"
  "Eh Baba mesa baka cemin K'anwata yanzu?" Allah sarki seya tuna da Baba, murmushin dole ya k'irk'iro sannan yace, "toh K'anwata sauran Sallah ba?"
 "Baka fad'amin ba meh shi Sallan ba ai."
  "Sallan da yazama wajibi akan kowani musulmi da zaran ya mallaki hankalinsa, wanda ake yinsa 5 times daily, Subh, Zuhr, Asr, Maghrib-"
   "And Isha!" tayi saurin katse sa.
  "Excellent" dad'i sosai yaji ganin memory loss nata beyi affecting educational stuffs nata ba. "Kin tuna shi?"
  "Eh Baba na tuna."
  "Good tashi toh kije kiyi alwala." Nan ma tace batasan me alwala ba seda yayi ta mata kwatance sannan ta soma tunawa, yana alwala tanayi har suka idar sannan yayi mata shimfid'a tare da d'auko mata hijabi.
   "Raka'ah nawa zanyi toh Baba?"
   "Yanzu kinga tunda kika fara rashin lafiyarki baki samu dama kinyi Sallah ko sau d'aya ba, Sallah kuwa idan ba mutuwa ba ba'a yimai uzuri so yanzu zakiyi La'asr raka'a hud'u-hud'u sau biyu, haka zaki cigaba dayi duk Sallan da zakiyi sekina yinsu bibbiyu zuwa nawani tsawon lokaci, innallaha gafurur raheem."
  "Toh Baba" ta fad'a ba musu. Yana zaune agun har ta idar. Da Maghrib ya shirya zasa Masjid nan ta tukuikuiye mai kaya ita karya fita ya barta, ya kaita gun Mama kuma tak'i.
  "Toh kinga idan baki bari na kaiki gun Mama ba zan tafi bazan sake dawowa ba."
   "A'a Baba please karka ce haka nayi al'kawari bazan sake sa6awa umarnin kaba."
 "Good girl tashi muje wajen Mama toh, ba abinda zata miki actually tana sonki ma sosai, bakiga kuna kama ba?"
 "Kama a ina?" Ta tambaya. Tuna halan ma fa yanzu batasan kamanninta ba yasa yace, "bari idan na dawo daga Masjid yanzu tashi in kaiki gun Mama."
   "Baba kace bazata min komi bako?"
 "Eh K'anwata tashi muje." A nitse ya kaita gun Mama tare da umurtanta da tayi alwala tayi Sallah.

   Tana idar da Sallan Mama ta juya ta kalleta "har kin idar Mamana?" Shiru tayi not ready to talk. Danne zuciyarta tayi tace _"kin ta6a jin inda uwa tak'i 'ya'yanta ne? Kisani Zainab kome kikayi min ina sonki saboda ni kad'ai nasan zafin haihuwarki."_ Take Zeezee ta juya tana yima Mama wani irin kallo as if though trying to remember something. Toh aina nasan wannan matar? Ta tambayi kanta.
  Dawowan Omar yaje ya d'auko family album nasu tare da ajiyewa gaban Zeezee dake mak'e a jikinsa. Picture'nta da Mama su kad'ai ya zaro ya miqa mata "wace wannan?" Ya tambayeta yana nuna mata kanta. Kai ta kad'a alaman bata san wace ba, "wannan fa?" Ya nuna kan Mama. Kai ta d'ago tana kallon Mama sannan tace, "itace Matar da kake kira da Mama ko?"
  "Exactly" hannu ya miqa kan dressing mirror tare da d'ago k'aramar mirror ya bata don kallon face nata "laaa! Wannan ba itace na hoton nan ba Baba?"
  "Kinga kuna kama ko? Toh ai kece wannan d'in."
  "Kana nufin nice a hoton nan da kuma madubin?" Kallon kanta ta sakeyi a mirror'n sannan back to the picture, tafa tabbatar itance but how comes? "Taya muke kama da ita toh?"
   "Bari kiga" ya amsa ta. Allah sarki hotonsa da Baba ya ciro ya ajiye mata, "su waye wannan?" Kallon pic d'in take bewildering, ga wanda de take ce mai Baba nan amman kuma k'wak'walwarta na soma ce mata babba na hoton ne asalin Baban nata. Wani irin sara da juyi kanta ya shiga yi mata wanda da wuri Mama ta kar6e album d'in gudun kar ya haifar mata da something bad. Rufe idonta da tayi kawai se bacci, sallan isha da k'yar Omar yasata a gaba tayi ta sake komawa baccin. Da wai sam ita a d'akinsa zata kwana seda yayi dagaske ta yarda zata kwana da Mama.  
     Banda mafarke-mafarken Mama data yitayi ba abinda ta tsinana a baccin, se raya mata mind nata ke tasan Mama.

  Haka a hankali a hankali Omar ke flashing wa Zeezee da old memories nata back har tazo ta gane ba shine babanta ba, toh ina Babanta yaje? Ta fannin Mama kuwa, ta soma sakewa da Mama ganin how free they are da Omar, a kullum idan suna zaune da Mama ba abinda take banda flashing mata back memories nata cikin ikon Allah Zeezee ta soma tuna Mama da sauran 'yan uwanta anan ta gane Omar ma ashe yayanta ne. Duk hakan yafaru ne within 3 weeks da Dr ya fad'a.

   Yau tana zaune a parlour ita kad'ai chan Mama ta shigo d'aukan ruwa, binta da kallo Zeezee tayi seda tazo gab da fita ta furta "Mama" a hankali. Wani dad'i sosai Mama taji wanda ta kasa 6oyewa seda ta zubda k'walla.
  "Mama, kece?" Ta tambaya Tana kallon cikin idanunta.
 "Nice Mama na, Mama ce Zeezee" da gudu Zeezee ta miqe taje tayi hugging Mama tana kuka sosai, itama haka Maman.
   "I love you Mama, I love you so much."
  "Ya Allah thanks for bringing back my daughter for me, I love you more sweetheart."
   "Ina Ya Ibraheem, Mariam, Omar and Yasmeen?"
  "Duk suna nan kina son musu magana?"
  "Eh Mama amman kafin nan ina Baba?"
  "Kin manta inda Baba yaje Zeezee?"
  "Wai yayi tafiya inji Ya Omar amman k'arya ne ko?" Kai Mama ta gyad'a mata a hankali.
   "Tell me ina yake toh?" Chan k'asa-k'asa tace;
   "kin manta Baba lokaci yayi?"
   "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Take idanunta suka sake kad'awa, "Mama yanzu Baba ya tafi ban nemi tubansa ba kenan? Baze sake dawowa ba?"
   "Zeezee Baba ya yafe miki" hak
 kalamun da Baba yace ta fad'awa Zeezee Mama ta sake nanata mata su "kinji? Ya yafe miki for a very long time now."
   "Mama ba k'arya kike min bako?" Ta tambaya tana hawaye.
   "Taya zan miki k'arya Zeezee? Babanki ya yafe miki komi, he asked me to tell you in person and that he misses being with you."
   "Nima na yafe masa Mama, I miss him so much" tasa kuka. "Shhh!" Mama tayi hugging nata "he is in a better place in shaa Allah." Kuka Zeezee ta shiga yi sosai, da k'yar Mama ta samu ta sata tayi shiru sannan tayi waya ta had'ata da Ibraheem.  Sosai Ibraheem yaji dad'in having his little sister back. Tubansa Zeezee ta nema inda ya nuna mata ya yafe mata for a very long time now, haka Mariam and Yasmeen ma.
  Getting to 4 Omar ya dawo from work, tun a bakin k'ofa Zeezee ke jiransa. Tana ganinsa ta mai oyoyo shima tare da neman tubansa, he can't ask for more his little sister is back. Dr, Mama ta kira ta sanar dashi this great news.
 "Semu godewa Allah gashi within three weeks d'in tayi getting back memories nata, am so happy for you people."
   "Thank you Dr, thank you so much."
  "Allah k'ara mana lafiya gabad'aya."
  "Ameen" ta amsa "se anjima mun gode."
  "Yauwa sannu" yayi hanging.

***
   Tun daga ranan Zeezee ta sake maida hankalinta kan ibadan ta sosai, a day never goes by ba tare da tayi tunanin Babanta ba ta zubar da hawaye, kullum kuwa cikin yimai addu'a ita da Mama suke. 2 weeks after samun sauk'in ta akayi rabiyar gado inda magada suka samu d'imbin arzikin mahaifinsu. Dukansu sunyi amfani da kud'in sunyi aikin lada dashi inda suke baran Allah ya kai ladan kabarin mahaifinsu. Banda Zeezee data yi amfani da rabin kud'in gadon nata gabad'aya don tallafawa addinin musulunci zallah. Saura takai  masallatai da gidan maryu saura gidan television da radio na yad'a muslinci da sunnan annabi. Inda tayi baran Allah da ya kai ladan duka kabarin mahaifinta. Zeezee bata tunanin komi yanzu banda addinin ta, mahaifinta da kuma Ya Al'ameen nata ko tunanin Adeel da Mama ta bata labari cewa ya kawo cartons na Malt guda biyu a rasuwan Baba batayi saboda ta riga ta ciresa a ranta kwata-kwata. Ya Al'ameen ne kawai a ranta.
   Islamiyya tayi joining inda kullum take cikin nik'af da dogon hijabi saboda batason ana gane mata fuska don har a yau tasan baza a rasa mutanen da zasu na kwatanta taba da wacce tayi sanadiyar mutuwan mahaifinta. A takaice de Zeezee an koma ga Allah.
   Sau dayawa takan zuwa gidan Mariam ta kwaso Ramlah da Ummie suzo suyi mata weekends, ba k'aramin son babies Zeezee ke ba yanzu musamman idan ta tuna ita bazata iya haihuwa ba. Tsaf zatayi musu wanka ta shiryasu ta kaisu gidan kitso kokuwa shopping suka zo kwana ma a d'akinta suke kwana. On working days kuma tun safe zata tashi tayi shara tayi mopping ba aikin da Zeezee batayi wa Mama, har wanki atimes. Kullum cikin sambad'a mata albarka Mama take tana cewa da Babanki na nan he would have been damn proud of you.

   ***
  Ta side na Adeel kuwa har yau ya kasa cire Zeezee daga ransa, da tunanin Zeezee yake tashi ya sake yini. Rayuwarsa da Ruky sam ba dad'i. Acikin ikon Allah Ruky ta sake samun wani cikin wanda a 5 weeks tayi 6ari komi ya 6antare, yanzu haka ma tana gida. Adeel daga ya dawo daga aiki se zaman d'aki wane amarya ko kira yaji ya jikin Ruky ma baiyi. Da yamma yau ya watsa ruwa ya shirya tsaf ya nufi unguwan su Zeezee, gaba da gidansu kad'an ya faka sannan ya fito daga motar yana dube-dube wanda shi kansa be san fa'idar yin hakan ba.
   5:30pm su Zeezee suka taso daga islamiyya, cikin nik'af nata take takowa gida. Don yadda Adeel ya mugun saninta daga tafiyar ta ma yagane itan ce sede he is still doubting. Da sauri-sauri har yana neman cin tuntu6e ya tinkareta tare da yin sallama. Wani irin mumunar fad'uwa gabanta yayi jin muryan Adeel, saboda a rayuwa baza ta ta6a mancewa da muryanshi ba. Kasa d'aga kai ta kallesa tayi a yayinda hawaye ke forming rapidly a idonta.
   Gefensa tabi da wuri ta wucesa sede kafin tayi nisa ya sake shan gabanta. Gefensan ta sake kuma bi wanda yanzu da sauri yayi blocking nata, d'ayan side nasa ta koma zata bi, nan ma yayi blocking nata.
   "Zeezee please answer me, koda bazaki min magana ba ki amsa sallama na." Har anan takasa d'aga kai ta kallesa. "Zeezee bada wata manufa nazo miki ba, ta'aziyya nakeson miki-" katse sa tayi da wuri, "naji nagode Allah ya bada lada, excuse me." Ta fad'a a takaice.
   "Zeezee please one more thing."
   "Malam inba wai so kake na tara maka jama'a ba ka matsa min a gabana."
   "Zeezee pl-"
  "One..." ta shiga counting "two..."
  "Am sorry" ya katse ta ganin how serious she is, "inhar hakan kikeso so be it but kisani Zeezee I will never rest until kinyi forgiving d'ina I want you to know that nayi regretting dukkanin abubuwan dana miki. Sharrin shaitaan ne ba komi ba wallahi, I love you morethan I can ever explain Zeezee please forgive me. Wallahi hak'k'in ki har a yau bina yake da Ruky, at first ta haihu d'an ba rai yanzu ta sake miscarrying baby'n forgive us please."
   "In don wannan ka d'ibo k'afafunka all the way here kasani ni na jima da yafe muku abubuwan da kuka yimin. We are all human beings and not above making mistakes, ni kaina me laifi ce, Allah ya yafe mana gabad'aya." Tayi maganan not looking at him at all. Ba k'aramin burgesa kalamunta sukayi ba, "thank you Zeezee, thank you so much I shall never forget this. You are indeed one of a kind, Allah saka miki da mafificinsa, ameen." Ba tare da ta sake cewa dashi k'ala ba tabi gefensa ta fice. Wani irin farin ciki ya tsinci kansa ciki atleast ya sauk'e wani abin, yanzu tunanin ya zeyi ya dawo da ita gidansa yake. From yadda Zeezee ke acting yasan it'll be hard for that to happen amman karkacaccen mind nasa se tunzirasa yake kan lallai fa ya dawo da ita. Shigan Zeezee ciki kuwa bata nunawa Mama Adeel yazo wajenta ba saboda bata ga amfanin hakan ba. Uniform nata ta tu6e taje ta samu Mama a kitchen suka gama had'a dinner.

  Washegari exactly time da Adeel yaga Zeezee jiya yau ma ya shirya yana jiranta. 5:35pm sega tanan, da wuri yaje ya sameta yana mata sallama sede ko sauraronsa batayi ba, binta yake tayi har seda ta kusan isa gida sannann yasha gabanta.




 
*MIEMIEBEEπŸ‘„.       Team #YGC!πŸŽ€*
 Beeenovels.blogspot.com
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„

Thursday, 23 February 2017

‘YAR GATA CE!

    *BY MIEMIEBEE*
*PAGE 52*
   February, 2017



Tun wajajen 7am Mrs Mukhtar taji rasuwan Baba wanda Mama ta sanar da ita ta broadcast mssg da aka yiwa kowa, amman ta rasa ya zata fara sanar da Zeezee. Da k'yar ta samu tayi gathering courage bayan k'arfin guiwan da mijinta ya bata ta shiga d'akin Zeezee tare da yin sallama.  Alokacin har Zeezee tagama shirinta tsaf sauran tafiya kawai take jira don taje ta duba lafiyan mahaifinta. "Wa'alai kumus salam. Ina kwana Aunty?" Ta gaisheta cike da ladabi.
  "Lafiya Zeezee har kin shirya ne?"
  "Eh, Aunty."
  "Bazaki karya ba toh?"
  "A'a sena dawo zanje naga lafiyan Baba tukunah." Nan fa Mrs Mukhtar ta sake jin bazata iya sanar da Zeezee ba mutuwan mahaifinta but tasan she have to.
  "Zainab." Daga yadda ta kira ta yasa gaban Zeezee fad'uwa danko bata ta6a kiranta da Zainab ba sede Zeezee.
   "Na'am Aunty?"
  "Zeezee..." sekuma tayi shiru.
  "Zeezee kinsani cewa duk me rai mamaci ne ko? Kowa a duniyan nan ze mutu wataran ya koma ga mahallicinsa ko ba haka ba?" Dum! Gaban Zeezee ya sake fad'uwa sede sam bata kawo a mind nata wai rasuwa mahaifinta yayi ba.
  "Aunty me kike nufi?" Kad'ai ta iya furtawa tana kad'a kai a yayinda hawaye ke forming rapidly a idanunta wanda ita kanta batasan dalilin hakan ba.
   "Zeezee you are no more a child ya kamata in sanar dake gaskiya, Baba lokaci yayi, Allah yayi mai cikawa yau da daddarre wajajen k'ar-" bata kai da idda maganan ba kawai taji rigijib! Fad'uwan abu a k'asa. Da gudu ta yo kan Zeezee only to find her fainted (a sume.)

   "Innalillahi! Zeezee! Zainab!" Bangida ta nufa ta ibo ruwa ta yayyafa mata sede ko motsawa Zeezee batayi. "Mukhtar! Mukhtar!" Tashiga k'walla wa mijinta kira wanda ya fito a gigice.
   "Mukhtar! Zeezee, Zeezee please do something."
   "Jeki d'auko key da wuri" ya buk'aceta a yayinda ya cinci6i Zeezee se asibiti suka yo inda akayi emergency ward da ita. Taimakon gaggawa aka shiga bata a yayinda hankalin Mrs Mukhtar ya kasa kwanciya. Cikin ikon Allah Dr's suka samu suka farfad'o da Zeezee sede gabad'aya bata cikin hayyacinta banda "Baba, Baba" da take ta furtawa.

   "Dr how is she?" Mrs Mukhtar tayi saurin tambayan Dr'n hankali a tashe.
   "She'll be okay in shaa Allah amman kome ya sameta?"
  "Dr rasuwa akayi mata, mahafinta ne ya rasu. In the process of breaking the news to her seta yanki jiki ta fad'i."
  "Ohh ayyah, Allah yaji k'anshi da rahma."
  "Ameen" both suka amsa.
  "Shi dama mutuwa haka yake but karku damu in shaa Allah zata samu sauk'i. She is just psychologically affected wanda hakan is normal."
  "Toh Dr mungode" cewar Mukhtar.
  "Zamu iya shiga ganinta?" Asked Mrs Mukhtar.
  "Sure please, excuse me" Dr'n ya amsa tare da ficewa. Nan suka shiga d'akin Zeezee inda take nan kwance bisa gado tamkar wata zararriya ta koma, se ambaton "Baba, Baba" kawai take. Duk kalan suratai da sannu da Mr and Mrs Mukhtar suke mata ba jinsu take ba.
   "Ku kaini gun Baba, Baba be mutu ba inya ganni ze tashi ya koreni saboda ya hanani taka duk inda yake. Ku kaini gunsa please nasan be mutu ba."
   "Zeezee bakida lafiya, kibari zuwa anjima idan kika d'an ji sauk'i." Mrs Mukhtar tayi explaining calmly.
   "Ku kaini gun Baba don Allah ku kaini wajen shi" kuka take sosai me tsuma zuciya. Ganin yadda take kuka sosai yasa dole Mr Mukhtar yama Dr magana akayi discharging nasu. A sannu a sannu Mrs Muktari tasa Zeezee a mota suka nufi TH inda su Mama suke.
   A lokacin da suka isa ma su Mama da sauran dangi suna shirin komawa gida ne da gawan Baba don cigaba da kar6an gaisuwa achan. Ko ta kan Mama Zeezee batayi ba da gudu taje ta rungume gawan Baba dake a lullu6e kan gado.

   Kuka take wane don shi aka kawota duniya, ba wanda yace da ita k'ala illa ma kallonta da suke suma suna kukan.
  "Baba nasan baka mutu ba, nasan kana jina, please say something you can't die, we need you alive. Baba bazeyi ka mutu ban nemi tubanka ba, please come back Baba. I need you to forgive me please come back. Baba ni ya kamata in tafi saboda kasamu kasha iska, ba kai ka tafi ka barmin duniyan ba. Please come back" ta k'are maganan tana jijjiga gawan Baba.
   Ihu ta rushe dashi ganin be mata magana ba har yanzu assuring her he is gone forever no coming back. Matse jikin Baba tayi a nata tana hugging nasa sosai. Mariam ce tayi k'arfin hali tace da Mama, "Mama ki fad'a mata Baba ya yafe mata please." Ita kanta Zeezee ta bata tausayi, itan da sukayi sharing happy moment with Baba ma kenan kafin lokacinsa, bale ga Zeezee da Baba ke fushi da ita for a very long time. A nitse Mama ta miqe ta nufi kan Zeezee tare da patting bayanta.
  "Zeezee ya isa haka kinji? Taso yi hak'uri."
 
  "No Mama don Allah kar ku fita da Baba wallahi be mutu ba yana jina, ku tsaya kuga ze tashi yace in fita mishi daga d'akinsa. He is not dead listen to me please."
   "Zeezee kibar magana haka da rungumar k'addara aka san musulmi. Baba lokaci yayi amman jiya ya bani wasiha na fad'a miki. Yace _ya yafe miki duk abubuwan da kika masa duniya wa lahira, da 6oyayye da kuma bayyananne. Yace min yau in Allah ya yarda ki koma gida ki cigaba da zaman ki achan, chan ne gidanki. Yace min he wants you to know that you'll forever bs his little sister and daughter and that he loves you so much Allah ya miki albarka ya baki 'ya'ya na garin da zasu kula dake ya kuma baki miji nagari and lastly kema ki yafe masa abubuwan da ya miki._" Mama ta k'are maganan cikin kuka sosai wanda seda yasa duk wani mahalukin dake gun kuka banda kaman Zeezee. Within seconds kuma se aka ji kukan nata ya d'auke. "Zeezee?" Mama tayi saurin tapping nata only to found her fainted body. Sumanta na biyu kenan, nan da nan akayi next room da ita inda aka shiga bata taimakon gaggawa ciki harda drip da aka samata saboda low water and sugar level data samu a safiyan yau, bayan nan ga yunwan da yaci jikinta wanda ke neman haifar mata da gastric ulcer. Alluran sa bacci aka yi mata, seda Dr ya tabbatar wasu Mama she'll be alright hankulan su yad'an kwanta. Mrs Mukhtar da Mariam aka bari akanta a yayinda sauran duk suka nufi gida don cigaba da kar6an gaisuwa achan.

   ******
   One hour sleep Zeezee ta samu sannan ta tashi da gaggaramin yunwa. Fuskan Mariam ne ya soma mata sallama, da wuri ta share hawayenta tare da mata "sannu" sede wani irin kallon da Zeezee keyi mata. Kafin ta hankara kawai taga Zeezee na neman 6alla connection na drip da aka sa mata. Da wuri Mariam ta haneta da yin hakan. "Ki sakeni Adda Mariam."
   "Zeezee What are you trying to do?"
   "Rayuwa ta bata da sauran amfani Adda Mariam I can't bear the thought that ni na kashe mahaifina."
   "Inji wa ke kika kashe Baba?" Mariam tayi maganan still not letting her go saboda yadda Zeezee keta faman k'watan kanta.
  "Ni na kashe shi Adda Mariam, nice silar rashin lafiyan dayayi sanadiyar mutuwarsa, I killed my own father Adda Mariam" ta rushe da kuka sosai.
   "No you didn't Zeezee, Baba lokaci yayi ba abinda muka isa muyi, rashin lafiya kuwa Allah ya riga ya k'addara masa shi tun kafin ya shigo duniya so stop blaming yourself kinji?"
  "That's not true, that's not true Adda Mariam just go leave me in kashe kaina nima yaso naje na sameshi achan lahira in nemi tubansa."
  "Wani tuba kuma again Zeezee bayan Baba yace ya yafe miki?"
   "That's still not true kawai Mama ta fad'a ne don kar hankalina ya tashi nasani Baba be yafemin ba nikuwa bazan iya cigaba da rayuwa da hak'k'in Baba akaina ba I'd rather commit suicide."
   "Get your senses together Zeezee, Baba ya riga ya yafe miki shike neman yafiyarki kema."
   "Meya ta6amin da ze nemi yafiya na?" Ta ce tana kuka sosai.
   "Kede kice kin yafe mishi saboda muma duka kafin... kafin" sekuma ta rushe da kuka "kafin lokacin sa yayi seda ya nemi tuban mu don haka nakeson kice mishi kema kin yafe masa."
   "Tunda Baba yake raye ban ta6a farinta mai ba, banda asara, bad luck da ciwon zuciya ba abinda na jawo mishi Adda Mariam, I know I am his worst daughter and child I can't ever forgive myself gani nake my hands are stained with his blood. Inhar abinda Baba ya buk'ata kenan kafin ya tafi ya barmu, toh ni na yafe masa har abada."

   Hugging nata Mariam tayi inda suka cigaba da kuka sosai. Tsan-tsan yunwa ko tsayuwan minti d'aya Zeezee ta kasa, wai ahaka ma don da taimakon drip da aka bata. Ba yadda Mrs Mukhtar batayi da ita ba taci abinci tak'i. Da k'yar suka samu tasha black tea se kuka take tana su kaita gida gun Babanta. Ta gama kur6e tea'n suka d'au hanyan gida.
   Dam gidan nasu yake cike da mutane da k'yar suka samu gu sukayi parking, da k'yar Zeezee ke tafiya ahaka ne har suka k'arisa ciki suka cigaba da aikin kuka.

***
   11:40am su Yasmeen suka iso a yayinda su Ibraheem suka iso wajajen 12::50pm. Kuka de ba babba ba yaro. Tabbas iyalan Late Alhj. Isma'eel Yusouf sunji wannan mutuwa na sosai sabida tun da suka taso wani na kusa dasu be ta6a mutuwa ba se akan mahaifinsu wanda suke matuqar sonsa fiye da yadda suke son kawunan su, its indeed a great lost to them, Allah ya jik'an Baba ya kai rahama kabarinsa, Ameen thumma ameen.
   K'arfe 01:20pm aka zo fita da gawan Baba wanda yake ajiye akan makara a d'akinsa inda aka fito dashi tsakar gida aka ajiye don bawa iyalansa daman yimai kallo da kuma addu'a na k'arshe. Hajiya Mama, mahaifiyarsa ce ta soma fitowa da taimakon k'annen Baba aka kaita gaban gawan d'anta. Banda kuka ba abinda takeyi. Da k'yar ta iya ya ta yaye laqafanin izuwa wuyansa sannan a sannu a sannu ta aza hannunta kan fuskarsa tana shafawa in a soothing yet pathetical manner "Allah ya ji k'an ka d'ana, har a kullum ina alfahari da kai ban ta6a nadaman haifanka ba. Na yafe maka dukannin abubuwan da kayimin na 6oye da bayyananne, ko da gan-gan ko rashinsa. Allah yayi maka rahama ya dubi kalan alkhairun da kayimin a rayuwa ya saqa maka da mafificinsu, ya d'aukaka darajarka a cikin shiryayyun bayinsa kuma ya maye maka bayanka a cikin wad'anda ka bari, yasa mutuwa hutu ce a gareka, ameen." Add'uan da akeyiwa mamaci ta biyosa dashi wanda duk gun suka amsa da "ameen."

   Mama was tha next person, itama guiwa ba k'arfi ta k'arasa gun da gawan ke shinfid'e. Kuka take sosai itama ta yaye fuskar nasa, nan fa sabon kuka ya sake fin k'arfinta. Addu'o'i sosai tayita yiwa Baba akan wanda tayi mai d'azu bayan data gama yimai addu'an ta had'a musu hannunsu se kuka kuma, ta tashi daga gun ma ta kasa seda su Mariam ne suka d'agata. Ibraheem ma kuka yake sosai ya k'ariso gaban gawan tare da yaye liqafanin, kuka yake sosai wane d'an yaro daga k'arshe yayi mai addu'a shima sannan ya tashi ya koma. Next was Mariam itama se kuka, duk according to their ages suka rik'a fitowa suna kuka sosai suna yiwa mahaifinsu addu'a. Kasancewar Zeezee ce auta, ita aka buk'ata last ta tako zuwa gaban gawan ma takasa, Yasmeen ce tayi assisting nata. Zubewa tayi a wajen se kuka tama kasa ta6a gawan bale tayi mai addu'a. Hannunta 6ari yake sosai ta d'aga da k'yar ta iya ta yaye liqafanin, nan fa ta sa wani irin kuka me tsuma zuciya. Hugging nasa tayi sosai "Baba I cannot live without you, you need to come back nasan baka mutu ba kanaji na, please say something inason inji da kunnuwa na ka yafemin, I want to be in your arms one last time, please come back you can't die. I want to make you happy one last time, nasan tunda aka haifeni I've been nothing but bad luck to you, Baba don Allah ka dawo nayi alk'awari to make you happy and proud. I'll never go against your command not even your wish, please Baba come back" ta sake sa wani erin kuka.
   "Mariam kuje ku d'agota" cewar Mama ganin kukan Zeezeen bana k'arewa bane. Guiwa ba k'arfi Mariam ta miqe ta nufi gun Zeezee tare da jan hannunta "tashi Zeezee yi hak'uri Baba ya riga ya yafe miki muma duk mun yafe miki."
 
   "Thats not true, ki sakeni ki barni dashi don Allah."
   "Zeezee ya isa please za'a fita dashi yanzu." Ganin abin ya gagari Mariam, Yasmeen ta shiga taimaka mata sede ina sun kasa d'ago Zeezee daga jikin Baba don yadda ta matse sa gagam a jikinta. Kuka take sosai na hak'ik'a tana sunbatu. Daga k'arshe seda Mama tasa Ibraheem daya je ya d'ago Zeezee. Shima seda yayi dagaske ya samu ya d'agata nan fa ta tada bori ita subarta a jikin babanta. Wani abin ma seda aka zo d'aukan gawan Baba za'a fita dashi.
   "Baba! Don Allah ku dawo min da mahaifina wallahi be mutu ba, karku tafi dashi don Allah I'm begging you guys please don't take him away." Idanunta da suka canza launi da komi ta d'ago tana kallon Ibraheem daya rik'eta gagam pathetically.
   "Ya Ibraheem nasan kana son Baba please don't let them take away Baba from us, ka musu magana su dawo mana dashi I beg of you please." Kuka yake har anan ya kasa ce mata komi nan ta kewayo da kallonta kan Mariam da keta faman kukan itama.
   "Adda Mariam, I know you love Baba so much please don't let them take him away." Anan datayi maganan har mutanen sun kai ga fita da gawan waje, wani irin ihu ta k'urma wanda tuni Ibraheem ya sake ta nan tasa gudu. Ta kaiga iskesu wasu maza suka samu suka rik'eta nan Omar ya kar6eta daga hannunsu. Se bori take tana ihu a dawo mata da Babanta. "Mama don Allah karki bari su fita mana da Baba wallahi be mutu ba." Da k'yar Omar yaja ta tare da zaunar da ita gefen Mama, ganin tana da niyyan tashi su Yasmeen suka danne ta. Sahun gawan su Ibraheem suka bi domin samun sallatan mahaifinsu.

   Tunda aka fita da gawan Baba, Zeezee ta tabbata fa yanzu shikenan Baba ya riga ya tafi ko shadow'nsa bazata sake gani ba bale taji muryansa kokuwa dariyansa, ya tafi kenan har abada no coming back. Nan ta fita daga hayyacinta gabad'aya, gatanan a zahirce a gidan amman hankalinta bayi nan ko kad'an. Ta had'a wani tagumi se hawaye kawai take zubarwa wane lalacaccen famfo.

    ***
   Cikin yardan Allah aka sallaci Baba a Gwallaga Central Mosque inda ya samu thousands and thousands of people da suka sallacesa suka kuma rakasa makwancinsa. Ibraheem da Omar akayi susa gawan Babansu a kabari amman ina sun kasa tsan-tsan tausayi da kuka. K'annensa biyu suka sa sa tare da yimai final addu'a sannan aka bisine sa. Allah yaji k'ansa ya kyautata k'arshen namu muma, ameen.

****
   Gida se cika yake ba ko inda mutum ze sa k'afa. Dangi from other states gabad'aya sun samu zuwa se aikin kuka ake ba babba ba yaro, inda wasu ke hirar mamaci. Dayawa ke cewa Zeezee ce silar mutuwan Alhj Isma'eel tunda a sanadin ta ne ya soma kamuwa da ciwon zuciyar da har yayi leading to mutuwarsa, a inda wasu kuma ke cewa itance ma ta kashe sa kawai. Wannan maganganu su suketa yad'uwa har a cikin gari. Daga k'arshe fita Zeezee tayi daga gidan da gudu gabad'aya ta nufi gidan Mrs Mukhtar dan kunnenta bazasu iya cigaba da jiye mata wad'ancan munanan kalamu ba na cewa ita ta kashe mahaifinta. Kallon hannunta kawai take se gani take wai ga jinin Baba nan kwance jina-jina akai. Hak'uri Mrs Mukhtar keta bata. Tun daga wannan lokaci Zeezee bata sake sanin inda take ba.

   A washegarin rasuwan ne Adeel yajiyo rasuwan Babansu Zeezee wanda ya mugun tausaya mata sosai har hawaye seda ya zubar mata, tuna yadda take jijji dashi even before suyi aure. Koda yace tayi abu se tace ita Babanta fa, har ma yake neman tasokanarta da 'Daddy's girl.' Gani yake he is partially to blame shima saboda shi yasata ta bijire wa mahaifin nata wanda yayi causing masa wannan cutar da tayi sanadin mutuwarsa.
  Tsaf shida Ruky Mama suka shirya suka zo yin ta'aziyya, hannu bibbiyu aka kar6esu duk da sanin komi started with Adeel. Bayan ya gaishe da Mama yayi mata ta'aziyya ya buk'ci ganin Zeezee inda Mama ke sanar dashi cewa bata gida a haka ma yanzu batada lafiya. Still yayi insisting yana son ganinta a tunaninsa kawai hanasa ganin Zeezee Mama keson yi. Seda Mama ta fayyace masa gaskiyan al'amari na cewa koda zeezee ta gansa yanzu ba gane shi zatayi ba saboda condition da take ciki. Ko jiya da Mama ta aika aje a duba mata ita chan gidan Mrs Mukhtar bata gane su Mariam ba, sede tayita kallon mutum tana kallon hannunta amman ba kalman k'ala.

   Wani irin tausayawa Zeezee ya sakeyi if only there's something he can do. Fatan lafiya yayi wa Mama sannan ya ajiye carton na maltina biyun daya kawo musu suka koma da Ruky. Itama Ruky gabad'aya ta tsorata da mutuwan Baba tuna fa alhak'in Zeezee na sharrin data yi mata na kanta har yanzu, dole ta nemi tuba.

   Al'ameen kuwa a sadaqan uku ne Mama Babba ke sanar dashi rasuwan Baba. Sosai ya tausayawa Baba dakuma iyalansa most especially ma Zeezee da har yanzu take da gurbi a zuciyansa.  Dukda auren da Mama Babba keson had'asa da wata 'yar uwarsa Murjah, hakan besa ya dena son Zeezee ba ya kuma fara son ita Murjan. Infact her love increases in him every single heart beat. Auren biyayya kawai zeyi saboda shi har yau bega mace ba bayan Zeezee, sonta a jinin sa yake despite abubuwan da tayi mai he still loves her like so much.

   A ranan da yaji rasuwan ba tare da 6ata lokaci ba ya kira Mama yayi mata ta'aziyya, yaso ace yana gari don ya samu daman expressing masu condolences nashi. Layin Zeezee itama ya buk'ata don yimata ta'aziyyan saboda ya gwada wanda ke gunsa it aiint going through.
    Anan ne Mama ke sanar dashi halin da Zeezee ke ciki. Sosai masoyin hak'ik'an ya sake tausayawa Zeezee. If only there's something he could do.
    Abu fa kaman wasa se worsening condition na Zeezee ke tayi, se kaman neman zarewa take ne oho, abun kaman hauka. In anji sautin muryarta toh tana kuka ne. Magana ma tabar yi, ko bayi takeji in bawai anyi timing nata bane an kaita sede tayi a jikinta, cin abinci, sallah komi nata ya tsaya kat! Abu kaman wasa-wasa har akayi sadak'an bakwai Zeezee bata san inda take ba gata nan ne kawai se yadda akayi da ita. Bayan sadak'an bakwai ne lokacin da mutane suka gama watsewa, wanda suka rage befi a k'irga ba. Se a nan ne hankalin Mama da sauran yaranta ya dawo jikinsu akayi wur-wur aka d'auko Zeezee daga gidan Mrs Mukhtar aka kaita asibiti. Bayan dogon nazari da bincike da Dr yayi ya nuna musu cewa ba abu neba na damuwa saboda hakan is normal ga duk wanda mutuwa ya ta6a sa sosai, she is psychologically and even mentally affected at her own case, but in shaa Allah bayan d'an wani lokaci she'll be back to normal. Wanda kafin nan ya zama dole a kullum ana karanta mata labarai masu dad'i masu sanya nishad'i dakuma kaita leisure places saboda yayi erasing bad memory'n dake lingering akanta na cewa ita ta kashe mahafinta. Har izuwa ga wannan lokaci kuwa koda wasa kar a mata furucin da bashida dad'i. A haka ne su Ibraheem suka dawo da ita. The next day Ibraheem da iyalansa harma da Yasmeen suka juya, inda suka ajiyeta a KD sannan suka zarce Abj. Mutuwan Baba har a yau kaman sabo yake a memory'nsu, they shall never forget about their beloved father.



 *MIEMIEBEE.        Team #YGC!*
Beeenovels.blogspot.com
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„

Tuesday, 21 February 2017

‘YAR GATA CE!

  *BY MIEMIEBEE*
Page 51
 *FEBRUARY, 2017*

Blog readers how are you guys coping with this version? Lemmi know your opinions please, ILY'all❤


     "Eh Alhj" nan da nan Mama tayi placing Ibraheem on the line. A lokacin wayan nasa na a hannun Hafsah 'yarsa wacce suke kira da Maamah tana game. 'Yar tasa sak shi ba abinda ya rabasu, haskensa ne kawai bata gama ibowa ba ta d'an had'a da duhun mahaifiyarta. Ganin hoton Mama yayi displaying akan screen d'in tayi saurin kai wa Ibraheem da Fateemah da suke zaune a d'akinsu wayar.

  "Daddy! Daddy! Maman Daddy is calling you."
   "Dagaske? Kawo in gani toh Maamah na."
  "O'o Daddy ina game."
  "Yi hak'uri muna gamawa zan baki."
  "Ni o'o."
  "Yi hak'uri Maamah ki basa kinji?" Cewar Fateemah dake lullub'e cikin bargo da alama laulayi ke damunta.
  "Zan baki nawa."
  "Ni banashon naki."
  "Yi hak'uri kiban ze yanke, ga chan ice cream naki a fridge jeki d'auko."
  "Yeyy!" Kai mai wayan tayi da gudu sannan ta nufa fridge ta d'au ice cream d'in ta shiga sawa a armpit (hammatarta) hakan ba k'aramin dad'i yake mata jin sanyi-sanyin. Fateemah na kallonta aman batajin zata iya mata magana saboda tasan 6ata lokacinta kawai zatayi dan kuwa ba jin magana Maamah ke ba, halinta sak na Zeezee dukda taka mata birkin da Ibraheem ke, gado ba gwaninta ba.

  Kasancewar wayar ta yanke yayi calling Mama back.
   "Assalamu Alaikum Mama."
  "Wa'alaikumus salam Babana ina wuni?"
  "Lafiya Mama ya gajiya? Kin kira wayan na hannun Maamah tak'i bani."
  "Takwaran nawa ko? Ya jikin Fateemah kuma?"
  "Alhamdulillah da sauk'i" ya amsa yana kallon Fateemar, daga nesan tamai whispering "kace mata ina gaisheta and ta gaida Baba da jiki." Nodding yayi sannan yace, "tana gaishe ki da Baba da jiki, ya jikin nasa?"
   "Toh alhamdulillah de shi yace in kiraka ma yanzu yana son kuyi magana."
  "Allah sarki ki bashi toh."
  "Yauwa" a speaker phone ta danna sannan ta matso wa Baba da wayar kusa dashi "ga Ibraheem d'innan Alhj."
  "Aina?" Ya tmbaya nan Ibraheem ya amsa "gani nan Baba sannu ko? Allah baka lafiya."
  "Ameen Ibraheem Babana, Allah yayi maka albarka."
  "Ameen Baba gobe in shaa Allah zan shigo in duba ka."
  "Toh Allah ya kaimu Baba na nace ka yafemin rashin adalcin danayi a tsakaninku tunda kuke yara, Baba yayi kuskure ka yafe mishi kaji?" Jin haka Ibraheem ya d'au k'afa ya fice daga d'akin nan Maamah ta shiga binsa tana kiransa da wuri Fateemah ta tareta tare da dawo da ita cikin d'akin. Dining chair yaja ya zauna gabad'aya jikinsa yayi sanyi, "Baba wani irin magana kuma kake haka?"
  "Yi hak'uri ka yafemin Babana."
  "Baba nifa ba abinda kamin, ni yakamata in nemi tuba a gareka ba kai ka nema a guna ba."
  "Bazaka iya yafemin ba Baba na?"
  "Baba inhar yafiya na kakeson ji toh ni na yafe maka duniya da lahira, Allah baka lafiya kaji? Gobe da sassafe zan shigo in shaa Allah."
  "Nagode d'a na Allah maka albarka ya baka ikon yin adalci a tsakanin 'ya'yayenka nan gaba."
  "Ameen Baba nagode, sannu kaji?"
  "Yauwa ina Yasmeen kuna kusa?"
  "A'a tana Kaduna bari incewa Mama ta had'aku."
  "Toh Babana nagode."
  "Sannu Baba, Allah baka lafiya" nan Mama ta d'aga wayar tare da cireta daga speaker phone. "Hello Ibraheem?" Cikin wani irin murya cike da tashin hankali dakuma tsoro da fargaba Ibraheem yace, "Mama what is wrong with him? Jikin nasa yayi tsanani haka ne?"
   "Ibraheem se addu'a."
  "Innalillahi! Mesa baki sanar dani ba tun d'azu ko a yau d'in in shigo? Mama mesa Baba yake magana haka?"
  "Ibraheem I don't know also" ta amsa hawaye na ciko mata a ido chan bakin k'ofa ta nufa tace, "Dr yace min chances na rayuwansa be kai 30% ba I don't know what to do Ibraheem." Shima Ibraheem besan a lokacinda idanunsa suka cike da hawaye ba "why didn't you tell me he is in a critical condition like this?"
  "Banason hankalinka ya tashi kai kad'ai na sanar wa hakan k'annenka duk basu sani ba."
   "Allah bashi lafiya Mama please take care of him."
  "I'll Ibraheem sekun shigo goben ka gaishe da Fateemah" anan ta katse wayar tana me share hawayenta. "Hafsah? Hafsah ina kike?"
  "Gani nan Alhj" tayi maganan tana dosan gabansa. "Hafsah Yasmeen fah? Ki had'ani da ita itama."
  "Toh Alhj" ba musu ta shiga trying line na Yasmeen sede sam bata samunta saboda d'anta bayi bar mata wayarta kullum cikin siyan sabuwar waya take dan kuwa sede Suleiman be gani ba seya jefata cikin ruwa. Atlast dana mijinta ta kirata anan ne ta same ta haka itama Baba yayi ta neman gafararta a yayinda take ta zuba kuka cikin wayan da k'yar ta iya fad'i mai ta yafe mishi itama. Tana ajiye wayan ta fad'a jikin mijinta tana kuka sosai, hak'uri yayi ta bata yana assuring nata in shaa Allahu Baba ze samu sauk'i and first thing tomorrow morning zasu wuce Bauchi.
   "All is going to be alright kinji Queen? Bar kukan haka ko kina son kisa Abba shima?" Kai zallah ta kad'a masa.
   "King Baba bashida lafiya I don't want him to die."
  "Subhanallah! Kiyi istigfaar wayace miki Baba ze mutu? Ze samu waraka in shaa Allah just have faith kinji?" Nan ma kai ta gyad'a mai. Pecking forehead nata yayi "tashi mu kwanta zuwa anjima mu tashi muyi Sallah mu rok'i Allah wa Baba koh?"
  "Thank you My King, I love you."
  "I love you more Queen tashi mu kwanta toh."

****
  Ibraheem kuwa tun gama wayansu da Mama ya kasa komawa d'akin se hawaye yake zubdawa tsili-tsili. Ahaka har Fateemah ta kwantar da Maamah sannan ta fito ta tsince shi zaune kan kujerar. A nitse ta k'arasa gunsa tare da kwantar da kanshi a dai-dai cikinta tana shafa gashin kansa to and fro. "Everything is going to be alright in shaa Allah Baba ze samu sauk'i Daddy'n Maamah lets just pray for him kaji?" Da k'yar ya iya mata nodding kai "he is in a very critical condition Momy'n Maamah ina ji ajikina bazan sake sa Baba a ido ba."
  "Shhh! Daddy'n Maamah please kadena fad'in haka, Baba ze warke in shaa Allah have faith okay?" Kai ya gyad'a da k'yar "tashi muje mu kwanta gobe da safe se mu wuce in shaa Allah."
  "Bakida lafiya, you aiint going."
  "Baba is like my own father, dole zan bika I love him as much as you do."
  "Thank you Fateemah I love you."
  "I love you also Daddy'n Maamah tashi muje mu kwanta na ciro maka kayan baccinka." A hankali ya miqe tare da kwantar da ita a jikinsa a haka suka isa d'akinsu suka gama shiri suka kwanta sede sam Ibraheem ya kasa bacci haka Fateemah ma ta zauna awake with him har lokacin da bacci yazo ya saceta. Gyara mata kwanciya da Maamah yayi sannan ya miqe yayo alwala ya shiga yin nafilfili yana taya mahaifinsa da addu'a.

*****
    Mama na gama shirin kwanciyar ta ta shimfid'a darduma a k'asa ta hau shirin kwanciya ganin haka Baba ya kirata, "na'am Alhj kana buk'atan wani abu neh?"
  "Ruwa nakeso Hafsah." Tashi tayi ta d'au masa Faro sannan ta rigingina kansa jikin gadon ta sa mai a baki tas ya kur6e ya sake neman k'ari.  A karo na biyun ma shanyewa yayi yana me sake neman k'ari. Hakan ba k'aramin tsoro ya sanya Mama ba saboda sau dayawa tana jin ana cewa wasu idan suka zo mutuwa ruwa suke sha kaman ba gobe. Batasan a lokacinda kuka ya ku6uce mata ba.

     "Hafsah ta kuma kukan me kike?"
  "Babu Alhj" ta fad'a da k'yar duk yadda taso hana kanta kuka ta kasa. Kanta ta d'aura a k'irjinsa "Alhj kasani ina sonka sosai, no matter what kaine mijina na nan duniya dakuma lahira, bazan ta6a mancewa da kai ba."
  "Masha Allah Hafsah ta nagode sosai kuma kisani nima ina sonki sosai daga ke har yaranmu ina sonku duka." Kukan ta cigaba dayi tama kasa amsa sa "toh kibar kukan haka mana, ko so kike nima inyi?"
   "A'a Alhj Allah baka lafiya."
  "Ameen Hafsah ina... ina Zeezee?"
  "Zeezee?!" Tayi exclaiming tare da d'ago kanta da jikinsa cike da mamaki.
  "Eh ita ina take?"
 "Tana gidan Mrs Mukhtar k'awata."
   "Gobe in Allah ya kaimu kice mata ta koma gida ta cigaba da zaman ta achan kinji?"
  "Alhj kana nufin ka yafe mata kenan?"
  "In shaa Allahu Hafsah, na yafewa Zeezee dukkanin abinda tamin nima inaso zuwa gobe idan suka zo duka dasu Ibraheem in nemi gafararta saboda itama ba laifinta bane Hafsah ni na 6ata mata tarbiyya. Su Mariam da ban 6ata nasu ba ai basu ta6a yomin abin kunya ba, itama Zeezee da ban 6ata nata tarbiyyan ba da dukkanin abinda suka faru basu faru ba. Da itama yanzu tana d'akin mijinta, meya fiye mata wannan? Ki ce mata tayi hak'uri ta yafemin don ni na yafe mata komi da bayyananne da 6oyayye duniya wa lahira kice mata I missed being with her, tell her she'll forever be my sister, I love her so much." Wani sabon kukan Mama ta sake rushewa dashi "in shaa Allah Alhj, gobe da kanka zaka fad'a mata hakan Allah ya kaimu kawai. Nasan ba wanda ze kai Zeezee jin dad'i a duniya gobe, saboda batada abinda ya fiye mata yafiyanka a gareta."
 
  "Naji dad'i na faranta mata, Allah yayi ma rayuwarta albarka ya bata 'ya'ya nagarin da zasu zo su kula da ita nan gaba ya bata miji na gari da kuma ze riqe ta amana ya rabata da sharrin dukkanin me sharri."
  "Ameen ameen Alhj nayi farin ciki matuk'a tun ba yau ba nake jiran rana kamar ta yau, ranar da hak'k'in iyaye ze tashi daga kan Zeezee." Murmushi kawai ya iya ya mata "Allah baka lafiya kaji Alhj? Kasani Zeezee na sonka sosai kuma tayi nadaman what she've made you gone through."
  "Ameen Hafsah nima ki gaya mata inasonta sosai."
  "In shaa Allah Alhj"
   "Masha Allah, baki k'aramin ruwan ba Hafsah."
  "Alhj gora uku be maka yawa ba?"
  "Beyi ba Hafsah k'ishi nake ji." Tana hawaye ta k'aro wani ta basa, rabi ya kwankwad'a sannan da kansa yace mata ya k'oshi. Gyara mai bargo tayi sannan ta miqe zata koma kan dardumanta da wuri yace, "Hafsah mu kwana tare anan." Cikin sautin kuka tace, "Alhj ai gadon nan baze d'auke mu ba kuma kaga bakada lafiya."
   "Karki damu ki taho mu kwanta tare kinji? Inason mu kwanta tare yau." Bata sake mai musu ba taje ta kwanta a gefensa a tak'ure.
  "Nagode Hafsah ta Allah miki albarka ya biyaki dukkanin abubuwan da kikayimin da gidan Al~Jannah."
  "Ameen Ameen Alhj."
  "Yauwa karki manta saqo na wa Zeezee fah? Kice mata Babanta ya yafe mata inason ta kuma ta koma gida da zama."
  "In shaa Allah Alhj ka kwanta kaji?"
  "Toh Hafsah Allah bamu alkhairi."
  "Ameen" ta amsa. Da mintoci kad'an Baba ya samu yayi bacci banda Mama da bacci ya k'aurace mata kwata-kwata. Imagining life without mijinta kawai take...

   MARIAM**** @11:40pm
   Wayarta dake ajiye a gefen tane ya shiga ruri wanda tana dubawa taga 'Dear' na flashing akan screen d'in, ba tare da 6ata lokaci ba ta d'aga "hello Sweetheart."
  "Na'am Dear" ta amsa tana sobbing.
  "Baki bar kukan ba har yanzu? Kiyi hak'uri kinji? We are in this together, in shaa Allah Baba ze samu sauk'i muna ta kan mai addu'a gobe in shaa Allah nima zan dawo."
  "Allah yasa, meetings naka fa?"
  "Nayi cancelling nasu already lafiyan Baba ya fiye mana komi."
  "Thank you Abban Ramlah I love you."
  "I love you more my princesses mother, ki samu ki huta kinji? Sena shigo goben."
  "Toh Allah ya kaimu."
 "Ameen, su Ramlah sun kwanta?"
  "Eh tun d'azu."
  "Kema ki kwanta kinji? I don't want you worried Baba will get well soon in shaa Allah."
  "Thank you ka huta gajiya."
 "Kema Sweetheart seda safe" anan ya jira ta katse.

   ZEEZEE**** @01:48am
  Juyi take tayi akan gadonta a yayinda taketa kuka kaman ba gobe. Tunanin mahaifinta kawai take, don kuka har sara kanta keyi mata tana gani dishe-dishe. ganin ba mahalicci se Allah kawai yasa ta miqe da k'yar ta d'auro alwala sannan ta shafa robe akanta don rage mata ciwon kan da takeji ta shiga yin nafilfili.

   *^*^*
  Sallah Ibraheem yayi tayi har pass 01 pm inda Fateemah ta farka tare da shafa gun kwanciyarsa taji wayan, hakan yasa ta miqe zaune anan ta gansa yana takan sallah. Itama alwalan taje ta d'auro tare da tada kabbara tayi joining nasa, hakan ba k'aramin farin ciki ta sanya Ibraheem ba.
 
  *^*^ Yasmeen ma haka k'arfe biyun dare mijinta ya tayar da ita sukayi alwala yajasu sallan nafila inda suka yita roqon Allah wa Baba.
   On Zeezee's side and Mariam ma haka ne sallan suke suma ba wasa.

•^••^•••^
    Yau Juma'ah k'arfe hud'u dai-dai Allah yayi wa Baba (Alhj Isma'eel Yusouf) cikawa, wanda mutuwarsa tazo masa cikin sauk'i a hankali a hankali Mala'ika ya d'au ransa wanda Mama dake gefensa tana bacci ma bata ji komi ba.
   Asuban fari Mama ta tashi ko ganewa gawan Baba ne a gefenta batayi ba saboda be wani kumbura ba cikin ikon Allah, murmushi ne kwance fal a fuskarsa. Bayan ta samu ta miqe ta miyar basa da bargon sannan ta zarce bayi tayi brushing tayi alwala sannan ta fito. Tana sanye da hijabi ta nufi kan gadon tare da zama a gefe "Alhj" ta kira sunansa a hankali.
  "Alhj tashi kaji tashi in taimaka maka kayi alwala kayi Sallah Asubah tayi." Shiru nan ma.
  "Baccin ne yayi nisa haka?" Ta tambayi kanta. "Alhj?" tapping nasa ta shigayi, ba k'aramin razana tayi ba ganin ko motsawa Baba baiyi. Hakan yasa ta matso da kunnenta dab da hancinsa dan jin futan nishi amman shiru takeji ba numfashi ba alamansa. Hannunta ta aza akan heart nasa cike da tsan-tsan tashin hankali don feeling heartbeat nasa, hukuncin da zuciyarta ta gama yanke mata na cewa Allah yayi wa mijinta, uban 'ya'yayenta cikawa ne ya mugun sa kanta ya sara. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta furta tana hawaye sosai. "Alhj! "Ta k'wala mai kira "Alhj! Don Allah kar ka tafi, innalillahi!" rungumesa tayi ta shiga sunbatu tana kiran doctors da nurses da muryan da Allah ya bata.

   Ahaka ne har wata nurse tazo ta sameta, da wuri ta je ta kirawo Dr'n daya duba Baba jiya, da k'yar nurses suka samu suka fita da Mama waje inda take ta leqe ta window tana kuka sosai. Dr na duban Baba ya kad'a kai ba amfanin basa pulse saboda har ya gano d'an kumburin da Baba yayi, tests kad'an suka yi akansa dan gano time of death nasa which was exact by 4:02am today being Friday (babbar ranar da Allah ke yafewa dukkanin bawansa da ya rasu a ranan tambayoyin kabari, Allah yasa Baba yayi mutuwar shahada, yasa k'arshen wahalarsa kenan. Allah ya dubi girman tuban da yayi ya yafe mai k'urak'uransa yabasa gidan Al~Jannah ya kyautata mana k'arshen mu yasa mun d'au darasi daga rayuwan Baba mu bawa 'ya'ya'yen mu tarbiyya na gari, AMEEN.)

   Tun da Mama ta hango ana rufe fuskan Baba da k'yalle tasani shikenan Baba ya tafi ya barta. Wani irin kuka ta sa tana sauk'a k'asa a haka Dr ya fito ya tarar da ita. Kansa a k'asa yace, "am so sorry Ma'am theres nothing we could do, mijinki ya riga ya cika tun wajen k'arfe hud'un dare, fatan mu Allah yasa ya cika da imani ku kuma Allh ya baku hak'uri, verily every soul shall taste the pain of death, I'm sorry" yana kaiwa nan ya fice. Nurses d'inma one by one sukayi wa Mama ta'aziyyah sannan suka fice. Ta d'au about 10 minutes a wajen tana kuka sannan daga bisani ta miqe ganin kukan batada wani amfani, ta koma cikin d'akin ta idar da Sallanta cikin natsuwa, tagama tofe addu'o'inta sannan ta ja kujera ta zauna kusa da Baba tare da yaye k'yallen da suka rufe mai fuska dashi. Hawaye ta soma a hankali se ji take kaman idan tayi mai magana ze amsa ta, ya kira sunanta kamar yadda ya saba. Wani irin zafaffun hawaye ta shiga kwararowa "ina sonka Alhj, amman nasan Allah ya fini sonka shiyasa ya d'auke ka ya kaika kusa dashi, Allah yasa mutuwa hutu ce a gareka, kasani ban ta6a nadaman kasancewa dakai ba, Allah ya had'a fuskokinmu a gidan Al~Jannah ya tura rahamarsa kabarika, Ameen"

    Mama ta d'au mutuwar Baba as k'addara ta kar6esa hannu bibbiyu, sam batayi irin haukan nan da wasu keyi idan anyi musu rasuwa ba, suna suratai suna cewa sun mutu sun lalace. Kukan zafin rabuwa bayan an zama d'ayan daya zama dole kawai tayi bayan nan tayi masa Addu'an da akeyiwa mamaci sannan ta biyosa da dukkanin addu'o'in data sani akanta ta tofe masa. Bayan nan da kanta tayi mai wanka ta suturcesa, har anan ba wanda yaji rasuwan Baba.

   Ibraheem Mama ta d'aga waya ta soma kira, lafiya sumul suka gaisa inda yake sanar da ita yanzu haka ma sun gama shiri zasu kama hanya.
   "Ibraheem ina son ka saurareni da hankali a matsayin ka na babba cikin yarana da musulmin da aka sani da tawakalli, kasani cewa duk wani me rai mamaci ne." Tun anan jikin Ibraheem yayi sanyi jira kawai yake yaji Mama ta furta mai abinda ransa ke ta raya masa.
   "Ibraheem Allah yayi wa Babanku cikawa yau da daddarre wajajen k'arfe hud'u."
   "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ya furta a hankali a yayinda idanunsa suka kad'a sukaji ja zirrr lokaci guda.
  "Mutuwa abu ne me zafi amman yazama dole muyi tawakalli mu rungumi k'addara, dukkanin me rai mamaci ne kaman yadda Babanku ya tafi muma wataran turn namu zezo. Sekun shigo, da sallan juma'ah a nan Gwallaga za'a sallace shi, Allah yasa mutuwa hutu ce a gareshi."
  "Ameen" kad'ai ya iya furtawa tare da yasar da wayansan a k'asa. Hakan yayi dai-dai da shigowar Fateemah don sanar dashi breakfast is ready sede ganin idanunsa ta gane cikawa mahaifinsu yayi. Itama take idonta suka cike dam da hawaye da gudu taje ta samesa tare da hugging nasa nan suka fashe da kuka sosai abin tausayi ba na miji ba mace.


  Hajiya (maman Baba) next Mama ta kira ta sanar da ita inda itama tayi salati tare da sa kuka sosai. Yasmeen ta gama yima Suleiman wanka ta shigo dashi riqe a hannu sannan ta ajiye sa kan gado ta kira sunan mijinta dake maqale da waya a kunne da "King, Wankan fa sauran kai." Kasa juyawa ya kalleta yayi bayan sanar dashi mutuwan Baba da Ibraheem yayi. "Abban Suleiman?" Ta sake kiransa "zamuyi latti fa." Yana kaffa-kaffa ya juyo a hankali emotion dake fuskarsa kad'ai says it all.
  "Abban Suleiman is something wrong? Why the face?"
  "Yasmeen" ya kirata a hankali tun anan jikinta ya bata Baba ya rasu ne kai ta shiga kad'awa "no no don Allah kar ka cemin Baba ya rasu please don't" gudu tasa zata bar d'akin sede kafin nan mijinta yayi sauri ya jata tare da forcing nata ta kwanta a jikinsa.
    "Sshhh he is in a better place in shaa Allah." Kuka take sosai tana sumbatu "he can't die please ka fad'amin wasa kake be mutu ba."
  "Yasmeen kiyi hak'uri Baba lokaci yayi Addu'an mu yake buk'ata ba kukan nan ba kiyi hak'uri." Ai kaman sake tunzirata yake ta kasa barin kukan ganin haka Suleiman ma ya sa kuka.


  Mariam ta gama shirya Ramlah school, Ummie kuma day care text message from Ya Ibraheem ya shigo wayarta tana kai dubanta taga biggest suprise of her life salati kawai ta saki sekuma aikin kuka, makarantar da yaranta basu jeba kenan ranan. Ko kiran da mijinta ke mata ma ta kasa picking se kuka kawai. Hakan yasa Ramlah da Ummie ma kuka, se hak'uri me aiki ke bata amman ina abin ya gagara.
 
   Zeezee was the last person to come to know about thier father's death.






* MIEMIEBEE.      TEAM #YGCπŸŽ€*
   Beeenovels.blogsot.com
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„

Monday, 20 February 2017

‘YAR GATA CE!

 
*BY MIEMIEBEE*
  *Febraury, 2017*
5️⃣0️⃣
 
  _Yo! Assalamu Alaikum Beautiful ones, I know I've been keeping you guys in such a suspence and for that MIEMIEBEE is sorry. To those who think they know me, well I don't think you know know me if you don't know that *Aunty Sis* and *Lubabatu Maitafseer* are my buddies😻. You guys are just simply amazing, my life is a blast with you two. Know that I love you so much and that may ALLAH SWT guide us together and may we continue to prosper. I'm indebted to you two. This page is in you honors, TheThree❤#youKnowWhatIMeanπŸ˜‚πŸ€³πŸ»_





Tooohh" Ta saki baki cike da mamaki. "Auta kasan da haka ka buga mata saki biyu lokaci guda?"
   "Mami wallahi sharrin shaitaan ne, I didn't mean it wallahi ina son Zeezee."
  "Ruky fa?"
  "Mschww!"Yaja k'aramar tsuka "ina miki maganan mutane kina kawomin na beyerabiyar can."
  "Oh! Da Alama gida ba lafiya kenan, toh kaje kayo bikon Zeezeen mana."
   "Bansan ina take ba naje gidansu bata nan da alama Dad nata be yafe mata ba har yanzu, bansan ina zan sameta ba her line is not going through."
  "Tooh kuma... ka tambayi Lubiee mana." Tayi suggesting.
   "She will not tell me tana ganin naci amanar best friend nata she'll never tell me."
   "Ko na kirata ne?"
  "Zaki 6ata lokacinki ne I know Lubiee batayin abu se in tayi niyyah."
   "Toh Auta ka cireta daga ranka kawai ka rungumi k'addara."
  "I can't Mami I love her." Ya fad'a a tsawace.
  "Kai don Allah free me bafa ni nace ka sake taba, kunje kun samu misunderstanding da matarka zakazo kana sauqe min fushinka."
   "Everywhere is just hell!" ya buga plate nasa kan table d'in "na tafi." Ko seda safe bata mai ba tana kallonsa har ya fice. Getting to 9 ya isa gida bayan yayi parking yafito instead ya zarce site nasa da Ruky seya nufi na Zeezee wanda tun tafiyar ta ko tako varendar be ta6ayi ba se yau, gun yayi k'ura putuk! Key'n k'ofar dake had'e da car key nasa yasa sannan ya juya ya bud'e tare da sa kai. K'ura ne da cobwebs ya mamaye ko ina. Yana tafiya guiwa ba k'arfi ya samu ya qarasa har cikin d'akinta. Wardrobe nata ya bud'e yaga wayam! Ba abinda tabari komi ta kwashe Allah sarki Zeezee ya furta a ransa.

    Side drawers yashiga ja yana dubawa kozega wani abinta amman duk ba komai, kominta ta tattara. A na qarshen ne yaci karo da wedding albums nasu guda biyu ciki ba wanda Zeezee ta tafi dasu nufin bata sake buk'atansa a rayuwarta kenan. Wani heart break ya sake ji. Bakin gadon yad'an kakka6e sa'annan ya zauna ya shiga viewing lovely photos d'in. Even though a ranan hankalinta baya jikinta tana tunanin gida, hakan be hana photos nasun yin kyau ba. Kalla ya rigayi har seda ya jiyo k'walla. Gabad'aya yaji ya tsani kansa yanzu meyasa ya hanke hukunci ba tare da yin dogon bincike da nazari ba? Addini beyi qarya ba dayace kafin a yanke hukunci ya zamanto anyi dogon bincike ga irinsa ai yanzu. Missing d'inta bil adadin ya shiga yi har don haka ya kakka6e gadon ya gyara ya kwanta gun yana rungume da photo album d'in ahaka har ya samu yayi bacci, Ruky kuwa koda tajisa shiru setayi zaton ko yana parlour ko sauran d'akunan don haka tana gama kallon series nata tayi kwanciyarta itama.

   *^*^*^
   Haka rayuwa on both sides ta cigaba da kasancewa ba dad'i. A kullum Adeel da tunanin Zeezee yake tashi ya kuma yini, Ruky abinda taga daman yi shi take Adeel be isa ya mata magana ba har wani shakka-shakkanta ma yake yanzu. On Zeezee's side kuwa tama bar fita waje yanzu kwata-kwata koda kuwa don siyan kati ne ta gommaci ta aika almajirai saboda abinda 'yan unguawa keyi mata sede bata fita waje ba shikenan sun shiga habaici suna zaginta kenan, abinda yafi cimata rai shine harda zagin Baba ma da suke.

   Shi kansa Baba basu barsa ba, basuyi a gaban idonsa amman a bayan idonsa dandalin hira da zaginsa suke bud'ewa. Yau kamar kullum Baba da Omar sukaje masallaci an idar da Sallah ana zaune ana tasbih wasu maza daga bayansu Baba wanda basu gane Baban bane zaune a gabansu suka bud'e dandalin hira suna zagin Zeezee suna aibanta Baba, kalamu ba dad'in ji duk anan Baba na jinsu se k'ona da rad'ad'i zuciyarsa keyi masa. Omar na sallame nafilarsa ya hau bayin Allan da masifa da k'yar aka samu aka sasantasu if not cewa yayi seya musu duka danko yafisu k'arfi ko kodaga mere look. Dama kullum ana gayawa Baba abubuwan da 'yan unguwa ke cewa akanshi be ta6a ji da kansa ba se yau, jikinsa ne yayi sanyi a lokaci guda da k'yar suka samu suka k'arisa gida da Omar as tafiya kad'an yayi se sun tsaya ya huta. Sun shiga gida Baba ya wuce d'akin Mama ko tanka Mama dake musu sannu da zuwa beyi ba, miqewa yayi bisa gado yana riqe da zuciyarsa dake masa ciwo sosai.

   "Omar lafiya? Meya sami Baban naku? Ko kunyi fad'a ne?"
  "A'a Mama kede go and calm him down kar ciwonsa ya tashi."
  "Gayamin meya faru Omar?"
  Be b'oyewa Mama komi ba ya fad'i mata abinda ya faru. Cike da tashin hankali Mama ta shiga d'akinsu inda ta tarar da Baba kwance akan gado sede meh? Baya motsi wani irin rikicaccen ihu ta saki sannan ta biyosa da "inna-lillahi-wa-inna-ilaihi-raji'un. Alhj!" Da gudu ta nufi kan gadon tana tapping nasa sede at all baya responding. Omar ta shiga kira seda ya fito a rikice jin yadda take ihu "Omar Babanku, don Allah kayi wani abu." Shima Omar d'in gabad'aya ya rikice ya nufi kansu yana kiran Baba sede baya amsawa.  Bayan nan ga kuma yadda heart nasa ke beating a hankali. Seda sukayi dagaske suka samu suka d'aga Baba ba tare da 6ata lokaci ba sukayi dashi asibiti inda aka wuce dashi emergency ward.

  Banda kuka ba abinda Mama keyi a corridor'n d'akin da lokitoci da Baba ke ciki suna aikin ceto ransa. Omar ne ke k'ok'arin calming nata don shima hankalinsa gabad'aya a tashe yake fatansu kar Baba ya tafi ya barsu don tun ba yau ba Mama take lura da yadda Baba kebin abin Zeezee a rai. Ya yafe mata komi ya wuce yaqi, ga irinta nan ai yanzu. Me za'ayi da gata a rayuwa? Dama-dama ma ace gatan da hankali ke d'aukawa ake bayarwa yaro ba erin wanda Baba ya riga bawa Zeezee ba.

****
    "Zainab! Zainab!" Kirar Mrs Muktar ga Zeezee wanda tuni ta gudu izuwa bayi ta 6uya a zatonta ma tayi bak'o ne shine Mrs Mukhtar ke kirarta dan kuwa ta rantse bazata sake kula wani na miji ba face Ya Al'ameen nata wanda she is sure shima yanzu ya riga yayi aure ya mata nisa.
   "Zeezee! Ina kike ne?" Mrs Mukhtar tasake kiranta a yayinda tashin hankali ke building a voice nata.
  "Zeezee!" A yanzu kam ta shigota d'akin.
  "Na'am" Zeezee ta amsa tare da fitowa daga bayin, tashin hankali ne kwance karara a fuskar Mrs Mukhtar wanda tun kafin ta fayyace wa Zeezee komi, tayi saurin tambaya "Aunty lafiya?" Kai zallah Mrs Mukhtar ke kad'a mata "Zeezee Babanki."
   "Baba!" Tayi exclaiming "meya samu Baba Aunty? Please tell me."
   "Ya sake samun heart failure Zeezee yanzu haka yana asibiti su Mama sun kaisa."
   "Innalillahi-" kasa qarisa salatin tayi se kuka wane lalacaccen famfo.
  "Zeezee ba kuka bane abinyi, ki sanya hijabin ki mu fice, yi hak'uri in shaa Allahu ze samu sauk'i."
  Hakanan through out the drive Zeezee ke ta kuka. Suna isa asibitin suka nufi inda su Mama dasu Mariam suke already se kuka suke. Da gudu Zeezee ta nufi inda Mama ke, sede kafin ta k'arisa Mariam tayi mata katanga stopping her.

   "Kin halaka Baba, Maman ma bazaki barta ba?" Tayi maganan idanunta na tsiyayar da hawaye sosai. Cikin kuka da tsan-tsan tashin hankali Zeezee ta soma da cewa; "Adda Mariam don Allah kiyi hak'uri and let me hug her I beg you please."
   "No way ki koma daga inda kika fito, tunda aka haifeki you've been nothing but badluck to us Zainab, wallahi idan abu ya samu Baba kisani I won't ever forgive you."
   "Adda Mariam ya isa please yanzu ba lokacin yin tashin hankali bane" cewar Omar a yayinda Zeezee tasake rushewa da kuka tana kiran sunan Mama amman itama Maman yau ta kanta take bata iya tacewa Zeezee komi ba. Mariam ta bari Zeezee ta zauna kusa dasu ma tak'i. Tana kuka Mrs Mukhtar tajata zuwa wani benchi dake chan gefe ta zaunar da ita tana lalashinta amman se kaman sake tunzirata Mrs Mukhtar ke.

  Not long enough Dr ya fito inda ya kira Mama zallah ya buk'aceta data bisa office nasa. Tana kuka tabi bayansa inda ya bud'e k'ofar ta samu tashiga tare da jan kujera ta zauna tana shessheqa.
   Tissue ya miqa mata tare da sanar da ita "please calm down mijinki na cikin critical condition bazan 6oye miki ba."
   "Subhanallah!" Ta furta tana kuka sosai "Dr is he going to make it?"
   "Agaskiya bazan 6oye miki ba, chances na rayuwansa is not upto 30% kunsan condition nasa be kamata ba kuna barinsa yana tunani haka. His heart is all damaged yaci ace zuciyar ma ta buga yabar aiki amman Allah be k'addara hakan ba. Ku sashi a addu'a bamu san me Allah ke ciki ba."
   "Dr dan Allah ba abinda zaku iya masa? He can't die don Allah ka taimakeni da 'ya'yana." Ta k'are maganan cikin kuka sosai.
   "I'm sorry Ma'am but we've done all we can sauran mun bar wa Allah kuyi hak'uri. Kuna iya shiga ganinsa amman please Karki kuyi abinda ze tayar mai da hankali Allah basa lafiya."
   "Amin Dr" ta amsa tana share hawayenta.

   ***
   Mama ya jikin Baban? Mariam tayi saurin tambaya. Kai zallah Mama ke kad'a musu, nan fa hankalin yaran ya sake tashi binta kawai sukeyi a yayinda take heading to d'akin Baba. Ganin haka Zeezee itama ta miqe zata bisu sede kafin takai da bakin k'ofan Omar yasa hannu yana kareta ayayinda Mama ta juyo in crying tone tayi stating "taya zakice zaki shiga Zeezee bayan kinsan kece silar rashin lafiyan nasa? Kiyi hak'uri ki tsaya anan kibari nida yayyunki mu shiga."
   "Mama yanzu bazan iya ganin Baba ba? Don Allah kuyi hak'uri kubarni inga mahaifina na rok'eku please."

   "Ya kike magana kaman baki gane abinda Mama ke nufi ba?" Cewar Mariam spitefully. "So kike mu barki ki shiga ki gama halaka mana shi?"
  "Ya isa Mariam" Mama ta katse ta "mu shiga." Ba tare da ta sake cewa uffan ba suka shiga tare da shutting door a face na Zeezee. Nan fa baiwar Allah abin tausayi ta kuma sauk'a har k'asa tana kuka a yayinda Mrs Mukhtar keta bata hak'uri.

   Kallo d'aya iyalan Baba suka iya suka mishi idanunsu ya cike dam da hawaye. Banda kuka ba abinda suke iya yi. Kallo d'aya za'ayi wa Baba asan da k'yar ya kwana yau Alhamis ya kwana da rai. Hakan ba k'aramin sake tayarwa family'nsa hankali yayi ba. Da gudu Mariam da Omar sukayi kansa, shi Omar na miji amman se kaman yama fi Mariam yin kuka musamman idan ya tuna fa just a while ago suke zaune a masallaci lafiya k'alau. Har Mama ta kasa barin kuka.

   "Ya'yan albarka ina kuke?" cewar Baba in a low and cracky voice.
  "Gamu nan Baba" cewar Mariam "sannu Allah ya baka lafiya."
  "Ameen" Mama da Omar suka amsa in unison. Hannunsa dake ajiye a gefe yake son d'agawa amman ya kasa, da Mariam ta gano haka seta d'aga ta had'a da nasan, shima Omar ya miqo hannunsa duk suka had'a gu d'aya.
   "Masha Allah suwa dawa ne anan?" Ya tambaya gashi de a zahirce idanunsa a bud'e ne sede ko bayi gani dasu ne masani se Allah.
   "Mariam da Omar ne anan Baba" cewar Omar yana share hawayensa da d'ayan hannunsa.
   "Sannu 'ya'yan albarka Allah yi muku albarka."
  "Ameen Baba" Mariam ta amsa "sannu." Se kuka suke sosai saboda raya musu da zuk'atansu ke na cewa Baba baze kwana ba yau.
   "Mariam" Baba ya kirata cikin dashasshiyar murya.
  "Na'am Baba gani."
  "Mariam 'yata ki yafemin rashin adalcin da nayi a tsakaninku tun kuna 'yan yara, ki gafirceni don Allah."
   "Baba wace erin magana kake haka? You've never once offended me don Allah kabar seeking forgiveness d'ina, what we are after at is your health."
   "Nasani Mariam amman inji da kunne na kin yafemin." Hannunsa ta sake matsewa gam cikin nata tana me sake kuka "Baba inhar abinda kakeson kaji kenan shikenan, ni Mariam 'yarka na yafe maka komi da 6oyayye da kuma bayyananne duniya wa lahira, Allah ya baka lafiya."
   "Ameen masha Allah Mariam nagode, Omar Baba na kaima ka yafemin rashin ad-" be idar da maganan ba Omar ya katse sa in a crying tone yace, "na yafe maka Baba, na yafe maka komi Allah baka lafiya."
  "Nagode 'ya'yan albarka,  Allah ya albarkaci  rayuwanku ya baku zuri'ah d'ayyiba,  sannan kuma ya haneku dayin rashin adalci a tsakanin 'ya'yayenku kunga abinda hakan ya haifar min. Kumin alqawari ko akan layi kuka ga iyaye suna rashin adalci a tsakanin 'ya'yayensu zaku tsaya ku musu wa'azi."
   "In shaa Allah Baba Allah baka lafiya." Mariam kije ki ibo su Hafsah daga islamiyya." Mama ta fad'a da k'yar.
  "Mama bazan iya barin Baba haka ba."
   "Karki damu nida Omar zamu kula dashi, tashi kije Mamana." Ba tare da tayi gardama ba ta share hawayenta, "toh Baba zanje in ibo su Ramlah daga islamiyya."
  "Toh sannu Mariam d'ina."
  "Yauwa Baba, zuwa anjima zan dawo Mama."
  "A'a  Mariam ki zauna da yaranki if not waze kula dasu mijinki bayi gari."
  "Mama koda me aiki ne zan barsu."
  "A'a ban goyi bayan hakan ba gani ga Omar duk abinda Babanku ke buk'ata ni da Omar zamuyi masa."
  "Are you sure Mama?"
  "Yes Mariam karki damu."
 "Toh shikenan amman if something goes wrong please don't hesitate to call me."
  "In shaa Allah ki shafa min kan takwara na."
  "Toh Mama" nan ta juyo tana kallon Baba da hannunsa ke rik'e dana Omar har yanzu. "Baba gobe in shaa Allah zan dawo get well soon Allah baka lafiya." Kai zallah ya gyad'a mata, anan ne ta samu ta fita.
   Zaune ta tarar da Zeezee kan bench tanata aikin kuka har yanzu, ko niyyan magana Mariam batayi mata ba hakan yasa Zeezee ta miqe tana kuka sosai takira sunan Mariam.
  "Adda Mariam?" Banza da ita tayi tana me cigaba da tafiya.
   "Adda Mariam don Allah kiyi hak'uri ki sanar dani halin da Baba yake ciki ba don hali na."
   Kaman bazata amsata ba tace, "da sauk'i" sannan ta fice ba tare data sake sauraronta ba. Kasa daina kukan Zeezee tayi har seda Omar ya fito daga d'akin shima kasancewar aiken sa gida da Mama tayi domin ya ibo mata abubuwan dazata buk'ata don kwanan asibiti.

   "Ya Omar" ta kirasa tana k'ok'arin miqewa daga kan benchin.
  "Na'am Zeezee." Ya amsata ba yabo ba fallasa.
  "Ya Omar ya jikin Baba?"
  "Da sauk'i."
  "Ya Omar ka fad'amin gaskiya please, I tried to talk to Adda Mariam but she is so mad at me."
  "Da sauk'i Zeezee addu'ar mu kawai yake buk'ata."
  "In shaa Allah Ya Omar, how I wish I can see him also and hold his hand." Tayi maganan k'walla na cikowa a idonta. "I miss my Dad Ya Omar, I miss him so much. I can't ever forgive myself for letting him suffer like this, nice sanadin rashin lafiyarsa." Ta rushe da kuka sosai. Shi kansa Omar tausayi ta basa dukda kuwa haushinta yakeji saboda ita ta fara haifarwa Baba da wannan rashin lafiyar. Dan irin kukan da Zeezee take me tsuma zuciya yasa Omar yajata jikinsa tare da hugging nata yana bubbuga bayanta. Hugging nasa back tayi tana me cigaba da kukan.
 
   "Ya isa, he is going to be alright in shaa Allah." Kai ta gyad'a seda tad'an yi shiru ya saketa nan ta shiga share hawayenta. "Ki zauna ina zuwa."
  "Gida zaka?"
  "Eh."
  "Zan bika."
  "Are you sure?"
  "Yes please."
  "Okay toh muje." Anan suka fice, Zeezee ce ta had'awa Mama dukkannin abinda zata buk'ata.

         *****
  "Hafsah?"
  "Na'am Alhj" ta furta tana k'ok'arin shanye kukan dake neman kub'uce mata.
  "Kina ina?"
  "Gani nan Alhj" nan ta sake matsowa kusa dashi tare da had'a musu hannayensu.
   "Hafsah ta ki yafeni kinji?"
  "Alhj kuma wani irin magana kake?"
  "Nide ki yafeni don Allah nasan sau dayawa nakan miki abubuwan da bakiso kiyi hak'uri ki yafemin please."
  "Alhj please ka dena, kabar magana haka. Ya kake ta neman yafiya sekace mutuwa akace maka zakayi? Please ka bari ya isa haka."
   "Hafsah ta inaji a jikina today will mark my last day, zuciyana namin ciwo sosai." Hawaye ne suka soma tsiyayowa daga kumburarrun idanunta. Jin shiru yace, "baza ki iya yafemin ba Hafsah ta? Yi hak'uri ki yafemin kinji?"
   "Alhj me kayi min da zaka nemi gafara na? Ni nace kayi offending d'ina ne? Please kabar maganan haka lafiyarka ce a gaban mu yanzu."
   "Baki fad'a ba amman nasan da hakan."
   "Alhj inhar jin yafiya na kakeson ji toh ni na yafe maka duniya wa lahira."
    "Nagode Hafsah."
  "Nima nagode Alhj Allah baka lafiya, Hjy (Maman shi) ta kira d'azu k'afafunta ke ciwo taso fitowa yau amman tace zata bari zuwa gobe."
   "Toh ba matsala, Allah kaimu."

  **^^**
   Har dare around 9pm Zeezee tak'i barin asibitin, ba yadda Omar beyi da ita ba ta ya kaita gidan Mrs Mukhtar amman tak'i ita tanason taga Babanta.
  9:30pm Mama ta fito waje don yima Zeezee magana. Alokacin Zeezee na miqe akan benchi tayi lamo "Zeezee" Mama ta kirata.
  "Na'am" ta amsa tare da miqewa a kid'ime.
  "Me kike har yanzu baki koma gida ba?"
  "Mama ya jikin Baba?"
  "Da sauk'i yana bacci ma."
  "Allah ya bashi lafiya."
  "Ameen tashi Omar yayi dropping naki Mrs Mukhtar nata kira."
   "Mama zan kwana anan."
  "Anan a ina Zeezee?"
  "Ko akan benchin I want to be anywhere close to Baba."
  "Zeezee kiyi hak'uri ki koma gida."
  "Mama don Allah kimin hanya, ina son inga Baba in gani da ido na wani halin yake ciki please Mama don't refuse my offer, I cannot forgive myself for what I've done to him."
   "Zeezee dama Allah ya riga ya k'addara wannan rashin lafiya wa Babanku sede kice ta sanadin ki hakan ya faru Wanda dama komi seta sanadin wani yake faruwa, so kibar blaming kanki ki taya shi da addu'a Allah shi basa lafiya."
  "Ameen Mama yanzu don Allah ba yadda za'ayi na gansa kafin na tafi?"
  "Zeezee kin fini sanin abinda hakan ze haifar."
  "Mama kince fa yana bacci."
  "Even still Zee-"
  "Mama please I beg you don Allah, this is all I ask." Zeezee tayi pleading abin tausayi. Mama zata sake magana Zeezee ta sake had'ata da Allah, she can't say no now. Muje.

   "Nagode Mama, thank you so much" a nitse tabi bayan Mama suka shiga d'akin inda ita Zeezee ta tsaya daga bakin k'ofar a yayinda Mama ta k'arisa ciki ta sake duba fuskan Baba don ta tabbatar da baccin yake. Hannu tayi wa Zeezee nan ta k'ariso ciki.
  Kallo d'aya Zeezee tayi wa Baba ta rushe da kukan zuci se hawaye kawai take tsiyayarwa. Binsa kawai take da kallo tana me sake tsanar kanta na sanya mahaifinta cikin wannan hali, duk anan kallonta kawai Mama take. Hannu Zeezee ta d'aga a hankali ta d'aura akan na Baba a hankali. Har Mama ta bud'e baki zatayi magana, ganin Baba be farka ba ta barta.
   "Baba I'm so sorry, Allah ya baka lafiya, your daughter loves you so much if only I can take away your pain." Tayi kusan minti biyu akansa sannan da k'yar Mama ta samu ta turata waje "kije gida Zeezee, Omar na jiranki a mota in shaa Allah gobe seki dawo."
  "Toh Mama take care of Baba please Allah bashi lafiya."
  "Ameen seda safe."
  "Allah tashemu." Tana kaiwa nan ta juya ta fice. Ciki Mama ta koma ta idar da  shafa'i da wutr nata, ta shiga canza kayan sawanta tana cikin haka ne taji Baba yaja doguwar nishi. Rabin kayan na jikinta rabi ta cire ta k'arisa kansa "Alhj?" Ta kirasa cike da tashin hankali. "Alhj?" Tayi tapping nasa "na'am Hafsah." Ya amsa at long last.
   "Alhamdulillah! Ka tashi kenan?"
  "Eh" ya amsa sama-sama.
  "Ya jikin toh?"
  "Alhamdulillah."
  "Barin canza kaya na ina zuwa." Da nod daya mata ta koma ta canza kayan nata zuwa na bacci sannan ta dawo ta zauna a gefensa.
   "Hafsah ina Ibraheem da... da... da Yasmeen?"
   "Ibraheem na Abj Yasmeen kuma Kd amman gobe in shaa Allah zasu d'auko hanya don dubanka."
   "Ina son ganinsu yanzu kiyi musu magana kice suzo."
  "Alhj ba gari d'aya fa muke dasu ba, Mariam, Omar da Zeezee ne muke gari d'aya dasu."
   "Ibraheem da Yasmeen fah?"
  "Suna chan Abj da Kaduna Alhj karka damu gobe zasu shigo."
   "Inason yi musu magana Hafsah."
   "Toh in kira maka su a waya?"
  "Zamu samu muyi magana?"
  "Sosai ma."
  "Toh kiramin Ibraheem shine babba aiko?"




*MIEMIEBEE.         Team #YGC!*
 Beeenovels.blogspot.com
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„