Sunday, 26 February 2017
‘YAR GATA CE!
*BY MIEMIEBEE*
Page 54
*FEBRUARY, 2017*
"Zeezee please kiyi hak'uri ki saurareni, slap me, insult the hell out of me, hit me anywhere you want and how but please don't shut me out. Wallahi Zeezee tun rananda na sake ki na shiga wani gaggarimin yanayi, give your very own one last chance please I beg of you, its all I ask."
"One last chance?" Ta d'ago kai tana kallonsa ta nik'af nata finally cike da mamaki. "One last chance so you can maltreat me again? One last chance so ka sake duka na? force me into bed? make me do yours and wife's laundry? cook for you? sweep-" katse ta yayi da wuri "no, no please-" ya fad'a wane zeyi kuka.
"Then why? Saboda kana nunamin Ruky ta fini k'ima da daraja a idonka?"
"No Zeezee enough of that please, I want you back because I love you and miss everything about you, your smile, fragrance, body, hair, everything about you. I miss it."
"I should have guess, ko ka manta am of no use to you tunda bazan iya haihuwa ba yanzu."
"I don't f*cking care Zeezee, all I want is you."
"You should have thought about that earlier kafin ka dakeni ka kuma buga min saki biyu."
"Zeezee please! Cut it out. Meh kikeson in miki kigane cewa I've regretted every single action of mine back then? In Ruky kikeson in saka I'll at this instant because I don't love her, ke nakeso Zeezee please pity your very own."
"What I want? What I want is for you to f*cking stay away from me Adeel plus you are nomore my very own, you never were. Bana k'aunar ka anymore Adeel ka riga ka fitamin a rai na, bana sonka. You came to me jiya da sunan tuba na kake nema and I did forgave you don't make me change my mind please."
"Zee-"
"I said go away!" Ta katse sa a tsawace.
"No Zeezee please listen to me, lets solve this out, Zeezee haka kikeson ki k'arisa rayuwarki as bazawara? Bana son ganinki haka, you are worth than this."
"Am I? Baka son ganina a haka ka buga min saki biyu? Mschww! am running out of patience just go away and never come back I don't ever need you in my life again."
"No, that's not true, you can't forget me this soon-"
"I can't?" Ta tambayesa "I was never in love with you Adeel, ko a da inma ba sonka nake ba. I came to realise that I was just afraid of you, a monster. Ya Al'ameen is the one I love and not you."
"That's not true Zeezee you still love me I know that please come back."
"Never."
"Haka kikeso ki cigaba da zama?"
"Koda hakan zan cigaba da zama meya maka zafi? Besides am going back to my truest love Ya Al'ameen."
"No Zeezee please don't, karki tafi ki barni I beg you please. Kimin komi amman karki koma gidan Maj- Gen."
"Give me one reason not to. Gidanshi zan koma I've made up my mind." Tana kaiwa nan tabi gefensa zata fice da sauri ya rik'o hijabin ta stopping her. Chak ta tsaya, kuka kawai taji ya fara kaman d'an yaro wanda itama tuni ya karya mata zuciya ta soma kukan.
"Zeezee please" yayi pleading in a crying tone. "Please don't leave me" ya k'arisa maganan yana sauk'a akan guiwowinsa a idanun jami'un da ke wucewa. "I beg you please karki koma gun Ya Al'ameen come back to me and let me prove my love to you one last chance, please Zeezee don't refuse my offer." Kuka ne sosai yaci k'arfinta yadda words na Adeel ke getting to her. Tanayi yana yi, "let me go, ka sakeni" kad'ai ta iya furta mai. Kai yake kad'awa still in the kneeling position. "Zeezee please." Fincike hijabin nata tayi ta ruga ciki a guje tana kuka sosai. As always Mama na kitchen taga wucewan Zeezee da gudu yau unlike always da zata tsaya tayi mata sannu. Barin duk abinda takeyi tayi taje ta samu Zeezee dake baje akan gado tana kuka me tsuma zuciya.
"Subhanallah!" Tayi exclaiming. "Ya da kuka haka? Meya faru?" Tayi maganan hannunta manne akan bayan Zeezee data kasa koda d'ago kai har yanzu.
"Zeezee? Yi hak'uri ki amsa ni kinji? Meya faru?" Da k'yar ta iya tsagaita kukan tace, "babu."
"Kamar ya babu kuma? Kina nufin haka kawai yau kika d'auro niyyan dawo min gida da kuka?" Kanta ta d'ago finally tare da share rolling tears nata. "Babu an yi mana wa'azi ne me ratsa jiki a islamiyya akan mutuwa se kawai na tuna da Baba."
"Allah sarki, in shaa Allah Babanku is in a better place kinji? Mu cigaba da yimai addu'a yi hak'uri kukan ya isa haka Mamana."
"In shaa Allah Mama thank you."
"Tashi ki tu6e uniform d'in toh." Da nod da tayi wa Mama, Mama ta fice. Duk yadda tayi don kawar da tunanin Adeel daga k'wak'walwarta ta kasa, haka ta kwana ranan da tunaninsa.
Washegari kuwa ko zancen zuwa islamiyya Zeezee batayi wa Mama ba, pass 3pm Mama ta shigota d'akinta, miqe kan gado ta tarar da ita tayi dunk'um tana tunani.
"Bade tunanin Baba kike ba yau ma?Zeezee shin wai sekin haifar wa kanki ciwon zuciya sannan zaki huta? Da rasuwan Babanku sati nawa but kin kasa ki daidaita rayuwarki, haba mana! Mutuwa da zafi amman ya zama dole ki hak'ura."
Tasowa tayi ta zauna "nifa ba tunanin Baba nake ba, ai kince in dena kuma ina iya k'ok'ari na ganin na ragen."
"Toh me kike zaune yi haka tun d'azu? Tun da kika gama ayyukan ki ban sake jin motsinki ba."
"Babu." Ta amsa blankly.
"Toh islamiyyan fa? Babu ne yau?"
"Akwai Bazan jeba ne" ((dalili kuwa shine bata son yau ma su sake had'uwa da Adeel she is simply avoiding him.)
"Lafiya dai ko?"
"Lafiya" tayi faking smile.
"A'a ban san ki da haka bafa, gayamin mene"
"Allah babu Mama, bana jin dad'in jiki na ne."
"Kinsa tunani a gaba ba dole ba, bale ma I don't trust this silly excuse, gayamin gaskian zancen meya hanaki zuwa islamiya yau? Keda baki ta6a fashi.l
"Mama babu."
"Zainab!"
"Na'am" ta amsa.
"Tell me, mene?"
"Mama..." sekuma tayi shiru. Isowa kusa da ita Mama tayi ta zauna a gefenta tare da rik'o hannunta "gayamin kinji? Am here for you."
"Mama its Adeel" ta fad'a hawaye na forming rapidly a idanunta.
"Subhanallah! What about him?"
"Mama shekaran jiya yazo har nan bakin gate on my way back home daga islamiyya na ganshi..." nan ta kwashe labarin komi tabawa Mama bata ragar da komi ba.
Ajiyar zuciya Mama ta sauk'e "ikon Allah! Ke yanzu me zuciyar ki ke raya miki?"
"Mama I don't know I've had enough of his torture, I don't need some more."
"Bakiya sonshi yanzu?" Kai ta gyad'a a hankali.
"Are you sure?" Sekuma ta kad'a kai da nufin a'a. "Mama its hard for me to admit that bana son Adeel saboda he was my first love, I loved him with all that I've got."
"I know Zeezee you must not repeat it again. Kina ganin ke ya tuba, tuban gaske?"
"He did Mama saboda he even knelt down in front of me, but it still isn't enough compared to abubuwan dayamin da nake gidansa, Mama ban ta6a fad'a miki bane but har forcing d'ina in to bed Adeel nayi, sometimes ma he'll be drunk and then sleep with me forcefully" ta k'are maganan cikin kuka sosai. Hugging nata sosai Mama tayi cike da tausayi. "Its okay Sweetheart baza ki komawa Adeel ba unless you want to kinji? Kibar kukan haka." Kai tayi nodding "thank you Mama."
"Always dear, share hawayenki ki shirya islamiyya idan aka tashi zan sa Omar yaje ya d'auko ki kinga ta hakan Adeel baze iya sake tsayar dake ba."
"Are you sure Mama?"
"I'm definitely am."
Ba tare da ta sake cewa uffan ba ta shirya tsaf ta wuce islamiyya. Sede yau ma kaman jiya, bayan Omar ya d'aukota daga islamiya suka tarar da maroon Genesis G80'n Adeel parked gaba da gidansu kad'an.
""Ya Omar gashi chan." Tayi stating ba nitsuwa a tattare da ita.
"Waye Zeezee?"
"Adeel, gashi chan don Allah do something." Tana idar da maganan sega Adeel yana fitowa daga motarsa, ita se yau ma ta lura da bak'in da Adeel yayi.
"Go inside Omar" ya buk'aceta. Da sauri ta bud'e motan ta fita nan Adeel ya shiga k'walla mata kira sam tayi kaman ba ita yake kira ba, tana kaiwa ciki tasa lock. Juyawan da Adeel zeyi yaga Omar, although besan saba amman jikinsa na basa wan Zeezee ne.
Hannu Adeel ya miqa masa sukayi sallama sannan Omar ya tambayesa purpose of being here inshi.
"I know ba lallai bane ka sanni, I'm Adeel Zeezee's husband-"
"Ex husband" Omar yayi correcting nashi. Baki na 6ari yace, "yes ex husband, Yaya please bikon Zeezee nake sonyi, ku yafemin ku dawo min da ita, I love her."
"Kasan kana sonta shine ka wulak'an tata ka buga mata saki bama d'aya ba har biyu? Please Mallam pack your wahala and go bamu buk'atanka."
"Yaya please karka min haka, idan ita Zeezee yarinya tamin haka, kai babba be kamata kamin haka ba kaima. Wallahi sharrin shaitaan ne I never meant to divorce Zeezee believe me."
"Bazaka tafi ta ruwan sanyi bane sena sa an maka koran akuya?"
"Yaya please..." ya sake pleading. Ganin Omar na neman tara masa jama'a yasa kawai ya tafi badon yana so.
Adeel be fasa zuwa gidansu Zeezee a kullum ba, infact he decided to make it a hobby. A kullum kuwa idan yazo da Omar suke had'uwa dan kuwa Zeezee a mota Omar ke barinta shi ya fito ya zazzage wa Adeel buhu-buhun rashin mutunci amman ba hakan zaisa gobe yak'i zuwa ba. Akan Zeezee ya ajiye pride nasa a gefe, inhar ze sameta he is ready to loss everything like everything. Kusan sati biyu Adeel ya jera yana zuwa gidansu Zeezee kaman maye. Ruky Mama sede ta kallesa saboda ko maganan arziki bayi had'asu don Adeel ya fita harkarta gabad'aya. In sunyi magana toh Ruky money monger tazo kar6an kud'i ne, wanda da yak'i da ya so dole ya bata kokuwa ta b'oye key'n motarsa. Yau ma kaman kullum yajesa gidan su Zeezee, bayan Omar ya korasa ya dawo gida rai a dak'ule only to find the gate locked harda kwad'o. Danqaree! Ya furta a ransa sannan ya shiga bubbuga k'ofan yana me sauk'e haushinsa akai. "Ruky! Rukayya! Ina wannan bayerabiyar ta shiga? Mschww!" Ganin fa bata gida yasa ya zaro wayansa daga aljihu a fusace ya shiga nemanta. Several missed calls yayi mata wanda ciki ba wanda ta d'aga as tasa wayar a silent se bidirin biki suke sha.
*^GIDAN BIKI^*
Wak'an girgiza k'wank'waso ke tashi wane ze har6a zuciyan mutum. Ruky da friends nata ne ke tsaye se rawa sukeyi, chan wata friend nata ta buk'aceta da sanin time, anan ne Ruky ta zira hannu tare da zaro wayanta nan taci karo da 28 missed calls from Baby. Tsuka taja sannan ta sanar da k'awarta ta.
"Toh ni nasan zaka dawo da wuri ne? Ina kullum se bayan Maghrib kake dawowa, mschww!" Fita tayi zuwa less crowded area ta shiga Calling nasa back wanda tuni ya d'aga kasancewar wayan na a hannunsa yana tsaye bakin gate d'in wane me maula.
"Ke mahaukaciyar ina ce? Gidan naki ne da zaki kama ki rufeni a waje?"
"Abeg Mallam free me oo, kai kanka ka fad'a ka ta6a dawowa gida at this time ne? Base bayan Maghrib kake dawowa ba?"
"Aww! Ma abinda zaki ce kenan saboda bakida tarbiyya koh?"
"Ai gaskiya ne."
"Da izinin uban wa kika fita? Na baki izini ne?"
"Kaman ya kabani izini, baka gida izinin wa kakeso in tambaya?"
"Aww kuma bakisan ki kirani ki sanar dani a waya ba wato."
"Banida kati" ta amsa a takaice.
"Yanzu da bakinki kika kirani ai."
"K'awata ce ta samin."
"Whatever come back home this instant kizo ki bud'e min gidana."
"Gidan biki fa nake."
"Allah yasa gidan mutuwa kike ki dawo Ruky bana wasa dake."
"Gaskia nikam da sakel wallahi."
"Zan sa6a miki kina jina? Wallahi na baki 20 minutes." Ding yayi hanging. Doguwar tsuka taja wane zata cire bakinta. "Allah ya sawaqa wallahi." Dai-dai nan isowar friend inta kenan, "ahh! Ruky Mama ya ana bidiri ke kina anan?"
"Kibari kawai Mamx, Adeel ne wai ya dawo gida."
"Meaning?" Ta tambaya tana tauna chewing gum.
"Meaning na koma gida."
"Dalili?" Ta sake tanbaya.
"Nayi locking gida kafin na fito kuma ba key a gunsa."
"Yo! Bashida gidan friends da zasa kafin nan ne? Nifa banison tak'ura a rayuwa wallahi shiyasa bazan iya zaman aure ba, shikenan mutum bashida 'yancin kansa se abinda wani ya fad'a, mschw!"
"Kibari kawai Mamx kuma fa be ta6a dawowa gida war haka ba."
"Ke kinsan meh?" Kai Ruky ta kad'a "ki sharesa kawai, kibari se Maghrib ki koma gida by then an gama duk abinda za'ayi anan."
"Ke bakisan Adeel da surutu bane wallahi."
"Ce mai zakiyi key'n motarki ta 6ace da k'yar kika samu."
"Amman fa kin kawo point wallahi, hakan za'ayi." Hi five sukayi sannan suka koma ciki suka cigaba da karya k'wank'waso.
Adeel har ya gaji da kiran Ruky Mama, gashi har tak'ara 15mins kan 20'n daya bata amman bata dawo ba, wannan raini dame yayi kama? Cikin motansa ya koma yayi zaman jirarta. Se chan 7:45pm ya hango wutan motarta yana nan zaune a motar har yanzu. A nitse ta fito ta bud'e gate d'in sannan ta k'arisa gun motar nasa tayi knocking bisa window, ko d'aga kai ya kalleta beyi ba, yin hakan sau biyu yasa ta koma motar ta tashiga, tana cikin kunnawa Adeel yasa kai ya shige gidan sannan ya jirata tayi locking kwad'o ta iso ta bud'e musu entrance door. Seda ta shiga yabi bayanta, a parlour ya tarar da ita "sa'an wasanki ne niko?" Yayi snarling at her.
"Kaman ya sa'an wasa na kuma Adeel?" Binsa takeyi a hankali gudun ya hanata kud'in kashewa.
"Bansani ba, minti nawa na baki kuma mintuna nawa kika k'ara akai?"
"Toh ka tsaya mana ka saurari dalili na. Key'n mota na ne ya 6ata a gidan bikin da k'yar na samu."
"Da kin ganni sanye da pampers ne sekice min haka and expect me to believe you. wallahi Ruky ki sani ba tsoronki nakeji ba just because ina d'aga miki k'afa ina ganin bakida lafiya doesn't mean I can't beat you up, wallahi kinji na rantse idan kika sake taka waje bada izini na ba Allah ya isa na as your husband na kanki, idan kuma bakisan ma'anan hakan ba try it keda mahaliccinki." Yana kaiwa nan ya fice zuwa d'aki inda ya hau tunanin Zeezee.
Doguwar tsuka ta bisa dashi, "wallahi k'aryanka ne" sekuma ta kad'a kai "ya zanyi yanzu don Allah? Gobe dinner I can't miss it for the world, shi wannan Adeel yanada problem wallahi, mazajen kowa na barinsu suyi yawo amman banda shi mschw wallahi sa'an ka d'aya kafini gaskiya anan dana zaune kan cikinka." D'ayan d'akin ta nufa ta canza kayan jikinta zuwa a light and simple one sannan ta fito ta nufa kitchen. Spaghetti me rai da lafiya ta dafa tare da had'a mai mango juice sanin its his favorite. A dining ta jera sannan ta koma d'akin data fito ta feffeshe jikinta da turare tare da sake seducing shirin dake jikinta. D'akin nasa ta nufa inda ta tarar da shi miqe bisa gado ya zura wa ceiling ido, ko bata tambaya ba tasan tunanin Zeezee yake, ita tun tana kishi ma har ya zame mata jiki, Zeezeen ma ta dawo ita batada case as long as zena bata kud'i ze kuma barta tana fita unguwa ba matsala. Kan gadon ta k'arisa tare da hayewa ta end d'in da yake ta zauna.
"Baby" ta kirasa cikin wata tantiriyar murya. Ko kallonta ma beyi ba bale yasan tanayi. "Haba! Baby am sorry don Allah." Nan ma banza da ita yayi.
"Baby yanzu bazaka d'ago ido ka kalleni bama? I said am sorry dagaske key'n mota na ne ya 6ata kaima kasan bazan shanya ka haka kawai a bakin gate ba ai ko? Yi hak'uri kaji I'm sorry."
Se anan ya juyo yana kallonta, sake bank'aro mai da k'irjinta tayi "tashi muje kaci abinci dinner is ready."
"Kije kici bana jin yunwa" yayi maganan yana kawar da kallonsa daga gareta cause he is not in the mood, tunanin ya ze dawo da Zeezee ne ke gabansa.
"Babe kaci lunch ne da zakace baka jin yunwa? Yi hak'uri muje I'll be the one to feed you." Haka tayita lalla6asa seda ya tashin, bayan tayi serving nasa tace zatayi feeding nasa sam yak'i shiwai shi zeci da kansa. Zama tayi gefensa se daddad'un kalamu masu sanya sanyi a zuciya take tayi mai, chan da lokacin bacci yayi ta sake d'aukan wani wankan tasa wasu arnan sleeping dress nata gata daman ba kad'an ba. Shisshige mai ta rigayi daren ranan seda tayi turning nasa on. A ranan ba k'aramin pleasure ta bawa Adeel ba. Da Asuba ta tashesa sukayi wanka sukayi sallah and in the morning ta had'a mai breakfast tare da shiryasa for office. Suna cikin karyawan ta kirasa a hankali yet romantically "Baby." Kaman baze amsa ba yace, "meh?"
"Baby baka hak'ura ba har yanzu?" Yi yayi kaman be jita ba. "Na fa san kana jina, me kakeso in sake maka domin ka hak'ura? Am sorry kaji?"
"Naji ya wuce."
"Meaning kayi hak'urin?" Nodding kai yayi mata "thank you Baby I love you." Nan ma kai ya mata nodding "toh Baby kaja baya da Allah ya isan kenan daga kaina?"
"That's it" yayi exclaiming "ai dama nasan ba tsakani da Allah bane kike duka wannan abubuwan nan da kikeyi."
"Allah tsakani da Allah ne please kaja baya da Allah ya isan yi hak'uri, bazan sake fita ba seda izinin ka amman incase of state of emergencies kaga ya zama dole, da Allah ya isanka a kaina kuma kaga ai da akwai matsala." Shiru yayi se cin abincinsa yake "Baby ba zaka ce ka yafe ba? Me kakeso for lunch yau?" Kai ya d'ago yana kallonta kaman bazeyi magana ba chan yace, "naji naja baya da batun Allah ya isan, you are free."
"Yeyy! Thank you" nan da nan ta taimaka masa yagama breakfast, sa6anin kullum yau har gun mota ta rakasa "Baby zan samu 5k please?"
"Again!" Yayi maganan yana tadda engine d'in motar. "Ke wai ATM machine kika maida nine ko meh? Kullum cikin tambayan kud'i naga ko shi ATM machine d'inma wani sa'in cewa yake ba kud'i."
"Haba mana don Allah bikin k'awata fa ake shikenan se ana yimata manni ni se in tsaya ina kallonsu? Yi hak'uri please."
"Ruky banida kud'i kiyi hak'uri yau, dubu nawa na kashe miki tunda muka shiga month d'innan?"
"Ni ba dogon surutu na buk'ata ba, zaka bani ne kokuwa a'a?"
"Kema kin amsa da kanki ai."
"Yama kyau wallahi" tana kaiwa nan tabar mai wajen "sekace ATM machine kullum bani wannan bani wancan, bazan bada ba."
Itama a ciki se gunguni take tana zaginsa "wallahi ba abincin ranan da zan girka da kai aikin banza kawai." Tuna tasan inda yake ajiye wasu kud'ad'ensa yasa ta saki murmushi sannan ta nufi d'akin. Cikin pocket na wani suit nasa tasa hannnu ta zaro d'imbin kud'ad'de, dubu goma ta zara ta miyar da sauran sannan nan da nan ta shirya gidan biki abinta, dinner'n da se dare za'a soma amman dan neman yawo tun yanzu zata ita.
*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*
Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment