BY MIEMIEBEE
PAGE 22
*December, 2016*
“A’a barshi K’anwata, toh wallahi Ibraheem ka bud’e kunnuwanka ka saurareni sannan kuma kaje ka samu d’an iskan Aleeyun can kace mai ya fita daga harkan K’anwata banason ya rabawa yarinya attention nata, waec nata ne a gabanta and nothing else. Kuma this should be the first and last inhar kasan ka gayyato friends naka ma kadena kiran Zeezee side naku da Omar kana jina ai?” Shiru... “Ba da kai bane?”
“Naji” yayi maganan harshly “zan iya tafiya?”
“Tashi ka tafi” seda ya galla wa Zeezee harara cike da horo sannan ya fice.
“Kuma Baba kace mai kar ya daken.”
“Barshi bare tab’a kiba, if he does ma let me know.”
“Toh Baba nagode.”
“Yauwa K’anwata Allah miki albarka.”
“Ameen” tana kaiwa nan ta fice.
“Hummm!” Mama ta numfasa, “Allah de kyauta ana ganin gaskiya amman ayita takewa.”
*~ *~ *~
Washegari around 9pm Mama tayi d’akin Zeezee ta sameta se bacci take sha. Bargon data ruhu dashi Mama ta kwaye “oya mik’e kije ki had’a mana breakfast.”
“Wai shikenan sede ba’ayi hutu ba mutum barena samun bacci ba?”
“Tashi nace kona kira Ya Ibraheem ya zane min ke.” Seda tayi wasting several minutes sannan ta mik’e finally tayi toilet. After a while tafito still Mama na tsaye a d’akin nata tace, “chips zamuyi breakfast dashi” shiru tayi taqi amsawa, “ko baki jini bane?”
“Naji.” Bayan fitan Mama ta gwada line na Adeel har sau biyu amman baya picking, morning text message me dad’i tamai sannan ta fice. Nan da nan ta gama fere dankalin ta aza mai kan wuta ta dawo d’aki ta hau chatting da friends nata. Twelve (12) more minutes Mama ta dawo d’akin nata furiously “sekin mana setting gidan on fire zaki samu sukuni ko?! Kin d’aura man gyad’a tun tuni kinzo kinyi zamanki anan kina chatting? Mik’o wayan nace!” Zatayi magana Mama ta daka mata tsawa “miqo nace!” Badan tanaso ba ta miqa mata ta fice se tura baki take gashi Baba bai gida.
Gishiri ta zabga wa dankalin tana sawa cikin mai yayi chaaa!! Kad’an ya rage be zube mata a jiki ba. Dan yadda man yayi zafi da minti goma dankalin ya gama soyuwa ya dawo bak’i k’irin. A garin kwashewa ta k’one kanta a hannu, nan fa tahau disco a kitchen d’in ana cikin haka Mama ta shigo. “Ya haka Zeezee?”
“Ni dan Allah abarni, abanza ansa mutum ya k’one yau wayyo Allah na!” fridge ta bud’e ta ciro k’wai tare da fasawa kan burnt hannun nata. Idon Mama na tozali da k’onannen dankalin ta saki salati “meh wannan!”
“Dankali mana!” Zeezee ta bada amsa in an I-don’t-care attitude.
“Shine bak’i k’irin haka?” D’aya ta gwada d’agawa takai baki aikuwa bai tonuwa, ciki ko alaman soyuwa beyi ba amman ga waje nan ya k’one k’urumus! Bayan nan kuma ga uban gishirin data zabga. Wani abun se girkin Zeezee!
“Ji gishiri! Dagangan kika yi hakan koh? Daman tunda na saki aikin kiketa gunguni, dagangan kika k’onan koh?”
“Kamar ya dagangan? Ni dan Allah kibarni, zanji da k’unan danayi ne kokuma masifar ki.”
“Aww! rashin kunya zakimin akan asaran da kika min? Nasan maganinki, Ibraheem! Ibraheem! Zo Babana.” Ba tare da b’ata lokaci ba yafito “na’am Mama.”
“Yauwa kalli abinda Zeezee tayi da breakfast namu ina mata magana kuma tana gayamin maganan banza.”
“Meh wannan d’in wai?” ya tambaya dan kuwa ya kasa tantance ko dankali ne kokuwa a’a.
“Wai dankali nace ta soya mana tayi wannan abu.”
“Ke bakida hankali ne?” yayi snarling at Zeezee, banza dashi tayi se hura ma hannunta iska take.
“Dake fa nake magana!”
“Dama abinda ka iya kenan, toh dagangan nayi ne ai kuma kunsan ban iya soya dankalin ba kuka sani yi” dama cike yake da ita gashi yasamu another reason na mata duka. Waje ya tura Mama ya shigo kitchen d’in ya mata dukan tsiya, Mama dake waje tana “ya isa haka Ibraheem” dan yadda Zeezee ke ihu amman ina se kaman k’ara mata Mama tace yayi, kirb’anta yatayi seda ya huce haushinsa kap akanta sannan ya barta. “Nan gaba ki sake had’amin waje gun Baba kiga inban miki wanda yafi wannan ba.” Ball da ita yayi sannan ya umarce ta data mik’e abin tausayi se kuka take ta mik’e duk jikinta zafi yake mata batasan da wanne zata fara ji ba.
“Oya d’iba dankalin ki sake ferewa ki soya me kyau kuma ko wallahi na miki wanda yafi wannan.” Gabad’aya taci k’aniyanta yau ko bakin rashin kunyan ma babu “badake bane?”
“Dani ne” nan ta nufi gun basket d’in ta d’iba yana tsaye a kanta ta gama ferewa ta tsaga tasa mai, yana d’an yin zafi tasa gishiri dai-dai ta juye cikin man. Ibraheem ya barta ta fita daga kitchen d’in kafin dankalin ya soyu ma yak’i haka tana tsaye gun har dankalin ya soyu ta kwashe suka karya. Gabad’aya Zeezee ji take dama ba’a k’addaro mata da wannan rana ba, gashi har yanzu ta gwada line na Adeel koya shiga baya picking.
*~ *~ *~
Seda Azahar Baba ya dawo nan Omar daya gama tara kud’in siyan motansa yaje ya samesa ya mai sannu da zuwa. “Baba dama cikon naira dubu d’ari biyar (N500,000) nake so zan sai mota.”
“Iyyeh! Umari nawa ya girma harka tara kud’in sai mota? Wani model ne?”
“Honda DC ceh.”
“Ahh Honda nada kyau, so kanada gurantee na motan?”
“Eh duk mun gama magana komi is in place.”
“Toh bari zan maka transferring kud’in a account naka.”
“Toh Baba nagode Allah ya k’ara bud’i.”
“Ameen Allah maka albarka ya kawo mace ta gari” bayan yafita Mama tace, “oh! Yau wata rana Alhj anyi abin kai toh Allah k’ara bud’i.”
“Ameen” yace mata “ina Zeezee nekam? ”
“Tana d’akinta tana bacci.”
“Ayyah K’anwata yayi kyau toh.”
A ranan Baba ya sawa Omar kud’in as promised, a washegari navy blue discussion continue na Omar ya iso kowa ya taya sa murna barin ma Mama, ita deh Zeezee ko fita taga motan ma tak’iyi dan bak’in ciki. Shikenan Ya Ibraheem, Adda Mariam da Ya Omar suna da mota Yasmeen ma tace mijinta yace ze sai mata mota ita kad’ai ce bata da mota. Kanta ta rufe a d’aki tayita kuka kaman ba gobe, tana cikin yi taji knocking bisa k’ofar d’akinta kamar bazata amsa ba tace, “waye?”
“Baba ne Zeezee” jin shine ta mik’e ta bud’e mai “bade kuka kike ba K’anwata?” Yayi maganan yana scruitinizing face nata. “Wani abu ne?”
“Babu” tace sama-sama tana share hawayenta.
“In shigo toh?”
“Ka shigo Baba” akan kujera suka zauna, “meya faru kike kuka K’anwata? In matsala kike dashi bazaki sameni ki fad’amin ba seki rufe kanki a d’aki kiyita kuka? Ko kinada gatan daya fini ne Zeezee?”
“A’a Baba.”
“Then why won’t you tell me your problem?”
“I’m sorry.”
“Then fad’amin mesa kike kuka?”
“Babu.”
“Kina son muyi fad’a ko?”
“Duk su Ya Ibraheem dasu Adda Mariam suna da mota Yasmeen ma tace min mijinta yace ze sai mata mota ni kad’ai ce banida mota.”
D’an dariya ya saki kalan ta manya, “shine abin kukan K’anwata? Allah kaimu ki gama secondary school mana kiga, kowani kalan mota kikeso zan saya miki.”
“Har sena gama Baba? Bayan ga ‘yan ajinmu su Sumee, Lieeymarh, Nafeesat, Billy duk suna da mota, Lubiee ma Abbansu ya sai mata ita da yayanta.”
“Hakane?”
“Eh wallahi Baba.”
“Toh share hawayenki kinji? Muddin ina raye ba abinda zaki nema ki rasa, in shaa Allahu nan da 2 weeks zan sai miki motanki kema.”
“Dagaske Baba?!” tayi maganan sounding thrilled.
“Eh mana K’anwata in ban farinta miki ba mawa zan farintawa?”
Tsalle ta daka ta d’ale cinyansa tare da hugging nasa “I love you so much Baba.”
“I love you too K’anwata” bata jima ba ta koma gefe ta zauna, “yauwa kuma banason ki fad’awa kowa wannan magana kinji ko? Ko Mamanku ne karki fad’a mata.”
“Bazan fad’awa kowa ba Baba amman wani iri zaka sai min?”
“Don’t you trust me? Its a suprise.”
“I can’t wait! Allah ya k’ara bud’i Baba. Yauwa ance zamu iya fara kawo kud’in neco registration namu.”
“Toh bari in kuka koma school ko a gobe kikeso kikai?”
“Eh a gobe.”
“Toh Allah kaimu.”
“Ameen Baba nagode.”
“Nima nagode” har waje ta rakasa sannan ta dawo d’akinta se tsalle take ita za’a sai mata mota, fatan ta Allah yasa mercedes-benz ce, a rayuwa ba motar dake burgeta kaman benz, benz is life!
★*★*★*★
Life moved on da k’yar abubuwa suka dai-daita tsakanin Zeezee da Adeel, a rayuwa ba abinda tafiso kamar taga ita da Adeel are on good terms suna shiri. Duk wani abinda tasan ze haddiso musu da matsala tana k’ok’arin kiyayewa saboda zaman lafiyansu ya fiye mata komi a duniya.
Yau ranar ta kasance Tuesday da yamma around 4:30PM tana kwance a d’akinta ita kad’ai. Ba kowa a gidan se ita Baba ya fita su Mama kuwa sun je gidan Kaka. Baba ne ya kirata nan da nan ta d’aga “hello Baba.”
“Na’am K’anwata kina gida?”
“Eh.”
“Toh kifito bakin k’ofa yanzu.”
“Toh gani!” mayafinta taja da waya ta fice tana fita taga the most biggest suprise of her life, sabuwar mercedes benz C300 ce fa fara k’al ko ledan jiki ba’a b’are ba. “Omg!” Kawai take ta nanatawa, kuka ta soma tsabagen murna, da gudu taje tayi hugging Baba. “Baba I don’t know the right words to use in thanking you, bansan ya rayuwa na zata kasance without you ba, you mean the world to me you are my hero, I love you so much, morethan you can ever imagine.”
“Zeezee na ta girma I love you as much K’anwata ga key naki nan.” Nan ya mik’a mata, wayarta ta bud’e ta shiga snapchat ta musu selfie ita Baba da motanta tayi adding caption _priceless gift from my Amiable Dad, ILH._ daga nan tayi ta d’aukan motar hoto, saura tayi shi kad’ai saura ita dashi. Ana cikin haka su Mama suka dawo a motan Omar. A gefen motan Baba sukayi parking suka fiffito “sannu Baba” suka yi mai ya musu sannu da zuwa.
“Toh wannan mota fah? Suwa sukazo sukayi parking anan?” Mama ta tambaya.
“Bana mutane bane nawa ne Baba ya siya min” ta k’arisa gunsa tare da kwanciya ajikinsa.
“Meneh? Dawo baya ban jiki ba” Mama tayi maganan disbelievingly a yayinda Omar da Ibraheem sukayi tsaye gun dumbfounded.
“Mota na ne Baba ne ya siya min.”
“Mota! Alhj mota ka sai wa Zeezee?! Da shawaran waye? On hi Hafsah! Mota de?” Ta k’arisa gun motan tana shafawa “kuma sabuwa ko hawanta ma ba’ayi ba.”
“Sabuwa?” Omar yayi maganan yana bin motar da kallo.
“Ni kibar shafamun mota, Baba kace tabar shafa min mota.”
“In bazaku fad’i alkhairi ba keda ‘ya‘yanki seku ja bakinku kuyi shiru.”
“Alhj amman wannan wani erin rashin hankali ne?”
“Sai ma K’anwar tawa mota shine rashin hankali? Ke kin manta kalan alkhairun da marigayiya tayi min ne?”
“Ai marigayiya kace, wannan kuma ba marigayiya bace wallahi tun wuri a mai da motan nan. Wani irin rashin hankali ne haka? Ban tab’a jin inda aka saima ‘yar 16 years mota ba.”
“Yau kinji ai tunda a gidan ki akayi, kuma ba miyar da motan da za’ayi, ina key d’in mu shiga miki da motan ciki.”
“Gashi Baba” nan ta bashi key d’in, a parking lot daya gyara dan parking motansa ya mata parking nata sannan ya kai nasa garriage, Mama da yaranta de suna ganin ikon Allah yau. Kaka ta kira ta irga mata gashi fa Baba ya saiwa Zeezee mota bayan ko gama makaranta batayi ba. Suna gama wayar Kaka ta kira Baba dan mai magana aikuwa ya mata k’arya wai se Zeezee ta gama makarantar zata soma hawa.
Zeezee kam na can a d’akinta tana ta kan applying makeup tana gamawa taci farar gown nata sukayi anko da motanta sannan taje ta cigaba da d’aukan selfie da motar tata. Ranan snapchat seda yayi kuka haka instagram ma. Lubiee couldn’t believe it dataga ansai wa Zeezee mota haka Adeel ma, shi shege girlfriend nasa na hawan C300 shikuma E350 4matic. Washegari Mariam tazo kallon motan *_‘YAR GATAN BABA_*
Cikin sati biyu Baba ya sa wani yaronsa ya koya wa Zeezee mota, tinting glasses d’in tayi da darkest colour, hakan kuwa ba k’aramin karb’an motan yayi ba dake farar mota ce. Kullum ba aikinta se wanke motanta, ko kad’an batason abinda ze tab’a mata shi. Yau da La’asr ta d’au wanka ta feffeshe da turare sannan ta d’au key’n motarta ta fice a waje taci karo da Mama “aikin kenan a penta fuksa a fita yawon banza sa’o’inki suna karatun jamb da waec ke kullum cikin fita unguwa koda shike ba laifinki bane na Baban naki ne tunda ya d’au mota ya baki.”
“Haters are gonna die.”
“Me kika ce?”
“Nace Allah barmin Maman Zeezee, gidansu Lubiee zani.”
“Zancen kenan kullum gidansu Lubiee. Seta gaji dake ai, ke bazaki zauna ki fara karatu ba ko?”
“Wai Mama ce miki akayi yanzu ana karatun waec ne? Answer kawai ake suburbud’a wa mutane.”
“Da kyau.”
“Eh man ku naku lokacin da ba’a baku ba flat F9 kuke fitowa dashi ba bayan karatun da kuke, nide in Baba ya tambayi ina nake kice mai na tafi gidansu Lubiee, ko akwai abinda kikeso?”
“Kan Uwarki nakeso ‘yar banza kawai.”
“Hohoho Maman Zeezee Allah barmin ke kiga ci gabana a duniya.”
“Mschww!” taja tsaki ta fice. K’arisawa gun motarta tayi ta hau gogewa akan wankewan da tayi d’azu. Tana cikinyi Omar ya fito ya k’are mata kallo sannan yace, “ke bud’emin gate.”
“Hehe! Su Ya Omar jiya ba yau bane fa. Levels don change yanzu, ni me sabuwan mota pil bance a bud’en gate ba sekai da seda wani bature ya hau ya baka zakace na bud’e maka?”
“Me kika ce?” yayi snarling at her.
“Babu nace barin gama gogewan na bud’e maka.”
“Da yafi maki kam” nan da nan ta gama ta bud’e mai yana fita itama ta fice. Music nata ta k’ure tana kad’a kai tana driving ana tab’a rawan dab, hankalinta a ruwan sanyi. Gidansu Adeel nata ta wuce, bayan ta samu gu tayi parking ta kirasa “hello My Very Own.”
“Sweetest Love.”
“Kana gida ne?”
“Yup wani abu ne?”
“Nop just kafito bakin gate.”
“Okay right away!” nan yayi hanging. Wayoyinsa ya tattara sannan yayi glancing kansa a mirror ya fice, yana fita bakin gate yaga Zeezeensa tsaye gefen motarta da sunglasses maqale a fuskanta tana mai wani mayen murmushi, murmushin shima ya mayar mata sannan ya k’arisa gun sukayi hugging as always kamar yadda suka saba sekace ba ‘ya‘yan musulmai ba. Bayan yayi releasing nata yayi pecking nata a kumatu “you are looking super sexy Barbie.”
“I know right Very Own toh ya kake?”
“Lafiya, you didn’t tell me you were coming” yayi maganan yana wasa da siraran yatsunta.
“I thought I might suprise My Very Own.”
“Best suprise ever!” ya sake pecking nata “so zamu shiga ciki ko we are going somehwere?”
“Going somewhere just the two of us.”
“I love you Babe.”
“I love you much more My Very Own” ta mik’a itama tayi pecking nasa a cheeks “lets go, hurry I’ll be the one to drive.”
“No way my Queen, allow your King to drive you.” Shi da kansa ya bud’e mata motan ta shiga sannan ya rufe ya zagaya ya tada motan suka fice zuwa Hysaan beverages ya siya musu roasted chicken da drinks daga nan suka wuce can bayan gari inda ba mutane yayi parking. Suna cin kazan su suna hira har suka gama se kusan to 6pm Zeezee ta isa gida.
*~ *~ *~``
Haka deh Allah ya cigaba da raya Zeezee har suka samu sukayi jamb nasu ta fito da 205 points. Ita kanta bata zata zataci ya kai haka ba saboda bawani karatun kirkin datayi as always tana kan waya da Adeel nata. Dama Baba yayi promising nata kan intaci fiye da 200 points ze sai mata duk abinda takeso, iphone 7s tace takeso aranan aka sai mata shi, haka tayita cika ‘yan instagram da snapchat da pictures na iphone 7s nata. Ana cikin haka bikin Ibraheem da Fateemah ya taso, preparation suke sosai ‘cause this is the first time Baba da Mama suke aurar da d’an su na miji. Not long enough aka soma wedding events, Zeezee de kam har ta kusa fin amarya shan kyau dan kuwa har Abj ta tura akayi mata gowns nata. Makeup artist da tama amarya makeup kuwa ita tayi mata nata.
Se palli take da rawan kai. A ranan dinner ta d’au mutane cikin motar tama tak’i ba yadda Mama batayi da ita ba amman tak’i, agun dinner kuwa table nata ita da Lubiee, Adeel, Uthman (boyfrined na Lubiee) seda friends nasu guda biyu ta tanadar musu suka zauna. Angama komi aka kai amarya Abuja. Zeezee dad’i kasheta yanzu ba Ya Ibraheem d’an shisshigi, cin duniyarta zatayi da tsinke hankalinta kwance. Wannan kenan!
Tunda Ibraheem yabar gidan iskancin Zeezee ya k’aru, daman ba wani tsoron Ya Omar take ba, hakan yasa ta sake raina Mama kota mata magana se in ta gadama tayi, cikin sa’a suka soma waec nasu har suka gama saura neco suyi goodbye da secondary school. D’an hutun dake tsakanin waec and neco Zeezee ta had’a akwatinta zata Abuja gun Ya Ibraheem simply because taje taga kalan zaman da suke da matarsa badan wani abu ba. Ta jirgi Baba ya biya mata, 1pm suka yi landing. Ibraheem da Fateemah duka sukaje d’aukota daga airport bayan angama hugging da gaisuwa suka dawo gida. Baki Zeezee ta sake data ga mansion na Ibraheem ashe de magabata basuyi k’arya ba irin wannan gida! Mschww ita da tasan Ibraheem zexo yayi kud’i haka data had’a Aunt na Lubiee da Ibraheem akan wanan Fateeman, haka kawai Zeezee ta tsaneta.
*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com
No comments:
Post a Comment