Tuesday, 20 December 2016

‘YAR GATA CE!

BY MIEMIEBEE
PAGE 18

  *December, 2016*



     On the 20th of Ramadhan Zeezee ta tashi ba azumi, dad’i kasheta tun on 15th take jiran date nata daman, se aukin son shan azumi da kuma k’in yin ramako. Ko wannan karan ana weeks to Ramadhan Mama tasa Ibraheem tsaye kanta sannan ta biya azumin nata. Da safe around 10:30AM ta tashi, wani irin sanyi ake wane a Moscow, Malam bahaushe yace jifa yazo dai-dai da zama. Dama bason wankan take ba jin wannan sanyi ta kwaskware jikinta ta canza inner wears tasa sabon kaya sannan ta fito a parlour taci karo da Mama ta gaisheta.
   “Se yanzu kika ga daman tashin?”
  “Eh sanyi ake shiyasa.”
  “Yayi kyau kinga Baaba harta gama aikinta ta tafi, in kin gama breakfast nakin seki wanke plates da duk abinda kikayi amfani dashi sannan ki share kitchen ki sake mopping.”
   “Wai duka aikin nan ni zanyi? Ita Baaban nan sekace aljana wai harta gama aiki mschw ni wallahi dama canza me aiki akayi.”
  “Nide na gaya miki ga Ya Ibraheem na gida, in kinason kanki sekiyi abinda na saki kona basa izini ya zane min ke k’azama kawai, dubi k’wansa a idonki amman de bakiyi wanka ba ko?”

   “Nayi mana” tayi maganan tana sa k’ark’ashin skirt nata tana ciro k’wansan.
  “K’arya kike bakiyi ba nasan ki ai.”
  “Toh a wannan uban sanyin mutum ya hau wankan safe sekace meh zuwa office, se can anjima zan yi” tana kaiwa nan ta zarce kitchen tashiga had’a indomie abinda ta iya.
 
  *~ *~
   Da Azahar bayan sanyi ya ragu rana yayi taking over Zeezee tayi wanka tasa ¾ leggings nata da vest ganin Ibraheem bai gida, bayan tagama had’a lunch nata nanma indomie ta d’au tabarma ta baje tsakar gida da kanta a bud’e tana cin abincinta bad’an kunya taje d’aki taci. Tafe side-by-side Mama da Baba suke tana mai rakiya, tana ganin Zeezee tahau surutu “haba Zainab! Meh hakan? Ke bakida kunya ne ko sekin gaya wa duniya yau baki yin azumi ne? Maza wuce d’akinki da Allah sakariya kawai.”
    “A’a Hafsah me kuma yayi zafi haka da zagi? Me aciki dan yarinya nacin abinci a tsakar gidan Babanta?”
  “Aww ma tambaya kake? What if ko friends nasu Omar suka shigo fah? Zeyi fasali ne?”
   “A’a gaskiya banason irin wannan tak’uri wallahi, kibarta kurum! ci abincinki Zeezee.”
  “Da kyau daman ka saba ai” bata k’arisa mai rakiyan ba ta dawo ciki. Bayan fitan Baba bada jimawa ba Ibraheem da friends nasa about 4 of them suka shigo gatsau! Kasancewar shine a gaba yana ganinta yamata ido kan tayi sauri ta fice aiko data gano haka ta juya mai kai ta cigaba da cin abincinta. Yace da friends nasan su juya kuma kunya yakeji haka suka zo wucewa suna kallon Zeezee ko ajikinta ba kayan arziki ne sanye da ita ba, bama wannan ba ace agaban friends na yayanta tana cin abinci a azumi. Bayan da tagama tayi dukkan aikin da Mama tasata da cuwa-cuwa kamar yadda ta saba. Koda aka soma aikin bud’a baki yau tak’i sa hannu acewarta ai ba azumi take dashi ba, saboda haka ba aikin da zatayi shide Ibraheem jira yake Baba ya fita yayi mata d’ankaren duka.

                 ★*★*★*★
    Life moved on, abubuwa da dama sun gudana ciki harda samun bud’i kad’an kad’an da Baba ya soma samu, abu fa kamar wasa arziki se dawowa yake fiye dana da, kowa se murna yake a gidan suna cigaba da addu’a suna kuma yiwa Allah godiya babu kamar Mama data d’au yanzu wai Baba yayi hankali, kodan abubuwan da suka faru a baya yaci ace Baba ya koyi darasi yanzu ya dena biyewa Zeezee. Ashe de kam abu na cikin duhu ne! Sabuwar ipad da waya k’irar iphone 6s ya sai wa Zeezee, ba ita kad’ai ba har Yasmeen sannan a babban sallah yayi ma kowa d’inki kala bakwai-bakwai Zeezee kam kala goma akayi mata wayyo ita dad’i kasheta. 2 weeks back sukayi resuming school tana Ss 2 kenan yanzu with fifteen (15) years old. Ana takan zama budurwa se pallin tsiya, sede fa har yanzu hankalinta na akan Ammar bawani paying attention d’in kirkin da take a school.

   Bayan Sallah da sati d’aya Mariam ta sake haihuwa tasamu ‘yarta Hafsah takwaran Mama anyi hidiman suna lau, Allah shi raya Mama.

   *~ *~ Saturday morning.
     Zeezee as well as her other siblings duk suna gida, Omar ma recently ya gama service ya shiga neman aiki.

    Knocking Mama tayi bisa k’ofan d’akin Zeezee sannan ta shiga da sauri-sauri ta b’oye wayarta ta soma faking bacci.
   “Wai bacci kike? Tashi zaku gidan Kaka yau (Maman Babansu) kafin nan tashi mu zab’i kad’an daga cikin kayakin ki zaku d’an bawa yaran da suke zama da ita kunce, Yasmeen harta bada nata set biyar saura ke.” Zumbur Zeezee ta mik’e zaune, “meneh? Bada kuncen kaya? Ni wallahi bazan bada komi ba shikenan abi asawa mutum ido kan kayakinsa gaskiya a’a.”
   “Kamar ya a’a Zeezee? Ke bakisan aikin lada bane, in Allah ya hore maka se ai ka taimaki na k’asa da kai ke kanki bakisan yawan adadin kayakinki ba, ko wanda Babanku ya d’inka miki recently bayan Sallah ma kd’ai sun isheki amman kice bazaki bada kuncen kaya ba? Maza tashi ki zab’a min guda biyar nace karki bari raina ya b’aci.”
  “Ni wallahi banaso” tayi stating tana shure k’afafunta kan gadon.
  “Zan kira Ibraheem fah!” Jin haka ta mik’e ta bud’e wardrobe natan, wasu kod’ad’d’un kayakinta guda uku tun tana Jss3 tafito dasu ta ajiye kan gadon “gasu nan ai sunyi ko?”
  “Tsumman goge tiles nace kibada ko kayan sawa?” Bankad’eta Mama tayi ta ciro wasu sabin kayakinta biyu sannan ta had’a da wanda suka d’an sha ruwa kad’an guda uku. Ihu Zeezee ta k’urma tashiga k’wala wa Baba kira, unfortunately bayi gida haka tayita kukanta har ta godewa Allah. Tana ganin Yasmeen nata shiri ita ko wankan ma batai ba, seda sukazo tafiya Ibraheem ya tambayeta, “kefa bazaki bane?”

   “Bazan jeba me ze kaini gidan Kaka ana zaman lafiya, ace ma mutuwa tayi mana amman tana k’alau sena hau zuwa gidanta adafa wa mutane tuwo a kuma sasu cin dole kuje Allah ya kare.”
   “Mu tafi Yasmeen bar fitsararriyar nan anan.” Maman data d’au duka yaran suka fita tana fitowa daga d’aki itama tayi shirinta zata fita kawai taga Zeezee “ya haka? Baki bisu bane ke?”
   “Meh ruwanki toh? Kin kama kin kyautar min da kayaki na” nan ta mik’e tazo shiga Mama ta d’aka mata dundi a baya “shegiya fitsararriya kawai”
  “Wallahi Baba ya dawo sena gaya mai kince min shegiya” tayi stating in a crying tone, kota kanta Mama batai ba ta fice. Wayarta dake cikin pillow case ne ya soma ruri, tana dubawa taga Ammar hesitantly ta d’aga, “halo Sweetheart.”
  “Yes Pretty are you free?”
  “Yes I am wani abu ne?”
  “Ki shirya zanzo in d’auke ki we are going somewhere.”
  “Zaka zo kuma Handsome? Ko ka manta inada brothers ne?”
  “Holy sh*t suna gida kuma ko?”
  “Actually no duk sun fita am home alone but they can come back at any moment.”
  “Kawai de kice you are not interested shikenan, I’ll go look for another date, hanging out fa za’ayi Ss2 Vs Ss3 kema kinsan you need to be there.”
  “Haba Baby taya zakace am not interested wallahi I am naji zan shirya yanzu sekazo.”
  “Yauwa Sexy, dress hottie kinji?”
  “Yes Boyfriend, I love you.”
  “I love you too Babe” yayi hanging.

    Tana ajiye wayan ta shiga cin faracunta she’s all confused batasan me zatayi ba, what if lokacin da yazo Ibraheem ko Baba suke dawowa su kamata fah? Kai ta kad’a amman inhar banje ba Ammar will be angry infact ze iya cewa ma lets break up cause mata rushing akansa suke. Bayi ta fad’a tayi wanka a gurguje tayi applying medium makeup sannan ta ciro wani red strapless gown tasa ta d’aura kanta me kyau ta feffeshe da turare. In 3 minutes time Ammar ya kirata bayan ta rufo ko ina agidan ta fita exactly kalan motan Ya Ibraheem Ammar yake hawa, da wuri-wuri ta k’arisa gun motan, wani irin mayen kallo Ammar ke binta dashi musamman dayaga d’an cleavage nata awaje. Ta bud’e motar dai-dai zata shiga kenan sega motan Ya Ibraheem wane daga sama batasan alokacinda ta saki fitsari kad’an a panties nata ba. B’ari ta shiga yi tama rasa nayi “Ammar ka fito! ka fito please” alokacin da Ammar ya fito daga motar har Ya Ibraheem yayi parking motarsa shima yafito yana nufan gunda suke in a swaying motion tace, “koya tambayeka waye kai kace you are my classmate.”
   “Sannu da dawowa Ya” tayi stating in a cracky voice hannunta se had’a gumi suke ayayinda zuciyarta keta harb’awa tana addu’a Allah ya sa karya mata abin kunya a idon Ammar.
   “Ina kwana?” Ammar ya gaishesa, ko amsawa beyi ba yace in a serious tone, “ina zakije da wannan shirin? Sannan kuma waye wannan?”
  “Ya ba inda zani, classmate d’ina ne yazo tambaya na materials da zai siyo mana na physics practicals namu ne” ta k’are maganan tana b’ari.
  “Nace waye wannan kuma ina zakije da wannan d’an iskan shirin?!”
  “Zeezee I’ll get going se mun had’u Monday at school zanje na siyo materials d’in” Ammar na kaiwa nan yaja motarsa ya tafi.

   “Saurayi kika fara kawowa gida ko?” Kafin ta hankara ya kwad’a mata mari a fuska, ihu tasa wajen tana kuka ahaka ya jawota ciki “ke ba wai ‘yar iska ba, zaki gane kuran ki agidan nan” belt ya zare ya hau dukanta seda yamata lik’is sannan yace, “nan gaba ko kwatancen gidanku bazaki wa ‘yan iskan yaran ba balle suce zasu zo d’aukanki.” Da k’yar ta mik’e zata nufi d’aki tana kuka ya dakatar da ita “where do you think you are going? Haka da kayan Baba zezo ya sameki yasan abinda kikeyi.”
  “Ya dan Allah ka rufa min asiri wallahi na tuba bazan sake ba.”
   “Karki b’ata miyan bakinki kina ban hak’uri saboda ba jinki zanba.”
  “Wayyo Allah na! dan Allah kayi hak’uri wallahi na tuba bazan k’ara ba.” Ba kalan had’a shi da Allan da batai ba yak’i hak’ura. Ana cikin haka Mama ta dawo nan ya irga mata komi sam bata sha mamaki ba, saboda tasan wannan ne dalilin dayasa tace bazata gidan Kaka ba kenan, not long enough Baba ya dawo shima Ibraheem ya irga mai komi sosai yasha mamaki da har baison believeling abinda Zeezee tayi. Kuka tahau musu a wajen tana rantsuwa akan k’arya ita sam wallahi ba saurayinta bane classmate nata ne.

   “Inhar classmate nakin ne meya zo yi?” Mama ta tambayeta, shi Ibraheem dan haushi ma barin gun yayi.
  “Amsan list na materials da ze siya mana na physics practicals.”
  “Shi ne kikayi wannan shigan?”
  “Toh ba nayi wanka bane zan d’au hoto yacemin gashi yazo na fito.”
  “Kai! Yarinyan nan k’arya take wallahi, saurayinta ne, inada tabbacin kina sane da zuwansa yasa kika k’i bin yayyun naki gidan Kaka.”
   “A’a wallahi ba haka bane, Baba Allah ba k’arya nake ba, ba saurayi na bane.”
  “Na yarda dake K’anwata ba saurayi sekin gama secondary ba?”
  “Eh Baba.”
  “Aww ka yarda da k’aryan data sharara ma d’in kenan? Humm wallahi Alhj ka cigaba da take gaskiya, ka kuma guji ranan da yarinyan nan zata ma abin kunya” tana kaiwa nan ta fice itama. “Zeezee kifad’an gaskiya shin dagaske saurayi ne yazo gunki?”
  “Wallahi a’a Baba ai bazan ma k’arya ba.”
“Shikenan jeki huta yi hak’uri kinji? Zanma Ibraheem magana.”
  “Bashi kad’ai ba har Mama d’azu ta d’ibe min kayakina wai za’a kai gidan Kaka.”
  “Karki damu gobe Omar ze rakaki shago na ki d’au turame biyar masu kyau abinki.”
   “Toh Baba nagode.”***

   Haka nan Baba ya cigaba da d’aure wa Zeezee gindi agidan komi tayi koda kuwa yasan ba dai-dai bane bayi tsawata mata ga kuma yadda yake spending money lavishly akanta, bada jimawa ba akayi auren Yasmeen, ansha budiri sosai barin ma Zeezee dake nan wane amarya itama dan yadda tasha gayu. Bayan biki aka kai amarya Yasmeen Kaduna.
 
   _Wednesday morning 11:30AM_
  Kowani d’alibi na a class yana d’aukan lesson banda Zeezee da Ammar da suka keb’e a wani empty class suna hira. Ana cikin haka wani teacher yazo wucewa ya kamasu. Ai kuwa Zeezee ta tsure tarasa nayi dan inhar aka kira Baba aka sanar dashi nata ya k’are. “What are you two doing here while classes are taking place?” Ya tambayesu both in an angry tone. Kame-kame suka shigayi both of them har teacher’n ya zagayo ya shiga class d’in “oya follow me to my office now!” Zeezee najin haka tayi ma Ammar ido se kawai ta yanki jiki ta fad’i k’asa ta soma wani irin mahaukacin tari da wani d’an banzan nishi wane ana cirewa kafiri rai, ganin haka Ammar da teacher’n sukayi kanta “whats happening to her?” Yayi saurin tambaya.
   “That was how I found her also Sir, I think she’s athmatic.” Ammar yayi stating yana k’ok’arin d’ago ta daga k’asa. “Is that the reason why you two are here alone?”
   “Yyes Sir, I was passing by and then saw her unconcious that was why I rushed in.”
  “Hurry lets take her to the sick bay” haka ya kinkimi Zeezee zuwa bay aka kwantar da ita har a yanzu bata bar tarin munafircin ba “is she asthmatic?” Nurse d’in tayi saurin tambaya “yes” Ammar ya bada amsa. Inhaler sabuwa ta b’allo ta bata, zugi biyu Zeezee tayi ta soma daidaita numfashinta kaman dagaske, bayan d’an hutawan da tayi a bay ta koma class. Su Lubiee se tambayarta suke ko lafiya nan ta labarta masu komi sukayi ta dariya.

   _Closing hours_
   Yau Baba da kansa yazo d’aukan Zeezee, dai-dai ta shiga mota kenan teacher’n d’azun ya fito ganin Baba da prado jeep ya nufi motan nasu ya gaishesa, zuciyan Zeezee se harb’awa yake Allah sa karya cewa Baba ya kamata dana miji su kad’ai a class, kawai seji tayi yana cewa Baba akai ta asibiti d’azu asthman ta ya tashi.

   Suprisingly Baba ya tambaya dama Zeezee nada asthma ne? Bayan ya sallami teacher’n da N5,000 ya tafi. “K’anwata kinada asthma ne dama?”
  “Wallahi Baba kawai yau ina zaune naji nishi na nawani sama-sama, chest d’ina na tightning nayita attishawa kuma amman da sauk’i yanzu.”
  “Kaman ya da sauk’i? Bari mu wuce asibiti Dr. Zakir ya duba ki, sannu ko?” Anzo gurin Zeezee tace a ranta. “Baba cikina na min ciwo inason using bathroom mubari ko gobe muje, wayyo!”
   “Toh Allah kaimu goben sannu ko, amman ko inhaler ne asai miki ai ko?”
  “Eh Baba” pharmacy suka wuce ya sai mata inhaler sannan sukayi gida. Haka kullum Zeezee ke raina wa Baba hankali tak’i yarda aje asibiti daga k’arshe kiran Dr. Zakir akayi aka irga masa symptoms na k’aryan da Zeezee keyi nan ya tabbatar musu da eh asthman ne, magunguna yayi texting wa Baba aka sai mata. Itade Mama kallonsu kawai take sabida tasan k’arya Zeezee ke. Tun daga ranan Zeezee ta samu sara ba aikin da take agidan in Baaba batazo ba sede in Mama tayi shara da kanta danko fakewa Zeezee ke tace asthman ta ze tashi idan tayi shara Baba ko ya d’aure mata gindi as always.

   _Few days later..._
  Kwanan Baaba uku batazo ba kasancewar batada lafiya, through out Mama ke shara Zeezee sede ta mata sannu da aiki. “Zeezee!” Mama ta kirata kan su wuce su share mata d’aki dan kuwa rabon d’akin Zeezee da shara tun da Baaba tabar zuwa, “shiga mu share miki d’akin mak’aryaciya kawai. Kalli wai wannan d’akin budurwa ko kan gadonki baki iya gyarawa ba maza kakkab’e ki gyara” tana tura baki ta jajja ending d’in ta tuttusa “gashi na gama.”
  “Ahakan ne kin gyara? Kifa sani ‘ya mace ce ke kuma dole wataran zakiyi aure kina gani ai ba Yasmeen ba Mariam yanzu next kece.”
  “Ai zan koya in na gama secondary school.”
  “Mschww!” Hannu tasa ta d’aga katifan ma gabad’aya dan share k’ark’ashin gadon. Ai kawai sega maguna k’ark’ashin gadon Zeezee tamkar pharmacy, maguna barkace.
  “Laaa’ila! Meh wannan? Drugs kike siyarwa?”
  “Nikam ki sauk’e min katifa na zan share d’akin da kaina.”
  “Ai dama nasani ba asthman da kike da, kuma wallahi a kunnen Babanku, ‘yar banza kawai kullum kisa ayita siyan maki magani masu tsada baki sha?”

  “Ina sha mana wannan fa ba maganin asthman bane na zazzab’in dana tab’a yi ne.”
  “Allah yasa na haukan da kika tab’ayi ne.”
  “Toh ki kawo tsinstiyan zan share amman karki gayawa Baba please Mama.”
   “Mschww!” yasar da tsintsiyan tayi ta fice, Zeezee da kanta ta shiga share d’akinta tana cikinyi Baba ya dawo ya tarar da ita “ya da haka? Mesa zakiyi shara bayan bakida lafiya, Hafsah! Ban hanaki sa yarinyan nan shara ba.”
   “A’a Baba ba ita ta sani ba kuma ma ai sharan kad’an ne karka damu I can manage, sannu da zuwa.”
  “Are you sure baze dameki ba? Kinsan fa bakida lafiya.”
   “Eh karka damu Baba.”





*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

1 comment:

Anonymous said...

hmm a daibi ahankali