BY MIEMIEBEE
PAGE 17
*December, 2016*
_I dedicate this page in honour of my dear supporters and huge fans *Amyna Malam, Baby Amrah* and *Haleema Abdullah* ILY'ALL๐ #OneLove❤_
_Several weeks later..._
Rayuwa de ta canza daga dad’i zuwa rashinta. Ba abinda ke tafiya wa Baba da iyalansa dai-dai komi ya tab’arb’are more especially ma Zeezee da batasan me k’addara ba bale ta rungume sa. She is used to samun duk wani abinda takeso at that very moment amman yanzu ko kud’in kati setayi dagaske take samu, kullum a cikin complaining take ita tagaji da rayuwan talauci ita kaza ita kaza, harta ipad nata sanda aka siyar danyi mata cikon school fees. Ibraheem na iya k’ok’arinsa dan har na terms biyu kusan dubu d’ari biyu kenan yake biya wa Zeezee as school fees. Without his help da anjima da cire Zeezee daga LYS.
A yanzu haka tana Ss1 tanayin sciences, Zeezee tana girma kyanta na ta dad’uwa, doguwa ce dai-dai, ta kuma k’ara kauri kad’an kan sirantakarta wanda hakan ya mugun fito da dirinta. Tun shigarta Ss1 ta rage karatu se aukin kula yeye samari, kullum seta yini tana waya kokuwa chatting. Kasancewar ayau friends na Baba daga Yola zasu zo yasa akayi lunch like no other, kap ‘yan gidan sun manta when last akayi miya yaji nama kaman na yau stew ne had’ad’d’e wanda yasha nama tako ina da coconut rice. 3:23PM Ibraheem ya dawo da Zeezee from school tana shiga ciki tayi kitchen Yasmeen tasamu tana d’an d’auraye used plates babu ko sannu ta ja plate ta shiga d’iban abinci, da wuri Yasmeen ta dakatar da ita.
“Ke wayace miki wannan namu ne? Ko bakisan Baba zeyi bak’i bane yau?”
“Semeh dan zeyi bak’i me had’i na da bak’insa? Nikan matsa min in d’iba abinci.”
“Mama! Mama! Kiga Zeezee wai abincin friends na Baba zata d’iba.” Daga ciki Mama tace da Zeezee karta tab’a ga nasu na gida can agefe amman dake Zeezee banda maganan Baba bana wanda takeji haka ta d’iba na friends nasan ta sa nama bakwai (7) akai ta k’ara mai. Baba na dawowa gida Yasmeen taje ta fad’a mai, masifa ya shiga yi mesa Mama bata hana Zeezee d’iba ba, “yanzu ina zan samu kud’in sai wani naman?”
“Toh kana blaming waye? Tana jin magana na ne? Bakai ka b’ata taba ai nace mata karta d’iban tak’i jina se kasan nayi yanzu.”
“Aww haka ma zakice ko? Instead kija mata kunne.”
“Ai kai da ka b’ata ta kai zaka gyarata saboda haka ni kabar cika min kunne.”
“Kin kyauta Hafsah, dake yanzu kinga bani samu kaman da dole ki zauna kina gayamin magana iya san ranki, kisani ba ahaka zan gama zama ba in shaa Allahu Allah zemin bud’i”
“Aini ba haka nake nufi ba don’t misinteprete my words” D’akin Zeezee ya nufa ya sameta secin abincin ta take tana chatting “sannu da zuwa Baba” tace dashi.
“Haba! K’anwata taya zaki kwashe nama har bakwai (7) ke kad’ai bayan kinsan halin da muke ciki a gidan nan.”
“Shikenan Baba nama d’aya kakeso in d’auka?”
“Eh mana ai babu ne yanzu lokacin da akwai ba na miyan nake baki duka ba?”
“Nikam gaskiya ban saba ba.”
“Kikace meh?”
“Nace kayi hak’uri.”
“Naji amman karki sake yin hakan yanzu me kikeson na bawa bak’in in sun iso?” Bayan Baba ya fita taja k’aramar tsuka “shikenan sekace ni na d’aura mana talaucin da za’a hanani cin nama, wallahi sede in ba’a siya ba in bahaka ba senaci.”
~* ~* ~*
Ana cikin haka promotional exams nasu Zeezee ya zagayo sam batta karatu se chatting da samari a daren da suke da Chemistry Mama tashigo d’akinta unexpectedly kawai ganin Zeezee tayi ta baje kan gado rungume da pillow tana waya da saurayi daman bata tab’a kama ta red-handed ba seyau, koda Yasmeen ta kawo mata k’orafi cewa fa ga abinda Zeezee keyi bata yarda ba saboda bata d’au rashin hankalin Zeezee har yakai ga haka ba. Wayar ta katse da wuri ta jawo littafinta ta soma karatu.
“Dawa kike wayan?”
“Kamar ya da wa kuma? Da Lubiee man na tambayeta formula ne.”
“Ni zaki raina ma hankali? Nace da wa kike wayan?”
“Da Lubiee mana nikam haa’an!” K’arisowa cikin d’akin Mama tayi a fusace “dawa kike wayan nace? Da saurayi koh?”
“Nide bada saurayi nake waya ba.”
“Oya miqo min wayan naki keda shi sekun gama exams.”
“Haka kawai se kimin siezing waya saboda Yasmeen tace miki da samari nake waya ni wallahi bazan yarda ba” nan ta b’arke da kukan munafirci ta miqe ta nufi d’akin Baba don kai mai k’ara, a hanya ta lab’e tayi deleting call nata da Ammar “ya haka meke faruwa?” Baba yayi saurin tambaya.
“Mama ce wai zata min siezing waya bayan ina browsing stuffs na school dashi.”
“Wallahi Alhj k’arya take kamata nayi tana waya da saurayi.”
“Saurayi?!” Exclaimed Baba.
“Laaa! Wallahi Baba sharri ne ni danake Ss1 ina naga ta kula saurayi, Yasmeen ce taje ta sameta wai inada saurayi alhalin k’arya ne.”
“Wallahi kar ka saurareta in tasan tanada gaskiya ta mik’o wayanta a duba.” Confidently Zeezee ta mik’a mata wayar, sede tayi duban duniya bataga kowani waya dana miji a call log dinba “ina number’n kinsamu?” Baba ya tambaya.
“Wallahi Alhj nina jita da kunne na sede in gogewa tayi.”
“Wallahi Baba sharri ne, yaushe ne na gogen? Ni Allah banida saurayi.”
“Ai nasani K’anwata, ba kalan tarbiyyan dana baki ba kenan.”
“Aww ka yarda da k’arerayin nata kenan? Kuma ma wani tarbiyyan ka bata?”
“Why not? Zeezee tayi k’araman da za’ace tana kula samari she is just four-teen (14) years.”
“Ba komai ka cigaba da d’aure ma k’arya gindi kamar yadda ka saba wataran zakayi nadama” tana kaiwa nan ta juya tana kallon Zeezee “kekuma Allah na kallonki” gwalo Zeezee tayi mata ganin Baba bai kallon direction nata, batare da Mama tasake cewa komi ba tafice.
“Ungo wayarki nasan sharri ne bazaki tab’a watsa min k’asa a ido bako? Keda saurayi sekin gama secondary school, promise?”
“Yes Baba nagode” ta amshe wayan tare da ficewa zuwa d’akinta tasa lock sannan ta haye gado ta cigaba da wayarta daga inda ta tsaya. Ahaka har suka gama exams Zeezee bata rubuta wani abin arziki ba kuma abin takaicin ma wai school mate nata take dating tana Ss1 yana Ss2 sunansa Ammar, irin millonaire school bad boy d’innan ne.
_One week later..._
A yau su Zeezee zasu karb’i result nasu, 9pm tagama shiri Omar yayi dropping nata, hira da selfie sukata sha da friends nata da kuma Ammar, yau ya kasance 3 months anniversary’n su da Ammar, shopping na k’in k’ari ya mata sannan suka d’anyi small party’n su. Not long enough form teacher’n su Zeezee ya raba musu results nasu, shi kansa sakamakon Zeezee ya mugun basa mamaki average nata daga 70.+ ya dawo 49. Sam yace seya kira Babanta yace bata karatu, da k’yar ta iya ta shawo kansa ya fasa. Correcting fluid ta nema ta gyara 49. d’in zuwa 69. Isarta gida ta zarce ciki da gudu da ledojin da Ammar ya bata gudun kar Mama ta ganta, ai tuni Mama taganta tabi sahunta da sauri “Alhj! Alhj! Kazo da kanka kaga yau” tayi maganan tana tare Zeezee daga rufo k’ofar d’akinta. Nan danan Baba ya fito ya samesu “meke faruwa? Har Zeezeen ta dawo ne, ya results d’in?” Tana kame-kame tace, “yayi kyau.”
“Wad’ancan ledojin fa daga gunwa?” Mama ta tambaya, stammering Zeezee ta shiga yi, “nn... Nna..”
“Na saurayi ba?” wabje ledan Mama tayi daga hannunta sannan ta zazzage komi a k’asa. Sega prefumes da chocolates masu heart shapes “ka yarda? Nace ka yarda yanzu aiko? Inba saurayi ba waze mata wannam siyayya? Ina result nakin?” kafin Zeezee tayi k’wararren motsi Mama tasa hannu ta wabje side bag nata tare da ciro result natan sede koda taga 69 gun tagane fake ne, ga kuma correcting fluid data gani gun tuni jikinta ya bata Zeezee ce ta gyara, “yanzu Zeezee har kinyi kaurin canza result naki kikawo wa iyayenki fake one gida? Innalillahi!” Result d’in Baba ya amshe yaduba sosai yasha mamaki jikinsa ya mutu lik’is, yama kasa cewa komi se kallon result d’in kawai yake ayayinda Zeezee tagama tsurewa se raba ido take. Daga bisani ya d’ago kai yana kallonta “kin kyauta kenan Zeezee? Abin naki har ya kaiga ki d’au correction fluid ki canza result naki ki kawo wa iyayenki gida saboda kin rainasu basu je boko ba? Cikin yayyun ki kin tab’a jin wanda yayi haka?”
“Baba nifa ban canza result d’ina ba-”
“K’arya kike” Mama tayi interrupting nata “meze kawo correction fluid kan printed result inba canzawa kikayi ba?”
“A’a barta Hafsah, barta” cewar Baba. “Mesa kikayi hakan?”
“Nifa ban canza ba Baba.”
“K’arya kike sake min? Laifi akan laifi, nace mesa kika canzan? Kuma what was your actual average?” Shiru tayi bata ce komi ba “dake nake magana Zeezee, meh average naki? Karki sa na kira form teacher’nku na tambayesa.”
“49.” ne tayi stating in a slow motion.
“49!” Mama da Baba sukayi exclaiming atare.
“49. Out of 100? Meya sameki Zeezee? Shin baki karatu ne? Kinsan fa da yaya ake samu ake biya miki school fees kika kawo min wannan sakamakon, acireki a LYS d’in a kawo ki Havardth kikeso?”
“A’a” tayi saurin amsawa tana kad’a kai.
“Then mesa kikayi failing woefully haka?”
“Seka tambaya ne?” Mama tasa baki, “samari take kulawa ai na gaya maka, kalli wannan shopping data shigo dashi inba saurayi ba waze bata? Ai na gaya maka wallahi in bakayi tsaye akan yarinyan nan ba seta janyo maka abin kunya” tana kaiwa nan ta basu waje “kin kyauta kenan Zeezee? Duk kalan gatan dana baki da abinda zaki sak’a min kenan? You are indirectly calling me a fool tunda har zaki iya canza result naki ki kawo min gida sannan kiyi believing zan yarda because you are taking me as a fool isn’t it? kin kyauta kenan?” Kai ta kad’a “a’a Baba kayi hak’uri.”
“Baki ganin yayyun kine da baza kiyi koyi dasu ba? Banason ina miki suratai Zeezee kidena sani, samarin dagaske kike kulawa ko? How old are you?” Fad’a sosai Baba yayi mata for the first time.
“Na tuba Baba bazan k’ara ba” bayan nan yayi mata nasiha sosai kamar dagaske ta ringa rusa mai kuka wajen tanata ta tuba bazata k’ara ba harda wai zata tattara kayakin ma ta miyar wa Ammar. Baba na barin wajen ta share hawayenta ta tattara kayakinta tayi ciki sannan ta d’au wayarta ta kira Ammar nata.
★*★*★
Ahaka har aka soma azumi, sam kaman ba da ba. Ada acika kan dining table dam da kayakin shan ruwa amman yanzu abin sam ba dad’i, Zeezee de kullum cikin k’orafi take ita fa tagaji sede Mama ta kalleta ta tab’e baki. Anyi azumi goma Baba ya siyo zannuwa irin ‘yan N5,000 d’innan masu kyau guda biyu nanma dan yayi k’arfin hali ne bayan shan ruwa ya tara iyalansa a parlour “dukanku kunsan yadda abu ya kasance min, yanzu da da ba d’aya bane ga zannuwa nan guda biyu d’aya wa Yasmeen d’aya wa Zeezee, Ibraheem Baba na nagode da komai Allah ya k’ara maka bud’i, Omar se kayi masa godiya shi ze maka kayan Sallah. Mamanku kuma ta k’ara hak’uri zuwa next week nad’an samu abu zan sai mata zanin itama.”
“Ba komai Baba” cewar Ibraheem bayan Omar yamai godiya.
“A’a nikuma sekace yarinya kabari kawai ansan babu ai karka damu addu’armu de Allah yayi maka bud’i.”
“Ameen Hafsah ta nagode.” Yasmeen ce ta numfasa tace, “ayyi Baba aini ko baka sai min kayan Sallan bama tunda duk kowa yasan halin da ake ciki yanzu.”
“Aw bakiso? Sena had’a da naki ai, meh kayan sallah d’aya zeyi wa mutum? Ai wannan abin kunya nema Lubiee taji anmin kayan Sallah set d’aya-”
“Ke jahilar inace?!” Ibraheem yayi interrupting nata angrily.
“Haa’a! Ni namaka magana ne? Ai baka min kayan Sallah ba bale kasamu bakin magana.”
“Ya isa haka Zeezee!” Baba ya tsawata mata juyawa kowa yayi yana kallon Baba yau shike ma Zeezee masifa a idon kowa! “Bakida hankali neh? Ma yayan naki kike gayawa magana? Ko bakisan dabadon taimakonsa ba da kin jima da dawowa nan Havardth da karatu, maza basa hak’uri.”
“Toh Baba ni na mai magana ne, wallahi Allah ze saqa min bayan talauci ga kuma masifa da rashin kwanciyan hankali” ta k’are maganan tana kuka “ko waya an kasa canza min tun jss3” zaninta dana Yasmeen ta had’a tabar gun a guje kowa se kallonta yake daga bisani suka maido da kallonsu kan Baba suna basa kallon ‘its all your fault’ kai ya girgiza “Allah shirya Zeezee toh.”
“Ameen” Mama tace “inta shiryuwan ce, Yasmeen muje mu had’a miyan suhoor d’in.”***
Kuka Zeezee ta tayi a d’akinta ita an had’a ta da kayan Sallah d’aya, Baba daya rage shi kad’ai a parlour se jin sautin kukanta yake. A sanyaye ya mik’e yayi knocking a k’ofar kamar wacce bazata bud’e ba ta tashi ta bud’e ranta a dak’ule. Bayan sun zauna kan kujera Baba ya shiga mata nasiha saboda shi kansa abin Zeezee ya soma basa mamaki, yarinyar da nasiha ba shiganta yake ba ko a kwalan rigarta ita zannuwan Sallah take so ba suratai ba seda Baba ya gama zuba tace, “nagode Allah k’ara bud’i.”
Washegari Mama da Yasmeen suna aikin kayan bud’a baki Zeezee na a d’aki as always tana chatting, dawowan Ibraheem ya taho da fruits bayan ya dire a kitchen yayi musu sannu da aiki sannan ya tambayi ina Zeezee.
“Tana d’aki as always” Yasmeen tabada amsa.
“Ita bazata fito tayi aikin bane?”
“Ai na gwada yi mata magana tak’i, Mama tasa baki kuma wai a’a abartan.”
“Mama hakan da kikeyin fa ba taimakan ‘yar nan kike ba, wace ita da zata ce bazata yi aiki ba?”
“Toh Ibraheem kana ganin laifi na ne? Katab’a jin nama Zeezee magana tajini? Sede in kai da kake dukanta, nikam ba haka iyayena suka girmar dani ba, bazan iya dukanta haka ba kullum. Ta cigaba da halin nata surely someday zatayi regretting” ba tare da ya sake cewa komi ba yafice se d’akin Zeezee knocking yake gbam! Gbam! Gbam! “Waye haka b’allan k’ofan za’ayi?” tayi maganar tana b’oye wayarta cikin pillow case.
“Bud’e k’ofan nace maras kunya kawai bud’e!” jin muryan Ibraheem ta mik’e aguje ta bud’e k’ofar sannan ta soma rik’e cikinta “maza wuce kitchen, wace ke ana aikin bud’a baki kina kwance a d’aki?”
“Ya cikina ne yake ciwo wayyo Allah!”
“Sekisha magani ai wuce kitchen nace.”
“Ya ai ina azumi kuma period d’ina ne yakeson zuwa wallahi bazan iya mik’ewa dakyau ba.”
“Ni zaki raina wa hankali? Ko bakisan nasan date naki bane wuce nace kona miki d’an banzan duka kan azumin naki.” Ganin ya kamata, ta mik’e da kyau.
“Ni shikenan kullum mutum baida hutu agidan nan ni wallahi na gaji ga bak’in talauci gakuma uban-” ai bata k’are maganan ba ya bige k’aramin bakin nata tare da fisgota a tsakar gida ya yasar da ita. Tuni ta soma kuka “maza wuce kitchen kije ki karb’i Mama, Mama fito daga kitchen d’in cinta za’a zo ayi ne? Ki mik’e wallahi kona zaneki” yayi maganan yana cire belt nasa, ganin haka ta mik’e tayi kitchen d’in. Da kansa ya fito da Mama daga kitchen d’in sannan ya tsaya kansu yasa Yasmeen tabata aiki in batayi ba kuma ya mauje ta. Haka tana kumbure-kumbure ta shiga yi bayan ta gama yamata nuni da ledan fruits d’in kan tashiga gyara water melon da paw-paw d’in, “ni wallahi nagaji ai ba engine ce niba ita Yasmeen me zatayi?”
“Magana kike?” Ya mata sending wani dirty look, miyau ta had’iye ta d’au ledan ta wanke fruits d’in sannan ta shiga yimusu gyaran walaqanci. Bada jimawa ba Ibraheem ya fita, ko cikakken two minutes ba’ayi ba Baba ya dawo nan Zeezee ta soma kukan munafirci “yada kuka kuma K’anwata?”
“Ya Ibraheem ne wai sena gyara wannan duka kuma cikina ciyo yakemin.”
“Ita Yasmeen ina take?”
“Tana d’aki.”
“Yasmeen! Yasmeen!”
“Na’am” ta amsa tare da fitowa “sannu da zuwa Baba.”
“Yauwa sannu zoki karb’i Zeezee kinji batada lafiya.”
“Baba wallahi k’arya take lafiyanta lau.”
“Baba wall-” tuna tana azumi ta gyara zancen nata, “dagaske ba k’arya bane Baba wayyo Allah na.”
“Yi ki karb’eta Mama na Yasmeen yi hak’uri.”
“Wallahi kinci darajan Baba ne maras kunya kawai” gwalo Zeezee tamata sannan ta mik’e ta nufi d’akinta ta cigaba da chatting from where she stopped.
Shigan Baba d’aki Mama ta mai sannu da zuwa sannan tace, “wallahi Alhj ka rage biyewa Zeezee, nad’au kayi hankali bayan ‘yan abubuwan datayi days back amman ashe ba haka bane.”
“Kamar ya Hafsah? Yarinyan nan she is not used to rayuwan da take living yanzu koshi ya isheta damuwa be kamata muna d’aura mata da namu akai ba.”
“To mud’in mun saba da wahalan ne? Ai kowa hak’uri yake.”
“Toh ai ku manya ne ita kuma yarinya ce, kuyi mata uzuri mana please! ko waya na kasa canza mata abarta hakan nan.”
“Yayi kyau, Allah kyauta amman de don’t come and cry to me when the head has been cut off already.”
I MISS MY OLD ACTIVE BLOG READERS๐ต๐ต
*© MIEMIEEE*
๐๐๐๐
www.beeenovels.blogspot.com
5 comments:
Ina tausayin baba, sannu da kokari ya kara basira, ya ciwon baya kuma, Allah ya kara sauki.
Alhamdulillah da sauki, thank you
Alhamdulillah da sauki, thank you
U re de most great Hausa novels writer
Allah Ya kara budawa
Yayi kyau baban xee xee yanxu ka fara gani.Allah ya Kara basira
Post a Comment