TANA TARE DA NI... PAGE 09
BY MIEMIEBEE
United Kingdom, London
*ANAS*
_shima bayan shekara d’aya..._
Acikin babban Beach dake waje da London, Anas ne mik’e kan wata doguwar kujera da blue sunglasses a fuskarsa kwata kwata short nicker ne kad’ai ajikinsa seda headphone dake kansa wanda ya had’a da wayarsa yana nin cool music. Kallon sama yake yayi nisa cikin tunani.
Bottled wata aka wulla masa a firgice ya mik’e ganin Musty ne yasa yayi murmushi wanda ya bayyano da fararen hak’waransa. “Kai! Abdoul where are you? Yau Anas yayi murmushi harda ciro hak’wara. Tell me why do you seem so happy?”
Murmushin ya sake, “my dreams are coming true one-by-one.” cewar Anas.
“Wani dream kenan Anas?” Musty ya tambaya.
“Humm!” yakuma murmusawa ta gefen da dimple nasa yake. “Ni dreams d’ina guda uku ne kacal a duniyan nan.”
Musty ya giara zama “ina jinka!”
“Kaga na farko to be a billonaire not a millonaire but a billonaire. After that kaga in nayi kud’i I can toy with women hearts, saboda one thing I've learnt in life is ba abinda mata sukeso fiye da kud’i a duniya, zanyi amfani da wannan damar in saye zuk’atarsu dashi, akan kud’i they are ready to sacrifice everything I mean everything harta family'nsu, kaga ko in nayi kud’i nasan ba macen da zata k’i ni ko akoi?” Ya tsaya ya tambayi Musty.
Musty dake jin dad’in wannan labari yace, “ai ko a yanzun ka ma ba macen da zata k’ika Anas you've got the looks and the blue eyes also.” Murmushi sukayi dukansu “ehemm. Ina jinka...”
“Yess! As I was telling you, inason inyi wasa da zuqatan ‘yan mata a k’alla 100-200. So nake na karya musu zuqatansu ta yadda barasu sake san kawo na miji cikin rayuwarsu ba, so nake su d’and’ana how it feels to be left alone.”
Kai Musty giad’a a hankali alaman yana gane abinda Anas ke nufi “so in ka karya masu zuqatan nasu what will you benefit from it?” Daidai lokacin Abdoul yazo ya zauna dawata American babe kan cinyarsa tasha bikini (pant and bra) “Hi Fauzy!” Tace da Anas sunan da ake kiransa dashi a can London kenan kasancewar su turawa sun saba da kiran mutum da family name nasa (ANAS IBRAHIM FAUZY)
Ba tare da ya kalleta ba yace “hey.” Abdoul ya d’ibi k’asa me laushi dake beach d’in ya watsa wa Anas. “Budurwar tawa ma seka ja mata aji ne? Kaifa Anas daban kake I keep on telling you.”
“Abdoul kaga magana muke da mazan nan kuma kallon wannan me farin gashin kusa dani amai yake sani so please ka koreta kokuma ku tafi tare.” Cewar Anas batare da ya nuna damuwa ba.
“Allah...!” Abdoul ya fad’i cike da mamaki wai ace baturiya ma bata burge Anas ba to wace zata burge sa!? Dariya sosai Musty ya fashe da ba k’arya maganan Anas ya sasa dariya. Baturiyar ce ta tsargu danko ba jin yarensu take ba. “Hey Auwal (family name na Musty) whats funny why you laughing?”
Dariyan yake har yanzu “ohh Emily its nothing don’t worry.” Bayanta Abdoul ya shafa “excuse us babe I'll be right back.” Kiss ta manna masa a cheek sannan ta tashi ta fice.
Fuska Anas ya yamutsa a k’yamance yana mamakin Abdoul wai har baturiya yake bari tana masa kiss. “Seka sake fuskarka ai tunda na miji da na miji kaga suna kiss ba.” Cewar Abdoul a little bit pissed off. Murmushi kad’an Anas yayi “LOL mamaki kawai kuke bani, I can’t waste my time on girls. They aiint worth it”
“Aini Anas da ban sanka ba senace gay ne kai.” Cewar Abdoul “anyways what are you two discussing about da kuka sa na kora Emily.”
“Labari Anas ke bani” cewar Musty yana jin dad’i. “Ehem ina jinka continue.”
Komawa yayi ya jinginu jikin kujerar sa yana kallon sama sannan ya cigaba “kace what will I benefit in nayi breaking hearts na mata?” Musty ya giad’a kai dukda ba kallonsa Anas yake ba. “I will benfit everything, zan ramawa Abuu abinda Ummimi ta masa, dukda ba direct kan Ummimin zan d’au revenge d’inba atleast ‘yan uwan ta mata zasuji jiki tunda ciwon ‘ya mace na ‘ya mace ce.”
Cikin rashin fahimta Abdoul yace, “wait wait nade san waye Abuu mahaifinka ba? what of Ummimi? Wace ita? As far as am concerned Ummie nasani mamanka har kana bamu waya muna gaisawa.”
Numfashi Anas yaja “well apart from my family you guys are the first people da zan bawa wannan labari so listen closely after na baku labarin seku fad’a min ko inada laifi in nace mata are evil creatures da be kamata a tausaya masu ba.”
_[Abuu kamar yadda kuka sani mahaifi na ne kanurin Bama ne dake jihar Borno. Ummimi kuwa mahaifiya tace unfortunately, asalin shuwa arab ce daga Maiduguri. Mu uku ne gun iyayenmu nine babba I'm 19 years old, followed by my brother Shettima shikuma he is 17½(sha bakwai da rabi) yanzu. Shekara 1½ (d’aya da rabi) ne tsakanin mu sekuma little sister’nmu my angel Amal she's just 9 years old.]_
_[Base on yadda Abuu yabani labari auren soyayya shida Ummimi sukayi. As you guys know scholarship nasamu nazo nan school d’in not like you guys da iyayenku suke biya muku da kansu. Abuu bashida wani arzikin azo agani, yanada arziki ne dadai na rufin asiri a yanzu haka in za’a kira masu arzikin garinmu Bama nasan definately za’a sa Abuu amman dekam bade da kafin sui aure da Ummimi ba. Shi da kansa yake bamu labarin irin rayuwar talaucin da sukayi shida Ummimi kafin a haifemu harkuma da aka haifemu so dayawa ana tashi a gidanmu ba’a sanin me za’a ci.]_
“You guys must be wondering ya akayi Ummimi shuwa arab da uban san kud’insu ta auri talaka kamar Abuu na ko?” Ya juya ya kalli abokansa. Kai suka giad’a a tare murmushi ya saki kad’an “well you don’t have to.”
_[Alokacin da Abuu yaje Maiduguri yin diploma ne ya had’u da Ummimi tana sayar da abinci a school nasu a lokacin iyayenta sun kasance talaka sosai amman kunsan shuwa arabs koda su talaka ne se masu kud’i sukeso unlike Ummimi back then, dukda tasan Abuu baida kud’i makaranta yake hakan be hanata falling masa ba kamar yadda shima ya juma da falling mata dan kyan ta dakuma hali, sosai Ummimi kyakkyawa ce kap mu yaranta kamanninta muka dauka sede nafi kama da ita fiye da Shettima da Amal wanda har yau in na tuna da haka se inji kamar inje inyi plastic surgery in canza kamanni na sam banasan abinda ze sa ina tunawa da ita but anytime I look at myself in the mirror ita kawai nake gani...]_
Musty da Abdoul da suke duhu sukace “ban gane ba” a tare. “Mesa ka tsani mahaifiyarka haka Anas?” Cewar Musty. “Shin yanzu bata gidanku ne?” Abdoul ya tambaya.
“Zakaji reason dayasa na tsaneta Musty, bata gidanmu Abdoul Allah kad’ai yasan ko tana nan aduniya ko lahira.”
“Babbar magana!” cewar Abdoul “kanada picture’nta inasan ganin ta.” Hannu Anas ya mik’a ya d’aga wallet nasa daga kan wata ‘yar table ya bud’o sannan ya ciro wata hoto “wannan family picture’nmu ne Abuu, Ummimi se nida Shettima time d’in ba m’a haifi Angel ba. Sede bara ku gane fuakarta sosai ba saboda na dirje da biro.” Nan ya mik’a wa Abdoul sosai kam ya dirje fuskar Ummimi a hoton se ansa ido sosai za’a d’an ga kutsirin fuskarta amman ko a hakan ma za’a gano kamanninta da yaranta musamman ma da Anas kamar yadda ya fad’i bayan Abdoul yagama gani ya mik’a wa Musty, shima daya gani yayi returning wa Anas, amsa yayi tare da mayar wa cikin wallet nasa sannan ya cigaba;
_[Sun yi shekaru biyu suna soyayya batare da sanin iyayensu ba lokacin da Abuu yagama polythecnic ne ya sanarda da iyayensa kan yasamu mata kuma yanasan ya aura dukda cewar ba aiki yake dashi ba. Kowa murna ya tayasa seda akaji batun Shuwa Arab ze aura ne hankalin kowa ya tashi gudun heartbreak da suke masa dan sunsan for sure in iyayen Ummimi sukayi learning truth about status na Abuu barasu yarda suba d’ansu wa talaka ba sunfi san wanda ze kawo masu gwala gwale yakai su Hajji da umara.]_
_[As expected da Ummimi tayi introducing Abuu wa iyayenta sam sukace ‘yarsu barta auri talaka ba suka masa kaca-kaca sannan suka koresa. Amman dan erin soyayyan da Ummimi kema Abuu yasa ta bijirewa iyayenta tace ita sam inba Abuu ba zata kashe kanta kuma she was serious duk suka tsorata ba yadda suka iya dolensu suka yarda mata saboda ita kad’ai ce ‘ya a garesu. A munafirce mahaifinta ya tura ‘yan uwansa suka tsare Abuu a hanya suka masa tsinannen dukar mutuwa basu barsa ba sanda suka ga baya numfashi jinyan wata d’aya Abuu yayi kafin ya samu sauk’i alokacin Ummimi ta tada borin inba a aura mata Abuu ba zata fad’a rijiya dole aka musu aure iyayenta wane bak’in ciki ya kashe su]_
_[Bama ta biyo Abuu aka basu BQ a family house nasu Abuu. Aiki Abuu yashiga nema dan earning living and to make his beautiful wife happy but kunsan yadda k’asarmu take sam be samu aiki ba haka ya soma noma, safe, rana, yamma, dare. Duk sanda yayi harvesting shuk’ansa once in a year yakan kai maiduguri ya siyar a wannan lokacin ne yake samun kud’i ya ma Ummimi siyayya and duk abinda ya kawo mata tana appreciating. Bayan shekara d’aya da aurensu aka haifeni Abuu yace ni ko ragon suna ba’a min ba sanda nayi wata uku tukuna. Sam basu ji dad’in haifan Shettima da akayi bayan shekara d’aya da rabi da haifa na ba dukda cewar kowani d’a da arzikinsa amman talaucin nasu yayi over. So dayawa ana wayen gari ba’a san me zamuci ba. Mahaifin Abuu ke turo mana abincin dazamu ciki.]_
_[Daga bayan Shettima kuwa Ummimi bata sake samun ciki ba. Shekarana goma a duniya lokacin Ummimi tasoma staying late at night seta fita tun safe bata dawowa se dare abin ba k’aramin damun Abuu yake ba. Da ya d’anyi bincike kuwa se aka gano wani Alhaji ne daga Yola take had’uwa dashi. Attajiri ne sosai yanada kud’i Abuu yace kullum cikin canza mota yake. Yana ganin Ummimi kuwa ta masa kyau ya fara nemanta ita kuma saboda cin amana tak’i fad’a masa tanada aure. Soyayya sosai suka fara sam Ummimi tadena kula damu kullum cikin dukan mu take kamar ba yaran cikin data haifa ba.]_
_[Koba abin duka ba seta bugemu musamman ma a weekends lokacin da wannan Alhajin nata ya koma Yola ba me bata kud’i. Ranar lahadi da sassafe baran tab’a mantawa da wannan rana ba. Da misalin k’arfe 8:00AM Ummimi ta tashi se had’a akwati take sam nida Shettima bamu damu ba acewarmu ko tafiya zamui duka sede naga kayakinta kad’ai take ta had’awa dana tambayeta in zataje kuwa ba kunya ba tsoron Allah ba tausayi ta kalli cikin idanuna tace min *talaucin mahaifinku ya isheni tattara kayakina nake saurayi na zezo ya d’auke ni in tafi inbar nan* atake kaina naji ya soma juyawa wace erin magana Ummimi take dama mata masu aure sunayin saurayi ne? Danni ban tab’a jin malamin islamiyan mu ya fad’a mana ba. Sema na d’au wasa take na shareta mukaje muna ta wasa nida Shettima. Abuu na zaune a Parlour ya tambayeni. Anas Baba na ina mamarku? Ko yau d’inma ta fita ne? A’a Abuu tana d’aki tana shirya kayakinta tace min wai saurayinta ze zo ya d’auketa. Take Abuu ya mik’e what!? Niko na sake nanata masa. Bada dad’ewa ba sega Ummimi tafito tana jan akwatinta.]_
_[Aysha ina zakije haka?_
_Aww d’an naka bai fad’a maka bane? Tafiya zan saurayi na na jira na._
_Haba! Aysha wace erin magana kike? Wani erin saurayi kuma? Cewar Abuu]_
_[Ai kasan sa Alhajin Yola, shi nake nufi, rayuwar talaucin nan ya isheni ni tafiya zan inje inji dad’in rayuwa na nima.” For the first time naga idan Abuu yacike da hawaye kafin in hankara naga yana kuka take nima na fara same goes to my brother. Rok’arta na soma haka Shettima ma banda Abuu dayayi mutuwan tsaye.]_
“Huhhh!!! Nagaji I'll continue some other day.”
“Haba! mana maza da Allah k’arasa mana.” Cewar Musty.
“Nace maku I'll continue tomorrow or later I promise, baki na yagaji da surutu kunfi kowa sanin ban cika magana ba ai nayi k’ok’ari ko?”
“Sosai kayi Anas namu me blue shining eyes. Yi hak’uri ka gama mana amma” Abdoul ya fad’i yana masa zak’in bak’i.
“Okay toh siyo min soda sena cigaba ishi nake ji.” Ba musu Abdoul ya tashi ya siyo masa ya dawo da sauri. “Gashi toh cigaba muna jinka please.” Bayan ya bud’e sodan ya kwankwad’e tas sannan ya cigaba kamar haka;
*©miemiebee*
beeenovels.mywapblog.com
No comments:
Post a Comment