BY MIEMIEBEE
“Last words da mukayi exchanging da ita are forever stuck up in my head.”
_[“Ummimi dan Allah karki tafi kiyi hak’uri indan plates dana fasa ne I promise baran sake ba. Ummimi I am sorry dan Allah karki tafi. Abuu ka hana Ummimi tafiya dan Allah kace mata I will be a good boy from now on.”]_ “Haka nata had’ata da Allah ko saurarena batayi ba”
_[“Yanzu Aysha bara kiji tausayin yaranki ki hak’ura ki zauna dasu ba? Kalli yadda suke kuka fa?”]_ cewar Abuu
_[“Mstww wannan kuma ku ya shafa nagaji da zama cikin talaucin nan, ace kullum se atashi ba’a san me za’a karya dashi ba gaskia nagaji daman tun farko sanda Abba na yace kar in aureka matsiyaci ne kai amman nak’i sauraronsa. Ga can miji Allah yamin har k’asar waje ze kaini saboda haka ban ga abinda zesa in cigaba da zama a wannan gidan ba.” Jakarta ta ja ta soma tafiya da sauri naje na kama k’afarta ina kuka ina rok’arta. “Ummimi please don’t leave us we love you dan Allah karki tafi, Abuu will find a better job dan Allah karki tafi...” wani wawan ball tayi dani da k’afa nafad’i na ji ciwo a elbow na har d’inki sanda aka min wajen...”]_
“Kun ga ci won?” Ya mik’o hannunsa ya nuna masu Musty. Ciwo ne babba sosai ace yau shekaru kusan goma amman hakan besa ciwon ya rage girma ba. Komawa yayi yasake kishingid’a.
_[ko waiwayo wa ta dubani batayi ba jakarta taja ta fice, asibiti Abuu yayi rushing d’ina. Tun daga ranan Abuu ya rasa walwala, Abuu da mukasani da fara’a da murmushi ya koma wani abu daban. Kullum cikin tunani, nida Shettima tun tafiyar Ummimi muka rasa gatanmu, kakarmu bata raye bale ace ita zata kula damu, abinci ma waninsa’in mancewa ake damu haka zamu kwana da yunwa Ummie sister’n Abuu ce data dawo daga Maiduguri tayi alk’awarin zama damu. A lokacin ina primary 5 zamuyi common entrance, ikon Allah ne kawai yasa nayi passing exams d’in saboda tafiyan Ummimi yayi affecting d’ina psychologically, mentally and socially.]_
_Tun daga lokacin na canza, na dena dariya, nadena wasa koda da Shettima ne kullum cikin tunani nake har wani psysho psycho na soma zama. Ganin haka Kaka yabawa Baba shawara akaini Maiduguri Boarding school a tunaninsa in ina cikin yara zan sake, unfortunately koda aka kaini can abun nawa be ragu ba sede worse da yayi ma, bana cin abinci bana magana da kowa karatu na kawai nakeyi saboda blue eyes d’ina yasa yara dayawa suna san zama friends dani ace warsu ma ni bature ne sam bana basu chance guda biyu ne sukaci galaba a kaina Baana da Kashim, su biyu kawai suka samu na sake dasu muka zama friends.]_
_[A lokacin da mukayi second term hutu bayan na dawo gida na tarar da Ummie da jaririya kuma a iya sani na Ummie bata da aure. Tambayarta nayi ko ‘yar wace me kama dani haka amsar data bani ne ya mugun sake tada min hankali.]_
_[“k’anwarka ce Anas, uwar ku d’aya uban ku d’aya. Shekranjiya Ummimi tasa wani almajiri ya turo ta cikin wata basket da wasik’a.” Zafaffun hawaye ne suka soma gangarowa kan kumatu na. “Mesa Ummimi zatayi haka Ummie? Mesa barata tausayawa wa baby’n nan ba? Me tamata itakuma da zata rabata da d’umin jikinta? Mesa Ummimi ta tsane mu haka Ummie?”]
_[“Anas nima bansani ba hak’uri zakayi, I'm here for you guys, bar kuka Baba na.” “Ina wasik’ar Ummie?”_ Na tambayeta. Acikin wata drawer ta d’auko ta mik’a min na karanta kamar haka...]_
[_ Ibrahim ‘yar da ke cikin wannan basket, ‘yarka ce da cikinta nabar gidanka. Allah ya taimakeni nasamu na haifeta ga abinka nan na kawo maka, banasan abinda ze sake had’ani da kai ko da ‘ya‘yanka..._]
[Hawaye ne suka soma sauk’owa kan kumatu na hannu na mik’a na amshi sister na da ko suna Abuu be sa mata ba dan tashin hankali. Hawayen idanuna na d’iga kan fuakarta ta bud’e idanunta a hankali tana kallo na se kamar Ummimi nake gani, *Amal* na kirata dashi ina hawaye. Daidai lokacin Abuu yashigo. “Amal kasa mata Anas?” Alokacin ban fahimce abinda yake nufi ba sanda na tambayesa yake fad’a mun yak’i sa mata suna ne saboda ni yake jira nayi naming nata tunda nace mata Amal sunan ta Amal kenan. Tun daga ranan na d’au alk’awari zanyi protecting Amal da raina, zan zame mata uwa.]_
_[Ban tab’a jin inason d’an Adam kamar Amal ba, simply because of tausayin da take bani har yau bata san tanada wata mahaifiya bayan Ummie ba, rok’ar Abuu nayi kar a fad’a mata gaskia banasan rayuwarta ta tab’arb’are kamar yadda nawa yayi. Komai ni nake wa Amal har noma nafarayi tun ina d’an yaro in nayi harvesting se in siya wa Amal kaya da kauan abinci as Abuu har a lokacin be samu aiki ba. Tun tana k’arama take sona ko kuka takeyi ina amsarta zatayi shiru kwana ma tare mukeyi da ita, ko yawo zanje da ita nake zuwa. Sam banso komawa makaranta ba da hutun mu yak’are gudun kar nayi missing nata. Ba yadda na iya haka na koma amman kullum da tunaninta nake kwana in tashi.]_
_[Ina jss 3 aka sa Shettima a school namu, jiki na jasa sosai ko kad’an bana barin school bullies su tab’a sa. Abokai na abokansa ne. Alokacin Abuu ya samu aiki rayuwar mu yasoma canzawa a hankali ya gina mana gida Amal kuwa se girma takeyi a lokacin tana da shekaru biyu da abu akai. Amal completes me, kullum tare muke da ita duk sanda nazo komawa school setayi kuka tace seta bini. Har dan haka nad’au alk’awarin barin sake dawowa gida ba se nagama school d’in gabad’aya bana san ganin kukan Amal. 3 years later nagama secondary school I was 16 years then Shettima kuwa yana ss1 time d’in. I can’t believe Amal dana ganta she was 5 years then, ta girma sosai in na ganta kaina kawai nake tunawa da muguwar Ummimi.]_
“Tun daga lokacin na cigaba da kula da sister na har ila yau. Ummimi kuwa bamu sake jin labarinta ba tunda ta bar gidanmu yau about 10 years kenan.” Numfashi ya saki tare da tasowa daga kan kujerar ya mik’e tare dayin mik’a “kunji labarina you guys are the first to know. Kunji dalilin dayasa na rasa happiness d’ina, dalilin dayasa na tsani Ummimi da kowace mace banda mata guda ukun nan; Amal, Ummie seda yarinyar danayi blaming nata akan laifin Ummimi har nayi raping nata wanda har yau ban san ya take ba, bansan kona kasheta ba bansan irin ciwon dana ji mata ba. I can’t ever forgive myself for what I did to her har se ranan dana ganta na nemi gafararta ta yafemin. She was just 15”
“Anas stop blaming yourself, ba’a cikin hankalinka kayi mata abinda ka mata ba in shaa Allah bata mutu ba someday in the future zaku had’u kuma zata yafe maka inhar ka bata labarin ka. Gaskia Anas kasha gwagwarmaya a rayuwarka, kayi witnessing bak’in cikin rayuwa at a very tender age. Ummininku sam bata kyauta muku ba.” Cewar Abdoul cike da tausayawa wa Anas ashe saisa kullum yake cikin tunani baya dariya, he has been through so much ba laifinsa bane because of how he is now.
“Anas if only zan iya taimaka maka da nayi, you've had such a horrible past just know that when ever you need a shoulder to cry on we are here for you.” Musty yayi assuring nasa.
Kallonsu Anas yayi tare da ciri sunglasses nasa rana ya haska blue eyes nasa da skin nasa yayi kyau sosai. Murmushi ya saki kad’an wanda ya bayyano da fararen hak’waransa “thank you guys, so now what? Kun ga laifi na saboda nace na tsani mata barin yi aure ba?”
Kai duk suka kad’a “wallahi ko k’adan Anas you have every single right ka tsani mata fiye da komai sede inda zaka yayyafa wa zuciyarka ruwan sanyi you can find love in your own way I'm sure Allah ze sak’a maku abinda Ummimi ta muku by kawo maku matan da zasu kula daku su soku tsakani da Allah badan kyanku ko kud’inku ba but tsakani da Allah and barasu tab’a barinku ba kai da wanka Shettima se mutuwa.” Cewar Musty. “Sosai dude Musty is absolutely right.” Abdoul ya mara wa Musty baya.
“Ofcourse you guys are right, but niko kad’an I don’t have faith in love to talk more of marriage, I wish to finish my life single ba senayi aure ba. Dama ai ana aure ne dan a haifafa I have Amal, she is like a daughter to me.” Musty ze sake magana Anas ya katsesa by changing topic of discussion d’in. “Yau da kuka sani na tono past d’ina dole se na sha 2 bottle na syrup d’incan if not barin iya bacci ba and also I feel like drinking yau muje bar (gidan giya) mud’an tab’a flavours da suke dashi.”
Tsaye sukayi duka suna masa murmushi sannan suka fice...
*FANNAH*
_One week later..._
Bam! bam! bam! bam! bam! “Salamu alaikum!! Salamu alaikum shin ba kowa ne a gidan?” Cewar Ya Khaleel dayafi kusan minti uku tsaye a bakin k’ofar gidansu Fannah yana sallama da knocking. Mami dasu Afrah sun fita, Fannah da Baba kad’ai a gida, Baba kuwa jikin sa yayi worse yau ko magana bai iyayi yana jin knocking da sallaman amman ba halin amsawa musamman ma dayaji Ya Khaleel ne. Fannah kuwa tana bayi tana wanka se sauri take tafito ta amsa sallamar.
Bayan minti biyu tafito daga bangidan har yanzun sallaman Ya Khaleel yake, hijabi ta d’aura kan towel dake jikinta gashin kanta dana jikinta duk sun jik’e kwance a jikinta. Da sauri ta fito “wa’alaikumussalam sannu da zuwa Kawu.”
“Se yanzu kika ga daman fitowa?”
“Kawu wanka nake-”
Katseta yayi “rufa min baki! Allah sa de ba na miji kika b’oye cikin d’akin ba.”
Da mamaki ta d’ago kai ta kallesa shima kallon nata yake wani kyantan ma se yau ya soma gani, gashin girarta da suka had’e sun kwanta kan fatar ta me uban haske. Haka sajen fuskarta ma. He can’t wait Fannah ta haifo masa jikoki kyawawa kamar ta.
“Ina sauran ‘yan gidan kuma suke?”
“Sun fita unguwa” tabasa ansa a takaice.
“Aww kekuma fah? Ai! Na tuna ashe baki fita yanzu saboda kar aganki a kiraki da sunanki karya ko? Anyways ina Baban naki yake? Inade be mutu ba tukun? Kice masa ya d’an k’ara k’ok’ari yajira yaga bikinki da Farouq. Nazo ne in sanar daku bikin ki da d’an nawa nan da wata d’aya ne nagama duk abinda nasan ya kamata komai na sai muku gado nede banyi ba. Wannan kuma keda iyayenki zakuyi bandamu ba koda sata zakuyi kokuma sayar da ‘yarku me uban bakin nan. Ni na tafi” Fannah bata ce komai ba illa hawayen dake forming a idanunta. Har ya juya ya soma tafiya sekuma ya dawo yana kallonta.
“Bakice komai ba ko baki jini bane? Kokuwa rashin kunya kike ji dashi?” Ya jefa mata wannan tambayoyi.
Hannu tasa ta share hawayenta, “A’a Kawu ko k’adan, kayi hak’uri kuma mungode in Mami ta dawo zan sanar da ita.”
“Yafi kam ki sanar da ita tun da wuri inma sata zatayi tayi ta had’a miki kud’in gado kokuwa kina kwana a k’asa in anyi auren dan Farouq da gadonsa ze tafi.” Yan kaiwa nan ya fice. D’aki ta ruga a guje ta baje kan katifarsu ta soma kuka, kuka take sosai abin tausayi.
“Bawan Allah mesa ka amshe min martaba ta? Mesa ka rabani da budurcina? Mena maka? Mesa se ni? Mesa ka juya min rayuwa ta upside down haka? Mesa se ni? Dalilin abinda kamin kasa rayuwata ta koma wani abu daban, banida gata banida ‘yanci banida masoya banida komai...” Ta kuma fashewa dawata erin matsanancin kuka. Ita da mutuwa zatayi dayafi mata akan auren Ya Farouq tasan definately kasheta zeyi a gidansa in har ta auresa ko a yanzun ma bai ragar mata ba bale ace tazama mallakinsa.
*© miemiebee*
No comments:
Post a Comment