TANA TARE DA NI... PAGE 08
BY MIEMIEBEE
Kasa cemasa komai tayi, kallonsa kawai take hawaye na gangarowa kan kumatunta, kuka ne yafi k’arfinta juyawa tayi tashiga gida da gudu ta tsaya daga wata lungu ta share hawayerta sannan ta k’arasa ciki. Mami da Baba ta tarar zaune yadda ta barosu. Basu ce da ita komai ba dan haka tashige d’akinsu da Afrah ta fashe da kuka bata san da wanne zata ji ba da rabata da akayi da budurcinta martabarta na k’arfi da yaji ne kokuma da auren wannan monster me suna Farouq tun be aureta ba ma yasoma mata rashin mutunci yana zaginta bale ace in sunyi aure, kwata kwata baida slightest regard mata.
Bada jimawa ba Mami ta aike Afrah shago siyo man giad’a tun kafin Maghrib yayi gudun kar abinda ya faru da Fannah yakuma samun Afrah. Afrah ne tashigo d’aukan hijabi a d’akinsu, Fannah dake kwance a kan katifa da Qur’ani tana karatu ta d’aga kai tare da tambayarta. “Ina zakije haka?”
“Shago fa Mami ce ta aikeni siyo man giad’a.”
“Okay, jirani muje tare nagaji da zama nan shiru ni kad’ai.”
“Toh sanya hijabinki muje Ya Fannah.” Nan Fannah tasa hijabi suka fito tare, “ya haka ina zaki Fannah?” tambayar Mami ga Fannah.
“Zan bi Afrah ne Mami nagaji dazaman cikin.”
“Toh Allah kare dan Allah in har babu anan shagon Ya Wakil dana mak’otansa karkuyi nisa ku dawo gida kawai, kunji?”
“In shaa Allah Mami” cewar Fannah sannan suka fice. A shagon Ya Wakil suka samu man giad’an sun jiyo zasu fice sega yaran unguwa sun taru suka soma wak’a
“Fannah kariya me bin maza Fannah kariya me bin maza.”
Hawaye tasoma yi bata tab’a tsammanin zatayi witnessing rana kamar ta yau ba, ranan da za’a ce tafita waje ana binta ana zaginta me bin maza.
“Ku wai bakuda hankali ne?” cewar Afrah “wanj irin ‘yan iska ne ku? Wallahi in baku bar nan ba zan jefe wannan munanan bak’ak’en kankun da dutse, jahilai kawai. Bara ku matsa bane?”
Ko ajikinsu ma magana ake masu wak’an su suka cigaba dayi. Mari wani ya sake ma babban cikin nasu Tasss! Kukeji a fuska take ya soma kuka saurayin na juyawa suka had’a ido hud’u da Fannah take ta kau da kanta. Kolar rigarsa Ahmad ya rik’e da hannu d’aya “kanajina in sake jin ka kira Fannah ko wata mace a garin nan da kariya kaga abinda zan maka ba kai kad’ai ba dukanku nan” ya nunasu da yatsa. “Kunjini ko bakuji ba?”
Baki na rawa babban yace, “munji dan Allah kayi hak’uri.” Ahmad na sakesa suka kwasa da gudu suka bar wajen. K’arisowa gabansu Ahmad yayi “Fannah kiyi hak’uri kibar kuka dan Allah, karki bari maganan yaran nan to get to you.”
“Ya Ahmad dan Allah kayi hak’uri” Fannah tace tana hawaye hannu kawai tasa ta rufe bakinta ta ruga a guje se kiran sunanta Ahmad yake ko sauraransa batayi ba. Juyawa yayi ya kalli Afrah da itama idanta suka cike da hawaye. “Afrah kiyi sauri ki bita kar wani abu ya sameta. Tell her tayi hak’uri ta rungumi k’addara in shaa Allah, Allah ze sak’a mata kuma kice mata I will never stop loving her koda ban aureta ba, da santa zan mutu kice mata tayi hak’uri, ina kan mata addu’a.” Kai kawai ta giad’a masa tabi bayan Fannah da gudu.
Tana isa gida ta tarar da Mami a tsakar gida se safa da marwah take. “Mami ga man giad’an.”
“Afrah meya samu Fannah tashigo tana kuka ta rufe k’ofar d’akinku nayi nayi da ita ta bud’e tak’i wani abu ne?”
“Mami wallahi Ya Afrah tausayi take bani, yanzu fitan mu almajirai suka taru suna mata wak’a suna kiranta da munanan suna Mami.” Ta k’are maganar tana hawaye.
“Allah sarki Fannah” cewar Mami itama tana hawayen, “Afrah inda zan iya karb’e pain da Fannah ke feeling danayi wallahi, it hurts me seeing my daughter in a horrible situation like this kuma ba abinda zan iya mata.” Hannu tasa ta share hawayerta addu’a zamu mata Afrah ko a islamiya ki fad’awa Malamanku su sata cikin add’ua kinji?”
“In shaa Allah Mami barinje in sameta.” Tana tashi taje ta k’ofar d’akinsu tun daga bakin k’ofar take jin sautin kukan Fannah. “Ya Fannah dan Allah kibar kukan nan batada amfani, addu’a zamu dage dayi, bud’e k’ofar kinji? Ya Ahmad yabani sak’o in isar miki, yi hak’uri ki bud’e.”
Fannah na jin Ya Ahmad ta tsananta kukanta haka ta tayi kusan na minti ashirin sannan ta tashi ta bud’e ma Afrah k’ofar bayan sun zauna Afrah ta isar mata da sak’on Ya Ahmad, se kuka Fannah ke Afrah na bata hak’uri. Comb ta d’auko da mai ta shafa ma Fannah a gashi sannan ta taje ta kama mata da k’yar, rabuwan gashin Fannah da giara tun kwanciyar ta a asibiti.
Haka fa rayuwa ta cigaba da kasance wa Fannah, bak’in cikin yau daban na gobe daban, sam bata fita daga gida yanzu saboda duk sanda ta fita se yaran unguwa sun taru suna mata wak’a. K’arshen yawonta bakin k’ofar gidansu ne in Farouq matsiyacin yazo. Makaranta ma ko ina tashiga nuna ta akeyi da yatsa haka suka gama exams nasu batasan me take rubutawa ba.
Kwata kwata ta fita daga kamanninta tayi duhu ta sake rama. Abinci ma ba kullum take ci ba rayuwa de takoma upside down wa Fannah baiwar Allah ba abinda ke mata dad’i ciki, Allah sarki!
_One year later..._
Alhamdulillah Fannah is trying to move on from her past. Hasken ta ya d’an dawo, ta rage tunani yanzu addu’a sosai ita da iyayenta suka dage dayi. Abun da yaran unguwa suke mata kuwa yanzu da sauk’i sosai seta fita kusan sau uku-hud’u ba’a samu matsala ba. Watanni uku da suka wuce akace su Ahmad sun bar garin Bama, koda yazo mata sallama k’in fita tayi badan komai ba wai dan ita a ganinta she don’t deserve him anymore bata san ma ya sake ganinta bale yaji yana santa. Shekarunta goma sha shida yanzu this year ta gama secondary school.
Baba kam sanda ya kamu da ciwon zuciya saboda erin wahalar da suka sha wancan shekarar, sak abinda ake ma Fannah haka ake masa in ya shiga cikin jama'a shima, ga bin abu a zuciya haka sanda ya kamu da ciwom zuciyan. Yanzu haka gasu nan ne kawai d’an aikin kanikancin dayake d’an yin ma yadena banda ciwon zuciyan dayake damunsa ga hypertension da ciwon sugar sam da angansa za’a tausayawa masa gashi ba kud’in kaisa asibiti a masa aiki.
Bakuma komai bane ya haifo masa da hypertension d’innan banda halin wansa Ya Khaleel, sam ya dage seya aura wa Fannah Farouq, abinda Baba bayaso kenan ita Fannan da za’a mata auren ma ta hak’ura ta rungumi k’addara yanzu tunda duk saurayin da ya soma zuwa wajenta tun gama makarantar ta se ‘yan unguwa sun korasa, daga yazo yau gobe bara a sake ganinsa ba.
Farouq kuwa ba kalan walak’ancin da baya wa Fannah musamman ma dayaga yanzu Baba bayida lafiya ko magana be cika san yi ba. Fannah kuwa dama ba mutumiya ce me hayaniya ba haka zezo ya zageta yazagi Babanta ba abinda zata ce masa illa tayi kuka, maganan aurensu kuwa Ya Khaleel ya dage se shiri yakeyi.
Yau ranar ta kasance Asabar, Mami, Afrah da Aiman sun je gidan suna a unguwar noma Fannah kuwa tana zaune a gida saboda bata san shiga cikin mutane gudun kar a fara nuna ta da yatsa ana kiranta da sunan data tsana wato kariya. Wanke wanke take tajiyo knocking bam bam bam a bakin k’ofa kafin ta wanke hannu tasa hijabi ta duba ko wayene already meshi ya shigo Farouq taga tsaye da alama ya bugu baya cikin hankalinsa.
“Ya Farouq me kakeyi anan a buge? Dan Allah ka tafi gida” Cewar Fannah murya na rawa.
Bece komai ba sanda ya iso inda take, atake ta soma b’ari incident daya faru da ita shekara d’aya daya wuce ya soma yawo a kanta shima wancan mutumin daya rabata da martabatan ta a buge ya zo mata, gashi ko hijabi batada. Baya baya take Farouq na matsowa kusa da ita sanda suka kai bango. Hawaye ke tsiyaya daga cikin idanunta “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri kabari.”
“In bari ko in fara? Ai kinsha yi da samarukan ki se me dan nayi dake yau? After all ni zan aureki.”
“Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri kabari.” Hannu ya aza kan gashinta me uban yawa yana shafawa. “Baba dan Allah kazo ka taimakeni Ya Farouq dan Allah kabari.” Kuka take tana had’asa da Allah. Finciko gashinta yayi da k’arfi “kice kina sona!” Ya daka mata tsawa.
“Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri ka sake min gashi da zafi.”
“Who cares? Tell me you love me!” Yayi demanding.
Bakinta b’ari yake se hawaye take zubarwa. Gashin nata yakuma ja fiye da yadda yayi d’azu, k’ara ta sakar. “Nace tell me you love me and you'll marry me ko in miki kaca kaca anan anyways dama ni zan aureki.”
Baba dake kwance a d’aki jikin sa yatashi sosai ko motsi dak’yar yake yajiyo muryan Farouq. Ja da ciki yayi yafito zuwa bakin k’ofar ya d’aga labile. “Farouq... Dan Allah kayi hak’uri kabar ta.” Cewar Baba a wahalance.
“Nak’i hak’urin Baba, seta ce tana sona kuma zata aureni wacce erin uselsess budurwa take ‘yan matan waje na ma suna cemin suna so na se ita wannan kariya me bin mazan.” Gashin nata ya sake ja “tell me you love me and you’ll marry me for the last time.”
“Farouq yanzu magana nake maka baraka jini ba?”
“Da Allah Baba ka rufa min baki da mata ta nake magana bada ubanta ba.”
“Farouq ina sanka zan aureka dan Allah kayi hak’uri ka sake min gashi” Fannah ta fad’i tana kukan azaba.
“Banji ba sake fad’a min.” Shiru tayi tana jan hanci se b’ari take ga shi yak’i sakar mata gashi. “Farouq dan Allah ka sake ta, mesa baka ji ne?”
“Baba nace kamin shiru ko? Kai bakasan addini bane? Ana shiga tsakanin mata da miji ne?” Yadawo da kallonsa kan Fannah “nace tell me you love and you’ll marry me ko sena rage miki kayan jikin kine?”
“A’a dan Allah karka min haka, kayi hak’uri.”
“Ke kariya kike kome baraki fad’a min abinda nakesan ji bane?”
“Ya Farouq ina sanka zan aureka, Ina sanka zan aureka dan Allah kayi hak’uri ka sake min gashi.” Murmushi yayi sannan ya sake ta tare da cusa ta jikinsa k’ok’arin k’watan kanta take amman takasa ga jikinsa duk warin giya. “Yawwa my beautiful Fannah I love you too, karki damu nan da ‘yan watanni za’a mana aure.” Kuka take sosai “Ya Farouq dan Allah ka sakeni.” Yasar da ita yayi a k’asa sannan ya juya yana tafiya nan da can ya fice.
Kuka sosai Fannah keyi so helplessly shi kansa Baba kuka yakeyi bare iya barin Fannah ta auri Farouq ba there has to be a way. Farouq besan darajar Fannah ba be kamata ace an barsa ya aureta ba inbanda wahala ba abinda zata sha a gidansa. “Fannah mama na dan Allah kiyi hak’uri in shaa Allah baraki auri Farouq ba, kiyi hak’uri barin iya tashi in taimakeki ba.”
Hannu tasa ta share hawayenta “karka damu dani Baba kabar kuka kar jikinka ya k’ara tsananta.” A sanyaye ta mik’e zuwa d’akinsu ta baje kan gado tana kuka kamar zata cire ranta.
****
Da dare around k’arfe 8:30PM.
“Abinda d’an mayen yazo yayi ma Fannah kenan Malam? Wallahi abun nasa yayi yawa gaskia k’ara zan kai wajen me gari.” Cewar Mami cikin tashin hankali. Bata tsaya jin me Baba ze fad’a ba ta fire zuwa d’akinsu Fannah a kwance ta sameta tana bacci a wahale numfashinta se sama sama yake dan yadda tasha kuka. Take idanunta suka cike da hawaye tayi kan ‘yarta tare da zura mata ido. “Fannah dan Allah kiyi hak’uri wallahi in shaa Allah baraki auri Farouq ba, zanyi duk abinda nasan zan iya in hana aukuwan wannan aure.”
_“Bawan Allah dan Allah karka lalata min rayuwa kayi hak’uri ka rufa min asiri I'm just 15.” “Nak’i baran hak’ura ba. Ita da ta tafi taji tausayin mu ne? se na k’wace abin yau yaso seki je ki fad’a mata, banga abinda ze hanani miki wannan abu ba yau.” “Dan Allah kayi hak’uri. Wayyo Allah Mami na ze kasheni...!!”_
Firgit! Fannah ta farka daga baccin da takeyi se nishi takeyi me nauyi, zuciyar ta na bugawa da k’arfin gakse jikinta duk yayi zufa se b’ari take. Mami na tab’a ta, ta k’urma wata erin ihu. Daga nan Mami tagane mafarkin incident na ranan tayi dama haka yake mata duk sanda tayi mafarkin seta tashi tana b’ari tana kuka da an tab’ata kuma seta tsala ihu. Yau k’imanin shekara kenan kusan kullum se Fannah tayi mafarkin daren da aka rabata da budurcinta martabarta.
“Fannah Mami ce ba abinda zan miki, Mami ce” a hankali ta sake gwada tab’a Fannah wani ihun ta kuma b’urmawa. “Mami ce Fannah, Maminki” a hankali ta tab'a hannunta sekuma batayi ihun ba hugging nata Mami tayi a hankali tana shafa kanta.
“Mami mutumin... Dan Allah kice karya dawo.”
“Shhhh! Mafarki ne Habibti mutumin yatafi bare sake dawowa ba. Mafarki ne kinji? In kawo miki ruwa?” Kai Fannah ta giad’a a tsorace Mami na mik’ewa taja zaninta “Mami dan Allah karki tafi, ze dawo. Ki zauna dani dan Allah.” Zama Mami tayi Fannah ta rungumeta gamgam wane za’a k’wace mata ita tana hawaye.
© miemiebee
No comments:
Post a Comment