Saturday, 3 September 2016

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 14
BY MIEMIEBEE


      “Hello Abuu?” Cewar Anas ta waya.
       “Anas Baba na ya kake?”
      “Lafiya Abuu I have a suprise for you”
     “Toh inaji Baba na.”
        “Nasamu aiki!” Anas yayi exclaiming.
     “Ahh toh Alhamdulillah a ina haka?”
     “A Flames Enterprises Abuu, kuma as Personal Assistance na CEO’n wajen.”
      “Wai wai! Kana nufin Alhaji Muh’d Muh’d??” Abuu ya tambaya cike da mamaki.
     “Shi Abuu salary na N500,000 da weekly allowances N5000.”
       “Kai Baba na namaka murna barin fad’awa Ummie se add’ua take ta maka.”
      “A’a bari Abuu I’ll call her dakaina banasan Amal tasan she is not the first person I called to tell.”
     “Uh!” Abuu yayi exclaiming “kai da wannan ‘yar takan.”
     Murmushi Anas yayi “Aikam Abuu ina karb’an first salary na shopping zankai Amal.”
     “Toh Allah maka albarka Anas yacigabada bud’i congratulations.”
    “Thank you Abuu se mun sake magana.”
     “So yanzu zaka shigo Monday d’in still?”
    “Eh zan shigo saboda in d’iba kayakina I have untill next week inyi resuming office.”
    “Okay toh yayi kyau, welldone.” Ahaka sukayi sallama.
 
      Anas na cikin searching contact na Amal wayarsa ta soma k’ara number ke kira bayan yad’an zura wa number’n ido ya gano Teema ce. Murmushi yayi sannan ya d’aga batare da yace komi ba.
 
     “Hello angelic blue eyes” cewar budurwar.
    “Yes” ya amsa ba tare da ya nuna damuwa ba.
     “Blue eyes fad’a muke ne? Tun jiya nake expecting call naka shiru.”
    “I have far worth important stuffs to attend to than you Teema.”
    Har tsakiyar kanta ta jiwo wannan zagi amman ta danne zuciyarta. “Blue eyes dama so nake in sani ko you are free zuwa anjima da yamma inason mu fita ne, like a date.”
     “What are you implying Teema? Kina nufin ni bansan abinda yakamata ba se kece zaki bani time da zamu fita date dake?” Ya fad’a a tsawace.
     “Blue eyes please calm down ba abinda nake nufi ba kenan naji kace gobe zaka koma Bama I want to spend some time with you kafin ka tafi.”
     “Huh!” Ya saki numfashi. Tare da jawo kad’an daga cikin gashin kansa yana wasa dashi da wata mirmushin mugunta a fuakarsa. “Nikuma banaso kinsan me Teema? Lets just end it bana sonki anymore lets break up, we are done karki sake kira na ko kin kira barin d’auka ba.”
    “Blue ey-” bata k’are maganar ba ya katse nan take ta sake kira kalan abinda yama Meeno ya mata. 8 of 100 ya murmusa sosai wanda ya mugun k’ara masa kyau.

    Amal nasa ya kira ya fad’a mata yasamu aiki. Tsalle ta riga dakawa haka suka sha hira sannan yace ta kai wa Ummie wayar. Sosai Ummie ta masa. Shettima ne k’arshe ya kira ya fad’a masa aikin daya samu, sosai Shettima uwar san jiki yamasa murna at long last ze soma jin dad’i dan yasan halin Anas be iya rowa ba inba wai dagangan zeyi ba, mutum ne me kyauta amman fa ma wanda yaga dama.
 
    ★★★★

           Da misalin k’arfe 3:30PM Fannah ta dawo gida da ledoji manya manya hannunta siyayya tama family’nta sosai. Mami, Afrah da Aiman duk suna tsaye tsakar gida hankali tashe a tunaninsu ko wani abu ne yasamu Fannah saboda duk sanda zata wani waje daga gun aiki tana kiran Mami ta sanarda ita wanda yau batayi ba.
 
     Tana shigowa Mami tayi kanta tare da rungomata “Fannah ina kikaje? You made us worried sick gashi nata kiran wayarki akashe.”
        “Wallahi game natayi seta mutu, kubar tada hankalinku please in shaa Allah ba abinda ze sameni. Kasuwa na wuce nad’an mana siyayya.”
    Nan Afrah da Aiman suka k’ariso tare da karb’an ledojin akan tabarma suka zauna tare da zazzage kayakin.

       Kitchen utensils ne, food items, seda sweets da chocolates dakuma atamfofi guda hud’u masu kyan gaske seda shadda guda biyu, se sauran k’ananun abubuwa irinsu tissue, toothpick da sauransu. “Fannah ina kika samu kud’i haka ko har anbiyaku albashin ne?”

        “Ko kad’an Mami, ina meeting dana fad’a muku za’a kaimu serving d’insu yau?” Mami ta giad’a kai “ashe harda Alhaji Muh’d Muh’d CEO’n Flames Enterprises.”
      “Haba keh!” Cewar Mami.
     “Ya Fannah kap Maiduguri fa ba wanda yakaisa kud’i!” Cewar Afrah.
    “Ya Afrah shine wanda muke gani a NEWS yawancin kullum?” Aiman ta tambayi Afrah. “Eh shi” Afrah ta amsa ta a takaice.
   
         “Toh shida d’ansa sukaje ni akace na kaimusu drinks nasu bayan nakai nakega se d’an nasa yace baya shan flavour’n drink d’in baban nasa ya kirani na canzo masa nazo tafiya kawai Alhj Muh’d d’in ya kirani ya mik’a min bandir na N500 kyauta bayan da aka k’are meeting d’inkuma da muka raba kud’in da aka bamu na tashi da dubu goma albashi na na wata fa kenan ga kuma dubu hamsin. Daga can na wuce kasuwa namana d’an siyayya dududu kayan dubu talatin ne anan.”

      Aiman mathematician har an buga lisafi “sauran miki N30,000 kenan.”
   Kallonta Fannah tayi tana murmushi “welldone ashe surutun nan naki ba’a banza bane tunda kin iya math haka.”
    “Math d’in ‘yan primary three ba” cewar Afrah tana duba zannuwan. Aiman zatayi magana Afrah tace, “Ya Fannah wannan zannuwa fah?”

      “Namu ne biyu na Mami ta zab’a ciki, guda biyu iri d’ayan kuma naki da Aiman.”
       “Haba Ya Fannah mena siya min turmin zani iri d’aya da wannan maras kunyan.”
        “Yo! Ked’inma ance miki inasan yin anko dake ne? Ya Fannah mungode sede har yanzu banga sweet d’ina ba.” Cewar Aiman.

      Nan Fannah ta bud’o jakarta ta ciro packet na sweet “ungo wannan duka naki ne kika rabawa ‘yan ajinku kuma ni ba ruwa na.” Amsa tayi tana tsalle “nagode Ya Fannah ai ko Ya Afrah ma barin bata bale ‘yan ajinmu masu kwad’ayin nan, wallahi Falmatan nan har k’wai na sanda taci ranan” Zani biyu iri d’ayan ta d’au d’aya tashige d’akinsu dashi. “Ke dawo nan waya ce miki ki d’auka?” cewar Afrah jan d’ayan tayi itama ta ruga tabi Aiman cat and dog kenan.
   
        “Fannah Allah miki albarka, Allah k’ara miki bud’i yaci gaba da kare mana ke. Mungode matuk’a da d’awainiyan da kike mana dukda kuwa ba responsibility’nki bane wannan aiki na ne da Babanku amman kinayi. Kiyi hak’uri.”
     Hannun ta Fannah ta rik’e bibbiyu cikin nata “Ameen nagode da addu’arki Mami amman dan Allah kidena min godiya ba godiya tsakani na daku Mami. Na ware dubu ishirin cikin kud’in gobe seki kai Baba asibiti a duba shi ko magani a basa tunda baramu iya affording aikin da za’a masa ba.”

        “Toh Fannah, sannu da k’ok’ari Allah miki albarka.” “Ameen” tace “barin je in samu su Afrah ciki, ki d’au zannuwa biyu anan shaddojin kuma na Baba ne.” “Toh mungode sannu.”

     Fannah na shigowa d’aki tasamu Afrah da Aiman se dambe suka dak’yar ta rabasu zani de gasu iri d’aya amman ahakan ma se anyi fad’a. Bayan ta rabasu ta kori Aiman dawayo in bahaka ba sun hau wasan habaici kenan. Ana kawo wuta ta had’a wayarta a charging. Kayakinta na cikin wardrobe take shiryawa a yayinda Afrah ke kishingid’e kan gado tana game a wayarta. Can ta nisanta sannan takira Fannah. “Ya Fannah!” “Na’am Ya Afrah, mene kuma yanzu?” cewar Fannah tana ninke kayakinta.

       “Kikace d’azu kinga Alhaji Muh’d Muh’d?” Kai Fannah ta giad’a batare da ta kalleta ba. “Okay da d’ansa kuma kikace sukaje wajen?” Afrah ta fad’i kalma d’ai d’ai.
     Barin abinda takeyi tayi ta juyo ta kallon Afrah “what are you implying?”
    D’an dariya Afrah tayi “guilty concious?? Ni bance komi ba kawai cewa nayi kinga d’an Alhj Muh’d?”
     “Nope ni bangansa ba.” Fannah tabata takaicaccen amsa.
 
     “Wow! Yau me hana mutane k’arya keyi? Hilarious.” Cewar Afrah tana mocking smile.

       “Kuma se akace miki k’arya nake. Allah ban ga d’an nasa ba.”
        “Toh ikon Allah kuma ke fa ke kika kai musu drinks nasu? Kodan had’ewarsa yasa baki gansa ba?”
    “Ke wallahi Afrah suratan banza sun miki yawa. Ni ko zaki samin wuk’a a wuya bansan kalar fatar sa bama bale insan ko kyakkyawa ne ko mumuna. Muryarsa kawai naji.”

      “Haba!” Afrah ta daka tsalle tare da baro inda take ta matso kusa da Fannah. “Ya muryar tasa take Ya Fannah? Fad’amin please kinsan su yaran masu kud’i muryarsu ma daban take.” Shiru Fannah tayi tana nazarin muryar Anas dasuka d’au d’an Alhj Muh’d ne. “Well ba hassada muryarsa nada zak’i irin zak’i ta mazan nan and yana cracking hakan nan. Barin miki bayanin yadda zaki gane kinsan muryar Lancelot nacikin season film Merlin ba?” Kai Afrah ta giad’a sau uku. “Toh haka murayarsa take sede kamar zatafi na wancan d’inma dad’i. Toh kinji, matsa min nacigaba da abin dake gabana.”

      “Iyye! Har kinsa na fara imagining wannan d’an billonaire nasan definately zeyi kyau sesa hakan ma ba’a nuna sa a NEWS gudun kar ‘yan mata su bisa.” Kallo Fannah ta bita dashi “kefa wallahi surutun banzanki sunyi yawa.”

         “Hummm! Afrah taja numfashi “Ya Fannah kenan. Kinsan muryarsa meaning kunyi magana kenan.”
      “Wai meke damunki bamuyi magana ba acewarki yaran da ubansu billonaire suna magana wa mutane anyhow ne? Ko kallona ma beyi ba dana ajiye masa drink d’in kamar yadda nima ban kallesa ba thank you kawai naji yace.”
   “Iyye! Amman daya miki magana fa? Zaki amsa?”
      “Ke qaniyarki, Afrah kika sake maganan wancan saurauyin bake ba kud’in kati se next month.” Tsit Afrah tayi bata kuma cewa komi ba, ahaka Fannah tasamu tagama had’a kayakinta cikin wardrobe.

           _One week later..._
     
           Anas ne tsaye gaban dressing mirror a d’akin da chairman yabasa. Yau ze soma zuwa office he is feeling nervous sosai. Sanye yake da mint blue shirt me long sleeves da cufflinks, seda jean trousers. Simple shiri ne amman yamugun amsar sa he is looking way smart. Jakar laptop nasa ya d’ago yasa laptop d’in ciki da sauran takardu kad’an sannan yasake kallon kansa jikin madubin sannan ya fice bayan ya karya ya wuce office.

       Yana isa gaban building d’in da za’a iya kira da mini sky scrapper ya tsaya. A k’alla floors za suyi 7-8, dogon gini ne sosai wanda jikin bangon yake glass. Building ne babba bakin k’ofar an rubuta FLAMES in caps. Wani button ya danna k’ofar glass d’in ya bud’u yana shiga k’ofar yayi scanning nasa bayan ya tabbatar baya d’auke da makami sannan wata k’ofar ta sake bud’uwa nan ne mutanen cikin ginin suka bayyana. Maza da mata kowa se aikin gabansa yake very organised. Wajen shiru ba hayaniya. Wajen dayaga an rubuta RECEPTION ya k’arisa mace ce tsaye wajen gabanta telephone ne da pack na pencil da biro seda files kuma. Tun kafin ya mata magana tace dashi “Hi” tana washe 32 inta acewarta taga bature.

       “Hello” ya gaisheta back, “erm I want you to direct me to Mr. Muhd’s office, the CEO.”

     “Okay American's most handsome” tace dashi. “Whats your name?”

     “Anas Ibrahim Fauzy.” Ya amsata a takaice. Baki tasake wangalau wai dama ba bature bane?

   “Excuse me, I mean your name. Name.” dan bata yarda muslimi bane.

   “Yes Anas Ibrahim Fauzy. Ko kema kin d’au Joseph ko Andrew ne sunan nawa? My name is Anas for goodness sake.” ya fad’a a tsawace.

        “I'm sorry blue eyes” ta fad’a tare da kashe masa ido. Tsuka yaja tare da kawar da idanunsa daga kanta.

      “Uhm are you two having an appointment with the CEO yasan da zuwanka?”

    “What nonsense? Da inbe san da zuwa na ba zanzo nan ne? Take me to your CEO” yayi demanding ba alaman dariya a tatare da fuskarsa. “Mesa yawancin kyawawan mutane basuda hali ne?” Cewar receptionist d’in a hankali aikuwa Anas ya jiyota harara ya watsa mata bayan d’an dube-duben da tayi a system dake gabanta tace, “I'm sorry Mr. Fauzy seems like ba sunanka acikin wad’ana zasu ga Mr. Muh’d yau maybe next time.”

           “Kinsan wani abu? Tunda nake a duniya ban tab’a ganin senseless mutum kamar ki ba.” Dadai lokacin elavator ya bud’u Mr. Muh’d ya fito daga ciki. Taku d’ad’ai kamar yadda ya saba yayi yatako zuwa gabansu Anas cike da girmamawa Anas ya gaishesa.

        “Ya Anas me kakeyi baka shigo ba har yanzu? I've been waiting for you”
        “Baba wannan receptionist d’ince ta rik’eni wai baran shiga ganinka ba.”
    “No Sir ba hak-”
   Katse ta Mr. Muh’d yayi rai a b’ace “this should be the last time da zaki sake hanasa shigowa nan he is Anas my son, copy that!” ya daka mata tsawa.
   “Yy..yyess sir, my aplologies please.”

     “You apologise to him not me.”
     Kallon Anas take yana mata murmushin mugunta, “Mr. Fauzy I'm sorry.” Harara ya watsa mata sannan yace, “apology accepted.” Nan Mr. Muh’d yaja hannunsa “come lets go in nuna maka office naka.” A floor na k’arshe yakai Anas inda aka rubuta *Mr. Fauzy* a bakin k’ofar d’akin. Office ne babba da split AC ciki, office kujeru ne manya guda biyu da table d’aya. Akoi telephone da flat screen desktop kan table d’in seda notepad, da pen dakuma pencil pack. Gefe guda kuwa fridge ne seda plasma TV. “This is your office, inda abinda be maka ba let me know se a giara” Godiya sosai Anas ya masa tun daga ranan Anas ya soma aiki.

     He is very punctual, duk meetings da schedule na Mr. Muh’d shi yake maganing kasancewar duk Enterprise d’in ba architecture’n daya kai Anas duk sandq za’ayi zanen project Anas keyi.

  *© miemiebee*

No comments: