BY MIEMIEBEE
FANNAH
‘kauyen Bama dake jihar Maiduguri, Borno.
Kyakkyawar budurwa ce zaune cikin wata ‘yar k’aramar d’aki bisa gaban wata ‘yar madubin da aka mak’ala a jikin bango. Ba komai bane a d’akin illa katifan dake shimfid’e a k’asa seda bakunan sa kaya da leather carpet ciki. Ba shakka basu da arziki. Dududu wannan ‘yar budurwa baratafi 15 years old ba. Tanada haske sosai, da sirirn hanci dakuma plumpy lips, idanunta ba laifi ‘yan manya ne dadai. Gashin girarta acike yake mekyawun gaske ba ruwanta da zana artificial gira [ba erinsu ni ba;( ] in kuwa aka k’are mata kallo sosai za’a ga alamar had’ewar girar ta guda biyu gu d’aya sede be munanta taba hasali kyau ma yak’ara mata. Gashin idanunta a cike suke kuma dogaye, saje ne a fuskarta kwance luf-luf wane na miji (kaman nawa, lol) gashin kanta dana girarta sun had’e dan yawansu. Hannunta gashi ne a kwance dogaye masu mugun kyau.
Siririya ce de tanada tsawo daidan shekarunta, tana sanye da wata atamfa maroon da torches na white and green, se murza wata ‘yar jan baki pink take a lips nata hankalinta kwance da anganta ansan batada matsala. A lokacin da wayarta k’irar Nokia Asha dake kan cinyarta tayi k‘ara, a hanzarce ta duba tana ganin sunan daya bayyana kai _Ya Ahmad_ tayi murmushin jin dad’i sannan ta bud’o sakon ta karanta kamar haka;
_my Fannah I'm outside waiting for you yanzu shigowa na gari ko gida ban lek’a ba just wanted to see you_
“yeyy!!” Ta fad’a a fili tana murna. Data gama sa jan bakin ta shafa powder tareda sa kwalli a fararen idanunta take ta dawo wata balarabiya. A garin mike’wa d’an kwalinta ya since ya fad’i k’asa tare da ribbons data k’ukk’ula gashin nata dashi. Fans ko kunsan ya gashin buzayen Maiduguri yake? Erin bak’i k’irin me santsi da tsawo kamar haukan nan? Haka gashin wannan ‘yar budurwa yake.
Ni kaina miemie dana gani sanda na tsorata dukda cewar ita kad’ai ce a d’akin hakan be hanata yin saurin tattara ribbons d’in gu d’aya da sauri ba tasoma k’ok’arin faka gashin nata gu d’aya saidai dan cikar gashin ta kasa, hannun nata suna nan sirara ba fad’i ga uwa uba gashi har tsakiyar bayanta. Kamar wacce zatayi kuka tafito d’akin “Mami! Mami!” Shiru kukeji wani mutum ne wanda bara’a kirasa da dattijo ba danko befi shekaru irin 44-45 dinnan ba ya lek’o daga wata d’aki wanda ya kasance opposite daga d’akin da Fannah tafito da alama mahaifinta ne dukda cewar basu kama kuwa. “Fannah uwata ya akayi? Tsaya mesa kike yawo da kanki a bud’e haka?”
Kamar wacce zatayi kuka tace, “Baba ribbon d’in ne yafita kuma nakasa d’aure gashin, Mami nake nema ta tayani.”
“Shine zakiyi kuka uwata?” Cewar mahaifin nata “Mami batanan tashiga mak’ota.”
“To baba Ya Ahmad fa yazo yana jirana a waje ko gida be wuce ba ya zosa nan.”
“Oh! Keda Ahmad d’inkin nan se Allah. Ina Afrah da Aiman toh?”
“Sun tafi islamiya Baba.”
“Yoh! Kekuma fah?”
“Kai Baba wai yanzu so kake kace ka manta sauk’an nawa? Abinda har Hajji kaje da kujerar da aka bani danayi na biyu.” “Haka fah, taho to in kama miki kan.”
“ Yawwa Baba na.” Da gudu taje ta zauna gabansa shima sanda yayi dagaske sannan ya kama uban gashin nata gu d’aya. Banda tsawon gashin gu d’aya. Wawan cika ne dashi saisa Fannah batta iya kamawa. “Toh nagode Baba.” “Yawwa ‘yar akbarka se ganin Ahmad ko?” Ta giad’a masa kai. “Ki sa hijabi fa tukun kuma kice ya gaishe min da mahaifinsa naji wai ya d’anyi rashin lafiya kwana biyu kuma ban samu na lek’a sa ba.” “Toh Baba zan fad’a masa in shaa Allah.”
D’akinta takoma tad’au wata maroon hijabi wanda ya sake ciro da hasken ta tasa, tare da d’aukar wayarta sannan tafito waje idanunta suna sauk’a kan Ahmad nata ta sakar dawata murmushin jin dad’i. Ahmad saurayi ne me k’imanin shekaru 23. Chocolate skinned yake, yana da kyau dadai gwargwado gasan murmushi. Tsayyayen na miji ne masha Allah!
“Ga sarauniyata ta fito.” Ya fad’a yana mai murmushi. “Gaskiya wankan nan yayi kyau sosai Fannah, kin ganki kuwa? Looking so take away.”
“Ya Ahmad kaide kullum seka riga zolayata. Ina wuni? Ya hanya? Gashi ko ruwa ban samu na d’auko maka ba duk na k’osa in ganka.”
“Laaa ai sarauniyata bata laifi ae, karki damu ni ganinki kad’ai ya kashe min k’ishi.” Hannu tasa ta tare fuskarta a kunyance. “To ya Ahmad mu zauna anan mana kar ka kaji a tsaye.” ta nuna wat benchi.
“Haka sarauniyar tawa tace? “Haka to za'ayi.” Bayan sun zauna Fannah tace, “ya hanya toh? Ya makarantar?” Hannu yasa ya dafe goshi sannan yace, “so hectic fa Queen, biochemistry akoi wahala. Ga Maiduguri zafi like hell”
“In shaa Allah ka kusa gamawa, Allah baka sa’a yaya na.” “Ameen sarauniyata.” Kefa ya school ‘yan matan ss2 koh?”
“Kai yaya! School alhamdulillah” Ta fad’a tana murmushi. Hira suka d’an tab’a na ‘yan mintuna. Shi Ahmad ba abinda yake sake jan ransa kan Fannah kamar san addininta dakuma yawan yarintar ta dakuma sa sa dariya da takeyi in suna tare. Fannah batta magana d’aya biyu seta sa alhamdulillah, subhanallah, masha Allah ko jazakallahu bikhair ciki. Yarinyace me tarbiyan gaske, ga hankali da girmama na gaba da ita koda wasa bata tab’a kiransa da sunansa gatsau ba dole seta sa yayan nan kuma bawai they are related bane tsantsan girmamawa ne kawai.
“Toh yaya na kar na ta jan ka da surutu nasan su Mama duk suna jiran ganinka, kaje gida ka huta.”
“Toh sarauniyata” hannu yasa cikin jakarsa yaciro wata leather sannan ya mik’a mata.
“Me wannan kuma yaya na?” ta tambaya suprisingly.
“ ‘yar tsarabar Maiduguri ne nace barin kawo wa sarauniyata, yi hak’uri ba wani abu me tsada bane.”
“Yanzu yaya karatu kakeyi amman seka rik’a kashe kud’inka a kaina? Ni gaskia kadena banso nafison kana kula da kanka a school.”
“Ko kad’an Fannah baran iya zuwa nan ba tare da na kawo miki komi ba. I prmise you this duk sanda na fara earning salary’n kaina I will spend it on you, ina sonki sosai Fannah ta.”
“Nima ina sonka yaya na. Nagode sosai, jazakalllahu bikhair Allah taimaka ya baka sa’a yaya.” nan ta mik’e.
Mik’ewan yayi shima “ameen my Fannah inasan addu’o’in ki agareni, ba k’aramin taimaka min suke ba.”
Ai saisa kullum nake including d’inka cikin prayers d’ina. Baba na naka sannu dazuwa also, yace ka mim’a gaisuwan sa gun Abba da jiki”
Toh my Fannah, I'll tell him so se munyi waya ko?” kai ta giad’a a hankali. Wai! Ai na manta kun kusa fara exams ma, barinso jn hana Queen d’ina karatu ba”
“Haba mana yaya ko wayan minti ishirin baramuyi ba?”
Da murmushi a fuskarsa yace ai baki tab’a neman abu kirasa guna. Allah kaimu daren toh”
“Yawwa yaya bo-bye” tamasa murmushi. Murmushin ya mayar mata “bo-bye Queen.” Ahaka tashigo ciki.
Tun kafin ta yo d’aki ta soma bud’o ledar, abaya ce me kyan gaske ga stones kota ina. “Wowww!” kukeji tana fad’i kamar Ya Ahmad yasan yadda nakeson abayah. Nan ta hau gwada wa kan kayarta bayan ta cire hijabin nata. Aiko daidanta tazo gwada yafa gyalen se kud’i ya fad’i daga ciki tana irgawa taga dubu biyar. “Yanzu Ya Ahmad wannan d’inne zece ba yawa. Baba! Baba!” Ta k’olla masa kira tana nufo d’akin nasa.
“Ya akayi uwata ta kaina?” Ya tambayeta a kishingid’e tare da kashe radio’n dayake ji. “Wannan kaya fa daga ina?”
“Masha Allah Ya Ahmad ne yakawo min yanzu kaga harda dubu biyar kuma.”
“Kai Allah shi mashi albarka, shi kullum cikin wahala yake miki? Gashi ko kayan yamiki kyau kika fito kamar balarabiya.”
“Kai! Baba dagaske?” Ta tambaya tana tsalle. “Sosai ma kuwa uwata.” ya amsata. Nan ta irga dubu biyu ta mik’a masa “gashi Baba ka rik’e wannan, Mama ma dubu biyu nida Afrah da Aiman kuma semu raba wannan.”
“A’a uwata rik’e abinki kinji? Ki saya abubuwan da bakida dashi” ya mik’a mata.
“Baba ni komai danake buk’ata inadashi ka karb’a kaji? Ko cafani sekayi dashi.”
“Toh nagode uwata, Allah miki albarka ya cigaba da kare min ke.” “Ameen Baba zan koma d’aki.” Nan ta fice, isarta d’aki bada jimawa ba k’annenta Afrah da Aiman suka dawo.
Atare suka shigo d’akin d’ayan tana nan kamar Fannah baratafi 13 years old ba whereas d’ayan kuma dududu intayi shekaru shine 3. “Ke wai Aiman kullum ne sekin tsaida mu akan hanya da sunan fitsari?” cewar 'yar babban (Afrah) kenan. “Anyin!” cewar Aiman yarinya ‘yar shekara uku se uban baki.
“Ni kike ma rashin kunya? Iyye?”
Fannah dake kwance kan katifa tana karatun History ta d’ago ta zauna “wai ke Afrah me damuwarki? Shikenan yarinya bara tayi fitsari ba?”
“Ya Fannah ni ban tsoma bakinki ba, nida Aiman nake magana.”
“Aww rashin kunya zakimin? Dama d’azu Ya Ahmad yazo ya bani kud’i nayi niyan baki kad’an daga ciki amman tunda rashin kunya zakimin na fas-”
Afrah ta katse ta, “a’a yi hak’uri Ya Fannah ta.” Da gudu ta haura kan katifar “yaushe Ya Ahmad d’in yadawo?”
“D’azu bakiga abayan daya kawo min ba!” Nan ta mik’a hannu taciro daga cikin wata bako take Afrah data kusan kamota tsayi ta amshi zata soma gwadawa Fannah ta k’wace “kefa bakida seti, akawo min kaya kiwani ce zaki gwada?”
“Su Ya Fannah manya masu samari.”
“Samari? Ai Ya Ahmad ba saurayi na bane miji na ne, kinga yana level 5 yanzu ina ss2 ina ss3 yana neman aiki ina gamawa se muyi aure by then yasamu aiki in shaa Allah”
“Ahh lallai fa soyayya ruwan zuma. I'm envious.” Cewar Afrah.
“Don't be, kema lokaci ne beyi ba Allah ze had’aki da mijin dayafi Ya Ahmad sona.” “Allah sa!” Afrah tafad’a da sauri “Ameen habibti” cewar Fannah.
****
“Fannah! Fannah! Zo da sauri da Allah” kirar Mami. “Na’am Mami gani zuwa.” Sunnah take da niyar yi kafin tayi nafilar Maghrib kasancewar lokaci ya kusa yi amman dan kirar Maminta ta fasa tajeta. “Gani Mami”
“Fannah yi hak’uri ki siyo min maggi ashago nan kusa wallahi bansan ya akayi ba har ya k’are ban sani ba yi hak’uri kinji mamana?”
“Yanzu Mami aike zakiyi shine sekin had’ani da Allah harda bani hak’uri. Ina kud’in?”
Nan Mami taciro hamsin ta mik’a mata. “Kinga ai kece babba Afrah yakamata in aika amman shegen yawonta tashiga nan mak’ota ganin jaririyar da Ameenatu ta haifa.”
“Ayya ba komai Mami barin yi sauri kafin su rufe shagon.”
“Toh Allah kare.” “Ameen” ta amsa sannan ta fice.
ANAS
“So Anas sauran ka 3 days kafire London kenan?” Cewar Shettima suna zaune a kan wata benchi a bak’in k’ofar gidansu. “Gonna miss me?” Anas yafad’a yana d’aga gira.
“Eh mana I will miss you, nide Anas wallahi ka canza tsoron zuwanka London d’innan nake nan da Bama ma kana shaye shayenka a b’oye bale ace kaje can inda ba idan kowa.”
“Toh yau kuma wa’azi zaka min? Kagannin nan yanzu haka akoi inda mukayi appointment da su Baana I will have my last drink a Bama yau kasan gobe zamu wuce Maiduguri, so kaga dole in sha in bugu tunda na k’arshe ne.”
“Amman kasan Abuu nagari ko? In ya ganka a buge fah?”
“Make up stories for me then, kamar yadda ka saba kace masa fad’a mukayi da wani. I'm going now.”
“Toh masallaci fah?” Cewar Shettima.
“Sena dawo zanyi sallar.” Daga nan ya fice inda suka saba had’uwa in zasuyi shaye shayensu ya je chan suka bugu like never, ko sanin ina suke in aka tambayesu ba sani zasuyi ba.
Daidai Anas ya tashi ze tafi gida kenan aka soma wani erin masifaffen ruwa ba yadda Baana basuyi dashi yajira ruwan yad’an tsaya kafinnan ma hankalinsa yad’an dawo jikinsa ba amman sam yak’i jinsu ana ruwan yasoma tafiya, yazo ma besan ina yake dosa ba dan yadda ya bugu.
****
FANNAH
“Oh No! Shagon Ya Wakil a rufe gashi Mami battada maggin da zata yi amfani dashi dole in k’ara gaba” haka tatayin gaba duk shagunan a rufe amman still bata hak’ura ba. Bada jimawa ba aka soma ruwa me k’arfin bala’i gashi daga can tana hango wata shago a bud’e ta koma gida ba maggin kuma battaso. Cikin ruwan ta cigaba da tafiya daidai ta shiga wata lungu taga wani na miji daga gani a buge yake, duda acikin duhu ne hakan be hanata tantance kyansa da blue eyes nasa daya d’ago yana kallonta ba. Take ta soma b’ari Allah sa ba gamo tayi ba. Mutum da blue eyes.
Addu’o’in kariya tasoma yi jikinta se rawa yake gu d’aya ta tsaya jiran yazo ya wuce tayi gaba itama. Daidai yazo kusa da ita seya tsaya hannu ya d’aga yakai kan fuskarta tuni Fannah ta soma kuka tunda take ba d’a na mijin daya tab’a tab’ata inba Babanta ba. Ga k’arfin ruwan saman koda tayi ihu bame jinta shagon data gani a bud’en ma har sun rufe.
*©miemiebee*
No comments:
Post a Comment