BY MIEMIEBEE
“Ni ba abinda nake nufi ba kenan, my point is adena kirar ‘yata kariya. Alhj Suleiman kai da d’anka zaku iya tafiya, abincin wani gub’an wani kamar yadda ka k’yamaci Fannah haka wani zeji kamar ya mutu mata. Ahmad Allah had’aka da rabonka, ka kasance masoyin Fannah na hak’ik’aamman there is nothing you can do now dole ka hak’ura kabi umarnin mahaifinka, in zakumin uzuri, I need to see my daughter.” Yana kaiwa nan ya shige d’akin Fannah.
Idanun Ahmad take suka kad’a sukayi ja, koda wasa be tab’a tsammanin akoi abinda ze shiga tsakaninsa da Fannah ba, yana santa fiye da yadda yake san kansa. “Abba dan Allah kar muyi haka, wallahi nasan Fannah is innocent.”
“Ahmad kaji na rantse maka kasake min maganan wannan kariyan zan tsine maka, ai saisa akace a bincike mutum shiru-shiru. Maza mu wuce gida, Alhj Khaleel nagode sosai Allah bar zumunci.”
“Bakomai Alhj Suleiman, ita gaskiya haka take daga k’in jinta kuma se b’ata. Allah rufa mana asiri.” Da fad’in “ameen” Ahmad dake hawaye shida mahaifinsa suka bar asibitin. Suna ficewa ya Khaleel ya b’alle da dariyar mugunta. “Ai dama nace in shaa Allahu ‘yarka barata auri wani ba inba d’ana ba. Kyakkyawar mace me addinin muslinci Farouq ya cancanta kuma ba kowa bace illa Fannah saboda haka tana warkewa zanje in samu Baba (mahaifinsu) in masa magana.”
Gida ya zarce yana isa ya soma k’olla ma d’ansa Farouq kira. “Farouq! Farouq! Zo nan” alokacin ya zauna kan wata tabarma bada jimawa ba Farouq d’in yafito da angansa an ga d’an iska wata shegiyar crazy wando ne a jikinsa da singlet. Ba laifi yanada kyau dadai dakuma tsawo. Bayan ya zauna yace, “gani Baba.” Ya Khaleel ya kallesa sannan yace, “d’ana ka kwantar da hankalinka Fannah ta kusan zama taka, Fannah taka ce! Yanzu ana sallamota daga asibiti zan wa kakanka magana.”
“Baba dagaske!” Farouq ya tambayi mahaifinsa cike da jin dad’i. “Da dana ce maka seka auri Fannah ka d’au wasa nake maka ne? Ai Fannah taka ce.” “Kai Baba na gode amman da akoi matsala Baba.”
“Ina jinka Farouq mecece matsalar yanzu in warkar maka da ita?”
“Fannah... Bata so na Baba ko kad’an zan iya irga sau nawa muka tab’a magana da ita, sam bata sona ta tsane ni.”
“A da kenan...” Ya khaleel ya fad’a yana murmushin mugunta.
“Ban gane a da ba kenan Baba.” Farouq ya fad’a a little bit confused.
“A da datake da tabbacin cewa akoi masu santa amman banda yanzu data rasa budurcinta, kap ba na mijin da ze so ta yanzu, ta zamo tamkar k’azantar da akeson a yasar ne yanzu. Ko baka gane ba?”
“Sosai na gane Baba na gode.”
***
Afrah ce tsaye kan Fannah tana kallonta hawaye suna gangara kan kumatunta a yayinda Baba da Mami suke zaune kan wata kujera, Aiman kuwa an mata shimfid’a a k’asa tana bacci. Hannu Afrah ta mik’a dan ruf’e Fannah mekyau da bargo taga kamar Fannah tad’an motsa.
“Barin je in kama ruwa” cewar Mami “ina zuwa yanzu.” Kai Fannah ta kad’a a hankali again. “Ya Fannah! Baba! Mami! Fannah tayi motsi.” Kafin su Mami su k’ariso Fannah ta soma bud’e ido a hankali tagama bud’e idanun nata ta sauk’esu kan family’nta dake tsaye a kanta suna murmushi da zubda hawaye a lokaci d’aya, murmushin tayi k’ok’arin mayar masu da k’yar.
“Ya Fannah!” Cewar Afrah
“Fannah! ‘yata” cewar Mami.
“Mama na!” Cewar Baba.
Kallonsu take a hankali cikin wata dashasshiyar murya tace, “Mami, Baba, Afrah.” Dad’a k’aruwa murmushin fuskarsu yayi Baba yace, “Afrah jeki kira nurse kice mata Fannah ta farfad’o.” Bayan minti d’aya Afrah dawata nurse suka shigo d’an dube-dube tayi wa Fannah sannan taceda su Mami “Alhamdulillah condition na ‘yarku is stable. Inda hali a had’a mata tea me kauri tasamu tasha se abata magunanta. Excuse me.”
Hugging nata sukayi one-by-one kowa na muranan dawowarta. “Ina Aiman?” ta tambaya a wahalance kusan a tare suka amsata “gata can tana bacci.” “Fannah ya jikin naki?” cewar Mami
“Da sau... Argh!” Tasaki k’ara.
A rikice Mami tace. “ina ke maki zafi Fannah?” Take idanunta suka cike da hawaye, “k’asa na Mami, zafi.” “Malam ko zaka d’an bamu waje dan Allah” cewar Mami cike da tausaya wa ‘yarta. Bayan Baba yafita Mami ta umarci Afrah ma da tafita ba gardama ta fice.
“Fannah kiyi hak’uri dole k’asarki ya miki zafi anji miki ciwo.”
Tana kuka tace “Mami ya rabani da budurci na ko? Mami banida martaba yanzu.” Ta fashewa dawata erin matsanancin kuka.
“Fannah ‘yata dan Allah kiyi hak’uri kukan nan k’ara miki rashin lafiya zeyi, kiyi hak’uri. Ki d’au wannan k’addara ce Allah ya turo miki.”
Cikin kuka tace, “Mami yanzu akoi d’a na mijin da ze yarda ya aureni? Nasan ko Ya Ahmad ze gujeni.”
Shiru Mami tai batace komai ba hakan ya sake tabbatar wa Fannah zancenta. “Yama riga ya tafi ko Mami?” Har yanzu Mami batace da ita komi ba se kuka ba sautin da takeyi. “Mami talk to me please, ki fad’a min gaskia.”
“Fannah kiyi hak’uri wannan jarabawa ce Allah keson gwada ki, in baki rungumi k’addara ba seki fad’i. Ahmad be k’i ki ba mahaifinsa ne ya tilasta masa se ya rabu dake saboda Kawu Khaleel yace masa saurayin kine ya miki wannan abu.”
“Mami amman ai k’arya ne, wallahi bansan shi ba acikin lungu kawai ya tsareni wallahi ban tab’a ganinsa ba inba ranan ba.”
“Shhhh! Fannah basekin min bayani ba sanin kanki ne Kawu Khaleel tinba yau ba baya sanki, yayi hakan ne kawai dan ya shiga tsakaninki da Ahmad dan yaga Ahmad nasanki tsakani da Allah.”
“Mami me na masa ya tsaneni haka? Mena ma wannan saurayin daya k’wace min martaba ta Mami? Shin na kasance mutumiyar banza ce da duk munanan abubuwa suke faruwa dani?” Hannu Mami tasa ta goge mata hawayen dake gangara kan kumatunta, “ko kad’an habibti, ita duniya haka take mutane masu kind heart su Allah yake jarabta saboda ya gwada nauyin imanin su. Wannan jarabawa ce Fannah you have to be strong.”
*****
*ANAS*
D’aki ne babba da gadaje guda uku ciki, haka wardrobe ma, sannan da bathroom aciki. A d’aya daga cikin gadajen Anas ke kwance akai da earpiece a kunnensa wanda ke had’e da wata sabuwar Iphone 6s ajiye kan cikinsa. Sanye yake da ¾ wando da vest bak’a ya zura wa ceiling ido se tunani yake. Bada jimawa ba wasu samaruka guda biyu suka shigo wanda suke nan sa’anin Anas, da angansu anga ‘yan hutu. Gado d’add’aya suka d’auka suka kwanta kai har alokacin Anas besan da shigowarsu ba.
Pillow d’ayan ya wulla masa a firgice ya mik’e ya zauna ganin su ne yasa ya sauk’e ajiyar zuciya. “Mehn! Yaushe kuka shigo bansani ba.”
“Well kayi nisa a tunani taya zakayi noticing shigowarmu?” cewar na k’arshen. “Waima tunanin me kake haka? Kullum fa cikin tunani kake ko ka bar mata da ‘ya‘ya ne acan gda 9ja?”
suka k’yalk’yale da dariya illa Anas daya tsaya yana kallonsu.
“Musty waikam meke damun Anas ne?” cewar d’ayan.
“Ji Abdul de da wata magana budurwarsa ce ni da zan sani?”
“Oh oh no please banda maganan budurwa anan” Anas ya fad’a in an angry tone.
“Wai Anas kai kullum haka kake ne? Ban tab’a ganin kayi dariya ba wallahi, whats wrong with you? And anytime aka kawo maganan girlfriend you seem so moody.” Cewar Abdoul.
“Nima de, abin have been bothering me.” Hannu yasa yaja d’aya daga cikin bedside drawer’n gadonsa tare da ciro wani syrup ya wulla wa Anas karap ya cafke. “Meh wannan kuma?”
“Wannan!” yad’an murmusa “lets say anti-problem kokuma problem reliever.” Shida Abdoul suka kwashe da dariya. Kallaon syrup d’in Anas yayi sannan ya ajiye kan bedside drawer’n nasa “no thanks barin sha ba.”
“Chill bro!” cewar Musty. “It'll ease all your problems just give it a try.” Haka suka ta cika masa baki kan in yasha ze manta yanada problem ko d’aya akansa seya d’auka ze sha seya tuna wa’azin da Abuu yamasa amman kuma problems sun masa yawa right now gana Ummimi gakuma na yarinyar daya yi raping. Rufa ido kawai yayi daga k’arshe yasa kwalban syrup d’in a baki. “Dude (maza) karka shanye duk-” be k’are maganar ba Anas ya kauda kwalban syrup d’in daga bakinsa sanda ya kwankwad’e tas.
Fuska ya yamutsa trying to adjust and in just 3 minutes Anas ya fad’a bacci, baccin daya jima beyi ba in a lifetime.
_7 hours later_
Daidai 8:30PM Anas ya tashi, ko sallan la’asar, maghrib da Isha beyi ba duk yini yayi yana bacci. “Holy shit!” Ya fad’i. Sede kuma kap ya nemi problems nasa ya rasa, da yayi niyan bare sake shan syrup d’inba amman dan yadda ya masa aiki he can’t resist it. Daidai ya mik’e ze shiga toilet Musty da Abdoul suka shigo da angansu anga wad’anda suka dawo daga party, dan aikinsu kenan. “Ya dude har ka tashi ne?” Musty ya tambayi Anas yana k’ok’arin zama.
“How did you like the syrub? Your problems will all be gone for good two days and after that seka nema ka sake sha, continiously” Abdoul ya ma Anas bayani tare da fad’awa kan gadonsa da baya.
“Great!” Anas ya ce, “I can’t remember any of my problems now saidai nata bacci ko sallan la’asar banyi ba.”
Tsuka Abdoul yaja “yanzu dan kawai yau ka rasa sallolin nan shine wani abu? Kaifa Anas kanada case, wannan blue eyes naka basu taimake ba. Nifa the first time I saw you nad’au American ne kai to seme dan ka share sallolin yau?”
“Tell him bro” cewar Musty. D’an murmushi Anas yayi lallai duk iskancin mutum dubu sun fisa, can a Bama sune ‘yan iskan gari nan kuwa a tafin hannun su Abdoul yake be sauraresu ba yashige toilet yayi alwala yafito ya rama sallolinsa.
Da misalin k’arfe 11:30PM su Musty suka kuma yin wanka suka yi shiri tsaf a yayinda Anas keyin zanen project da aka basu a school. Da suka zo fitane suka juya suka kallesa tare da kad’a kai. “Anas wai kai ko kad’an baraka gwada zuwa clubbing d’innan bane? Wallahi its fun, more fun than wannan jakin project da kakeyi na 5 marks kacal.” Cewar Musty ransa a b’ace.
“No kuje kawai, I have to get this done, maybe next time.” Anas ya sanar dasu yana d’an murmushi.
“Dude listen to him, ko na yau ne kazo muje club d’innan.” Cewar Abdoul. Kai kawai ya kad’a masu bayan sun fice yayi rounding up abinda yakeyi ya kira Ummie bayan sun gaisa yasa ta mik’a ma Angel nasa suka ta hira abinsu. Anas na mutuwan san Amal badan komai ba dan abinda Ummimi ta mata.
Ace yarinya kwanan ta d’aya a duniya amman dan rashin imani tasa a dawo da ita gida ko shayar da ita batayi ba.
_2 days later_
Da misalin k’arfe 12:30PM Anas na kishingid’e kan wata couch (kujera me fad’i da akan iya bacci akai) yana bacci. Ya soma mafarki;
_“Ummimi dan Allah karki tafi kiyi hak’uri indan plates dana fasa ne I promise baran sake ba. Ummimi I am sorry dan Allah karki tafi. Abuu ka hana Ummimi tafiya dan Allah kace mata I will be a good boy from now on.”_
_“Yanzu Aysha bara kiji tausayin yaranki ki hak’ura ki zauna dasu ba. Kalli yadda suke kuka fa?_
_“Mstww wannan kuma ku ya shafa nagaji da zama cikin talaucin nan, ace kullum se atashi ba’a san me za’a karya dashi ba gaskia nagaji daman tun farko sanda Abba na yace kar in aureka matsiyaci ne kai amman nak’i sauraronsa. Ga can miji Allah yamin har k’asar waje ze kaini saboda haka ban ga abinda zesa in cigaba da zama a wannan gidan ba.” Jakarta ta ja ta soma tafiya da sauri naje na kama k’afarta ina kuka ina rok’arta wani wawan ball tayi dani da k’afa sanda na ji ciwo a elbow na...”_
“UMMIMI!” Anas ya kira da k’arfi a yayinda ya farka daga baccin dayakeyi duk zufa yakeyi se nishi yake da k’arfi ganin mafarki yake yasa hankalinsa yad’an kwanta. Wani erin mahaukacin bacci yakeji saboda jiya kwana sukayi a studio amman saboda duk sanda ya rufe idansa mafarkin Ummimi yake yasa ya kasa baccin abu d’aya ne yasan inyasha ze gusar masa da problems nasa which is syrup na problem reliever (giya) da Abdoul ya basa ranan.
Kash! Saidai basu gida sun fita yawo gashi bacci yakeji. Gwada jirarsu yayi na ‘yan mintuna ganin basu dawo ba yasa ya kira sa a waya kai tsaye ya tambayesa ina yake ajiye syrup daya basa ranan yana san sake sha. Dad’i sosai Abdoul yaji finally Anas is ready to change, bayanin ina yake ajiye wa ya masa yakuma tabbatar masa in zasu dawo gida ze sake siyowa tunda wanda ya rage kad’an ne.
Exactly inda Abdoul yamasa kwatance yasamu syrup d’in bud’e sabon kwalb’a yayi yakafa a baki sanda yashanye tas, ko cikakken minti biyu beyi ba yasoma jin bacci me nauyin gaske tsalle kawai yayi ya fad’a kan gadonsa yasoma wani erin mahaukacin bacci me uban nauyin gaske
*© miemiebee*
No comments:
Post a Comment