Friday, 6 April 2018

RANA D'AYA

   BY MIEMIEBEE

PAGE 03



_How can I turn you guys down when the love and devotion speaks this much??šŸ˜©šŸ˜ Yanzu haka kuka k'i yarda a cigaba da posting RANA D'AYA after Ramadan😩 kaman maita harda masu cewa koda sau d'aya a sati ne šŸ˜‚ nida mutane na se Allah but know that ina alfahari daku sosai sosai wallahišŸ’–. Though my schedule is tight, I'll still manage and squeeze time to type once in a week like you guys requested before Ramadan approaches, so here is chapter three. Juma'ah zuwa juma'ah zakuna samun post in shaa Allah, happy reading!ā¤ļø_



     Ta kai ga yankan lungun gidansu kenan sega Mami tafito sanye da mayafi "Ina zaki Mami?" Tayi saurin tambaya "Maggi zan siyo nan shagon Usmanu ashe ya k'are ban sani ba gashi har miya ya kusa nuna. Kiyi sauri kije ki kula min dashi dama na rage ichen seki k'ara" Mami ta sanar da ita.

    "Toh Mami ki dawo lafiya" ta amsata, da k'ingishinta ta shiga takawa amman ta tsaya chak sanadin kiran da Mami tayi mata, hakan yasata kewayowa "Na'am?" Ta amsa.

  "Nace nawa Afzal ya baki ne?" Nan fa oganniyan taku ta shiga kame-kame tana ta6e baki. "Ya haka? Tambaya fa nike miki, nawa ya baki?"

  "Dubu d'aya" ta fad'a chan k'asa-k'asa.

  "Har dubu? Mu gani" ta buk'aceta, nan Amal ta d'ago ta nuna mata. "Yo shine kika tsaya kina rarraba ido kaman 6eran da aka kama yana sata?"

  "Uhnmmm ni zan wuce kar miyan ya k'one" ta fad'a tana dodging had'a ido da Mami tasan tabbas idan suka cigaba da had'a ido Mami na iya gano k'arya take, bata kai ga taka k'afanta ba Mami ta kira sunanta "Baby!" Chak ta tsaya zuciyar ta na har6awa.
   "Na'am?"
  "Juyo ki kallen" saidai ta kasa, seda ta d'au tsawon lokaci sannan ta juyon. "Fad'a min me kikayi? Tabbas babu gaskia a tattare da ke fad'i me kikayi."

  "Mami me kuwa zanyi? Ni shikenan kullum kina cikin zargi na" ta zum6uro baki.

   "Munafuka bazaki bar k'arerayin nan naki da kike tasowa dasu ba ko? Nace fad'a min me kikayi wallahi idan kika bari har Afzal yazo gobe na tambayesa naji gaskiya daga bakinsa jikinki zai gaya miki."

  "Wai duka na zakiyi? Ai Papi baze bar ki ba" da sauri ta buge bakinta tuna Papi bayi gida yayi tafiya.

  "Sam bazan dake kiba amman inada wanda ze daka min ke kaman ganga, Malam Bunu na islamiyyan ku zan kai mai k'arar ki nacewa har yanzu baki daina k'aryan banzan nan ba."

  "A'a don Allah Mami kiyi hak'uri wallahi dorinan shi me baki uku ne na tuba."

   "Yauwa fad'an me kikayi toh."

  "Ki rantse baza kimin komi ba."

  "Sa'ar kice ni? Zaki gayan ne kokuwa?"

 "Mami dan Allah kiyi hak'uri."

  "D'aya" Mami ta shiga k'irge "Biyu-"

   "Zan fad'a zan fad'a" Amal ta katseta a rikice. "Dubu hud'u ya bada shine na miyar masa da sauran saboda kudin abubuwan da suka rage basu kai hakan ba."

   "Oh! Amman 'yar nan anyi wawiya wallahi shi daya k'irga kud'in ya baki besan me yakeyi bane kome? Ai da niyyan kyautatawa ya bada."

   "Toh-" ta fara magana.

  "Rufa min baki da Allah!" Mami ta katseta cike da takaici "Yanzu fisabilillahi Allah ya kawo mana arziki har gida ki miyar da hannun kyauta baya Baby? Meye muke dashi da zaki miyar masa da d'umbun kud'i haka iyye?" Don takaici Mami ji take kaman ta mauje ta, tana gwada yunk'urin hakan kuwa Amal tasa ihu gashi ba halin gudu k'afarta baze barta ba, dan tausayi de kawai Mami ta barta. "Shin ya amshi kud'in yanzu?"

  "Eh mana tun yaushe ma."

  "K'arya kike nace k'arya kike. Fa bazan haifeki ki tsaya kina raina min hankali ba nace ya amshi kud'in da kika miyar masa ko ya?"

  "Ya kar6a..." hannu Mami ta d'aga kaman zata doketa "Nace ya kar6a ko be kar6a ba?" Zata kuma wani k'aryan Mami tayi kaman zata sauk'e mata mari, tuni ta shiga bada asalin rahoton "Wallahi be kar6a ba k'arya nakeyi."

   "Nasan za ayi hakan ai, ki kiyaye nifa Baby! Ki kiyayeni ina fad'a miki wallahi ranan da nace zan tarke ki a lungu bazaki ji dadi ba. Yanzu ina kud'in tunda kince be amsa ba?"

   Chan k'asa-k'asa tana me zum6uro baki tace "Na yasar mai a k'asa da yak'i kar6a."

  "Kud'in kika yasar?!" Tas kukejin sauqan mari a bayan Amal daya sata sakan wani irin rikicaccen ihu bawai don marin yayi zafin da zaisa ta yin kalan ihun bane sai don shagwa6a irin nata. "Amman yau na tabbata kina da ciwon hauka maza wuce muje ki ibo kud'in kuma Allah yasa muje har 'yan tsince-tsince sun d'auke kiga abinda zan gwada miki a gidan nan yau, dama gashi Papin ki bayi nan balle ya shiga miki." Kukan munafurci kaman yadda ta saba ta shiga yi tana me maquro d'an k'wallan daya ciko mata a ido. Haka Mami ta sata gaba da k'ingishin nata suka k'arisa dai-dai spot d'inda abin ya faru wanda a dai-dai lokacin wasu almajirai suke k'ok'arin d'iban kud'in wani ihu Mami tasa "Karku ta6a zaku 6ace" ai kafin tace pim ta nemi yaran ta rasa tasan sarai idan ba hakan tace ba kwashe kud'in zasuyi su gudu su barta da innalillahi. Da sauri taje ta tattara dubu ukun cus ta k'irga, wani hamdala ta saki sannan ta amshe na hannun Amal dake faman murza idonta tun d'azun. "Maza wuce gida kuma Allah yasa miyan ya k'one kiga abinda zan miki."

  "Toh ni Allah ne da zan hana miyan k'onewa?" Ta tambaya tana zum6uro baki.

  "Zan buge bakin nan fah" da sauri ta sa hannu ta toshe bakin nata kafin hannun Mami yayi landing a kai "Maras kunya kawai wuce gida saura kuma ki tsaya hira da Azee a hanya kiga abinda zan gwada miki mutum se shegen almubazaranci." Tana kaiwa nan ta yanki kwanan shagon Usama, itama Amal a hankali ta shiga takawa da k'ingishin har ta isa gida.

   Saidai wani hanzari ba gudu ba, takai gab da shiga ciki kenan sega k'awarta Azee wacce Mami ta ja mata kunne akanta, se ince kusan rashin jinsu d'aya saidai kawai ita Azee a gaban Babanta take hakan yasa tafi Amal jin tsoron ido da bakin mutum unlike Amal.

  "K'awas ya na ganki da bandeji waine a k'afa?" Tayi saurin tambaya tana doso ta, idonta na akan k'afan Amal.

   "Hmm kede K'awa bari kawai wani reckless bawan Allah yau Allah ya had'ani dashi, ina zaman zama na yayo kaina da mota ya bigeni."

  "Subhanallah shine baki sanar dani ba? Sannu ya k'afan toh?" Nan suka hau hira Amal ko gabad'aya ta mance da miyan da Mami tace ta kula dashi.



****       *****        ******       *******

   Isan Afzal gida keda wuya as tun da ya hau tuk'in yake tunanin abinda Amal tayi masa, tafasa ransa yake sosai tabbas baze bari ta gudu unpunished for what she did ba, komin ji da dad'ewa seya rama. She wants to play games? Then she got it. Yana isa gaban wata makekiyar gida da bature ke kira da mansion ya yanki corner inda ya tsaya dai-dai gaban fancy iron gate d'in. Securities biyu ne masu uniform tsaye a bakin k'ofan suna gadi, sannu da zuwa suka mar sannan suka bud'e gate d'in. Tafiya kad'an yayi ya kuma cin karo da wani iron gate d'in nan ma securities biyu ke guarding wajen bayan sun mar sannu da zuwa suka bud'e masa giving him a safe passage. Tafiya yake through the driveway a hankali exploring the beauty of the mansion. A sannu a sannu ya k'arisa last parking lot meh glassy display sannan yasa motarsa ciki ya yi parking ya fito. Makekiyar flat da me bada labari bata san daga ina zata soma labarta saba Afzal ya wuce ciki. Sashin fari ya shiga wanda ko ba a sanar da mutum ba zai san na mai gidan ne wato Abbansa. Knocking yayi bisa entrance door d'in sannan ya bud'e tare da sa kai. Makekiyar parlour ne da aka k'ayatasa da abubuwa masu tsada masu d'aukan hankalin d'an Adam. Komi aciki white, golden and red ne banda cinema'n dake manne jikin bango, ga ko ina tsaf ko dust baka gani illa k'amshin turaren wutan dake tashi.

   "Sannu da zuwa Prince" wani na miji dake sanye da uniform ya fad'a yana doso Afzal da yayi zaune bisa one of the various golden X red royal chairs.

   "Thank you Abba na gida?" Ya tambayesa.

  "Eh yana d'akinsa" ya basa amsa a takaice.

  "Good, help me speak with him please."

  "Yes sir" ya amsa. Da fad'an haka ya juya ya shiga ciki ta wani k'ofa, yakai tsawon minti biyu sannan ya dawo. "I'm sorry amma kaman Master bai da shirin ganinka" mutumin ya sanar dashi. Dama Afzal yasan za'ayi hakan ba kowa yake blaming ba illa Amal ji yake kaman idan ya kamata karya saketa se ta daina numfashi, 'yar gudun hijira kawai ya furta a ransa. "Please tell him I'm sorry yayi hak'uri ya fito" ya fad'a da damuwa karara bayyane a fuskansa.

  "I did amman baida niyyan fitowan ne, yak'i nakega idan Hajiya tamar magana zai sauk'o, I'm sorry excuse me" daga fad'in haka yayi kan dining table inda ya cigaba da goge-gogen da yakeyi. Ganin fa zaman da yakeyi a gun baze haifar masa da komi ba ya miqe ya fita. Side na Ummi ya nufa direct don neman taimakonta. Kaman kullum seda ya ciro hanky daga aljihunsa ya toshe hancinsa sannan ya k'arisa ciki. Ko bai tambaya ba yasan yau ma da akwai hayak'in kullum d'innan, anayin abu dai-dai amman ita Ummi idan batayi over ba bata jin dad'i. Site nata kullum yana cikin hayak'i da k'amshin turaren wuta. Had'add'en parlourn ta daya k'unshi combination na white, dark and light purple ya wuce making it to her room. Knocking yayi bayan ta amsa da 'yes' ya bud'e ya shiga, miqe akan gado da zani d'aure a k'irjinta ya tarar da ita tayi ruf da ciki a yayinda 'yan mata biyu ke mata tausa, hayaqin d'akin is indescribable ba shakka yau d'inma gyaran jiki ake mata. Shi yarasa amfanin wannan abu, shin ta gyara jikin nata takai ina? Abba deh ba saurayi bane yanzu haka zalika itama ba budurwa bace. Murmushi kad'an ya saki tuna reaction nata anytime idan yace mata ita ba yarinya bace yanzu ta tsufa. Shi de ya rasa ta ina ta zama yarinya, mutumin da ya kusan approaching 50 kam ai ya manyanta. "Waye ne?" Ta tambaya kasancewar kanta na facing opposite direction na k'ofar. Kafin Afzal ya amsa 'yan mata biyun suka rigasa "Prince ne."

  "Oyoyo My Prince" ta fad'a tana k'ok'arin zama a yayinda 'yan mata biyun dake kanta suka ja gefe "Sannu da dawowa Prince" kai kawai ya musu nodding.

  "Toh kuma kayi tsaye gun ka k'ariso ciki mana" Ummi ta fad'a tana janyo mayafi tare da lullu6e jikinta. Kyakkyawar mace ce me uban kyawun jiki wanda idan ba wai an fad'i shekarunta bane mutum baze ta6a sanin takai hamsin ba kaman yadda Afzal ya fad'a. Irin skin nata ake kira da kalan wankan tarwad'a gashi kuwa daya samu gyara se wani glowing yake like gold, ga k'iban nan tubarkallah nama du sun nannad'u a wuya. Kallo d'ai za ayi mata asan matar alhaji ce.

   Tana da kyau sosai haka Afzal ma amman abun mamaki sam mutum baze ce mahaifiyar sa ceba saboda rashin kaman su, sam kyawunsu be zo d'aya ba. Afzal yafita haske sosai wasu sukan ce mar fari ma, ita kuwa tafi sa dala-dalan idanu da kuma dogon hanci. Hancinsa na nan shiba dogo ba shiba gajere ba gashi nan de k'arami acikin oval shaped face nasa.

     Da hannunsa yayi mata nuni cewa hayak'in d'akin is unconducive ya mar yawa.

  "Kai deh da ace kanada asthma da turaren wutan gabad'aya zaka hanamu yi a gidan nan toh ya akayi?"

  "Ummi please mana! I want to talk to you" ya fad'a tare da had'e giransa, hancinsa kuwa har a yanzun na toshe da handkerchief.

  "Toh ya kakeson inyi? Bawai kaman ina da k'arfin koran hayak'in nan a lokaci guda bane."

  "Toh kizo muje parlour concentration d'in is less a chan."

  "Halan baka ka gyaran jiki ake yimin ba."

  "Fisabilillahi kullum gyaran jiki, gyaran jiki ko amarya albarka" har anan be sauk'e hanky'n daya toshe hancinsa dashi ba.

  "Jimin d'a!" Tayi exclaiming full of wonder. "Da meye ce inba amaryar ba? Naga da gyaran jikin ne na iya na karkato da hankalin Abbanka kaga har yau bemun kishiya ba."

  "Toh whatever ni ki fito muyi magana."

  "Wai me ne da bazaka iya fad'ansa daga bakin k'ofar ba? Aure zakayi? Kuma ka bar min k'ofa a bud'e tun d'azu ko bakasan hayak'in fita yake ba?"

  "Exactly ki fito muje parlour" ganin batada niyyan motsawa yace da 'yan matan suyi excusing nasu ba gardama suka fita suka basu waje, ita de Ummi binsa da kallo kawai take ko mey yake da shirin yi? K'arisowa cikin d'akin yayi da dogayen k'afafunsa tare da tsayuwa dab a gabanta sannan ya shiga janta. "Ummi dan Allah ki tashi kin de san kina da nauyi."

  "God help me" ta fad'a sannan ta miqe suka fito parlourn inda suka zauna akan two seater side-to-side. "What is it?" Ta tambayesa.

  "It's Abba he's mad at me" ya fad'a a takaice.

   "Toh kuma har wani sabon abu ne wannan? Kade san Abbanka da zafin fushi da zuciya sekace kai anan."

  "Ummi please!" Ya fad'a tare da buga k'afansa a k'asa.

  "Okay, okay toh meh dalilin?" Labarin duk abinda ya faru ya bata be bar komi ba. Numfasa tayi bayan da ta gama sauraronsa tace, "Toh Allah kiyaye aukuwan na gaba amman meyasa ba ka sanar dashi abinda ya farun ba?"

   "Yak'i ma ya saurareni kashe wayan yayi gabad'aya kuma yanzu ma daga site nasa nake, nasa Micheal ya mar magana still yak'i fitowa."

  "Toh ni yanzu me kakeso in maka?"

  "Like what a question" ya fad'a tare da juya idanunsa da suke nan farare k'al. "Kiyi mishi magana of course, he always listens to you."

   "Nifa banason kana jawo ni cikin matsalarku haka kawai kazo kasa nima yak'i cin abincina na sati."

  "Ummi please kinsan Abba be iya yin fushi da mutum ba yanzu ba k'aramin aikin sa neba ya daina min magana for a whole week!"

   "Toh ai nima abinda nake gudu kenan kar yabar cin abincina na sati."

   "Toh yau aka fara hakan ne?" Ma ta 6ata mar rai. Ai da k'yar idan Abba ya ta6a jera watanni biyu yana cin abincin Ummi ba tare da yayi fushi ba. Haka yake da an 6ata mar rai seya d'aga k'afa wa mutum, abun takaicin kuwa shine se ya nemi abinda zai fi damun mutum sannan yayi using nasa against that person. Se kuma shi gado ba gwaninta ba, shima Afzal haka yake da shegen zuciya da fushin nan irin na Abbansa ko fad'a sukayi da Ummi seya d'aga k'afa daga cin abincinta da kuma yi mata magana in banda gaisuwa ba abinda ke had'asu har se ya sauqo, shima gaisuwan don ya zamo masa dole ne. Abinda ke bawa Ummi mamaki shine bayan shi kansa Afzal d'in ya iya ma mutane fushi meye a ciki don Abbansa yayi masa?

   "Aww abinda zaka ce kenan? Ashe dai ba dad'i, ashe idan aka maka haka bazaka ji dad'i ba amman kake ma mutane, ai halin Abban naka da kai seku ta fama kaga barin je in k'arisa gyaran jikin nan yau Abbanka yace zamu fita date kaga ko zama be kama ni ba."

 "Ummi please talk to him ni wallahi abinda yasa hankalina ya tashi ma saboda yace akwai abinda yake son sanar dani ne kuma daga yadda yake maganar nasan magana ce me muhimmanci."

  "Oh! Dam-" se kuma tayi shiru tuna yadda Abba ya jaddada mata cewa no matter what kan kar ta kuskura ta sanar da Afzal halin da ake ciki yafi son ya mar maganan da kansa.

  "Dama meh?" Yayi saurin tambayarta.

  "Babu bance komai ba bari in shiga daga ciki." Kafin ta kai ga miqewa Afzal ya rik'o hannunta restricting her. "Ya haka Prince?"

  "Ummi there is something you're not telling me" ya fad'a yana mata kallon cikin ido don tabbatar da abinda ya fad'a.

  "Kai de da assumption se a hankali ni nace wani abu ne? Sakeni du Allah."

  "Ummi please tell me mene Abba keson sanar dani?"

  "Wallahi prince seda Abbanka ya ja min kunne kar na fad'a maka don't worry he is planning on telling you himself."

  "Taya ze fad'an bayan yamin fushi?"

  "Toh ka kwantar da hankalinka zan masa magana, zan mishi bayanin komai anjima idan mun fita in shaa Allah ze sauk'o kar ka damu kaji my handsome Baby?" Ta k'are zancen tare da aza hannunta akan ha6ansa tana mai wasa sekace wani jariri. Hannun nata ya cire yana zum6uro baki ashe de shima ya iya shagwa6an shine yake ma Amal kallon bakwai saura kwata don itama tayi wa Maminta bayan gashi babba dashi shima yana yi.

   "Oww had'a min rai zakayi? Shikenan sena fasa basa hak'urin" ta fad'a da gan-gam.

   "A'a please don't ni ba 6ata miki rai nake ba" yasa murmushin dole. Murmushin ta mayar masa tare da pecking nasa a kumatu "An kai maka abincinka a site naka ko zakaci anan?"

  "Nah am full" yayi maganan yana aza hannunsa kan flat muscled abdomen nashi.

  "Toh sallah fa kayi?"

 "Zanyi idan na shiga" ya fad'a tare da miqewa.

  "Alright I love you."

  "I love you too" ya amsa sannan ya kama hanya ya fita tare da nufan site nasa wanda shi kuma kominsa is in black and white. Abinda ya kama daga parlournsa, dining table, d'aki, closet, toilet and bathroom. Kitchen ne kawai pure white. Bathroom ya fad'a yayi alwala sannan yayi sallah ya rage kayan jikinsa tare da barin shorts da singlet zalla. Akan gado ya miqe tare da k'ure AC'n d'akin, ragowan aikin daya rage mar a office yakeson k'arisawa amman ji yayi ya gaji gabad'aya ko d'aga yatsa bazai iya ba don haka ya jawo wayansa daga kan side table tare da shiga Twitter inda ya shiga bin feeds nasa, yana gamawa dashi ya shiga Instagram se Snapchat, k'arshe ya leqa whatsapp wanda daga nan bacci yayi awon gaba dashi.

   \•\•\•\•\ A cikin City star.

    Zaune Abba da Ummi suke a filin da Abba yayi reserving musu. Ummi ansha kyau kaman ba gobe se k'amshi take. Tana sanye ne da royal blue lace me torches d'in yellow wanda ko ba'a fad'a ba mutum na sani kaya ne me bala'in tsada ga wani arnen d'inkin da akayi mishi wanda ya mugun kar6arta. "Kin ganki kuwa Baby? You're looking so takeaway" Abba dake sanye da sky blue half jamper ya sanar da ita yana mey mata murmushin sosa zuciya.

  "Kai My Dear kai de bazaka dena flattering d'ina ba ko?" Ta fad'a cike da kunya tana blushing.

  "Ai kema kin san gaskia nake fad'i gashi har yanzu koda wasa 'yan matan waje sun kasa kawar min da hankali daga gareki, ba don komi ba kuwa se don wannan kwalliya, gyaran jiki da son k'amshin naki, keep it up."

  "Kai My Dear toh nagode in shaa Allahu kuma zan cigaba, amman kaima bakaga yadda kayi kyau bafa ai nasha fad'a maka half jumper suna ma kyau kak'i ji na."

  "Na gano hakan nima yanzu shiyasa kika ga na sanya yau." Hira jifa-jifa suka cigaba dayi har izuwa lokacin da orders nasu suka iso. Cike da k'asaita suka shiga ci suna hirar jifa-jifan har yanzu. Sun kusa gamawa Ummi tayi gyaran murya "My Dear?"

  "Na'am?" ya amsa tare da d'ago kansa yana kallonta cike da soyayya sai kace yau ya soma sata acikin idanunsa.

  "D'azu Prince yazo ya sameni" ta tsaya deliberately don jin mey zaice. Shi kuwa tunda yaji ta ambaci 'Prince' yaji yayi losing appetite nasa ma gabad'aya. "Ya da tura plate naka gefe kuma My Dear? Kode na fad'a wani abu ne?" Tayi saurin tambaya.

  "Na k'oshi" ya fad'a yana kawar da kansa yana me kallon gefe.

  "Dan Allah kayi hak'uri nayi shiru barin sake cewa komi ba amman ci abincin kasan banason kana kwana da yunwa yi hak'uri" ta hau lalashinsa, cike da dabara ta mayar masa da plate d'in gabansa da k'yar ya yarda ya cigaba da ci seda ta tabbata ya k'oshi sannan tace, "My Dear kamar hak'uri don Allah Prince yaro ne kuma fushinka a gareshi babban tashin hankali ne wallahi, baka ga yadda ya shigo site d'ina ba d'azu cike da tashin hankali bayan yayi ma Micheal magana daya maka sallama kak'i fitowa dan Allah ka sassauta masa."

   "Hmm Hajiya Mariam kenan, shin ya sanar dake abinda yayi min?" Ya tambayeta "Ya fad'a miki sau biyu ina kiransa bai d'agawa? Bayan da na samu ya d'aga kuma yace min meeting suke inyi hak'uri and I agreed saboda Prince be cika min k'arya ba sede inyi ma yaro jiran duniya da Baban yarinyan nan amman yak'i zuwa, wannan abin kunyan dame yayi kama? Haka mutumin nan ya gaji da jira ya tafi."

   "Bance yayi dai-dai ba amman da kayi mar uzuri My Dear accident yayi encountering wanda daba don Allah ya tsagaita ba da sede a kiraka ace maka kazo ka d'au gawan d'anka."

  "Haka yace miki?"

  "Yes My Dear and ba k'arya yake ba sanin kanka ne Prince bai cika k'arya ba se idan ta kama so I believed him."

  "Allah kare aukuwan na gaba" kad'ai yace.

  "Ameen ka hak'uran?"

  "Da hak'uri na da rashinsa ai du d'aya ne."

  "Taya ya zamo d'aya kuma My Dear? Idan har ka hak'ura muna isa gida ka kirasa ka mar maganan nan da kakeson yi mar ko ze d'an samu peace of mind please." Murmusawa yayi cike da k'asaita yadda manyan alhazai keyi.

   "Hajiya Mariam you're a blessing to this family, a da kafin in aureki ban zata zan iya sake walwala ba a duniyan nan, na d'au bayan rasuwan Fateemah bazan sake tsintan kaina a cikin kalan farin ciki da walwalan da nake ciki ba a yau saidai tun da akayi mana aure kika canza dukannin wad'annan abubuwa.  Ke ce sanadin duk wani walwala da farin ciki da nida d'a na muke ciki a yau, you mended my broken heart. Hajiya Mariam bakida burin dayafi kiga our family stays together and happy yau nasan duk inda Fateemah (asalin mahaifiyar Afzal, yar Mariam wacce suke uwa d'aya una d'aya. Ta rasu ne bayan sunan Afzal da kwana biyu sanadin breast cancer) take tana alfahari dake, kin so Prince tamkar d'an da kika haifa."

   "Dear kenan" ta murmusa cike da jin dad'in wannan kalamai daga bakin masoyinta. "Ai d'an 'yar uwata tamkar d'a na yake so kadena min godiya banida kaman ka da Prince a duniyan nan. Kuma a kullum ina godewa Allah daya bani ikon farinta maka da Prince, addu'a na kuwa baifin Allah hore mana dogon rai mai albarka in cigaba da kula daku ita kuma marigayiya Allah ya cigaba da kai Rahama kabarin ta."

   "Ameen Hajiya Mariam ta" ya amsa a yayinda memories da sukayi sharing da marigayiya suka shiga dawo masa.

  "Zaka mar maganan idan mun koma?"

  "Queen d'ina ta sa baki ai dole na."

  "Kai amma naji dad'i a ringa ma Prince sassauci please kasan yaro ne."

  "Ke kuma ki cigaba da shagaltasa  kinji ba?" Dariya kalan na manyan mata ta saki sannan ta zuk'e cocktail drink da take rik'e dashi. Hira kad'an suka ta6a sannan driver ya dawo dasu gida. Waya Abba yama Afzal akan yazo ya samesa a site nasa yanzu, alokacin Afzal na zaune a parlour yana playing game. Take ya kashe ya mik'e tare da zira farar jallabiyansa daya rataya jikin hanger sannan ya fito. Knocking yayi aka amsa sannan ya shiga, Abba da Ummi ya tarar akan two seater suna zaune looking so takeaway da alama yanzu dawowansu. Besan ya rayuwarsa zata kasance ba without these two: they simply complete him and he loves them so much. K'arisawa yayi ya durk'usa a k'asa tare da gaishe da Abba cike da ladabi da kuma yiwa Ummi sannu da dawowa.


   RANA D'AYA
  #RD
   Love... King_miemiebeešŸ‘„āœØ