BY MIEMIEBEE
PAGE 04
"Ashe abinda ya faru kenan toh Allah kare aukuwan na gaba" fad'in Abba.
"Ameen Abba thank you" ya amsa a nitse. Numfashi me nauyi Abba ya fisga sannan yace, "I'm sorry for my outburst on you, yaci ace na baka dama kayi min bayanin abinda ya faru kafin in yanke hukunci."
"Ba komai Abba ni ya kamata in baka hak'uri I'm sorry in shaa Allah hakan baze k'ara faruwa ba" ya amsa cike da girmamawa da kansa a sunkuye.
"Masha Allah, Dama Alhj Abdallah ne keson ganinka."
Alhj Abdallah? Afzal ya nanata a ransa, wani Alhj Abdallah d'aya? And saboda meh?
"Alhj Abdallah Abban Nazeefah" Abba ya sake fad'a ganin kaman ya jefa d'an nasa cikin duhu.
"Ohh!" yayi exclaiming se yanzu ya fahimci wa Abba ke nufi. Alhj Abdallah Abban Nazeefah wanda ya kasance aminin Abba kuma second neighbour'n su, gida d'aya ne a tsakanin su. "Abba ina fatan lafiya dai ko?" Ya tambaya a takaice.
"Eh toh it depends, kafin nan ina son muyi wata magana da kai Prince shin ka nada tsayayyiya kuwa?" Zuciyarsa yaji ya mugun har6a bade aure Abba ke shirin masa ba don kuwa be shirya ba, sam ba mace d'ayan da ta ta6a yimasa acikin jerin 'yan matan da Allah ke had'asa dasu. To cut the story short, shi baida ko budurwa d'aya ma balle ace ya cire tsayayyiya a cikin su. Ko da yake London karatu 'yan mata ke binsa and not the other way round, kuma koda wasa be ta6a saurara masu ba haka zalika da ya dawo Nigeria ma yanzu, kusan a kullum se 'yan mata sunzo gunshi a office bayan wanda ke binsa har gida. A sanadin hakan ya hana secretary'n shi barin kowa cikin office nasa in ba wanda ya sanar da ita da zuwan su ba.
"Kayi shiru ko kafi son ku tattauna da Umminka ne tukuna?" Fad'in Abba jin shirun yayi yawa.
"A'a Abba ba abin tattaunawa don a gaskiya banida tsayayyiya" ya basa takaicaccen amsa bayan nazarin daya samu yayi.
"Toh Alhamdulillah" Abba ya saki hamdala wanda ya d'aure wa Afzal kai. Meh hakan ke nufi? Kafin ya kawo wani tunanin a ransa Abba ya cigaba, "Dama Alhj Abdallah ne ke tunanin had'a ka da 'yarsa Nazeefah" wani irin mumunan buguwa zuciyan Afzal yayi wanda sanadin hakan yaji zazzafan ciwon kai na neman afka masa.
"Aure fa kenan Abba?" Ya tambaya cike da mamaki.
"Yes Prince aure kuma kaga jifa yazo dai-dai da zama kenan tunda kace baka da tsayayyiya." Holy crap! Ji yayi kaman ya kashe kansa domin haushi, meyasa bema Abba k'arya yace mar da akwai tsayayyiyar ba a farko? But he can't blame himself saboda baida masaniya akan wannan zance Abba ke shirin sanar dashi. In da kuma k'aryan yayi yace yanada tsayayyiyar and Abba ya buk'acesa da yayi introducing nata ya zeyi? Meyasa Ummi bata sanar dashi wannan ne maganar da Abba ke shirin sanar dashi ba? Nazeefah fah? Wancan fand'ararriyar yarinyan da sama da friends nasa uku sunyi dating nata. 'Yar karamar yarinya amman se shegen rawan kai da falli, idan za'a k'irga samarukan cikin Maiduguri masu ji da kansu toh d'add'aiku ne basu fita da ita ba sam batada kamun kai ga d'an banzan rainin da take ji dashi a takaice de ya tsaneta. Meyasa Abba ze yarda da k'udurin abokin nan nasa? Meyasa ze yarda ya bada only son nasa wa 'yar da batada ko kamun kai? He need answers.
"Prince kayi shiru" fad'in Abba sede har yanzu Afzal besan da wani bakin zai soma magana ba couple with the fact that baida ra'ayin aure ko kad'an yanzu. For crying out loud he's just 25 years old ina laifin abar shi yakai koda 30 ne. "Afzal?" Fad'in Abba for second time.
"Nnn... na'am Abba" yayi stuttering.
"Bakace komai ba" ya sake ce dashi.
"Abba bansan me zance ba, Abba yarinyan can batada kamun kai dan Allah kar ka amince da wannan k'udiri" ya fad'a cike da tashin hankali.
"Tabbas ba k'arya acikin zancen ka Prince, Nazeefah tayi zara ta fi k'arfin iyayenta kullum complain da Abbanta ke min kenan. Amman idan ka duba, rashin kamun kan nata ne dalilin da yasa Abban nata ke son aurar da ita so she can change her ways. Sanin kanka ne Alhj Abdallah d'an boko ne aurar da yaro at a very tender age sam baya d'aya daga cikin tsarinsa, dalili ne ya kawo hakan kuma kaf cikin yaran abokansa tare da ni amininsa ba wanda yaga yayi masa ya kuma yaba da hankali da tarbiyyarsa kaman kai Afzal, ka gane amincewa da wannan aure kaman yin jihadi ne. Wata k'il idan akayi mata aure zata canza wannan gur6a66iyar rayuwar data d'au wa kanta" Abba yayi concluding.
"Abba ni kuma fah? Ban shirya yin aure yanzu ba, ban ta6a kawo tunanin aure ba a nan kusa, Abba please don't give me out" ya fad'a a maraice.
"Kayi hak'uri Afzal am not trying to give you out nasan wannan babban abu nake nema daga gareka shiyasa naso muyi maganan as father and son insan meye point of view naka, idan har baka son yarinyar kuma baka tunanin ko a nan gaba zaka ita yin hakan, fine bazan yi maka auran dole ba. Kai kad'ai Allah yabani Afzal and da sani na bazan ta6a yanke hukuncin da zai cutar da kai ba, ina sonka fiye da duk wani mahaluk'i a duniyan nan. Sanin mune nan kaf yarinyan nan Nazeefah bata kai ta cutar da kai ba in kuwa har zatayi hakan toh wallahi bazan ma bari a yi nisa da zancen nan ba. Da tunda mahaifinta ya tunkare ni da maganar zan ja masa layi but we all know bata kai tayi ma wani abun ba. Afzal I've known Alhj Abdallah for a very long time, tun ina masters dina. Da nauyi Afzal in ba haka ba da zan koma in sanar dashi cewa lallai-lallai kai baka amince da wannan k'udiri ba, bazan bari a cutar min da kai ba Afzal. I'll appreciate it if you'll reconsider your decision amman idan har kai kaga you can't find it in your heart to love that girl zanyi iya k'ok'ari na in fahimtar da shi abokin nawa."
A hankali maganganun Abba suke shiga jikin Afzal suna tasiri. Kaman yadda Abba ya nuna cewa rashin halacci ne ga abokinsa idan har bai cika masa wannan buri ba shima Afzal haka yake gani. Gani yake idan har be bawa Abbansa goyin baya ba toh rashin kyautatawa ne why because tun zaman shi da Abba wannan ne karo na farko Abba ke neman abu a gurinshi da ya kuma nuna muhimmancinsa haka. Tabbas auren Nazeefah baze kashe sa ba toh why can't he sacrifice his happiness for his father's??
Ya d'au tsawon lokaci yana nazari amman ya kasa deciding akan komai, ji yayi k'wak'walwarsa ta toshe gabad'aya, a sannu a sannu ya d'ago kansa dake dafe tun d'azu ya shiga magana a hankali "Tabbas k'in amincewa da k'udurin Alhj Abdallah rashin halacci ne a gareka Abba kamar yadda nima rashin baka goyin baya yake rashin kyautatawa a matsayina na d'anka. Moreover, koda ni ne na tsinci kaina a cikin wannan halin da kake ciki I would do thesame" ya tsaya. Sosai Abba yaji dad'in kalamun nan da suke fitowa daga bakin Afzal. A kullum godiyanshi kenan ga Allah na basa d'a mai hankali mai kuma tunani kaman Afzal wanda yake gudun b'acin ransa wane aikata sa6o wa ubangijinsa.
A hankali Afzal ya shiga magana "sai dai-" wanda Abba yayi saurin katse sa a nitse.
"Karka damu Prince ba wai don ka auri yarinyan nan hakan na nufin nan a gaba idan Allah ya had'a ka da wacce kakeso bazaka iya auranta bane wallahi ni ko bayan wata d'aya da auran naku ne ka kawo min wacce kakeso I'll respect your decision in aura maka ita kuma ba abinda Nazeefah ko iyayenta suka isa suyi da hakan, you're a husband to four wives, all I'm asking is kayi hak'uri ka amince da k'udurin mahaifin 'yar nan."
"Abba..." ido Ummi ta masa don haka yayi shiru.
"Ba seka amince right away ba Prince, take as long as you want to make up your mind I shall respect every decision you take fata na kawai zakayi considering wannan situation, kasani k'in amincewar ka ga auran 'yar nan kaman tozartani ne a idon amini na da kuma duk wani mutumin da labarin nan ya iske sa. Kaje na sallameka Allah yima albarka, thank you for your time."
"Toh Abba ameen, seda safe Ummi goodnight" da haka ya miqe ya fice zuwa site nasa inda ya zube a kan gado a yayinda kansa keyi masa wani irin sara, ji yayi komi ya dena tafiya masa a duniyan. Ina ma Allah ze d'au ransa cikin wannan dare (wa iyya zubillah) don komi ya wuce. Ina ma ba a ta6a k'addaro masa da rana irin ta yau ba. Upon all the women out there Nazeefah ze aura? Yarinyar daya tsana fiye da mutuwarsa, fiye da duk wani mahaluk'i a duniyan nan kuma yake da tabbacin itama ta tsanesa as much ba don komai ba kuwa se don tsan-tsan tsana da k'yaman da yake nuna mata a fili, a bayyane a fuskan sa anytime path nasu yayi crossing. God help him. A da har ya fara gyangyad'i kafin kiran Abba amman yanzu baccin nasa ya nema gabad'aya ya rasa ba don komi ba se don tashin hankali. Ido ya zura wa ceiling yana k'ok'arin tattaro hankalinsa, ana cikin haka yajiyo knock a bakin k'ofan d'akinsa se yanzu abin ya fad'o masa ashe beyi locking main k'ofar site nasa ba.
"Come in" ya fad'a cikin wata irin kasalacaccen murya. K'ofan na bud'uwa sega Ummi bayyane a bayansa tana sanye da hijabi tazarce. Kallonta yayi ba tare da yace komai ba har izuwa lokacin da ta k'ariso ciki ta zauna akan gadon ta inda yake kwance. "Prince tashi ka zauna muyi magana" ta buk'ace sa.
"Ummi dan Allah kibari ba yau ba abinda nakeji is already enough for me to handle just leave me alone I'm sorry."
"Haba Prince ya kake magana haka? Taya kake tsammanin zan iya barin d'ana k'walli d'aya tal acikin irin wannan yanayi? Tashi ka zauna kaji Baba na yi hak'uri" da k'yar ta samu ya zauna d'in.
"Gaya min what is going on in your mind me kake tunanin yi yanzu?"
"Ummi I don't know" ya fad'a abin tausayi "Am so confused I don't even know what am feeling" ya k'arasa tamkar zeyi kuka.
"Shikenan ya isa ka kwantar da hankalinka in shaa Allah komai ze tafi kamar yadda kakeso it's just a matter of time."
"Ta yaya Ummi when Abba wants me to desperately marry his friend's daughter? Sanin kanki ne Ummi na tsani Nazeefan nan ko gidan nan ta shigo gaisheki ba k'aunan hakan nake ba yarinyar she's so stubborn."
"Zata gyara in shaa Allah Prince wannan ba komai bane."
"Yanzu Ummi kema kin goyi bayan zancen auren nan kenan?" Ya tambayeta tamkar zeyi kuka.
"Prince da amincewa na da rashin sa duk d'aya ne wallahi one thing am sure is aure bazai auku ba har se idan ka amince kuma har idan baka son yarinyan nan ba wanda ya isa ya saka aurarta."
Kai ya kad'a cike da takaici "Ummi ki dena magana as if ina da choice, kina ganin yanzu idan na ce wa Abba bazan auri yarinyan nan ba komai zai cigaba da gudana a tsakanin mu kaman yadda yake a da? Kina ganin Abba baze yi holding grudge akaina ba nak'in sake min magana har duniya ta nad'e? Kin deji da kunnenki abubuwan da ya irga a parlournsa d'azu that idan har ban amince da wannan aure ba toh kaman neman tona mar asiri nake shirin yi acikin jama'a which I'll never do so to my own father."
"Then you have a choice to make, ka yarda da k'udirin Abban naka kawai."
"It's not that easy Ummi bana son Nazeefah kuma bana tunanin zan ta6a iya sonta wallahi na tsaneta tsana na sosai."
"Ya Salaam!" Tayi exclaiming "Ya kake magana haka sekace ta gaza ta wani fannin ne iyye Prince? Yarinyan nan de kyakkyawa ce masha Allah son kowa k'in wanda ya rasa gata kuma daga babban gida bugu da k'ari ga iyayenta manyan mutane masu k'ima a idon jama'a, kaf garin nan ana darajasu, what else do you need?"
"What else do I need?" Ya tambayeta cike da mamaki "Kamun kai, tarbiyya da kuma mace mai addini which Nazeefah is clearly lacking. Sam bata d'aya daga cikin jerin 'yan matan da zan iya so, bana buk'atan kyawunta da kud'in mahaifin ta cause I have all that, I'm rich and handsome."
Numfasa tayi, "Tabbas ba k'arya acikin maganganun ka Prince addini ma cewa yayi idan na miji zeyi aure abinda ze fara dubawa acikin qualities na matar shine addininta, k'arfin imani kenan, shi arziki da kyau duk a baya suke biyowa."
"Exactly Ummi that's why I need you to please help me, do something wallahi ina cikin tsaka mai wuya."
"Ya kakeson muyi Prince? Wallahi in har da akwai wani alternative da na bima don ka ku6uta daga auren wannan yarinya amman babu, hak'ura zakayi ka aureta don ka farintawa Abbanka rai."
"Ummi ni kuma shikenan kin yarda in jefa kaina acikin k'uncin rayuwa kenan?"
"Come on Prince" ta fad'a tare da kwanto sa a jikinta tana shafa gashin kansa a hankali. "Ba wanda yace don ka auri Nazeefah zaka jefa kanka cikin k'unci, da ikon Allah zaka koyi sonta, Nazeefah is a very loving lady kawai don baka ta6a ware lokaci ka santa bane, batun rashin kamun kai kuma idan kukayi aure zata gyara, karuwai ma akayi musu aure suka shiryu balle ita da kanta ke rawa kad'ai?" D'ago kansa yayi daga jikin nata sannan a raunane yace, "You like her don't you?"
"Prince..."
"Bana sonta Ummi kuma kin san ni idan na tsani abu na tsanesa kenan har abada."
"Kul!" Tayi saurin katsesa "Kar ka kuma cewa haka, ita soyayya ba'a yimata haka, saidai idan baka bud'e mata zuciyarka ba tabbas zata shige, kai deh kawai yanzu kayi k'ok'ari ka bawa Nazeefah chance am sure zaka koyi sonta as time passes by."
"I don't think so" ya kawar da kansa.
"Tell me something Prince" tayi maganan tare da sashi maido da kallonsa a gareta, "Kana da watan da kake so ko ba haka ba?" Bata basa daman yin magana ba ta cigaba "Meyasa baka sanar da Abbanka ba toh? Kaga if only you did da duk hakan bai faru ba."
"Ummi wallahi ba wata ni banida kowa wallahi."
"K'arya kakeyi Prince" ta fad'a tana kallon cikin idanunsa don gaskata abinda ya fad'a.
"Ummi ana wasa da wallahi ne? Wallahi babu" ya kuma jaddada mata.
"Hmmmm" taja nishi cike da k'in yarda "Duk had'add'un kwanukan da ake shigo dasu kusan kullum acikin gidan nan da sunan an kawo wa Prince abinci kace duk cikinsu babu wacce tayi maka?"
"Hmm Ummi kennan" ya fad'a tare da murmusawa kad'an ta gefen lips nasa wanda a sanadin hakan dimple nasa ya lotsa "Har yanzu baki san waye Afzal ba, bakisan kalan macen da zata iya burgesa ba har ta iya sace zuciyansa. Mace mey kunya nakeso, wacce duniya da abinda ke cikinta basu dameta ba, mace wacce take da Haddan Qur'ani koda ace ba duka ba, wacce ta rik'e addini, wacce zataji kunyan kallon cikin idanu na tace min tana so na, wacce zata lullu6e jikinta idan zata fita waje ba wacce take yawo ba d'ankwali balle mayafi akan layi ba, ko kuwa wacce ke zuwa party tana bin maza. Bana k'aunar macen da za'ace kaf cikin lungunan garin nan ta zagaya da mota sekace BOSEPA (kamfanin kwashe bola da dotti) kokuwa wacce take bin maza here and there. Sam macen da ta fad'a acikin jerin wad'annan basa burgeni."
"Toh Afzal na ji ka kuma na gamsu da duk wani abinda ka fad'a kuma kamar yadda Abbanka ya fad'a maka nima hakan zan kuma nanata ma wallahi kade ji rantsuwa ko? At any moment ka bud'i baki kace min Ummi ga wannan inason ta da aure zan sa hannu inga sena cimma maka wannan buri na ganin wannan 'ya ta zamo matarka, kaide abinda nikeso da kai kawai kayi hak'uri ka amince da auren yarinyan nan ku rabu lafiya da mahaifinka."
"Ummi idan kuma banida ra'ayin auren sama da mata biyu fa?"
"Se kayi adapting hakan Prince kokuwa ka bawa Nazeefah chance a zuciyarka and learn to love her those are the only options you have."Dogon numfashi yaja sannan ya sake a hankali, "Thank you" kad'ai yace da ita.
"Zan saka a addu'a ni kuma idan har wannan aure alkhairi ne toh Allah ya tabbatar mana dashi ya bada sa'a ya kuma bada zaman lafiya idan har kuma otherwise ne toh Allah kawar da zancen."
"Shikenan Ummi thank you."
"Bari in baka waje ka kwanta ko? I don't want you to overthink yourself Prince ka kwanta kayi bacci kawai kabar komi a hannun Allah, kad'au wannan aure as k'addaran da Allah ya k'addaro maka don ya auna iya adadin imanin ka kaji?"
"Toh Ummi" ya fad'a a hankali.
"Gobe akwai office ko?"
"Eh" ya amsa blankly.
"Toh Allah ya kaimu sleep tight okay?"
"I will, I love you."
"I love you too" ta fad'a mar tare da pecking nasa a temple sannan ta miqe ta tashi "Ka tashi kayi locking site naka kuma."
"Manta dashi please" ya fad'a chan k'asa-k'asa sannan a fili yace, "Toh I'll follow behind you." Tana fita ya cire jallabiyansa yaja comforter ya kwanta ko k'ofan d'akin nasa ya kasa tashi ya rufe balle na site d'in gabad'aya. Baccin da Ummi tace yayin yikeson yi amman sam ya kasa, tunanin ya cigaba dayi har...
Washegari...
Saboda rashin samun baccin da Afzal be samu yayi ba yasa ko masallacin dake cikin gidansu ya kasa takawa ya fita sabida se daf Asuba nauyayyen bacci ya afka masa, a d'akinsa ya idar da Sallan ya koma kan gado inda ya soma bacci wane gawa totally forgetting ya kamata ya tashi by 6 ya shirya office.
Ba shine ya tashi ba se goma da rabin safe nan ma don rurin da wayansa keyi ne akan bedside drawer. Cike da kasala idonsa a rufe ya miqa hannu ya ja wayan tare da swiping ba tare da ya duba wa ke kira ba, sauk'e wayan yayi akan kunnensa don ko rik'ewa ma baijin zai iya.
"Triple A?" Cewar wanda ya bugo wayan daga d'ayan 6angaren.
"Na'am Sultan?" Ya tambaya wai tsabaragen baccin da yakeji yama kasa tantance muryan aminin nasa. Mutumin da suka kasance tare dashi tun forever, tun kindergarten (nursery school) har ila yau.
"Don't tell me bacci kakeyi har yanzu" Sultan yayi exclaiming cike da mamaki jin gyangyand'in dake tattare da muryan abokin nasa.
"Shhh! Kayi magana a hankali please bacci nakeji" yayi chanting har anan idonsa a rufe.
"You better get your shitty ass up ko ka manta kuna da meeting ne a office naku yau kuma kai zaka wakilta? Yanzu secretary naka ta kirani take cemin she's been trying to reach you but all your lines seem switched off nima if not ina da private numbanka off hand da bansan ya zan iya contacting naka ba."
"F*ck!" yayi growling cike da tashin hankalin a yayinda ya bud'e idanunsa. Gabad'aya ya mance akwai wani abu wai shi office Gosh! Ya zeyi da meeting d'in yanzu? Daman wakiltan Boss nasa zeyi kaman yadda Sultan ya fad'a kasancewar shi manager'n nasu yayi tafiya seya buk'aci Afzal dayake Assistant nasa da ya wakilce shi.
"K'arfe nawa ne don Allah maza?" ya tambaya a gigice, gani yake kaman idan ya tsaya neman position na agogon d'akinsan ma ze 6ata mar lokaci.
"Thirty five minutes pass 10" Sultan yayi stating.
"The f*ck!" Yayi exclaiming a birkice tare da miqewa "I'm late for the meeting already!" Yayi exclaiming "Meyasa baka kirani ba tun d'azu?"
"See you! Wato baka gode bama dana kira ka yanzun?" Ya tambayesa cike da mamaki.
"It makes no difference!" ya amsa a d'an fusace.
"Ba laifinka bane nasan maganinka, ma tsaya meyasa ka makara haka? Tun jiya fa ban sake ji daga gareka ba are you sure all is well with you?"
"Guy alot has happened I'm telling you, yanzu call back my secretary ka tsarata kace mata ciwon ciki ya kamani jiya da daddare kaima yanzu Abba ke sanar da kai."
"A nawa kenan?"
"Come on!"
"Alright se yaushe zaka fito?"
"I dunno yet amman duk abinda akwai zan sanar da kai please call her As Soon As Possible nagode."
"No big deal" ya fad'a tare da katse wayar. Fad'awa kan gadon yayi da bayansa yana mamakin ya akayi ya makara haka yau amman tuna ya kasa bacci daren jiya sai kusan asuba ya kawar da tunanin daga kansa. Se kuma mamakin da yake ace sa6anin kullum be je ya gaishe da Ummi da safe ba kamar yadda ya saba kafin ya fita office amma ko tazo ta duba sa ko lafiya batayi ba? Ba shakka yanzun tana baje kan gado tana bacci. Kai ya kad'a sannan ya miqe ya fad'a bathroom yayi wanka. Yana cikin karyawa a kan dining table ya soma jin hayaniyan Ummi tana magana da wasu, bada dad'ewa ba se gata nan ta shigo tana sanye da nightie nata da babban mayafi akai, da alama yanzu tashinta daga bacci.
"Prince?!" Tayi exclaiming cike da mamaki a iya saninta de Afzal baya wasa da aikin shin toh yau meh ya faru? Mey yakeyi har war hakan a gida yau bayan ba wani public holiday bane?
"Prince lafiya?" Ta kuma tambaya jin be amsata ba.
"Toh Ummi ki shigo mana a bakin k'ofan ne zan gaisheki?" Ya tambaya yana turo light pink lips nasa.
"Shikenan Esther ku tafi" ta sallami masu aikin tare da jawo k'ofan sannan ta k'arisa ciki ta zauna a kujeran dake gefen damansa. "Good morning" ya gaishe ta yana sipping coffeen shi.
"Prince me ya hana ka zuwa office yau?" Ita ko ta kan gaisuwan ma batayi ba, kafin ya samu daman amsata ta shiga auna body tempreturensa k'ila baida lafiya ne tayi tunanin hakan a ranta.
"Ummi please!" Ya fad'a a tak'ure tare da sauk'o da hannunta daga fuskansa. "Am fine I just happened to overslept lokacin dana tashi kuma na makara shiyasa banje office ba" ya bata amsa.
"Ban san ka da haka ba fa Prince nima yanzu tashi na kenan daga bacci mai wanke mota ke sanar dani cewa baiga fitowanka ba haka mai bayin flower ma."
"Yes like I said na makara ne" ya sake jaddada mata.
"Meyasa ka makaran Prince? Tunani ka tsaya yi jiya baka samu ka kwanta ba se yau da Asubah ko?"
"Kusan hakan" ya amsa ta a takaice yana k'ok'arin kai fork daya nannad'e mar fried egg, ketchup da fries a jiki baki.
"Toh ya kake? Ka kira office ka sanar dasu?"
"I did don't worry."
"Yauwa nac-" wayanta daya shiga ringing ne ya katse ta daga fad'in abinda tayi niyya, duba screen d'in tayi taga Abba ke kira wani dad'i ne ya ziyarci zuciyarta. "Kaga Abbanka ke kira bari inyi picking kayi shiru please" ta fad'a eagerly tare da d'agawa.
"Hello Good morning my sunshine" ta fad'a tana kashe murya, wai tsohuwa da rangwad'a. Kad'an ya rage coffeen dake bakin Afzal be bi kansa ba don dariyar data k'eto masa, shikam soyayyan dake tsakanin Abba da Umminsa mamaki yake basa, ace sam basu gajiya da junansu? They've been married for 25 years now amman sekace newly weds a da shima yana tunanin kasancewa da everlasting lover nashi someday but not anymore yanzu da akeson yi masa auren dole da Nazeefah.
Hannu ta mik'a ta mintsine shi, da sauri ya kama hannun nata yana mai cigaba da dariyar da yakeji, murmushi ta saki tana mai miyar da hankalinta akan wayan a yayinda Afzal ya cigaba da wasa da yatsunta wanda ta k'ayatasu da jan lalle yadda larabawan Sudan keyi. Don tsiya irin na Afzal, zoben azurfan dake yatsansa ya zaro yana mey k'ok'arin sanyawa a nata yatsan bayan sarai yasan koda Kudu da Arewa za'a had'a ba shiga zoben zeyi ba, badon komi ba kuwa se don girman size na yatsan Ummi d'aya yana matsayin na Afzal d'aya da rabi in beyi biyu ba ma kenan. Ita de bata san yaushe Afzal ze daina mocking k'ibarta ba yabarta tasha iska bTaga bawani k'iban azo a gani take dashi, k'iba ne wanda yawancin matan alhazan nan keda, kuma koda tayi k'atuwa dayawa kaman yadda yake fad'in ma taga haka baby'n ta yake sonta like die ina ruwanshi?
"Toh My Dear zan sanar dashi sede gashi yau ko ganin ka banyi ba tun bayan Asubah, ka kama ka fita ba tare da ka sanar dani ba."
"Yi hak'uri My Queen bacci kike so peacefully banso in ta dake ba but I'm sorry na kusa dawowa ayimin kwalliya me kyau" Abba ya fad'a daga d'ayan 6angaren wanda hakan yasa Afzal dake ta sauraron wayan nasu tun d'azu murmusawa.
"An gama My Dear a dawo lafiya I love you."
"I love you too" yace mata sannan ta katse wayan tare da ajiyewa akan table tana wani murmushin jin dad'i kamar yadda ta sabayi anytime sukayi waya da Abba.
"Toh murmushin ya isa haka mey Abba yace ki sanar dani?"
"Prince fa ni ba kakar ka bace tam!" Ta fad'a tana nuna mar 'yar yatsarta wanda hakan ya sasa dariya ba shiri.
"Haba Queen d'in Abba na, my only Queen also."
"Noi!" Ta fad'a tana turesa da hannunta "Ni d'ince Queen taka? A yau ka samu macen da kakeso nasan mancewa zakayi dani so ba seka min zaqin baki ba ka zolayeni."
"LOL" ya murmusa sosai wanda hakan ya sake fiddo da kyawunsa da fararen hak'waransa da suke nan kaman shi ya jerasu. "Ummi kenan believe it or not you'll always and forever be my Queen banida kamarki Ummi I love you so much" ya k'are maganan tare da placing mata peck a hannu.
"I love you more my Prince so Abbanka yace in sanar da kai cewa yana son yi maka magana."
"Again?" Ya tambaya restlessly "Bade wani auren yakeson sake yimin ba ko?" Dariya comment nasa ya bata don haka ta tsaya yi "Ko kad'an Prince ai ban bari ayi maka haka."
"Toh meneh?"
"Kaji Prince da wani tambaya taya kake tsammanin zan san me yake son sanar da kai?"
"Bawani fad'i gaskiya de Ummi yau ma yace karki sanar dani ne."
"Allah ban sani ba Prince kaji na rantse."
"Toh shikenan Allah dawo dashi lafiya."
"Ameen bari inje inyi wanka nima kar Abbanka yazo ya ganni ahaka."
"Aje a sha k'amshi deh, k'amshin da baya k'arewa ba" ya fad'a cike da gatsine.
"Naji" ta amsa tare da tureshi da kafad'a a yayinda ta miqe.
"Ki turo d'aya daga cikin maids d'innan su share min site please."
"Toh Prince" da fad'in haka ta fice. Breakfast nasa ya k'arisa ya hau latsa wayansa har izuwa lokacin da Abba ya dawo ya tura Micheal da ya kira sa.
RANA D'AYA
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
No comments:
Post a Comment