Tuesday, 27 December 2016

‘YAR GATA CE!

BY MIEMIEBEE
PAGE 24

  *December, 2016*



    Tsaye Mama da Baba suke a corridor’n k’ofan da Zeezee ke ciki, kallo d’aya za’ayi musu asan suna cikin babban tashin hankali sam sun kasa zama gu d’aya se safa da marwah suke wajen. Ana cikin haka k’ofan d’akintan ya bud’u, kusan da gudu su Mama suka nufi gun “Dr. How is she?” Sukayi tambayan in unison.
  “You two must be her parents, am I right?”
  “Yes” Baba ya amsa a yayinda Mama ta gyad’a kai.
  “Karku damu she is in a stable condition, alhamdulillah bataji wani ciwo ba kanta kawai tad’an fasa ta gefe wanda a sanadin haka glass ya samu ya shiga amman mun cire har anyi d’inki yanzu haka ma zaku iya shiga ganinta.”
  “Alhamdulillah” kawai ke tashi wajen “mutumin data bigen fah?” Baba ya tambaya.
   “Eh an kawo min report nasa d’azu, kariya biyu ya samu a k’afa seda gefen kansa daya fashe shima bayan nan alhamdulillah.”
   “Toh alhamdulillah mun gode Dr. Bari mu duba ‘yar tamu.”
  “Excuse me” yana kaiwa nan ya basu waje. D’akin sukayi rushing kwance suka tarar da Zeezee kan gado ta rik’e gefen kanta da hannu “sannu k’anwata sannu” Baba yayi maganan yana dafe kafad’arta.
  “Sannu Zeezee how are you feeling?” asked Mama. Kuka tasa musu, da k’yar suka samu tayi shiru “Baba kaina ciwo.”
  “Ai dole ne dama Zeezee mugode wa Allah ma anan abin ya tsaya beyi gaba ba.”
  “Baba mutumin dana bigen fah? Ya mutu?”
  “A’a yana raye be mutu ba.”
  “Alhamdulillah” tace.
  “Hmm aini shiyasa ban goyi bayan wannan motar da aka siya mikin ba, yanzu da tsohon ya mutu azumi sittin (60) ya hau kanki, kai kuma inhar danginsa suka k’i yarda seka biya diyya, duk wannan wani irin tashin hankali ne?”
  “Qaddara bata wuce ranarta Hafsah, koni nan zan iya yin hatsari nakai mutum lahira, bawai zancen dan Zeezee is too young to drive bane.”
  “Ai dama kai bazaka tab’a shiryuwa ba inba wai kuka da hawaye Zeezee ta saka ba.”
  “Toh ya isa, yarinya batada lafiya ba suratai yakamata muyi ta mata akai ba, godiya wa Allah ya kamata muyi tunda anan Allah ya tsaida qaddaran. Sannu ko K’anwata kina jin yunwa?”
  “A’a ni akaini gida banason zaman nan.”
  “Karki damu bari jikinki yayi k’arfi.”

   ★*★*★*★
    5 days Zeezee tayi a asibiti akayi discharging nata. Kusan duk friends nata including Adeel sunzo sun gaisheta, shida Lubiee kanma kusan kullum suna kanta. 2 weeks ya d’auketa kafin nan ta warke gabad’aya, bada jimawa ba suka fara neco. Motarta kuwa tuni Baba yakai aka gyara mata yadawo sabo k’al ba kalan jan kunnen da Mama bata mai ba kan yabari se in sun gama makarantar yaso ya gyara mata amman inaa yak’i. Zeezee kuwa ko bayan incident d’in bata shiryu tabar speeding kan hanya ba, ana gama paper zata tara su Lubiee and others su fita yawo. Ranar da suka yi Geography Adeel yazo school ya d’auketa daga school bayan sunci abinci a Mr. Biggs suka wuce chan bayan gari ya nemi waje yayi parking se hirarsu suke sha gwanin sha’awa. Wayarta ya d’aga yayi entering sunansa as password sannan ya shiga cikin photos yana kalla, yana cikin haka yayi coming across pic na wani d’an saurayi ai take ya fusata “waye wannan?” Ya tambayeta harshly. Koda ran Mama ne ya b’aci Zeezee bata rikicewa haka se in na Adeel ne, “Very Own wani pic?”
  “Wannan!” Ya nuna mata wayan. “Ko zakice baki san shi ba.”
  “Nasan shi but Very Own calm down wallahi ba komai a tsakani na dashi.”
  “Then meh pic nasa yakeyi a wayanki? Ban hanaki barin photos na maza a phone naki ba? You’re cheating on me with him right?”
  “Omg No! Am not, wallahi ba komai tsakani na dashi, he’s just a friend-” ya barta tayi explaining kanta nma yak’i, ita kanta ta manta dalilin daya hanata goge pic d’in.
  “You are lying!” dan banzan zuciya irin nasa besan a lokacin da yayi wurgi da wayan nata ba seta k’ofa yayi, raga-raga yayi kan kwaltan. Hannu Zeezee ta aza kan bakinta in shock, hawaye kawai tasoma zubarwa, wayyo iphone 7s nata!
  “Adeel wallahi ba saurayi na bane kaima kasan I only belong to you be kamata ka fasa min waya ba.”
    “Na fasan do something about it if you can, just shut up and get out, dama tun ba yau ba nasan am not the only one.”
  “Adeel idan ka sauk’eni anan a ina zan samu abun hawa kayi hak’uri please.” Wai shi ya fasa mata waya amman ita ke basa hakuri while actually she can’t remember when last ta bawa Mama hak’uri amman in Adeel ne kullum cikin basa hak’uri take.
  “I said get out!” Ya tsawata mata sekace wani mahaifinta.

    Gefen titi guda ta nufi ta tsuguna tana me cigaba da kuka abin tausayi, tafi minti goma haka sannan daga bisani Adeel ya fito ya nufi inda take tare da mik’ar da ita har a yanzu kukan take. A hankali ya share mata hawayen nata “am sorry kinji?” Hugging nasa tayi tana kuka sosai “wallahi ba saurayi na bane, am not cheating on you Adeel please believe me.”
  “Is okay I trust you, am sorry kinji?” Har mota ya sata sannan ya tattara broken pieces na wayar nata ya cire sim d’in cikin, yaja mota ya kaita gida. Tun shigarta gida take addu’a Allah yasa kar ayi noticing yau wayanta bayi tare da ita. Da Maghrib Zeezee na zaune a d’akinta abin duniya sun mata yawa ita yanzu in Baba ya tambayeta ina wayanta me zata ce mai? Tana cikin wannan tunani Mama ta kirata zuciyarta na harb’awa ta mik’e a sanyaye ta fice, “na’am Mama, sannu Baba” ta gaishesa.
  “Yauwa K’anwata sannu, yau lafiya dai koh najiki shiru?”
  “Lafiya Mama kin kirani.”
  “Eh wayanki zaki aramun nawa airtime ya k’are.” Nanfa Zeezee ta shiga raba ido, “baki jini bane?”
  “Naji Mama wayana ya fad’a a ruwa d’azu so na shanya.”
  “Shine baki fad’amin ba akai miki gyara?” Fad’in Baba.
  “A’a karka damu Baba ze farfad’o in shaa Allah.”
“No wonder yau ba’ayi ta d’aukan selfies na asara ba, jeki shikenan.” Kwana zaune Zeezee tayi ranan as tana nazarin ina zata sake samun wani iphone d’in.

    The next day Adeel ya kirata ta d’ayan line nata wanda duk ‘yan gidansu ma basu san tanada wayar ba kan taje ta samesa a so so place, suna gama paper’n taje ta samesa da motar ta. Kallo d’aya ya mata ya gano da akwai matsala murmushi ya saki sannan ya tambayeta ya paper.
  “Lafiya qalau” ta amsa sama-sama “why did you call for me?” hannu ya mik’a a seat na baya ya fito da wani packaged leather jikin attached with a small card.
   “Meh wannan?”
  “Naki ne open it.” Amsa tayi ta karance letter’n amar haka;

   _I’m sorry Sweetest Love for going wild mad at you yestarday, I hope you can find it somewhere in your precious heart to forgive me am sorry. ILY_ D’an murmushi ta saki sannan ta bud’e pack d’in, sabuwar rose gold iphone 7pro taga aciki kafin ta tambayesa nawaye ne yace, “naki ne Babe, I’m sorry accept my apologies.”
   “Omg! Very Own! You’re the most sweetest thing that has ever happened to me thank you so much.”
  “Your sim is ready, I love you.”
  “I love you too” tayi hugging nasa. Bayan ta kunna wayan yace;
  “Akwai wani d’an party’n da clique d’ina sukayi organising a Yankari I want you to be there” yayi maganan yana shafa hannunta.
  “Har Yankari Very Own?”
  “Nan da Yankarin ne har?” Yayi maganan a bit angry.
  “I’m sorry please don’t be mad ba wai ina nufin bazan je bane, I mean kaga yanzu fa 4:30pm har yaushe zamuje Yankari in koma gida? Baba ya hanani staying late at night.”
  “Shikenan ke baki kai ki kula da kanki ba? Such a Daddy’s girl.”
  “Bawai haka bane Very Own understand mana.”
  “Da fitowa fili kikayi kikace you don’t love me it would have been better.”
  “Omg! Adeel” ta kama hannunsa da nata bibbiyu, “please kabar fad’in haka wallahi I love you morethan so much.”
  “If you really do then do this for me Babe, be there I really want you to be there.”

     “Very Own-” katse ta yayi;
  “Zakije yes or no? Stop wasting my time.” Shiru tayi totally speechless “I guess the answer is no” yana kaiwa nan ya bud’e motar ya fice not minding ya rufe mata k’ofan. Bayansa tabi ta shiga k’wala mai kira amman kota kanta beyi ba. “Adeel please don’t go ka tsaya please...” yana kaiwa gun motansa ya shiga ya fice. Hawaye ta soma yi a wajen unstoppingly da k’yar ta k’arisa gun motarta ta share hawayenta sannan ta d’ago wayan ta shiga kiransa sede har 5 missed calls be d’auka ba. Hankalinta sam baya jikinta ta shiga driving, ikon Allah kad’ai ya kaita gida.
  Tana isa tayi wulli da kanta kan gado ta cigaba da rusa kukan seda tayi me isarta ta mik’e ta watsa ruwa ta sake gwada layin Adeel har 2 missed calls be d’aga ba, texting nasa tayi _Very Own you don’t have to be mad anymore, your happiness means the world to me text me your location I’ll be there. ILY_
   
  **
  Yana a d’akinsa yana kan shirin zuwa Yankari message na Zeezee ya shigo, da kaman baze d’aga ba sekuma ya bud’e bayan ya gama karantawa ya murmusa sannan ya kirata take ta d’aga “hello Very Own I’m sorry dan Allah kayi hak’uri it won’t happen again.”
  “Thats my lady I love you.” Sanyi sosai taji a ranta “I love you more so where will I meet you up?”
  “Zanzo in d’aukeki.”
  “Toh I’ll be waiting.”
  “Aha and also kinsan how you’ll dress koh? Party-like”
  “Yes Baby.”
  “Yauwa Babe sena zo” yana kaiwa nan ya katse. Da sauri-sauri ya gama shiri itama haka. Crazy pencil jeans trousers nata tasha da wani top dake nan kaman vest saman sa had’e yake da sark’a dogo me fad’i black colour. Mininal makeup tayi applying tasa assesories nata sannan ta b’urma babban hijabi kai ta fito that was by 5:20pm kenan. “Ina kuma zakije?” Mama ta tambayeta.
  “Kati zan siyo anan shago.”
  “Toh Allah sa” batayi ta kanta ba ta fice a dai-dai wani shagon dake bakin corner ta tsaya ta kira Adeel in less than five (5) minutes ya k’ariso. Ba tare da b’ata lokaci ba ta shige ciki sede Ya Wakeel me shago yaga shigewarta cikin motar. Pecking nata yayi a kumatu sannan yace, “ya da hijabi kuma Babe?”
  “Don’t worry” hijabin nata ta kwaye ta wurga back seat “thats my babe you are looking super sexy.”
  “Thank you.” Motan ya ja suka hau tafiya ayayinda take d’aura kanta. Sun d’au tsawon lokaci kad’an suka isa Yankari inda duk sauran party rockers d’in suke.
  “Mu fita koh?” Hannunsa ta rik’e “Very Own promise me I’ll be safe with you ba abinda ze sameni please” tayi pleading. Tausayi ta basa, hannun nasa ya cire daga nata sannan ya kwantar da ita ajikinsa “don’t worry Babe, you are safe with me nothing will happen to you. ”
   “I trust you and love you.”
  “I love you too lets go then.”

   ***
    Loud music ke tashi wajen, gabad’aya ba wuta se turning club lights, maqale jikinta tayi ana Adeel duk tsoro takeji seyanzu takeji dama ta sani da bata biyosa ba, what if abu ya sameta yanzu? VIP table ya kaisu suka zauna sam tak’i sakesa, abinci akayi serving nasu taci tak’i gudun kar ansa abin bugarwa aciki taci ta bugu.
  “Babe aiint you hungry?” Kai kawai ta kad’a masa “you don’t trust me?”
   “I do, inda banyi trusting naka ba zan biyo ka nan ne?”
  “Toh why won’t you eat?”
  “Am not hungry” ta k’irk’iro murmushi.

  _7:12PM_
    Zeezee ta warware sosai har tayi new friends wasu ‘yan iska first class wajen, se rawa suke suna goga jikinsu dana maza. Wayanta dake pocket nata ne ya soma ringing tana kai dubanta taga Amiable Dad dum! Zuciyarta ta buga hannun Adeel taja zuwa waje “Very Own Baba na kira na me zanyi please?” Tayi stating all confused, wayar ya amsa a zatonta ma picking zeyi tayi saurin fad’in “no please karka d’aga.” Gani kawai tayi ya kashe wayan gabad’aya.
  “Adeel Baba na ne fa yake kira, how could you?”
  “Babe kin cika tsoro, let them be you are safe with me.”
  “Kabani waya na!” Tayi maganan a tsawace, kallonta ya tsaya yi ransa na tafasa. Wayar ya wurga mata “mani kike d’agawa murya? Gashi kiyi duk abinda kikeso, bullshit kawai!” yana kaiwa nan yabar mata gun. Hawaye ta shiga yi ga wayan a hannunta ta kira Baba ta kasa gashi bata taho da motar taba bale ta koma gida, Adeel is her only way back home. Ita yanzu ba Baba ba bakuma Adeel ba, bazata iya yin 2-0 ba. Waje ta nema ta zauna tasha kukanta har seda ta godewa Allah sannan ta share hawayenta ta gyara makeup nata ta koma ciki in the midst of some bitches ta samu Adeel zaune se hira suke suna dariya. Wani irin wawan kishi taji ya rufeta tsam amman she can’t blame him ita ta jawo komi.

   A nitse ta k’arisa wajen, koda ya ganta beyi ta kanta ba, gabansa ta nufa, “Adeel I’m sorry” tayi maganan a hankali, yi yayi kaman be ganta ba, “I said am sorry please” hannunsa ya mik’a mata sannan ta jasa zuwa wurin da akwai privacy. “Adeel am sorry please” sekuma ta rushe da kuka, kallonta ya tsaya yi daga bisani yayi hugging nata “Babe if you’ll do as I say bazamu na fad’a ba, kidena crossing d’ina.” Hugging nasa back tayi “I wont ever please kadena kula wancan hoes d’in.”
  “If you’ll give me all of yourself and listen to me I won’t.”
  “I’m all yours Adeel just promise me bazakamin abinda ze tab’amin pride (budurci) d’ina ba.”
   “Never Babe, your pride belongs to me but only if mukayi aure so stop worrying yourself on that kinji?” Kai tayi nodding “I love you.” Hawayenta ya share mata suka koma ciki suka cigaba da partying.

  _9:21PM Gidansu Zeezee_
  Dawowan Baba gida kenan wannan shine fitansa na tara tun d’azu yake neman Zeezee. Duk inda yasan tana zuwa yaje ba Zeezee ba labarinta, har report yakai wa police hankalinsa ya matuk’ar tashi sosai, bashi kad’ai ba har Mama da Omar.
   “Ina K’anwata ta shiga? Ina aka kaimin K’anwata? Ba halinta bane staying late at night, duk laifin kine Hafsah be kamata kibarta ta fita shagon ba, tunda Omar na gida mesa baki aikesa ya siya mata katin ba?”
  “Kamar ya laifi na Alhj? Kasan de Zeezee ba magana na takeji ba koda nace mata kada tafitan eventually se tayi.”
  “Toh baga irinta ba yanzu yarinya ta b’ata, wallahi duk abinda ya sami K’anwata kisani kece sanadi mschw!” Yana kaiwa nan yaja motansa ya sake fita for the 10th time yana zagaya unguwa yana tambayan mutane ko sunga Zeezee. Sede duk inda ya tambaya se suce mai sun ganta ne lokacinda take dawowa daga school. At last ya wuce shagon Ya Wakeel daya raina, aikuwa Ya Wakeel yace tabbas ya ganta tana shigan wani Mercedes-benz bak’a dawani saurayi ciki.
  “Zeezeen! Kaga tana shiga cikin motan wani?!” Baba yayi maganan disbelievingly.
  “Tabbas! Na ganta da idanu na Alhj.” kai Baba ya shiga kad’awa.
  “Wallahi k’arya ne ban yarda Zeezee na zatayi wannan abu ba kai de kawai kace kana son yi mata sharri ne shikenan in bahaka ‘yar 16 years zakace tabi d’a na miji? To zuwa ina?! Wallahi k’arya ne ba kalan tarbiyyan dana bata ba kenan.”
  “Shikenan Alhj amman nide kam naga Zeezee tana shiga motan wani.” Ko k’arisa sauraronsa Baba beyi ba yaja mota ya koma gida a fusace still not believing any of Ya Wakeel’s words sede his words kept on dancing in his head. “Ya Alhj? Any good news?” Banza da Mama yayi ya wuce d’aki, sam brain nasa yakasa comprehending abinda Ya Wakeel ya fad’a mai, what if its true? Kai yayi saurin kad’awa “noo it can’t be possible, sharri ne.”
  “Sharri mawa Alhj?” Mama dake zaune a gefensa ta tambaya. “Dan Allah ka gayamun.”
  “Hafsah wallahi sharri ne, Zeezee bata bi wani namiji ba sharri ne.” Zumbur Mama ta miqe tare da dafe k’irji, “Zeezee tabi wani na miji? Innalillahi wa inna ilaihi raji’un nawa yak’are nashiga uku!”

   For the 1000th time Baba ya sake gwada line na Zeezee switched off.
  “Hafsah kin yarda Zeezee zatabi wani d’a na mijin waje? Kin yarda?”
  “Alhj ba batun na yarda koko a’a bane fatan mu Allah yasa yadda ya d’auketa ya dawo mana da ita lafiya ba tare da yamata wani abun ba dan Ya Wakeel babban mutum ne bazeyi wa Zeezee sharri ba.”
  “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, mena ma Zeezee a rayuwa da zatayimin haka Hafsah? Yarinyan nan bata tab’a neman abu tarasa a k’ark’ashina ba, koda banida hali zan kwatanta, mesa zatayimin haka? Mesa zata nemi tozartani cikin jama’a?”
  “Alhj yanzu duk ba wannan ba addu’a zamuyi Allah sa ta dawo gida lafiya. Dalilin dukannin wannan abubuwa kuwa shine ILLAN GATA daman ni seda na gaya, sam tarbiyyan daka d’aura Zeezee akai gurb’arcacciya ne kaima kasani amman kak’i saurarona, ba abinda nafi guje mana kamar rana irin ta yau yanzu inhar wani abin b’atanci ya samu Zeezee ya zamuyi? Ina zamu sa kanmu acikin jama’a? Bama wannan ba in ta kamu da ciwon zamani kaman Aids fah? Wayyo Allah ka rufa mana siri ka dawo mana da Zeezee safe and sound.” wayarta ta ja ta sake gwada layin Ummien Lubiee kan ko Zeezee ta biya chan, sede har yanzu amsar d’aya ce bata zoba, Allah sa a sameta. Lubiee kanta couldn’t believe it dataji Zeezee bata dawo gida ba har yanzu, where could she be?



*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

4 comments:

Anonymous said...

lallai akwai aiki

Unknown said...

OMG,cant wait to read page 25,tnx sis you are really trying,Allah ya Karo ideas masu amfani.

Unknown said...

Ahab indai baba ne zeezee tana kalallameshi zaice sharri aka mata

Unknown said...

Maganin baba kenan! But i pray notin happens to her for mama's sake. Well done dearie