👮👮👩👩💥💥💥💥💥
HEEDAYAH!
💥💥💥💥💥👩👩👮👮
2⃣2⃣
written by miemie👄
Suka kama hanya suka fice heedayah ta bisu da kallo, kafafun mummy kasa daukarta sukayi jin kanta kawai tayi a qasa, ba abinda takeyi se hawaye haka daddy ma heedayah ta kariso gun da gudu tayi kan mummy tana gogemata hawaye "bar kuka mummy na" mummy tace "heedayah take ur daddy inside" heedayah batayi musu ba ta tashi taja daddy'nta suka shiga ciki tace "daddy na bar kuka, kar ka kula daddy'n don moha dinnan ya cinye gdan in ana cinyewa ba kana da gdaje dayawa ba semu koma sharada ai ko GRA, bar kuka kaji daddy na?" Tasa hannu ta goge masa hawaye zuciyar daddy radadi take masa sosai kasa rikewa yayi jikinsa ta hau rawa sosai can anjima yabar motsi heedayah ta kwala ihu atake mummy da nanny suka iso parloun "heedayah meya faru??" Kasa fadin komi heedayah tayi se kukan datakeyi tana nuna daddy da yatsa mummy sukayi kansa ta tabbatar da daddy baiya numfashy tana kuka ta dau wayarta ta kira family dr dinsu yace gashy nan zuwa nan da nan ya iso yabama daddy immediate treatment yace "ma'am akoi dan abubuwan dayakamata kuna avoiding inbahaka ba rashin lafyan alhj will only get worse," mummy tace "ina jinka dr," dr yace "ma'am na farko, kudena yawan masa maganganun dazasu ringa tsinka masa zuciya, na biyu kudena yawan sasa kuka, hasali ma duk abinda kukasan baida dadin ji kudena fada masa" mummy tace "toh dr nagode in shaa Allah it won't happen again," dr yamusu fatan alheri sannan ya fice. Can guessroom dake sama mummy ta haura ta shige bangida ta rufe kofar ta ringa kuka kamar ba gobe batasan kuma ina zata sa kanta ba gashy abbanta bayya nan, if only yana raye da shi kadai ze iya cire ta acikin tsaka me wuyan da take ciki ynxu, kwata kawata ta manta daddy nada gdaje bayan wanda suke ciki, haka tata kuka a bangdan can heedayah taji shiru ta shiga neman mummy har Allah ya kawo ta dakin taji karan kuka a bangida ta karasa tana kokarin budewa amman yaqi buduwa, "mummy open the door, pls kibar kukan pls" itama ta fashe da kuka uwa nayi 'yan nayi miemie na gefe tana miqa musu tissue, tausayin heedayah ne yakama mummy sosai dan a 'yar shekarunta bekamata ace tana facing problems da tension haka ba, ta budo kofar heedayah tayi hugging nata tightly munmy tace "is okay my princess kukan ya isa haka kinji? Everythng is gonna be fine jekiyi sallah ki kwanta kinji?" Heedayah ta dago jajayen idanunta tace "mummy wai daddy'n don moha ya ce mufita mubar gdan nan?" Mummy ta share yar kwallarta "waya gaya miki?" Heedayah tace "ni naji da kunne na" mummy tace "heedayah listen to me, kinga banson wannan abu yayi affecting naki, karki kula daddy'n muhammad zamu bar masa gdan ai akoi Allah ko?" Heedayah ta gyada kai mummy ta cigaba "good semuta addu'a Allah kawo mana karshen wannan abu, zan nemo mana new home semu koma ciki ko?" Heedayah tace "ai ba sekin siya mana new home ba mummy, daddy yacemun yana da wani gda a sharada da GRA" se ynxu hankalin mummy yadawo jikinta ta tuna tace "heedayah Allah miki albarka ynxu zo muje daki muyi alwala muyi sallah seki huta ko?" Suka fice bayan sun idda sallah sunyi addu'a sosai mummy tasa heedayah baccin dole amman ina heedayah taki a tare suka koma daki suka sami daddy kwance akan gado da hawaye na gangara akan fuskarsa suka karasa kansa mummy tasa hannu ta goge masa hawayen tace "habibi kukan ya isa kaga dr yace kadena kuka u'll worsen ur situation ya isa pls" ta tashy ta fara duban wardrobe ta inda daddy ke ajiye files nasa taga gun wayam! Ba komi hankalinta ya kuma tashy daddy yafara motsa jiki, heedayah tace "mummy daddy nason yafadi wani abu," mummy takaraso tace "habibi wani abu ne?" Girgiza kai kawai daddy keyi da alaman a'a mummy tace "a'a meh?" Se faman jijiqa kai daddy keyi yana kokarin daga hannunsa amman yakasa sede in aka sa hankali za'a gano gun da yake aje files nasa yake kokarin nunawa, mummy tace "ba files din?" Ya gyada mata kai, tace "toh na ina? Ina ka kai?"Jijiqa kai kawai yake tayi can mummy tace "ko duka files nakan ne babu kaba alhj ismail?" Daddy ya gyada kai a hankali yafara zubda hawaye, wani tokari mummy tajiyo a zuciyarta shiknan nata ya kare kuma, takuma tambayansa ya kuma gyada mata kai heedayah tafara maganan zuciya "in ta haka envelope dana gani a hannun daddy'n don moha shine wanda mumy ke nema knan" mummy tasa hannu ta gogewa daddy hawayensa sannan tace "if only... Habibi if only zaka iya gayamun mesa kaba ma wannan mugun mutumin daka dauka abokinka ne dukiyar ka kab ba tare da kayi shawara dani ba, bansan ina zan kaimu ba ynxu, abbana bayida rai, aikina bawani salary babba bane da har zan iya biya mana kudin haya, innalillahi, sede dan abinda na samu acikin gado na, Ya Allah ka kawo min qarshen wannan masifa" ta soma maganan zuciya "Alhj lawal is my only hope ynxu, dole in kirasa in masa bayani ko ze iya taimaka mun" nan tabar maganan zuci tace "heedayah miqo min wayar daddy da tawa" heedayah ta miqo mata ta lailmo number'n alh lawal a wayar daddy sannan ta dura acikin wayarta tayi dialing ringing sau uku yayi alhj lawal ya daga "assalamu alaikum"...
To masu karatu ko wani munafincin kuma alhj lawal ze kulla se Allah kubiyoni dan ji...
No comments:
Post a Comment