TANA TARE DA NI... PAGE 43
BY MIEMIEBEE
Bacci meh rai da lafiya Fannah tayi wanda ta jima ma batayi ba se chan bayan azahar ta tashi. A hankali ta bud’e idanunta jin kanta tayi kan pillow cike da mamaki ta duba harda bargon ma, toh waya shigo ya rufeta? Waya kunna mata AC? Ko kad’an bata kawo Mr. Fauzi arai ba saboda tasan halinsa, toh kode Yusuf ne? Toilet ta nufa ta wanke fuskarta tare da brushing sannan tafito ta ninke bargon tsab ta had’a da pillown sannan ta d’aga tafito dashi a hannunta floor na office nasu Yusuf ta nufa akan table nasa ta tsincesa bayan sun gaisa tace, “gashi nagode, shine akan ka tada ni narufe kaina kayi min wahala haka?”
Cike da mamaki Yusuf ke kallon Fannah totally speechless. “Nikuma?” ya fad’a a k’arshe. “Ina zan samu bargo da pillow a office Fannah? Kode har yanzu baccin naki be wassake bane?”
“Yusuf banasan wasa please amshi kayan ka, inkuma so kake kabarmin seka fito fili kace Fannah na baki.”
Murmushi me sauti ya saki. “Fannah wallahi am serious ni banma san wai kina bacci ba kide zagaya ki tambaya waya sani ko Boss ne dakanshi nema ya rufe ki.”
“Dariya kakeson bani komeh? Boss ya rufeni ina bacci? Impossible barinje in tambayi Ahmad da Kacallah.”
“Zaki b’ata lokacin ki ne saboda Boss ya aikesu tun d’azu.” Yi tayi kamar bata jisa ba what if abinda Yusuf ke fad’i gaskia ne? ahaka har tashiga elevator ta hauro sama tana tsaye bakin k’ofar office na Anas amman takasa shiga inkuma ba nashi bane fah? Yace tacika shisshigi da k’yar de tasamu tayi knocking a hankali.
Daidai Anas ya d’au bottle na beer nasa ze sha kenan knock yashigo. Haka kawai yau yaji yana san yad’an bugu saboda ya kwana biyu be sha ba tunda Fannah na bacci bare d’an sha abinsa kuma ba ma haka ba so yake yabar tunanin Fannah, ba abinda ya tsinana wa kansa yau, wai mesa ma yaje ya rufeta d’azu da take bacci? Tausayi ne ya fad’a a fili. I don’t love Fannah I just pity her yayi reminding kansa. “Who is it?” Ya tambaya.
Chan murya k’asa k’asa a hankali tace, “Fannah ce.” Da sauri ya rufe bottle d’in tare da jawo drawer’n gefensa ya rufe. Turare ya feffesa cikin office d’in dan kashe warin giyan tare da kimtsawa sannan yace, “come in.” Tana shiga yaganta da pillow da bargon, kallonta yake har sanda ta k’ariso gaban table nasa. Shiru tayi tana nazarin taya zata fara masa maganan, shima shirun yayi tare da had’a hannayensa biyu k’ark’ashin hab’ansa yana kallonta kamar hoto. Can ta fara kamar haka;
“Ermm Mr. Fauzi ban sani ba ko wannan naka ne, na tambaya su Yusuf duk sunce ba nasu bane.”
Kallonta har yanzu yake da wani murmushin tsiya karara a fuskarsa. “Wato dan kin maidani dustbin shine zaki kawo min?”
Kai ta d’ago tana kallonsa “No Sir ba abin da nake nufi ba kenan-” katseta yayi
“Shine mana, kin tambayi saurayinki Yusuf yace ba nashi bane shine kikace bari ki kawo wa dustbin shikam ze karb’a koba haka ba?”
“No Sir thats not what I mean, in ajiye maka a ina?”
“Ba nawa bane” ya bata takaicaccen amsa. Kanta ne ya d’aure. Kamar ya ba nasa ba? Toh na waye? Ita se yanzu ma ta tuna ranan da Mr. Fauzi ya rufeta a d’akinsa ai taga bargon nan akan gadonsa, to mesa zece ba nasa bane?
“Sir but ranan naga bargon nan a d’akinka.”
“Aww mak’aryaci kikeson ki kira ni dashi kenan, ince miki ba nawa bane kice nawa ne”
“No Sir ba abinda nake nufi ba kenan.”
“Inma tunani kike wai da kike bacci ni naje na rufe ki toh you are mistaking dan ni ko shiga office naki banyi ba.”
“I’m sorry” tace cike da kunya ita de tasan ranan tabbas taga wannan bargo a d’akin Mr. Fauzi kuma gashi yace ba nashi bane. “Jeki ajiye kidawo am waiting for you.” Bayan minti d’aya Fannah ta dawo “yes Sir.” So yake ya ce mata suje suci abinci amman girman kai ya hanasa. Seya bud’e baki ze fad’a se yayi shiru.
Ganin baida niyyan magana Fannah tace, “Sir you called me.”
“Ina sane ai” yabata amsa. “Ko ban tambaya bama nasan kinajin yunwa lets go and eat.” ya fad’a in an I dont care tune.
Qarya tayi niyyan masa tace tana azumi seta tuna yasan batada tsarki. “Sir I’m not hungry thanks.”
“Toh ni inaji lets go” zata sake magana yace, “banasan musu” bayan sa ta nufa bayan ya rufo k’ofar office nasa Fannah ta juya zata nufa public elevator, hijabinta ya rik’o. A tsorace ta juyo tana kallon had’add’un yatunsa daya k’ayata su da zobunan azurfa masu tsada rik’e da hijabinta sannan back to fuskarsa. Beso suka had’a ido ba “mu shiga nawa” yace mata. Kai ta giad’a masa a sanyaye tabi bayansa suka shiga private elevator’nsa ba wanda yace ko uffan ahaka har suka sauk’a driver yayi driving nasu zuwa wani hotel na daban ma yau. Abinci me rai da lafiya Anas ya mata ordering. “Eat” yace mata alokacin daya d’aga spoon nasa, ba musu ba gardama itama ta d’au spoon suka soma ci.
Ko da yagama cin nasa zaman jirarta yayi data gama ya tambayeta, “a k’ara miki?” Kai ta kad’a masa bayan ya biya suka koma office d’an errands kad’an Fannah tayi wa Mr. Fauzi, lokacin tashinsu nayi ta wuce gidah.
Shima Anas yana gama abinda yakeyi ya kama hanyan gida, tuk’i yake hankalinsa kwance ya d’ibo bottle na giyansa biyu yau a paint house nasa ze kwana, unguwar shiru yake ba mutane sosai yana cikin tuk’i yaga mota ya fito from nowhere yayi blocking nasa, ikon Allah ya tsaya gani reverse ya gwadayi a take yaga bayan san ma anyi blocking. Toh su waye ne? Kafin yanemi amsa wa tambayan daya ma kansa yaga maza uku sun fito daga motar gaban nasa da angansu anga ‘yan maye ‘yan bayan gari. Murmushi kad’an ya saki dan in ‘yan su uku ne acikin minti biyar ze gama dasu. Kafin ya yi yunk’urin yin wani abu yaji ana knocking jikin window’nsa. Window’n yayi wining “munada problem neh?” Ya tambaye gayen.
“Dade ka fito tukuna.” cewar gayen. Ba gardama ya fito ya tsaya nanne yaga duka duka mazan guda biyar ne. “Will you guys let me pass or senayi muku abinda bakuwa so?” Familiar murya ya jiyo daga behind nasa yana cewa;
“Kokuma mu mu maka abinda baka so ba Mr. Fauzi” yana kai dubansa gun da ya jiyo muryan idanunsa suka sauk’a kan Farouq yawani pake kan driver’s sit cike da isa ya taso tare da takowa gunsu Anas.
“You’ve had your time the other day now is mine.”
Wani erin dariyan rainin hankali Anas ya saki harda tafi “you are such a genius Farouq. Wai ka d’au dakai da wannan mashirmatan daka taran zaku iya min wani abu ne?”
Dariyan bosawa Farouq ya saki “Mr. Fauzi kenan kasani sarkin yawa yafi sarkin k’arfi. Apologise to me, tell me sorry akan abinda kamin jiya and I will let you a save passage.”
“Ni in ce maka sorry?” Yayi murmushi “never!”
“ATTACK!!!” Farouq ya fad’i nan maza biyar d’in suka soma nufuwa wajen Anas. Sleeves nasa yayi rolling tare da ciro Rolex agogonsa kafin ace me suka b’arke cikin mumunar fad’an BIYAR akan D’AYA. Farouq na tsaye a gefe yana kallon yadda Anas yake destroying masa mutane, duk se kamar yafi k’arfinsu dukda suma suna k’ok’ari dan har sun fasa masa baki amman yafi cin uwarsu. Tsawa Farouq ya daka musu “wai zakuce shi kad’ai yafi ku duka k’arfi ne?”
Ai se kamar maganar Farouq k’arfi ya k’ara musu. Sunayi Anas yanayi har suka samu sukaci galaba akansa hanci, baki ba wanda basu fasa masa ba. Hannayensa suka kama ta kowani gefe a lokacinda Farouq ya taso daga inda yake. “Ohhh look at you Mr. Fauzi abin tausayi, ina k’arfin naka yaje? Ina polisawan naka? Kud’in ka ya ceto ka mana.” Fuskar Mr. Fauzi dayake yoyon jini Farouq ya d’ago “tell me meh had’inka da mata ta Fannah?”
Murmushi Anas yayi dukda azaban dayake ji. “Kaikuma tell me meh had’inka da alak’a na da ita? Mind your damn business.”
“Bakinka be ruhu ba kenan har yanzu. Rik’e min shi dakyau” yace da mazan nasa. Gagam suka sake damk’e Mr. Fauzi punch me rai da lafiya Farouq ya kai masa wanda seda idanun Anas suka juya. “Nace meh alak’arka da matata?”
“Fannah is not your wife” ya fad’a a wahalince. “Take note”
“Har yanzu baka bugu ba.” Naushi yakai ma Anas a ciki wanda sakamakon hakan ya saki k’ara sosai dan azaba.
“For the last time me had’inka da Fannah?”
“Kanason kaji me had’ina da Fannah? *FANNAH IS MY GIRL, I LOVE HER.*”
Cike da b’acin rai Farouq ya cukumo kolar rigan Anas “me kace? Sake nanata abinda ka fad’a inji”
“I LOVE FANNAH, KUMA NI ZAN AURETA BA KAI BA, FANNAH TAWA CE!!!”
“You really want to die.” Naushi lafiyayyu guda uku ya kai wa Anas aciki biyu kuma a fuska. Kaca-kaca suka ma Anas, duk wanda ya kallesa bare so sake sa idanunsa kansa ba duk jikinsa jini.
“Me alak’ar ka da Fannah? Kace min baka son ta kuma baka santa ba.”
Da k’yar yake maganan “NEVER!! I LOVE FANNAH, ko kasheni zakayi bare canza komai ba.”
A fusace Farouq yace, “Baaba” na gefen daman Anas “je cikin trunk na motan can kaciro min sandan chan nakega inba dukan mutuwa na masa ba bare shiga hankalinsa ba. Zakace baka son Fannah ko yaya?” Shiru Anas yamasa bece komai ba se nishin wahalan dayake yi abin tausayi.
“Farouq ga ‘yan patrol zuwa fa!” Baaba yayi exclaiming da ihun gaske ai kamar kyaftawan ido su Farouq suka lodu a mota suka bar wajen a 360. Anas na kwance helplessly a k’asa. Bayan motan patrol d’in ya k’ariso polisawan suka diddiro ganin mutum a k’asa, plate number’n motar Anas d’ayan ya karanta yaga “Mr. Fauzi.”
“Guys Mr. Fauzi ne!” da gudu sukayi kansa suka d’ago sa zuwa motar sa tare da miqar dashi a back seat. “Abba lets go, mu kaisa asibiti push the start button.” d’ayan officer’n ya fad’i. A wahalince Anas yace, “no karku kaini asibiti just drive me home, to my paint house.”
“Sir but you are badly injured.”
“I know, ku kaini paint house d’ina kawai.”
“Okay sir ina ne paint house d’in?” Nan Anas ya musu kwatance murya yana d’aukewa. “Sir su wa suka maka haka?” Har ya bud’e baki ze kira sunan Farouq seya tuna in ya fad’a musu definately zasu kama Farouq su rufe sa kuma, in hakan ya faru kuwa Fannah barata ji dad’i ba. “Nima bansan suba” yama officers d’in k’arya “ ‘yan iskan unguwa ne kawai.”
Daidai gaban paint house nasa suka iso. “You can go now zan k’arasa da kaina nagode.” Cewar Anas idanunsa suna kafewa.
“Sir amman kace barakaje asibiti ba? Wannan mutane sunji maka ciwo fah.”
“Don’t worry I can take care of myself.” Bottles na giyansa guda biyu yaciro da k’yar yake iya tafiya dan kalan dukan dayasha wajen Farouq da mutanensa, ahaka har ya samu ya isa ciki ko k’ofan ma yakasa locking. Bayi ya nufa da rarrafe da taimakon sink ya mik’e ya kalli fuskarsa a madubi. Sam beso sake kalla ba dan irin ciwon da suka ji masa. Ruwa ya gwada wanke fuskar nasa dashi. Aiko ruwan na tab’a fuskar ya saki k’ara dan azaba daga k’arshe hak’ura yayi yakoma d’aki tare da rage kayan jikinsa yabar short nicker kawai. Kwalba d’aya ya kwankwad’e tas dan samun bacci, yana shanye wa kuwa bugeggen bacci ya d’ibesa ko sallan maghrib beyi ba bale na isha. Wayoyinsa dake cikin mota kuwa se kiransa su Ummie suke ba iyaka amman bai d’aukawa hankalin kowa ya tashi, ko da sukaje office nasa suka tambaya kuwa, kowa ya shaida Mr. Fauzi yabar building d’in lafiya.
*****
_Washegari..._
8:10AM yama Fannah a office sede tata knocking a bakin k’ofar office nasa amman shiru chan ta gwada bud’ewa taji a rufe alaman Mr. Fauzi bezo bama kenan! To meya rik’esa? Shida ko lattin minti d’aya baya yi. Meya faru? Mesa bezo ba? Ko baida lafiya ne? Minti 15 ta k’ara tana jiransa amman ba alamansa. Gashi yanada board meeting by 10:30AM. Ganin ba mahalicci se Allah kawai ta sauk’a k’asa ta samu Kacallah tare da tambayansa ko sunyi waya da Mr. Fauzi.
“A’a wallahi nima Fannah na kirasa ta duka layinsa baya d’agawa tun jiya na rasa dalili.” Kawai setaji gabanta na fad’i. “Toh nagode” tace masa.
Wayarta taciro ta kirasa har ya tsinke be d’aga ba. Tashin hankali. To ina yashiga? Amal ta kira ta tambayeta ko Anas na gida cike da tashin hankali Amal tace mata itama tun jiya suke neman Anas bedawo gida ba.
Napep ta tsara bata tsaya ko inaba se paint house na Anas motarsa tagani fake gaban gidan wani hamdala tasaki har ta ciro wayarta zata kira Amal ta sanar da ita se kuma ta fasa, bari de ta tabbata ko yana ciki tukuna. Door bell ta danna sau uku amman ba response. Tana gwada murd’a hannun taga k’ofar abud’e ba sak’e sak’en da bezo mata ba toh kode barayi ne suka shigo masa? Subhanallah amman ai kuma ga motarsa. Ciki tashiga ta lek’a kitchen ba alaman ko motsin mutum “Mr. Fauzi!” ta kira sunansa shiru d’ayan d’akin ta bud’e taga nan ma bayanan toilet dinma haka, guest toilet ma ta duba bata gansa ba. Daga k’arshe d’ayan d’akin ta bud’e a hankali kwalban giya ta soma cin karo dashi, se fad’i gabanta yake ta d’aga tare da k’arisawa cikin d’akin tana taku a hankali cike da tsoro. “Mr. Fauzi!” Ta kira sunan sa alokacin data gansa kwance kan gado yayi ruf da ciki se bacci yake yi ba ko riga jikinsa se bedsheet daya ja zuwa tsakiyar cikinsa.
A nitse ta k’arisa gefen gadon tare da ajiye kwalban kan side drawer. “Mr. Fauzi!” Ta sake kiran sunansa shiru be amsa ba. Toh kode mutuwa yayi ne? Sede kuma tajisa yana numfashi. Jijjik’asa ta hau yi har se lokacin daya soma motsawa. “Waye ne?” Ya tambaya cikin bacci.
“Sir Fannah ce, Fannah Aleeyu.”
“Fannah? Me kikeyi anan? Ban rufe k’ofan bane?”
“Eh sir baka rufe ba, you need to get up kanada board meeting by 10:30AM.”
Cikin bacci yace, “barinje ba kiyi cancelling, tell them barin samu zuwa ba.”
“Sir but why? Kayi hak’uri ka tashi please.” Bece da ita komai ba ya cigaba da baccinsa. Pillow’n daya rufe fuskar sa dashi ta d’aga. Ido ta zaro tana salati alokacin da taga irin ta’addancin da aka ma Anas a fuska. Meya samesa? Waya masa duka haka?
“Subhanallahi Mr. Fauzi meya sameka? Omg!” ta tambaya a kid’ime a lokacin da ta tsuguna gabansa.
Da k’yar ya iya bud’a baki yace, “ki rufe min fuska banasan hasken nan.”
Ignoring nasa tayi “Mr. Fauzi waya maka haka da fuska? Fad’a kayi da wani neh? Meya sameka?”
“Bansani ba nima just leave me get out.” Haka kawai yaji baya san Fannah tagansa a bad condition irin na yau, bayasan yasa ta cikin damuwa bayasan taji tausayinsa.
“No Mr. Fauzi I’m not leaving you like this.” Hannu tasa ta dafe goshinta bata ma san ta ina zata fara ba. Hawaye kawai taji yana gangaro mata kan kumatu dan uban tausayi irin nata. Hannu ta aza ta tab’a gefen idansa daya kumburo dan bugun daya sha. K’ara ya saki wanda yasa ta mayar da hannunta baya da wuri. “Sorry” tace cikin kuka. Idanunsa na sauk’a kanta yaga tana hawaye abinda baya so kenan.
“Miss Aleeyu leave please, goo.”
“I can’t leave you like this, Mr. Fauzi asibiti yakamata muje su duba ka.”
“Barinje ba” yabata takaicaccen amsa idanunsa a rufe.
“Please” ta rok’esa tana hawaye ganin yadda aka masa destroying kyakkyawar fuskarsa da a yanzu mutum bare so ya kalla sau biyu ba.
*© miemiebee*
No comments:
Post a Comment