TANA TARE DA NI... PAGE 44
BY MIEMIEBEE
“Miss Aleeyu barin je ba kema leave I can take care of myself” hannu ya mik’a ze amsa pillow’n se kawai ya saki k’ara dan zafin dayaji a cikinsa saboda blows da Farouq ya riga kai masa. A rikice tace, “meneh Mr. Fauzi?” Kafin ya amsata ya mata k’arya ta kwaye bedsheet d’in daya ruhu dashin, hannu ta aza kan bakinta cike da mamaki “Subhanallahi Mr. Fauzi dan Allah meya sameka? Ina kasamu wannan ciwuka? Kalli cikin ka? Ya Salam!!!” Ta fad’i tana hawaye tana kallon cikin Anas da yayi har wani purple brownish colour dan azaba.
“Mr. Fauzi meya same ka please?” Ta sake tambaya hankali tashe.
“Nace miki babu in kinsan kuka zaki tayi anan kuma go, leave, I can take care of myself.”
Innalillahi! what do I do now ta tambayi kanta barata iya barin Anas haka ba he is badly wounded ga fuska ga ciki meya samesa ko b’arayi ne suka shigo suka masa duka? Amman kuma ai gidan tsaf yake ba abinda aka b’arnata. Toh meneh?
“Mr. Fauzi please kayi hak’uri mu kaika asibiti kaji? Yi hak’uri.” Ta fad’a still tana hawaye dan tsantsan tausayi. Danko ba wanda zega ta’addancin da aka ma Anas be tausayawa masa ko be zubda hawaye ba.
“Nace miki barinje ba kitafi please.” Wayarta ta ciro zata soma dialing number’n Amal dan sanar da ita halin da ake ciki.
“Me zakiyi?” ya tambayeta.
“Zan kira Amal ne in sanar da family’nka I’ve found you tun jiya suke neman ka.”
“No karki kira su hang up.”
“But Sir-” katse ta yayi ta hanyan daka mata tsawan da seda shi kansa ya masa ciwo “I said hang up!” Kansa ya dafe yana muntsika fuska cike da azaba. Nan ta katse ta matso kusa dashi “Sir kanka ke ciwo?” Niyan shareta yayi da farko sekuma ya giad’a mata kai a k’arshe. Jakarta ta ajiye kan side drawer ta nufa toilet tare da fitowa da bowl cike da warm water data d’iga dettol ciki dakuma towels guda biyu, jakarta ta ture gefe tare da ajiye bowl d’in akai. Kallonta yake “me zakiyi?”
“Sir your face is a mess, zan goge maka ne.”
“Banaso just leave.”
“No Sir I’m not leaving mesa kai zaka taimaka min amman ni bakasan na taimaka maka? Saboda bankai inyi offering maka help bane? Saboda ka raina ni banida standard? Saboda ni talaka ce? Is that it Sir?”
“No Miss Aleeyu that is not my point...” sekuma yayi shiru.
“Toh kabari in biyaka taimakon dakake min koda na yau ne.” Shiru yayi chan ya giad’a mata kai.
A ranta tace, Ya Allah kar ka kamani da laifi saboda zan tab’a na mijin da ba muharrami na ba, baida lafiya ne taimako zan masa, astaghfirullah.
Nan ta tsoma d’ayan towel d’in cikin ruwan d’umin tare da matsewa a hankali ta d’an tab’a gefen bakinsa daya fashe. Towel d’in na tab’a wajen yajiyo zafi sosai hannunta ya kama “Sir nasan zeyi zafi hak’uri zakayi kaji? Sorry” a hankali ya sake hannun nata. Tana sake tab’a wani waje ya saki k’ara “arghhh! Ya isa kibari ze warke da kansa, go home”
“Mr. Fauzi please mana kabari koda germs d’inne a kashe tunda baraka je asibiti ba. Please”
Haka a nitse cike da tausayi ta riga bin duk ciwon da ke kan fuskarsa tana gogewa a hankali, sosai Anas ya riga sakin k’aran azaba in towel d’in ya tab’a masa kan ciwon ita kuwa duk lokacin daya yi d’an ihu seta basa hak’uri. Tagama da fuskarsa sauran cikin. D’ayan tsumman ta d’aga ta sa cikin ruwan kamar yadda tayi d’azu bedsheet daya rufe jikinsa dashi tasa hannu ta kwaye zuwa cibiyar sa.
“Me kuma zakimin?” Ya tambaya yana k’ok’arin jan bedsheet din gam ta rik’e tana me hanasa yin hakan. “Ba abinda zan maka Sir zan d’an matse maka wajen ciwon ne.”
“Don’t worry ze warke da kansa. Wai ke bakia jin tsoron zama da namiji kad’ai ne under thesame roof?” ya gwada tsorata ta ko zatace ta hak’ura zata tafi.
“Ina ji amman in da kaine bana ji, I trust you Mr. Fauzi nasan ba abinda zaka min shiyasa. Yi hak’uri in d’an matse maka cikin kaji?” sanda ya k’are mata kallo sannan ya giad’a kai.
A hankali ta aza hannunta kan cikinsa ta matse towel d’in kai. K’ara ya saki sosai dan azaba tare da rik’o hannunta. “Awwchh! Kibari ya isa ze warke da kansa, arghhh!”
“Sir hak’uri zakayi sauran kad’an sorry.” Haka tata lalashinsa kamar d’an yaro. Towel tasake canzowa tare da k’aro ruwan zafi kan ruwan dan ya riga ya huce. Bayan ta zauna ta sake tsoma towel d’in ciki, cikin siririyar muryarta tace, “Sir did you get drunk yestarday” Shiru yayi kamar be jita ba. “Sir?” Ta kirasa. “No” ya mata k’arya danko besan taga kwalban a bakin k’ofa ba.
“Toh wancan fa kwalban meh?” Ta tambayesa a nitse. Kai ya d’aga yaga kwalban sekuma yaji kunya. “Toh me ruwanki dan nasha? You are not my mother ko ita mahaifiyar tawa bata isa ta hana niba, stay out of my personal li-” be k’arisa fad’in ‘life’ ba yasaki ihu “arghh!” Sanadiyar tab’a masa kan inda ke masa zafi sosai da Fannah tayi. “I’m sorry” tace “sauran kad’an.” Chan ta nisanta, “Mr. Fauzi will you listen to me in na fad’a maka wani abu?” Kamar wanda bare ce komai ba seyace “meh abun?” Sanda ta sake matse towel d’in ta mayar kan cikinsa tana daddanewa kan ciwon a hankali tace, “if I were you, in za’a maidani kai abani kyanka da kud’inka da ilimi da komai da kake dashi I will thank God barin na wasting rayuwa na akan shaye shaye ba. Masu shaye shaye sune wanda basuda aikin yi, wanda basuda ilimi basuda komai se shaye shayen da sukeyin. Amman kaga kai komai Allah ya baka Mr. Fauzi, you are handsome, rich and very intelligent, me kake nema? Don’t you think bakayi adalci wa Allah ba ta hanyar masa godiya da shaye shayen da kakeyi?” A hankali ta d’ago idanunta tana kallonsa shima kallon nata yake da blue eyes nasa sannan ya kawar da kallonsa daga gareta.
“Kayi shiru Mr. Fauzi, do you think you are fair to Allah? Bayan ya gama baka komai seka gode masa ta hanyar bijire wa dokokinsa na hana kowane muslimi shaye shaye”
“No I’m not” ya fad’a ransa b’ace, muryarsa cike da weakness. “Ke bakisan mesa na mayar da drinking abinyi ba kidena intruding min cikin personal life. Get up and leave” yace a lokacin daya d’aga hannunta daga kan cikinsa.
“Yafi ace ka rasa mahaifiyar ka ko mahaifinka kokuma d’aya daga cikinsu ya gudu ya barku? Is that the reason kake shaye shaye?” Kallonta yake totally speechless chan kuma ya tuna ashe ranan ta karanta masa diary, cikin chan tagani. Hannunta ta raba da nasa ta mayar kan cikin nasa.
Hannun nata ya kuma d’aga daga kan cikinsa “ya isa you can go banasan maganan nan, saboda kin karanta min diary hakan be baki daman fad’a min whats right or wrong ba. I’m still your Boss”
“I know Mr. Fauzi, you are my Boss. Ammana in saboda mahaifiyar ka kake misleading precious rayuwarka ta hanyar shaye shaye you are destroying your bright future. Hakan na nuna you are weak yana nufin ka barta taci nasara kanka kenan. Show her you are strong ko ba ita you can live your life, ka mance da ita and move on if possible forgive her if not ka mance da ita. You have a very bright future kadena b’atawa ta hanyan shaye shaye kaji Mr. Fauzi?” Shiru yayi bece komai ba as ya wula cikin duniyar tunani yana nazarin duk abinda Fannah ta fad’a masa. Tabbas ba k’arya ko d’aya cikin abinda ta fad’a masa dan kuwa haka Shettima ma kullum ke fad’i masa sede koda Shettima ya masa magana bai san sauraro amman yau da Fannah tamasa maganar seyaji yanasan yayi moving on ya manta da abinda Ummimi ta masa sede bawai ze yarda ko ya aminta da mace bane a rayuwarsa ever again he is already broken.
“Can you do that Mr. Fauzi for Amal’s sake?” Kai ya kad’a mata da nufin “a’a.” “For mahaifinka?” Nanma ya girgiza kai. “Ummie?” girgiza kai still yayi. “For Shettima?” Nan ma haka. Cike da kunya tace, “for me?” Jiran masifar sa take setaji yace, “yes” a hankali sounding defeated.
Idanunta ne suka sake bud’uwa cike da jin dad’i da murna. “Dagaske Sir? Zaka dena shaye shaye and move on?”
“Yes” ya sake fad’i. Dad’i taji sosai wanda ta kasa b’oyewa. “You promise Sir?” ta tambaya dan sake tabbatawa.
“I promise” yace. Sede duk maganan nan da suke baya kallonta. “Look at me please Sir” tace cikin murya me dad’in sauraro. Yi yayi kamar be jita ba. “Please” ta rok’esa a hankali ya dawo da blue eyes nasa kanta. “Da gaske baraka sake tab’a giya ba?” Ta tambayesa suna kallon juna. Kai ya giad’a a hankali “I promise.”
“Mr. Fauzi thank you, thank you so much nakega am the happiest woman on earth yanzu, tun ba yau ba nake addu’ar Allah nuna min rananda zaka dena shaye shaye se gashi Allah ya nuna min yau, thank you so much.” bece me komai ba. Nan da nan ta gama matse masa cikin yadawo clean ba jini ko d’igo d’aya jikinsa sede zafin da yakeji. Tashi tayi zata toilet ta zubar da ruwan Anas ya rik’o hannunta a hankali takai dubanta kan hannun nasa sannan kuma zuwa kan Anas d’in tanasan tace masa ya sake mata hannu amman kuma tana tsoro kar yace ze canza mind nasa batun shaye shayen da yace ya dena.
Godiya yakeson mata amman girman kansa ya hanasa, seya bud’e baki zeyi magana se wani abu ya tsaida shi. Da k’yar ya iya ya sauk'e girman kan yace;
“Thank you.” ya fad’i a hankali ko kallonta baiyi. For the first time daya soma mata godiya kenan. Ita kanta abin ya bata mamaki, yau Mr. Fauzi ne yake mata godiya?! “You’re welcome Sir” ta amsa sa a takaice da murna fal a ranta. Hannun nata ya sake ta fice zuwa toilet bayan ta fito ta zauna bakin gadon kamar d’azu “sir kayi sallan Asuba?” K’arya yakeson mata yace ‘eh’ sekuma yaga ba amfani tunda ta riga tasan kad’an daga cikin sirrinsa. Kai ya girgiza mata. Kawai se jikinta ya bata ko isha ma beyi ba.
“Isha fa?” ta tambayesa a hankali cikin dabara yadda bare fusata ba. Nan ma girgiza kai yayi. “Toh Maghrib da La’asar fah?”
Can k’asa k’asa yace, “nayi la’asar.”
“Masha Allah its not too late, barin had’a maka warm water sekayi wanka dan jin dad’in jikinka sekuma kayi yi alwala ka rama sallolin da ake binka koh?” Haka kawai ya tsinta kansa cikin san cika wa Fannah qudiri dakuma burinta.
Kai ya giad’a mata. Nan ta mik’e cikin minti biyu ta had’a ta dawo. “Sir ina bath towel naka?” Nuni ya mata da hannu wajen ta nufa ta ciro “gashi” ta mik’a masa zan jira ka a parlour tana kaiwa nan ta fice.
Sanda yayi dagaske sannan ya samu ya miqe daga kan gadon, bayi ya fad’a. Shigansa bayi da minti d’aya Fannah ta dawo ta nemi sallaya ta shimfid’a masa bayan tayi amfani da wayarta ta gano Qibla. Nan ta fice, kitchen nasa ta nufa ta d’anyi dube dube sede bataga abinda zata dafa masa ba. Fridge nasa ta bud’e froze chicken data gani ciki ta ciro takoma kitchen d’in. Soya masa tayi duka incase ko zeci zuwa rana. Flask ta nema ta juye ciki, tare da had’a masa coffee cikin flask sannan taje tayi arranging dining table masa. Daidai lokacin Anas yafito, k’amshin designer turarukan daya feshe kansa dashi tun daga sama har k’asa ne ya bugi hancin Fannah. Kai ta d’ago tana kallonsa. Sanye yake da ¾ wando fari da farar vest wanda ya bala’in masa kyau, ga wani sheqin da jik’ak’k’en gashinsa ke, kumburin fuskarsan ma ya ragu sosai, sede alamun ciwo da yankan dake ta bakinsa da gefen ido. Da sauri ta kawar da kanta kafin yace ta cika kallo dayawa. A hankali yake tafiyar har ya iso kan dining table d’in, zaman ma da k’yar yayi harda d’an k’ara “argh!” Tare da rik’e cikinsa.
“Does it still hurts?” Ta tambayesa cike da damuwa. Kai ya girgiza mata amman ita tasan zafi yake masa. “I made you breakfast I hope you like it.” Yana kallonta tayi serving nasa kajin tare da juye masa coffeen cikin cup ta tura masa gabansa. “Zan jiraka a parlour, eat please.” Kallon abincin yayi sannan ya kalli Fannah. A hankali ta juya zata fice, hijabinta ya rik’o chak ta tsaya bata juya ba.
“Lets eat together” yace da ita.
“Sir naci abinci I’m full nagode.”
“Please.” Ya fad’i wanda besan lokacin daya fad’a ba shi kansa, meke damunsa? Haka kawai yaji in ba ita bare iya cin abincin ba.
‘Please?’ ta nanata a zuciyar ta. Dagaske Mr. Fauzi ne yau yace mata please? Lallai!
A nitse ta juyo, kujera opposite him ta zauna tana watsa da yatsunta. Plate ya jawo ya juye mata ragowar kazan duka. “Eat” yace da ita. Baki ta bud’e data d’ago kai taga uban kajin daya tara mata gabanta.
“Sir ina zan kai wannan? Yayi yawa.” Hannu ta mik’a zata ja flask d’in a yayinda ya d’aga daga kan table d’in gabad’aya ba tare da yace komi ba.
“Sir please ka rage yayi yawa.” Ignoring nata yayi “lets eat I’m hungry.” Nasa ya soma chi itako har yanzu bata tab’a plate d’in ba ina zata kai wanga kaji?
“Miss Aleeyu eat.” Miyau ta had’iye a hankali ta d’au cinya d’aya ta soma ci. Zaman makokin ne ya isheta tayi gyaran murya sannan tace, “Sir do you want to talk about it?” Sanda ya nisanta sannan yace, “about?” Ba tare da ya kalle ta ba.
“Abinda ya sameka.” Kai ya girgiza “No.”
“Okay...” tace a hankali “but Sir next time ka kiyaye please koma mene neh.”
“Okay” yace mata kamar d’an yaron da mamansa ke masa fad’a. Haka kawai yaji bayasan fad’awa Fannah gaskian al’amarin yasan definately zatayi blaming kanta zatace duk akanta fad’an ya tashi kuma hakan ne komai a sanadin ta ya faru sede bayasan tayi feeling guilty.
“Sir?” ta kira sunansa. “Yes” ya amsa yana sipping coffeensa. “Mesa kace kar na kira Amal na sanar da ita I’ve found you?”
“Saboda banasan susan inada gida anan.” Sam bata fahimce me yake nufi ba, so yake yace bawanda yasan yanada gida?
“Ke kad’ai na fara kawo wa cikin nan, ko Shettima besan I have a paint house ba.”
Meh Mr. Fauzi yake nufi kenan? Does this mean tanada wani matsayi a zuciyarsa da har ya b’oye wa kowa gidan sa hatta family’naa amman ita ya sanar da ita ya kuma barta tana shiga???
*© miemiebee*
No comments:
Post a Comment