BY MIEMIEBEE
Da misalin k’arfe 7:30AM su Fannah suka isa garin Maiduguri daga can suka tsara taxi se sabon gidansu. Ba laifi gidan gaskia yayi arha d’akuna biyu ne da bayi biyu dakuma kitchen. Fannah takasa b’oye murnanta, finally barata auri Ya Farouq ba.
Ya Kaheel da d’ansa Farouq kuwa haka kaman zararru suka riga bin gida one-by-one a Bama su a dole suna neman Fannah da family’nta sam hankalinsa be basa Maiduguri su Fannah suka tafi ba. Har dare suna neman su Fannah ganin ba mahalicci se Allah yasa suka hak’ura suka dawo gida disappointedly.
Fannah kuwa yanzu rayuwa yasoma mata dad’i, a hankali ita da family’nta suke settling a Maiduguri hankalinsu akwance basuda wata tsoro yanzu, Government school me kyau Mami tasamu aka zuba Afrah da Aiman. Fannah kuwa ko kad’an bata sa rai kan zata cigaba da makaranta ba se sanda Baba yayi suprising nata kud’in daya kamata abiya akaisa asibiti ya yafe kan Fannah tayi proceeding karatun ta. Admisson aka nemo mata a Polythecnic course na Business Administration.
Sosai taji dad’i. Koda ta soma zuwa makaranta kuwa kullum cikin hijabi da nik’af take, mazan makarantar su basu ma san ya fuskarta take ba bale ace su gano kyawunta su soma binta. Haka Allah ya cigaba da yima rayuwar Fannah albarka, karatu take sosai ba wasa, Mami tana d’an sayarda irin gwanjon kaya hakan nan dashi suke cafanin gida. Baba kam jiki se worse yake ba kud’in kaisa asibiti a kullum burin Fannah ta gama karatu tasamu aiki ta kai Babanta asibiti.
Ya Khaleel kuwa koda ya kira Mami a waya bata d’aukawa haka yagaji ya bari. Rayuwa de alhamdulillah...
★★★★
_4 YEARS LATER..._
★★★★
Abubuwa da dama sun gudana a both rayuwar Fannah da na Anas. Fannah tanada k’imanin shekaru ishirin a duniya yanzu. Kyanta yagama fitowa, hips nata da dukiyar fulaninta daidai jikinta beyi yawaba kuma be kasa ba masha Allah. Fannah takai mace duk inda ake neman mace, shekarunta kusan biyu da gama poly tayi graduating under Business admin da excllent result. Sede aiki ne har yau babu ta kasa samu, duk wad’anda ake bata ba related to course nata bane daga baya dole ta hak’ura ta karb’a aiki as a waitress (me serving abinci ko drinks a shago kokuwa wajen taron jama’a) a wani babban coffee shop. Dad’in abin Coffee shop d’in nasu sananne ne sosai cikin garin Maiduguri yawancin meetings kokuma party ko biki da akeyi a Maiduguri a Coffee shop nasu Fannah ake zuwa a d’ibi waitresses kuma duk lokacin da akayi haka kud’i suke samu sosai. Da wannan take samu ta biya kud’in school fees na Aiman dana Afrah, amman de yanzu Afrah itama tagama makarantar tana neman kusan shekara da gamawa.
Fannah na k’ok’ari sosai dan tasa Afrah a makaranta sede abun ya gagara, jarin Mami ya jima da karyewa lokacin da jikin Baba yatab’a yin tsanani dole ta tattara ribanta da uwarkud’in business natan duka aka kaisa asibiti. A takaice de yanzu Fannah ce breadwinner’n family’nta duk akanta sukayi depending. Allah sarki Fannah ‘yar Albarka Allah cigaba da miki albarka, ameen.
Samari kuwa ba ta kansu take ba, sau afi a k’irga in aka d’ibesu serving food and drinks a meetings alhazai masu ji da naira suka ganta sesun neme ta amman saboda duk sanda ta tuna da past nata, ta tuna bata da budurcinta martabarta setaji barata iya k’ara yin soyayya ba saboda definately randa aka gano gaskia ita ba budurwa bace za’a guje ta abinda bataso kenan. Bature yace prevention ia better than cure sesa tun farko ma bata sa kanta cikin soyayyar. Daga wanda zata musu k’arya tace takusa aure se wanda zata ce musu tanada aure.
Zancen mafarki kuwa har yau bata dena ba kusan kullum setayi mafarkin mutumin dayayi raping nata wai ya dawo ze sake raping nata, Mami kullum ke calming nata in tayi mafarkin rananda Mami batta kusa kuwa haka zata riga kuka tana b’ari har wayewan garin Allah, Allah sarki!
K’arfe 2:00PM...
Dadai lokacin tashin Fannah daga aiki kenan kafin ta tsari napep ta dawo gida kuma 2:30PM yayi. Tana shigowa gida Aiman dake carafke tsakar gida tasoma mata “Oyoyo Ya Fannah” cewar Aiman dake da shekara 8 kenan baki kam masha Allah. “Oyoyo Aiman” cewar Fannah tare da hugging nata. “Ina sweet d’ina Ya Fannah?”
“Laaa kinga yau na mance ban siyo miki ba in shaa Allah zan siyo miki gobe, yi hak’uri kinji?”
“Ai dama haka kike cewa kullum inda saurayin kine ai baraki mance ba.” Cewar Aiman tana guna-guni.
“Ya SALAM!!!” Fannah ta zaro ido “ban hanaki maGanan saurayi ba? Ni narasa ina kikejin wanga zance.”
“Sekin tambaya ne Ya Fannah?” cewar Afrah data fito daga d’aki “wannan maras kunyan kuma.”
“Ai wallahi Ya Afrah ko kiyi shiru ko in fad’awa Ya Fannah batun wancan saurayin dayazo wajen ki d’azu da Mami batta gida.”
Kai Afrah ta dafe “banza! ai kin riga kin fad’a matan kuma wallahi kisani baran sake baki chocolates ba in yakawo min.”
“Wait wait wait Afrah saurayi kika soma kawo wa gida bada sani na ba?” Cewar Fannah in a serious tone.
“Ya Afrah fa ba saurayi na bane munafircin wannan munafukan ne, Ibrahim nefa classmate d’ina na secondary school.”
“Meaning? Afrah bawai zan hanaki yin samari bane kawai becareful karki yarda da maza so easily zasu kaiki ne su baro ki.”
“In shaa Allah ya Fannah I'm very vigilant.”
_6 hours later..._
Mami da su Fannah ne zaune a d’akinsu suna d’an tab’a hira. “Fannah nace wannan karan se ankai har k’ashen wata za’a biyaku?”
“Eh Mami” ta amsa da fara’arta “wani abu ne?”
“Fannah Habibti nasan kina mana sosai in ba ke family'n nan would have been dead by now, mungode sosai Allah cigaba da miki bud’i ya miki albarka kuma.”
“Ameen Mami dan Allah kidena min godiya, you guys deserve all that I'm doing for you. We are family. Kina buk’atan kud’i ne? Kaman nawa?”
“San samu dubu biyu kinga Maman-”
Katseta Fannah tayi “a’a Mami ba sekin min bayanin me zakiyi da kud’in ba” nan ta ciro wallet nata ta irga N4000 gashi jiya mun samu ankai mu wani meeting da akayi na commissoners so anbiya mu kud’i. “Nan N4000 gashi zdmiki aiko?”
“Fannah N2000 ma ya isheni dan Allah ki rik’e sauran kema kinada buk’atunki ai.”
“Mami dan Allah ki amshi ai ni na baki.” Hannun Mami tabud’e tasa mata kud’in ciki. “Nagode Habibti Allah miki albarka yakuma k’ara bud’i.”
“Ameen Mami nagode da addu’arki Jazakillahu khairan. Barinyi sallah in kwanta k’arfe bakwai zan fita gobe akoi meeting da za’ayi muzamuje muyi serving abinci can.”
“Toh ki huta gajiya nima barinje in samu Babanku. Seda safe.” A tare Afrah da Aiman da Fannah duk sukace “Allah bamu alheri” sannan Mami tafice bayan ta amsa da “Ameen karku manta kuyi addu’a”
Ya Fannah zan d’an samu d’ari biyun kati ne? Cewar Afrah tana b’oye fuskarta.
‘Yar murmushi Fannah tayi “saboda kisamu na kiran samari ba”
“Haba! Dan Allah Ya Fannah wallahi a’a.”
“Toh Allah kaimu gobe zan baki, kwanan nan bana spending much muku kuyi hak’uri tara kud’in nake ne Afrah inason kai Baba asibiti kinde san ya jikin nasa yake.”
Kai Afrah ta giad’a alaman tasani sosai. “Mun gode sosai Ya Fannah Allah k’ara bud’i.” Da amsar “Ameen” suka kashe wuta suka kwanta.
★★★★
*ANAS*
Sosai Anas ya k’ara kyau, fari da fresh, shekaru sun k’aru yazama cikakken saurayi yanzu me shekaru ashirin da uki (23) a duniya. Jikinsa muscular yake, packs nasa na nan guda hud’u dadai ba guda shida irin na wrestlers ba. Tsayayyen na miji yake yad’an k’ara kauri kad’an kan sirancinsa wanda yasake fito da kyansa. Sede kam hali na nan na shaye shaye dukda cewar har a yau Abuu da Ummie basu san yanayi ba, duk wanda yaji ance Anas na shaye shaye ma bare yarda ba saboda erin hankalin dayake nuna wa mutane, kominsa a b’oye yake. A da se in yayi mafarkin Ummimi ko na yarinyan dayayi raing yake sha amman banda yanzu, haka kawai in ya rasa abin yi ze kurb’a abinsa. Allah shirya.
A wannan shekaran yagama makarantarsa na London. Tun tafiyarsa be dawo gida ba sanda ya k’are shekaru biyar d’in cur! Cikin ikon Allah kuwa yafito da excellent result, school nasu sunyi dashi ya soma musu aiki dan iya zanen Anas as an architecture amman sam yak’i saboda san cika burinsa na karya wa mata zuqatansu, yafisan yayi da matan Nigeria kaman sa ba tsinannun turawa ba. Amal tasa ta girma sosai shekarunta 13 yanzu, ba abinda ya rabata da Anas kyau kawai ya d’ara ta da kad’an. Amal an d’an soma wayo amman har yanzu halin autan ta nanan dakuma rashin kunya da rashin shiri da Shettima. Shettima har yau besan ya girma ba shekarunsa ishirin da d’aya da abu a ka amman hakan be hanasa papiro Fannah da gudu in tamasa rashin kunya. Cat and dog Ummie ke ce musu.
Anas kuwa saide in bai gida sarai fa yasan Amal ce da laifi amman haka zebata gaskia yabawa Shettima laifi se in sun keb’e yake basa hak’uri. Sosai Anas yaya ne me hankali, yana kula da k’annansa ba kamar da ba kuma yanzu in yana cikin family’nsa yana murmushi da walwala sosai seda Amal ne kawai yake dariyan da har za’a ga fararen hak’waransa tas. Su Baana da Kashim ma suna nan sun bud’e ‘yar sana’a tare and alhamdulilah Allah na sa musu albarka. Shettina kuwa yasa san jiki a gaba, sam bayasan yin abu wa kansa yayi depending da Abuu kawai ‘cause yanzu masha Allah Abuu arziki se bunk’asa yake tunanin komawa Maiduguri ma yake sede har yanzu nothing is certain yet.
A yanzu haka Anas yana garin Maiduguri yazo neman aiki kwanansa uku kenan yau yakeda shirin fara fita neman aikin, Allah bada sa’a.
Construction industries yasoma bi sede yawancin su se suce basu d’iban masu aiki yanzu ya dawo bayan wasu ‘yan watanni dukda kyan result nasa kuwa haka ya gama yawo a ranar farko besamu aiki ba. Ranar biyu ma haka ya jera kusan sati yana neman aiki kap babu har yayi giving up kan monday ze koma Bama ze huta yanzu a weekends a gidan chairman daya sauk’a.
Yana kwance a guest room kan gado Iphone nasa yayi ringing yana kai dubansa yaga “My angel” Amal kenan. Da murmushi kan fuskarsa ya d’auka.
“My Angel” ya fad’i.
“Na’am Ya Anas d’ina ina wuni?”
“Lafiya qalau Angel ya kike ya school?”
“Lafya qalau Ya Anas, yaushe zaka dawo baka samu aikin bane har yanzu?”
“Ban samu ba Angel ina kan nema har yanzu amman nakega monday zan dawo. Kinasani cikin addu’a ko Angel?”
“Sosai Ya Anas yanzu ma dana idar da sallah sanda nasaka ciki”
“Yawwa My Angel ya Ummie toh?”
“Lafiyarta qalau. Ya Anas kaga Ya shettima d’azu ya mareni.” Ta fad’i kamar zatayi kuka.
Yana kishingid’e jin Amal tace Shettima ya bugeta yasa ya zauna tare da zaro blue eyes nasa. “Ya mareki? A dalilin meh?”
“Wallahi ba abinda na masa Ya Anas kawai fa abokansa ne sukazo yace in gaishesu nikuma nak’i saboda hak’ori na na ciwo shine bayan da suka tafi ya mareni a bayana wajen har yayi pink.”
Sarai yasan Amal da rashin kunya daga ji ba k’in gaishe da abokan nasa kad’ai tayi ba in aka bibiya halan har zaginsu ma tayi.
“Toh yi hak’uri Angel yanzu zan kirasa in sissilesa na dawo kuma zan rama miki.”
“Yawwa Ya Anas ba-bye.” Ding! Ta kashe.
Komawa yayi ya kwanta tare da zira wa ceiling ido yana murmushi wa kansa daidai lokacin wayarsa tayi k’ara yana kai dubansa yaga number ke kira, zurawa screen d’in ido yayi yana nazarin wacece can yace wannan number Meenor ce. Sanda ya kusa tsinkewa sannan ya d’aga batare da yace komi ba wata murya ce me zak’in gaske ta soma magana a hnakali dukda cewar cikin tashin hankali kuwa take.
“Haba dan Allah blue eyes, menayi kuma wannan karan? Tun jiya nake ta trying number’nka sarai kana gani ignoring d’ina kawai kake.”
“Toh nayi, zaki iya yin wani abu ne?” Gatsau ya bata amsa.
“A’a dan Allah blue eyes kar muyi haka dakai I'm sorry, I love you.”
“Meenor nomore of that we are done, karki sake kira na please ko kin kira ma barin d’auka ba.” Karap ya katse wayar. Kafin ya ajiye ta soma kira again sa number’n nata yayi a call divert tare da sakar da murmushi hakwaran samansa suka bayyana. “7 of 100 kenan.” ya cize light red lips nasa. Ma’ana cikin mata d’ari daya d’au alwashin ze kariya masu zuciya yaci nasara kan guda 7 wannan ma tun kafin yasamu aiki yazama billonaire kenan!
*© miemiebee*
No comments:
Post a Comment