Wednesday, 8 August 2018

RANA D'AYA!

BY MIEMIEBEE
PAGE 32




    "Assalamu Alaikum Aunty ina kwana?"

  "Sofin gaye ya kike?"

  "Lafiya k'alau Aunty ya Hindu?"

  "Hindu tana gida ni na fita school ya uwar d'akinki?"

  "Hmmm Aunty ina da labari mey dad'i miki."

  "Kai Sofin gaye har ta gama haukacewan ne?"

  "Gashi Uncle jiya yazo d'akina yana tambayata ko meke faruwa na tsara mishi labari kaman yadda kikace inyi yanzu haka yace ze nemo malami ayi mata ruk'iya don shima ya fara zargin ko aljanun ne."

  "Kin min dau-dai shin ta sake yi masa girki?"

  "Ai hanata yayi yau gata chan a d'akinta se kuka take."

  "Bravo alaiki Sofin gaye tsaraban ki na nan na tanadar miki."

  "Toh amma Aunty yanzu idan aka kira Malamin ya duba ta yace lafiya fah? Za a iya gano ni ke k'ara mata gishirin fah."

  "Inji wa? Taya za a gane ki bayan duk malaman ruk'iyan nan kud'i kawai suke so? Da mutum nada ciwo da bashida shi muddin an kaisa gun su se sun bada magani dan abasu kud'i in return saboda haka ki kwantar da hankalinki in shaa Allah baza a kama ki ba kede ki cigaba da gashi."

  "Toh Aunty."

  "Mission number one complete muddin akayi mata maganin kar ki sake 6ata mata girki mu barta nan haka se idan an kwana biyu se mu fara mission number two."
 
  "Ohh kar in sake sa mata gishirin?"
 
  "Eh mana baya riga ya hanata yi mai girki ba yanzu?"

  "Eh."

  "Toh kinga idan akayi mata maganin seya zammana kaman dama akwai matsalar amma an samu an magance yanzu."

  "Nagane."

  "Yauwa jeki sameta kiyita bata hak'uri idan Ya Afzal ya dawo kice d'azu ma kin ganta ita kad'ai tana suratai."

  "Toh Aunty" da haka sukayi sallama. Wani irin dad'i maras misaltuwa Nazeefah taji burinta ya cika ta haukatar da Amal ta sa Afzal ya daina cin girkinta, ita taso ace ta6in hankali ma Afzal ya soma zarginta da shi bama aljanu ba yadda za a d'auketa akaita chaan asibitin mahaukata ta fara rayuwarta ta bar mata Afzal nata amma hakan ma be 6aci ba.

  ****
   Da Azahar Afzal ya wuce restaurant yaci abinci daga chan ya biya gida gun Ummi kallo d'aya tayi masa ta gano akwai matsala.

  "Prince?"

  "Ummi" ya amsa a ksalance.

  "Meke faruwa?" ta tambayesa.

  "Ummi it's Amal."

  "Subhanallah lafiya dai ko?"

 "Ummi I don't know na rasa gane ta6in hankali ne yake neman kamata ko kuwa aljanu ne suke mata wasa da hankali."

  "Subhanallahi meya faru? Wani abun tayi ne?" Labarin komi ya kwashe ya bata batare da ya skipping komai ba.

  "Shine baka ta6a bud'an baki ka fad'a mun ba Prince? Allah sarki Amal gata mahadacciyar Qur'ani oh! kowa da tasa jarabawan amma anya kuwa aljanu ne? Ba ta6in hankali ba?"

  "Ummi I don't know I'm totally clueless kuka take yau seta yimun breakfast amma na hanata saboda ko tayi ba iya chi zan ba banda gishiri da borkono ba abinda yake cikin girkinta yanzu."

  "Kuma ba ita take sawa ba?"

  "Gashi na tambayi Safiyya tace a gabanta Amal tayi girkin bata sa gishiri ba shiyasa nake zaton ko aljanu ne."

  "Kuma gashi yarinyan tace tana ganinta tana magana ita d'ai?"

  "Har sau biyu ma tace."

  "Ikon Allah kode aljanun ne toh?"

  "Shine nima ban sani ba mu fara kaita psychiatric hospital (asibitin mahaukata) ne su duba ta ko mu fara dana gargajiyan?"

  "Toh nide gani nake kaman aljanu ne amma a fara kaita asibitin idan sun kasa gane kan abun se mu dawo na gargajiyan, akwai sanannen malamin dana sani yana ruk'iya sosai zan nemesa."

  "Toh yanzu ya zan fara sanar da ita zan kaita asibitin mahaukata Ummi? Wallahi bazata amince ba bayan nan kuma gani zatayi kaman naci amanarta ne ina danganta mata ciwon hauka kuma bana son su Mami suji maganan nan se idan abu ya gagara tukun zamu sanar dasu ko ba haka ba?"

  "Tabbas kayi tunani Prince tunda de yanzu Amal responsibility'n muce."

  "Toh kinga..."
 
  "Ka san yadda zaka sanar da ita Prince ai matarka ce zata fahimce ka in shaa Allahu."

  "Toh Ummi I'll try, please karki manta kiyi wa Malamin magana."

  "In shaa Allah Prince kuma duk abinda akwai ka kira ka sanar dani Allah ya bata lafiya."
 
  "Ameen bari zan koma" rakiya tayi masa sannan ta dawo ciki. Yana isa gida Safiyya tayi mishi sannu da zuwa sannan ya k'arisa d'aki inda Amal ke mik'e akan gado amma ba bacci take ba ko da taji shigowansa bata juya ta kallesa ba Sallama yayi ta amsa ciki-ciki ba tare da ta kewayo ba. Kayan jikinsa ya rage sannan ya k'arisa gefen gadon ya zauna a gefenta.

  "Kitten?" Ya kirata sede bata amsa ba. "I called you twice baki d'aga ba why?"

   "Ban san inda na jefar da wayan ba" ta amsa ba tare da ta kallesa ba. Hannu ya mik'a ya mik'ar da ita zaune "How're you feeling?" Ya tambayeta.

  "Kaci abinci?" Ta mayar masa tunanin da take tayi tun d'azu kenan, shin yaci abinci, mey yaci? Ya k'oshi? It pains her alot idan ta tuna Afzal baze sake cin girkinta ba yanzu, sosai zuciyarta keyi mata k'ona.
  Allah sarki sosai ta basa tausayi, bata ma damu da lafiyarta ba, ita burinta kawai taji yaci abinci ne, "Kefa kin ci?" Ya tambayeta.

  "Yaya I really want to cook for you koda sau d'aya ne ka barni in sake yi maka girki please Yaya I miss feeding you" ta rok'esa yayin da idanunta suka shiga cikowa da hawaye.

  "Kitten please cut it out, kibar kukan haka."

  "Then allow me cook for you and feed you one last time."

  "Baby" ya ambaci sunanta had'e da rik'o hannunta cikin nasa yana murzawa a hankali "Ba kida lafiya ki bari se in kin samu sauk'i kinji? I myself miss your cooking kinsan kece best cook d'ina ko?"

  "Yaya can't you see? I'm perfectly okay wallahi lafiyata k'alau ba abinda yake damu na" kwantar da ita yayi a jikinsa yana shafa bayanta a hankali "Zamu kaiki asibiti gobe su duba ki in shaa Allah idan kika samu sauk'i se kiyi resuming normal duties naki ki cigaba da yimun girki kinji?" cike da rashin fahimta ta d'ago kanta tana kallonsa "Asibiti Habib Albi?"

  "Kitten I'm so sorry-"

  "No" ta furta cike da tashin hankali tare da janye jikinta daga nasa.

  "Kitten please understand me-"

  "No Yaya" da sauri ta janye hannunta da yake k'ok'arin rik'ewa "Mey kake nufi da hakan? Ina da hauka?" Ta tambayesa cike da d'umbun mamaki.

  "No Kitten ba haka nake nufi ba" ya amsa a rud'e shima, a rayuwa ba abinda yafi tayar masa da hankali kaman yaga Amal tana kuka, da zaran yace ze rik'e hannunta se ta ja da baya.
 
   "Ni Mahaukaciya?" Ta ambata da mamaki yayinda hawaye ke bin k'uncinta.
  "Kallon mahaukaciya kake mun Yaya?"

  "Kitten please-"

  "Yaya.." kasa cewa komi tayi kawai ta rushe da wani irin masifaffen kuka yayinda ta mik'e da hanzari dan bar mai d'akin. Hannunta ya cafko ya kwantar da ita a jikinsa had'e da matse ta gagam wane wani na shirin k'watar masa ita. Kokowa take sosai ya saketa amma yak'i hak'uri ya ta bata yana shafa bayanta a hankali har seda ya sauk'ar da temper'nta. A hankali ya d'agota yana share mata hawayen nata "Kitten please understand me bawai cewa nayi kina da hauka ba, bazan ta6a kwatanta ki da mahaukaciya ba but contrary to abubuwan da suke faruwa bakiya tunanin ko akwai wata matsala?"

  "Yaya ashe Allah ze kawo ranan da zaka yi mun kallon mahaukaciya?" Ta tambayesa hawaye na bin k'uncinta.

  "Kitten I will never refer to you as that kema kin sani I love you and I only want the best for you, dan za ki ga psychiatrist doctor (likitan mahaukata) bawai hakan na nufin kinada hauka bane, ze iya yuwuwa wani matsalan ne daban yake damun ki psychologically ko stress ko makamancin hakan."

  "There is no stress Yaya and I'm not losing my mind ni ba mahaukaciya bace kana tsammanin zansa gishiri acikin girki ba tare da na san nayi hakan bane? I told you ni bani kesa gishiri da attarugu ba, ba ni bace!" Sosai ranta ya 6aci taya upon all people Afzal baze yarda da ita ba? Taya za'a ce mijinta tilo yana yi mata kallon mak'aryaciya kuma mahaukaciya? Cikin tsananin kuka tace, "I thought you love me Yaya, I thought you trust and believe in me."

  "Of course I do Darling, I love you with every burning fiber in my soul and I do trust and believe in you than I do myself."

  "No Yaya inda har kana nufin abinda ka fad'a da baza ka fara tunanin kaini gun likitan mahaukata ba, da zaka yarda dani idan nace maka bani kesa gishiri da borkono cikin girkin ka ba."

  "I know Kitten nasan ba ke kike sawa ba shiyasa na fara zargin ko aljanu ne suke miki wasa da hankali."

  "Aljanu? Yanzu kuma mey kallon iskokai kake mun Yaya? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" juyawa tayi da niyyan bar mai d'akin bata ma jin zata iya yi masa magana. Da sauri ya sha gabanta "Kitten please ki fahimceni ki sani lafiya nake nema miki wallahi na gaji da ganinki haka cikin k'unci da kuka kullum, kiyi hak'uri ki bari a magance miki wannan matsala please."

   "Ni bana tattare da aljanu I know how I feel saboda haka ba wanda zeyi mun ruk'iya, nasan kaina kuma na dogara da addu'o'in da nakeyi."

  "Kitten bawai ina jayayya da hakan bane ni kaina sheda ne game da yadda bakiya wasa da addu'o'in kariyan nan I'm aware of everything."

  "Toh mey kake nufi Yaya? Kallon mey iskokai da ta6in hankali fa kake mun how do you expect me to feel and react?"

   "Darling I'm sorry but I'm just worried, ke da bakinki kika ce bake ke sa gishiri da borkonon nan ba kuma na amince da hakan I trust you Kitten amma toh wa yake sawa? Bakiya tunanin akwai wata 6oyayyan al'amari? Kuma baza mu ta6a iya gano inda matsalar take ba bale a magance miki se har idan kin amince kin bada had'in kai Kitten. I promise no harm will come to you, I've got you Baby, ba wanda yace kina da ta6in hankali I just need to find out what's really going on. Please calm down everything is going to be alright in shaa Allah okay?" Ya k'are yana matso da ita kusa da shi. Cike da dabara ya kwantar da kanta a k'irjinsa yana shafa kanta "I love you so much" ya furta mata, a hankali yaji hannayenta a bayansa tana hugging nasa back "I love you too" ta furta. Washegari Afzal be fita office ba, wanka sukayi tsaf tare suka shirya, da kansa ya had'a musu breakfast sannan suka wuce psychiatric hospital inda aka duba Amal akayi mata gwaji da dama akan washegari su dawo su kar6i sakamako.
 
   Washegari Afzal ya koma ya amshi results d'in shi kad'ai kasancewar daga office ya biya wajen sede da mamaki sakamakon ya nuna ba abinda yake damun Amal, hankalinta dai-dai yake dana mutane ba wata matsala. Hakan ba k'aramin d'aure wa Afzal kai yayi ba don haka kawai ya yanke hukuncin aljanu ne toh sukeyi mata wasa da hankali nan take ya kira Ummi yayi mata bayani dama ta riga tayi magana da Malamin yace koda yaushe suka shirya suje yana jiransu. Address kawai ta tura masa.

   Gida gun Amal ya koma yaci ace ya koma gun Nazeefah dake kwanan Amal ya k'are amma baze iya barin Amal cikin wannan yanayi da iska suke wasa da hankalinta haka ba har se idan ya samo mata lafiya. Nazeefar yayi niyyan kira ya sanar da ita halin da ake ciki se ya sha'afa. Itako chan a gidanta ta gama girki ta gama komi jiran zuwansa kawai take amma shiru gashi har shida da rabi yayi. Jin shirun yayi yawa gashi be kirata ya sanar da ita dalilin hakan ba ta d'au waya kawai ta kirasa a karo na farko ya d'aga suka gaisa.
  "Kin jini shiru ko?"

  "Eh Ya Rouhi lafiya?"

  "Amal ce bataji dad'i ba I'm afraid I can't make it today ina fatan hakan ba matsala."

  "Allah sarki meke damunta?"

  "Ermm... ermmm zazza6i ce" yayi mata k'arya haka kawai yaji baya son ya fayyace mata gaskiyan al'amarin. Amal na kwance kan cinyansa tana sauraransu.

  "Ayyah ka gaisheta da jiki da Allah, Allah k'ara mata lafiya zan kirata in gaisheta."

  "Ameen in shaa Allah ba wata matsala ko?"

  "Ba komai."

  "Toh seda safe I'll call you tomorrow."

  "Alright take care" wata mak'irar murmushi ta sakar yayin da ta katse wayar. "Ai kad'an ka ga se zaman gidan chan ya gagareka you'll see."

  "Nazeefah na gaisheki" ya sanar da Amal had'e da sanya hannunsa cikin gashin kanta yana massaging mata cikin kai a hankali, kai zalla ta gyad'a masa. "Kina jin yunwa?" Nan ma kai ta kad'a a hankali.

  "I called Ummi earlier batun Malamin tace ta riga tayi mai magana so she sent me his address gobe zamu kaiki baki da wani test a school ai ko?"

  "Babu" ta amsa ciki-ciki. Wace irin msuiba ce wannan? Tana ji tana gani ana dangata mata ciwon aljanu ciwon da tasan ba ta da shi. Kan nata ya cigaba da massaging mata chan ya dafa musu indomie bayan sun gama ci sukayi wanka sukayi sallah suka tofe addu'an bacci sannan suka kwanta. Washegari da yamma bayan sallan La'asar suka wuce gidan Malamin. A mota ya barota ya k'arisa ciki bayan sun gaisa yayi wa Malamin bayanin abinda yake damunta ciki harda ce masa da Safiyya tayi akan Amal ita kad'ai tana magana ya kuma buk'acesa da koda ya shigo da Amal d'in kar yayi maganan komai a gabanta. Bayan Malamin ya fahimce shi ya koma ya shigo da Amal karatu Malamin ya shiga yi mata amma ba alamun komai a tattare da ita, bayan ya k'are karatun yayi mata hayak'i nan ma ko alaman aljanu babu.

  "Gaskiya bata tattare da iska sede ze iya yuwuwa shafanta sukeyi su barta amma bawai sun shiga jikinta ba."

  "Toh yanzu ya kenan Malam?" Afzal ya tambaya.

  "Sede ince ta dage da addu'a ta kuma rage kalle-kalle da fita da kai a bud'e. Zan baku turaren almisky tana amfani da shi tana kuma shan man hul6a ta na karatun Al~Qur'ani sosai in shaa Allahu iskokan zasuyi nesa da ita."

   "Tana yi sosai wallahi Malam mun gode in shaa Allah zata kiyaye duka ababen da ka irgon."
  Almiskin ya d'iba musu da man hul6an Afzal ya biya kud'in. Tun shigansu mota har suka dawo gida Amal bata mai magana ba. Waje ya fita ya kira Ummi ya sanar da ita abinda Malamin yace.

  "Ai Malamin ya iya aiki da ikon Allah zata samu sauk'i kuma shi ba ta kud'i yake ba kaga idan wani ne yanzu ya rink'a raina mana wayo kenan yana mana k'arya akan lallai akwai aljanun a jikinta ayita ruk'iya ana kashe kud'i ana bata wuya."

  "Hakane kam wallahi thank you so much Ummi."

   "Ya Amal d'in toh?"

  "Lafiyarta."

  "Tana kusa ne ka had'amu?"

  "Eh toh" nan ya bud'e k'ofan ya dawo ciki ya k'arisa ciki. "Kitten?" Ya kirata.

  "Uhmm?" Ta kewayo tana kallonsa

  "Ga Ummi tana son ku gaisa" ba gardama ta amsa suka gaisa sannan ta miyar masa. Ya so ya sake kwana mata amma baya son ya shiga hak'k'in Nazeefah dayawa dan haka ya shiga tattare abubuwan da ze buk'ata. Yana gamawa ya kewayo kan Amal dake mik'e kan gado "Kitten zan koma wajen Nazeefah" ya sanar da ita yana takowa inda take hannunsa ya mik'a mata kamar wacce bazata kama ba tasa nata ciki a nitse ya mik'ar da ita yana shafa fuskanta a hankali.

   "Kina amfani da turaren kinji? Man hul6an kuma kina sha safe da yamma kaman yadda Malamin ya fad'a nasan kina karatun Al~Qur'ani sosai ba sena ce kiyi ba Allah baki lafiya Sweetheart I love you so much." Kai ta gyad'a masa a hankali "Muje in raka ka" da sauri ya rik'o ta kafin ta ku6uta daga hannunsa yana mey zagaye hannayensa a 'yar kunkuminta.

   "Where's my cheerful and loving Kitten please tell her I miss her so much and that I want her back"  yayi maganan yana shafa kan lips nata a hankali da babban yatsansa. "Allah baki lafiya Kitten I can't wait for you to get better, I love you so much."

  "I love you too Habib Albi" ta sanar da shi a hankali ya mik'a yayi owning lips nata kissing her gently and taking her fears away seda nishinta ya kusan d'aukewa ya saketa ya shiga shafa fuskanta a hankali "Take care of yourself okay? Duk abinda kike buk'ata ki fad'awa drivernki yaje ya siya miki idan kuma Safiyya zata iya seta girka miki amma kar ki sakeyin girki se kin samu sauk'i kinji?" kai zalla ta gyad'a masa. "Na ajiye miki kud'inki a gaban mirror ki kwanta ki d'an huta kafin Maghrib Sena dawo."

  "Thank you bara in raka ka."

  "A'a kiyi zaman ki I can manage" peck ya sauk'e mata akan goshi sannan ya fice. Koda ya koma gun Nazeefah hankalinsa gabad'aya na akan Amal ne minti minti yake d'aukan waya yana kirarta yana tambayarta ko lafiya se yanzu yake regretting meya hanasa amsan lamban Safiyya da ita zena kira yana tambaya ko lafiya baya son abin da tak'urawa Amal tasa, sosai yake missing nata ji yake shima kaman ba shida lafiya. He can't explain how much he's missing her giggles, laughs and smiles. Suna zaune a d'aki Nazeefah na masa tausa tayi gyaran murya "Ya Rouni?" ta kirasa cikin wani irin salo.

  "Yes Rabba'atul Bait?"

  "What's wrong tun shigowanka jiya na ganka wani iri meke damunka?"

  Be 6oye mata ba ya sanar da ita gaskiyan al'amarin "It's Amal Rabba'atul Bait I'm worried about her."

  "Allah sarki zata samu sauk'i in shaa Allah muna kan mata addu'a."

  "Thank you Rabba'atul Bait."

  "Don't mention love amma ciwon nata zazza6i ne kawai?"

  "Wani abu ne?"

  "A'a d'azu dana kirata ne take cemun wai abun nata harda iska-iska haka."

  "Ita da bakinta?"

  "Eh" ta jaddada masa dukda kuwa tasan k'arya takeyi basu ma yi waya da Amal ba yau bale har wai Amal ya sanar da ita akan iskokai ne suke damunta.

  "Malamin yace basu shige ta ba kawai sun shafeta ne amma ya bamu magani in shaa Allah zata samu sauk'i."

  "Allah sarki Amal, shin bata karatun Al~Qur'ani ne? Kasan ance aljanu basa kama me yawaita karatun Al~Qur'ani."

  "Tana yi kinsan shi jarabawa kowa da irin nasa, Amal mahaddaciyar Al~Qur'ani ce kullum seta d'au Qur'ani tayi karatu I guess wannan itace jarabawarta." Haushi taji sosai Amal na da haddan izu sittin akanta ita tana nan tana fama da izu goman k'asa. Taya bazata tsani Amal ba bayan ta ko ina seta nuna tana son ta k'ureta.

  "Allah sarki Allah bata lafiya toh" ta fad'a ba don tana so ba tana k'wak'ulo murmushin dole.
 
  "Ameen" ya amsa.

****
  Duk da kwanan Nazeefah ne hakan bai hana Afzal zuwa duban Amal da safe kullum kafin ya wuce office, da kwanan ta ya zagayo kuwa komi shi yake k'ok'arin yi mata, ba k'aramin kula da ita yake ba. Da yamma idan ya dawo daga office zasu d'au Qur'ani suyita karatu har zuwa Magriba. Tun ranan da suka dawo daga gun Malamin Afzal be sake gane kan Amal ba. Gabad'aya yanayinta ya canza a gidan sa6anin yadda suke zama suyi hira suyi dariya yanzu kam jugum sede shine ma yayita zuba ita befi tana amsa sa da eh ko a'a ba. Hakan ba k'aramin damun Afzal yake ba he can't explain how much he's missing her.

   Yau sati biyu kenan tun dawowansu daga gun Malamin, cikin ikon Allah ta shiga sake sakewa da Afzal ta fara yi mai hira har suka koma zama yadda suke da. A hankali a hankali suka fara shiga kitchen tare suna yin girki har yazo ya fara barinta tanayi ita kad'ai. Afzal baze iya kwatanta irin murna da farin cikin da ya tsinta kansa aciki ba da Amal ta soma yin girki ba matsala yanzu, Ummi ya soma kira ya sanar da ita. A kullum son Amal dad'a k'aruwa yake a birnin zuciyansa, tabbas baze iya rayuwa ba ita ba.

   Yau ya na tashi daga office ya wuce gida straight he can't wait ya iso gida ya samu Kitten tasa. Fresh flowers ya tsaya ya saya mata a florist shop sannan ya k'arisa gida. Sede sa6anin kullum yau Kitten tasa bata fito ta tare sa ba k'arisawa ciki yayi amma Safiyya kad'ai ya tarar bayan ta mai sannu da zuwa ya tambayeta ko ina Amal take ta ce mai tana d'aki. D'akin nasu ya k'arisa sede be ganta ciki ba, kasa kunnen da zeyi yaji splashes na ruwa a bayan gidan don haka yayi knocking bisa k'ofan "Kitten I'm home."

  "Welcome home Habib Albi."

  "Mey kikeyi wanka?"

  "Eh" ta amsa.

  "In shigo?"

  "Ka shigo Habib Albi" ta amsa tana murmushi, kayan jikinsa ya rage ya d'aura towel sannan ya d'au flower'n ya shiga bayin. "Here this's for my adorable Kitten."

   "Awwn thank you Habib Albi" tace tare da amsa "I love orchids" ta sanar da shi "Don't mention Love, matsa min toh in shiga" batayi gardama ba ta gyara masa ya shiga ya zauna had'e da riginginar da ita a jikinsa. Wasa suka tayi cikin tub d'in k'arshe suka wanke jikinsu suka d'aura alwala sannan suka fito. Sosai yaji dad'in kwana biyun da sukayi tare ba k'arya yayi missing delicious nata baze fasa yima Allah godiya ba da ya bawa Kitten nasa lafiya. Musamman ya koma gun Malamin da yayi musu maganin ya mishi kyautan kud'i. Kaman kar ya tafi yau da kwanansa ya k'are, yadda ta saba raka sa haka tayi ta kaisa har gun mota inda ya shiga kissing nata awajen be saketa ba seda ya tand'e jan bakin data shafan tas sannan ya sallameta ta dawo ciki. Yana isa gidan Nazeefah ta taresa da wani hot kiss nata itama bayan sun k'arisa d'aki seya karanci yanayinta ya sauya a lokaci guda.

  "Rabba'atul Bait lafiya?"

  "Ai kai zan tambaya Ya Rouhi" ta amsa tana turo baki

  "Da nayi me Sweetheart?"

  "Ba wani Sweetheart d'innan ai nasan inda ka ajiye ni."

  "Haba Darling meya faru haka?" tasowa yayi daga gaban mirron ya k'arisa inda take had'e da zauna a gefenta.

   "Gaya mun waya ta6a mun Rabba'atul Bait d'ina."

  "Ba amaryarka bace."

  "Amal?" Kai ta gyad'a cike da shagwa6a.

  "Me kuma tayi?"

  "Cemin tayi kullm ka fita seka taho mata da flower ni dai-dai da RANA D'AYA ko yashi baka ta6a ibowa kace gashi Rabba'atul Bait wannan naki ne shin kana ma sona kuwa Ya Rouhi?" Mamaki da kunya yaji duka a lokaci d'aya. Be ta6a tsammanin hakan daga gun Amal ba. Wani irin abin kunya take shirin yi masa haka? Taya zata na fad'awa Nazeefah abinda yake mata? Meye riban hakan?

  "Bayan nan kuma tace sede baka je gida mata ba baka bari ta zauna a ko ina se a kan cinyanka, ko abinci akan plate d'aya kuke ci ni duk baka mun ko d'aya Ya Rouhi" ta sanar da shi kar kusha mamaki komi nan Safiyya ne ke fad'a mata. Afzal baze iya kwatanta irin tsananin kunyan da yaji ba yayinda ya kasa daina mamakin dalilin da zai sa Amal tayi masa haka, shin mey ya buga mata kai? So take ta 6ata tsakaninsa da Nazeefah?

  "Rabba'atul Bait I'm really sorry" ya furta cike da disappointment, a hankali ya d'agata ya zaunar da ita kan cinyoyinsa.

  "Ba komai dama nasan kafi son Amal akaina ai."

  "Please don't you ever say that nasan nayi kuskure amma kiyi hak'uri I'll make it up to you in shaa Allah I promise." Hannayenta ta zagaye a wuyansa "Can I count on you?"

  "In shaa Allah Rabba'atul Bait, I love you so very much."

  "I love you more Baby" ta amsa fuskanta ya shiga bi yana kissing har seda ya kai kan lips nata.

***
  Bayan sallan isha ya d'auketa a mota suka je suka ci abinci a waje daga chan suka wuce 3G inda ta kwashi jakukkuna guda uku masu kyau, tana jiran taji yace bari ya d'auka wa Amal kaman yadda ya saba fad'a ta ji yayi shiru yau kud'in kawai ya biya suka fito. Ai kuwa idan haka ne plan nata ya fara aiki kenan, da alama bai ji dad'in abinda tace masa Amal tayi bane shiyasa ko jakar ma yak'i sai mata, ai ko idan haka ne ta ringa 6ata Amal a gabansa kenan se tasa ta fita masa a rai gabad'aya. Zata sa Safiyya ta musu ido sosai tana d'auko mata rahoto.

***
   Kamar yadda ta d'au alk'awari hakan ta cigaba da 6ata Amal gaban Afzal, duk abinda yayi ma Amal se Safiyya ta kwashe ta fad'a mata itako idan kwanan ta ya zagayo seta maraice fuska tace ai gashi-gashi abinda Amal ta kirata ta fad'a mata. Sosai abun yake k'ona ma Afzal rai be ta6a sanin Amal da halin nan ba se yanzu shin meye ribanta na fad'awa Nazeefah abubuwn da yakeyi mata? Sabida ta 6ata tsakaninsu ne take hakan kokuwa dan ta nuna wa Nazeefah a fili baya adalci a tsakaninsu? A kullum 6aci ransa yake idan Nazeefah ta irga masa abubuwan da yayi ma Amal wanda beyi mata ba amma dai-dai da RANA D'AYA be ta6a tunkarar Amal da maganan ba. A tunaninsa da kanta zata gano abinda takeyi ba dai-dai bane ta daina amma ina abun se worse yakeyi ko bathroom slippers ya sai mata be sai wa Nazeefah ba seya ji a bakin Nazeefah sosai abin ya isheshi har ya zamma ko tsinke ya daina saiwa Amal yana kai mata idan har ya sai mata abu to ya sai wa Nazeefah ne amma special treatment kam ya daina bata.

     ****
     Yau ranan ya kewayo kwanan Amal wanka tayi tasha kwalya tasa sabon d'inki ba k'aramin kyau tayi ba sannan tayi zaman jiransa se after six ya iso shida kullum 5:30 ya shigo. Tun daga bakin parking lot taje ta taresa sede kaman zuwansa na biyu da suka wuce yau d'inma haka ya shigo fuskansa a d'aure, d'aure fuskan yau d'inma yafi na kowanne, ko attempting kissing nasa da ta gwada yi se taga yayi dodging abinda be ta6ayi ba shin meke faruwa? Jakansa ta gwada amsa nan ma ya hanata ya wuce gaba, cike da mamaki ta bi bayansa suka k'arisa ciki.

   "Ya office?" ta tambayesa bayan sun shigo d'akinsu.

  "Lafiya" ya amsa sama-sama ko kallonta beyi ba. Toh me tayi yake shasshareta haka?

    "In sirka maka ruwa ko?" Ta tambayesa.

  "Yanzun na yi a chan gida karki damu."

   "Toh muyi tare" ta sake fad'a duk don ya amince. "Maybe next time" ya amsa nan ma ko kallonta beyi ba. Wow! Shin meke faruwa? Ta tambayi kanta.

  "Toh abinci fah?" Ta sake tambayansa a hankali, sosai jikinta ya mutu da irin short-short answers da yake bata.

  "Nazeefah ta bani" ya amsata, amsan da a iya zamansu be ta6a bata ba.

  "Habib Albi amma kullum fa kana ci idan ka dawo."

  "Bana jin yunwa Amal" taji ya kirata gatsau da sunanta. Tirk'ashi! Bata sake yi masa magana ba se chan wajajen k'arfe tara. A tunaninta wai ko stress ne daga office yake sanya sa yin abinda yake yi bari ta barsa ya huta. Bayan ta k'are karatun Al~Qur'ani ta d'an ta6a na bokon ta fito ta sami Afzal dake zaune a parlour yana kan tattara documents nasa yana sanya su cikin briefcase. K'arisawa tayi ta zauna akan cinyansa.

   "Sekin yi hak'uri kin tashi na buge k'afa na d'azu zafi yake mun" yayi mata k'arya.

  "Subhanallahi! Sannu shine baka sanar dani ba? Mu shafa maka man zafi ne?"

  "Karki damu I'll be fine" da haka ya sauk'eta.

  "Baka ci abinci ba Habib Albi."

  "Bana jin yunwa."

  "Kana nufin yau abinci na zeyi kwante kenan?"

  "I'm sorry but I guess yes excuse me" yana kaiwa nan ya d'aga briefcase nasa ya koma d'aki. Mamaki ne sosai ya cika Amal shin mey tayi wa Afzal yake shareta haka? A iya saninta de bata mai komai ba meyasa yake shareta haka toh? Safiyya ta kira ta tayata suka juye abincin suka sa a fridge sannan ta bi Afzal ta koma d'akin inda ta tarar da shi yana tu6e kaya da alama wanka zeyi. "Habib Albi wanka zakayi?" Ta tambayesa inda ya gyad'a mata kai zalla.

  "Muyi tare?"

  "Bacci nakeji Amal ki bari ko gobe" har cikin ranta taji zafin yadda yayi rejecting nata, ta rasa mey tayi yake yi mata haka amma tabbas tasan da akwai abu a k'asa amma bazata masa magana nan take ba zata yi masa uzuri halan wani abun ne yake damunsa. Haka tana ganinsa ya wuce bayin ya watsa ruwan ya fito ya sanya boxers nasa, bata ce da shi komai ba ta mik'e ta shiga itama fitowan da zatayi ta gansa da coke da cookies yana ci so ashe yana jin yunwa amma yayi mata k'arya wai baya ji don kar ya ci girkin ta. Mey tayi masa yanzu da baze ci girkinta ba? Hmm duk yadda ranta ya 6aci da kuma yadda taso tambayan sa dalilin da yasa yakeyi mata haka kwana biyu ta danne zuciyarta ta fasa. Wani shara-sharan rigan baccinta ta sanya tana ta zirga-zirga a d'akin duk don ta karkatar mai da hankali amma ko d'aga ido ya kalleta beyi ba bale yasan tana yi. Yana gama cinye cookies nasa yayi disposing goran da ledan ya haye gado ya kwanta had'e da juya mata baya. Addu'o'in baccinta ta tofe sannan ta samesa akan gadon ta gangaro da pillonta kusa da nasa inda yayi shiru kaman be jita ba.

   "Habib Albi?" Ta kirasa shiru yayi kaman baya jinta. "Habib Albi I miss you" ta sanar da shi. "Please turn around" ta buk'acesa amma ko ya motsa bale tasan yanayi. A rayuwa baya son munafikin mutum mey yayi zafi da zata na kiran Nazeefah tana yi mata gulman abubuwan da yakeyi mata se yazo nan kuma ta tsaya tana maraice fuska tana acting kaman wata salihar k'warai.

   Amal ta kasa bacci ranan se tunanin dalilin da zaisa Afzal yana shareta haka ta kwana tana yi, be ta6a dawowa be nemeta ba se wannan karan gashi ko da ta gwada nemansan ma yak'i ya kulata kuma sarai tasan ba bacci yakeyi ba lokacin.

    Washegari ko da ta gaishesa sama-sama ya amsa, yana shiga bayi don yin wanka ta wuce kitchen ta shiga had'a masa breakfast sede da ya fito ko kallon kulolin nata beyi ba bale yayi tunanin ci. Yana cikin had'a black tea se gata ta fito don serving nasa.

  "Karki damu bazan ci ba."

  "Bazaka ci ba kuma Habib Albi?"

  "Eh" ya jaddada mata.

  "Toh mey kakeso in girka maka?"

  "Karki damu ina Safiyya? Safiyya!" Ya k'wala mata kira nan da nan ta fito daga d'akinta ta gaishesa sannan Amal.
 
   "Zo ki soya mun k'wai biyu kiyi sauri I'm already late" Sandarewa Amal tayi wajen ko k'ala ta kasa cewa yayinda zuciyanta yakeyi mata k'ona sosai wato ya gwammace Safiyya ta soya masa k'wai da yaci girkinta? Hmm. Haka ba yadda iya ta koma d'aki ji take kaman tayi kuka.
   Gashi tun da ya fita office ranan be dawo gida ba har wajajen tara na dare. Ba irin kiran duniyan da Amal batayi masa ba amma yana ganin calls d'in yak'i d'agawa a rayuwa baya son munafikin mutum taya zata na d'iban duk abinda sukayi tana kai wa Nazeefah kuma ya tabbata ba k'arya Nazeefah takeyi ba idan ba a bakinta ba a ina Nazeefah zata na jin dukkan abubuwan da suke faruwa idan yaje mata kwana? Ace wai har kayan abincin da ya siya ya kaiwa su Papi seda ta kira Nazeefah ta fad'a mata, dan kawai yana kyautata mata da iyayenta shikenan seta shiga neman 6ata tsakaninsa da uwar gidansa tana sanya sa looking maras adalci a fili, yanzu mey ze faru idan Nazeefah taje ta fad'awa iyayenta har magana ya kai kunnen Abba? Sam be santa da wannan munafikin hali ba kode k'awaye ne suke zigata? Toh ta cigaba shi de baze yi mata magana ba.

    Amal na zaune a parlour tana jiran dawowan Afzal se taji k'aran gate. Agogo ta duba taga ana neman goma ko meya rik'esa se war haka yake zuwa gida? Yet she's still grateful Allah ya dawo mata da shi gida lafiya. Da hanzari ta mik'e Afzal na bud'e k'ofar ta ruga taje tayi hugging nasa.

   "Habib Albi where've you been? I've been trying your number but you weren't picking up wallahi hankalina ya matuk'ar tashi." Cike da tak'ura ya janyeta daga jikinsa "Meeting muka yi se yanzu muka tashi ni kuma ban sake duba waya na ba" yayi mata k'arya bayan gidansu Sultan yaje ya yini throughout.

  "Bakada lafiya ne?" Ta tambaya tana shafa fuskansa.

  "I'm just stressed out lemmi take a shower" yayi maganan yana sauk'e hannunta daga fuskansa.

  "Kawo jakan naka in rik'e maka."

  "Bari karki damu" nan ya wuce ta ya k'arasa d'akin ji tayi tamkar tayi kuka bata ma iya ta bisa d'akin ba a parlourn ta cigaba da zama yayinda tunani ya mamaye mata k'wak'walwa ji take kaman tayi kuka ta rasa mey tayi masa yake bata wannan attitude. Se chan ta iya ta mik'e ta bisa d'akin. A kwance ta tarar da shi yana jin motsinta ya 6oye wayansa da yake ta faman chatting da Nazeefah k'ark'ashin pillow yana pretending kaman yana bacci. "Habib Albi?" Ta kirasa shiru yayi yak'i amsawa a hankali yakejin takunta har lokacin da ta k'ariso kan gadon ta zaune gefensa.

  "Habib Albi bazaka ci abinci ba?" Nan ma shiru yayi mata sarai kuma tasan ba bacci yake ba. Hijabinta ta cire ta kwanta a d'an space dake gabansa had'e da kwantar da kanta a k'irjinsa tana mey zagaye hannunta kan cikinsa sannan ta ja musu bargo ta rufesu. "Goodnight Habib Albi I love you" ta furta a hankali bacci me wuya ya d'auketa chan tukuna shima Afzal baccin ya d'aukesa.
  Kasancewar tana da morning lectures washegari se suka gama shiri kusan a tare, dukda cewan se shareta Afzal yake. Yau kwata-kwata ma k'in karyawa yayi wai ze fita da azumi. Gano itama school zata se yayi mata k'arya wai bazeyi ya kaita ba yana da meeting driver ya kaita kawai. Kud'in makarantar ta ya ajye mata ya fice ko kiss daya saba yi mata beyi ba yau haka ma jiya. Na matuk'a hankalin Amal ya tashi ta rasa mey tayi Afzal yake yi mata haka, Maamah ce ta karanci yanayinta a makaranta ta tambayeta ko lafiya.

  "Babu" ta amsa.

  "Taya zakice babu Amal? Tun d'azu fa na lura banda tunani ba a inda kike tayi mey ne?"

  "Maamah it's Yaya."

  "What about him."

  "Wallahi ni kaina ban sani ba, na rasa gane meke damunsa kusan sati kenan yau idan yazo baya sakewa dani seda yata d'aura mun fuska ko girki na baya son chi d'an tsaraban daya saba siyo mun idan ze dawo gida ma ya daina I don't know why."

  "Subhanallahi Ya Afzal d'in?"

  "Wallahi aka ce mun Yaya zemin haka wataran bazan yarda ba kinga tun da ya fita office jiya be dawo ba se kusan goman dare nasan sarai ba wani meeting da sukayi k'arya yake mun gashi ba kiran duniyan da ban masa ba haka yata ignoring calls d'ina maganan da nake miki haka yanzu ko nema na bayayi."

  "Ikon Allah this's serious toh ke mey kikayi masa? Am very sure Ya Afzal baze fara shareki haka kawai ba dole da akwai sila."

  "Wallahi ban yi masa komai ba Maamah I can't take this anymore bana jin dad'in yadda Yaya yake fushi da ni haka wallahi ko karatu na kasa yi jiya gashi muna da test gobe I can't stop thinking about him, I miss him so much bazan iya rayuwa ba shi ba" ta k'are maganan idanunta na cikowa da hawaye.

  "Ke kuwa kar kiyi kuka mana" Maamah tayi maganan tana kwantar da ita a jikinta "Yi hak'uri don't cry komi mey wuce wa ne."

  "Har zuwa yaushe toh Maamah?"

  "Kiga toh kiyi confronting nasa mana ki tambayesa mey kikayi yake shareki haka talk to him Amal silence is never a solution."

   "Maamah bana son hakan ya 6ata masa rai."

  "Toh haka zaku cigaba da zama ne? Har zuwa yaushe? Kiyi masa magana dole da akwai abu a k'asa tunda shi yak'i yayi confronting naki ai ke se kiyi hala wani laifin kikayi masa baki sani ba."

  "Bazan iya ba mey zan fara ce masa? Bana son yaga kaman rashin kunya nake shirin yi masa I respect him alot."

  "Ai ba rashin kunya aka ce kiyi masa ba Amal cike da kissa zaki tambayesa idan laifi kikayi masa ya yafe miki da haka har ze sanar dake abinda kikayi masa seku daidaita tsakaninku."

  "Okay I'll try."

  "Yauwa yanzu tashi muje muyi karatu nasan idan kika je gida ba iyawa zakiyi ba in shaa Allah everything will be fine."




RANA D'AYA!
#RD

Love... King Miemiebee👄✨

5 comments:

  1. In dai INA guje wa safiyya da uwar dakinta ranar da dubunsu zai cika. Miemiebiee Allah ya kara karfin ido da kuma basira.

    ReplyDelete
  2. Allah ya kara basira muna jiran na yau,

    ReplyDelete
  3. Nazeefah I hate u with passion, muguwa kawai kuma said Allah yasa kama da Amal ai kishi ba hauka bane.
    Oshey Miemiebee

    ReplyDelete