Saturday, 30 June 2018

RANA D'AYA!

  BY MIEMIEBEE
 PAGE 15

 
    Yana dawowa gida ya tarar da Nazeefah zaune a parlour ta sha wanka tayi kwalyanta ras tana kallo. Sannu da zuwa tayi masa tare da mik'ewa. Shiru yayi yana nazarin amsawa kokuwa chan de yace "Yauwa sannu."

  "Food is ready, zaka ci anan ko in kai maka d'aki?"

  "A k'oshe nake" yace da ita sama-sama yayin da ya shiga tafiya.

  "Afzal shin baka jin hak'uri ne kam?" tayi sauri ta sha gabansa "Me kakeson inyi ka hak'ura?"

  "Nifa ki dena bani hak'uri don bance miki ina buk'ata ba."

  "Then me ke hana ka cin girki na?"

  "A jinki zaki je ki samu Unmi a bayan idona ki had'a mata k'arya da gaskiya sannan kizo nan kina proving min innocence? LOL" ya sa dariyan rainin hankali. "Try harder."

  "Wallahi ni ban yi maka sharri gun Ummi ba."

  "Ohhh!" ya numfasa had'e da zaro lumsassun idanunsa waje "So kike kice Ummi na k'arya kenan?"

  "Ni ba haka nake nufi ba kawai ce mata nayi ta baka hak'uri nothing more."

  "Toh nak'i, nak'iyin hak'urin just let me."

  "Afzal please mey kakeson inyi maka ka hak'ura ka dena d'aura mun fuska haka? In hak'uri ne kakeso zan yita baka shi I'm sorry but please let's put a stop to this, shin zama hakan be isheka bane?"

   "Be isheni ba infact yanzu ma ya soma min dad'i, excuse me" yana kaiwa nan ya wuce d'akinsa. Sosai jikinta yayi sanyi amman dukda hakan bata kariya ba, dining ta nufa ta d'ibar mar abincin a plate ta d'au goran ruwa tayi d'akinsa luckily ta samu a bud'e. Shiga tayi taga ba kowa aciki da ta kasa kunne setaji alaman mutum a cikin bayin. Zama tayi daga gefen gadon nasa tana jiransa, be dad'e ba se gashi ya fito d'aure da towel a iya kunkuminsa yayinda droplets na ruwa ke d'iga daga kansa yana bin well defined abs nasa, omo Nazeefah ta kasa d'auke idonta daga kansa, ko kyaftawa ta kasa, yadda skin nasa ke wani glowing k'ark'ashin ranan da ya hasko d'akin kad'ai ya sata mance ina take, burinta a lokacin kawai ta aza hannunta akan jikinsa.

  Ta fannin Afzal kuwa mamaki sosai ya sha da ya ganta a d'akinsa, a d'akin ma wai akan gadonsa. Gadonsa de! Shin waya bata izinin? Banda nan ga wani mayen kallon da takeyi masa wane zata cinyesa, ganin kallon nata ba na k'arewa bane yayi gyaran murya hakan ne ya dawo da ita daga duniyan tunanin data fad'a. Kanta tayi saurin sauk'arwa cike da kunya tare da mik'ewa "Dama abincin naka ne na shigo maka dashi" bata jira jin mey zey ce ba ta fice binta da kallo yayi sannan ya nufi kan abincin ya tsaya yana k'are mai kallo.

  Toh kode wani abun cutarwan ta sanya masa aciki yadda ta k'osa seya ci? Yayi tunanin hakan a ransa. D'agawa yayi ya kai hancinsa dukda cewa yasan shunshuna abinci haramun ne. K'amshin spices zalla yaji ke tashi sede hakan be sanya sa cin abincin ba. Miyarwa yayi ya nufi wardrobe nasa ya ciro shorts da singlet, yana cikin sanya singlet nasan ne wayansa ya shiga ruri k'arisawa gefen gadon yayi ya d'aga ganin Amal ke kira se yaji gabad'aya jikinsa yayi sanyi ya mutu kaman wanda baze d'aga ba ya amsa.

 "Halo Yaya?" Ta soma da cewa.

  "Na'am Lily" ya amsa.

  "Yaya are you free today?"

  "Wani abu ne?"

  "Na had'a maka Aldeb ne nake tunanin ko zaka zo ka d'auka."

  "Kash wallahi ban tsammanin zan iya zuwa aiki ya rik'eni yanzu haka ina shirin zuwa meeting ne" yayi mata k'arya.

  "Toh Yaya ya zamuyi kenan?"
   
  "Se zuwa wani lokacin in shaa Allah Lily thank you."

  "Toh ba yadda za'ayi in kai maka ne ko a gida?"

  "Kibari zuwa wani lokacin kawai kinji?" Ba don tana so ba kawai tace masa "Toh shikenan Allah kaimu" da haka ta kashe wayan ta sauk'e.

  "Ya wai?" Falmata da ke shirin rakata office na Afzal ta tambaya.

  "Wai baze yuwu ba seko wani lokacin."

  "Baze yuwu ba kuma? Wani irin juyayyan magana ne haka?"

  "Wallahi ban sani ba Falmata, ban san meke damun Yaya ba ina fad'a miki tun kan lokacin da ya gane cewa Ya Abdul saurayina ne ban sake gane kan sa ba."
 
   "Hmmm Baby kenan ke yanzu har se an zauna an fad'a miki abinda ke faruwa?"

  "Abinda ke faruwa kaman ya kenan?" Ta tambaya cike da rashin fahimta.

  "So kike kice wai baki san dalilin da yasa Ya Afzal ke nuna miki wannan halaye ba?"

  "Wallahi ban sani ba Falmata dan Allah ki fad'a min" ta amsa tana me tattaro hankalinta duka a gareta.

  "Kin deji rantsuwa ba kaffara ko? Wallahi son ki Ya Afzal yake" dum Amal taji zuciyarta ta buga, yadda kuka san an sanar da ita mutuwan Mami haka jikinta ya mutu a wajen ko k'wak'k'warar motsi ta kasa tafi minti biyu zaune shiru a wajen sannan daga bisani ta shiga kad'a kanta tana k'aryata batun Falmata "K'arya ne hakan baze ta6a faruwa ba. Ba yadda za'ayi Yaya ya fara sona, Falmata it doesn't even make sense."

  "Ko meyasa? Meyasa Afzal baze fara sonki ba Amal bayan kullum kuna tare?"

  "A'a Falmata dan Allah kibar zancen nan ko matan duniya sun k'are Yaya baze ta6a cewa yana son k'waila kamata ba. Ke ni bama tsarirsa bace har mey Yaya zeyi da mace kamar ni? Kiyi tunani mana."

  "Shikenan Baby ki k'aryatani iya son ranki amman de gaskiya d'aya ce wallahi Ya Afzal sonki yake idan ba kishinki yake ba har mey yayi zafi don yaji kina da saurayi ransa ze 6aci yayi fushi dake? Bayan nan keda bakinki kikace tun lokacin chan har izuwa yanzu baki sake gane kansa ba kiyi tunani mana akwai 6oyayyen al'amari anan."

  "Tabbas akwai amman ba wai Yaya sona yake ba."

  "Toh shikenan amman de ki zauna kiyi tunani da a banza ne zeyi maki duka wannan d'awainiyyar da yake mikin Baby? Haba mana ai ko ba a fad'a miki ba yaci ace kin gano hakan da kanki ko shi d'in ki mayara dashi baho ne wanda be san meye zeyi da kud'insa ba? Kin deji rantsuwa ba wallahi ba mey maki wannan d'awainiyyar a banza in ba mahaifanki ba."

  "Ni nasan Yaya, nasan abinda ze aikata da abinda baze iya ba. Komi da kika ga Yaya namun tsakaninsa da Allah ne, idan da har so na yake kaman yadda kika fad'a da idan munyi waya baze na tambaya na ya Ya Abdul ba."

  "Aikin banza, wallahi 6ad'da k'afa yakeyi."

  "Falmata idan har da sona Yaya yake ina da tabbacin daya furta min idan ko beyi hakan ba ze samu Papi ya fad'a masa amman beyi ko d'aya ba taya kike tsammanin zan kawo tunanin hakan a raina? Kamar yadda nasan Yaya baze kalleni da idon so ba nima wallahi bazan iya kallonshi da hakan ba so please bana son sake jin maganan nan kafin har magana ya iskesa kisa ya fara min kallon wacce bata da godiya batin duk abinda yayi min in bud'i baki ince ina sonsa."

  Duk yadda Falmata taso fahimtar da Amal lamarin ina abun ya gagara ita k'wak'walwarta ma ta kasa d'aukan mata maganan, wai taya za'a ce Yaya yana sonta? Yaya deh? K'arya ne.

   Chan dare wajajen k'arfe tara Amal na mik'e akan katifar ta tun tafiyan Falmata take ta tunanin abinda ta fad'a mata, ta kasa daina tunanin hakan. Wayanta dake gefenta ne ya shiga ruri yana me tsamurota daga duniyar tunanin data fad'a. Lek'awan da zatayi taga Ya Abdul ke kira ba tare da 6ata lokaci ba ta d'aga.

  "Halo Baby?"

  "Na'am My heartthrob" ta amsa. "Ya kake?"

  "I miss you" yayi admitting.

  LBaby I missed you too se yaushe ne zasu dawo min da kai?"

  "Se ko next week."

  "Har next week? Shi d'inma under question mark? Gaskia ni zan nemi wani saurayin shikenan kai kana cikin tafiye-tafiye kullum?"

  "Haba girlfriend yi hak'uri mana nima ba a son raina bane, guess what?"

  "Tell me."

  "Akwai tsarabar dana tanadar miki."

  "Kai Baby? Na meh fah?"

  "Toh kuma ana sanar da mutum tsaraba ne?" Ya had'e rai tamkar tana gabansa.

  "Ai ni baby'nka ce zaka iya sanar dani ko ba haka ba?"

  "Kuma haka ne fah."

  "Yauwa dearest ome tell me toh."

  "Ina bracelet nan da Daddy ya saiwa Maamah kika ce kinason irinsa?"

  "Eh Baby bear" ta amsa anxiously.

  "Toh wanda Baby'nki ya saya miki har ya fi nata kyau."

  "Kai Baby! Dagaske!" Tasa ihu.

  "Yes Love."

  "Awwwnn I love you soo much nima ina kan tanadar maka da tsarabata."

  "I trust my Baby."

  "Your baby is honored."

  "Toh ya kike yasu Mami?"

  "Lafiyansu k'alau ya chan d'in? Ina fatan ba wacce tasa maka ido kasan fa kullum se nayi maka add'ua."

  "Kai Baby karki damu I'm safe."

  "Ahtoh duk wacce tace maka tana sonka ma kace mata kai anyi maka mata a gida."

  "An gama Baby" yayi assuring nata.

   "Yauwa Baby na" hira kad'an suka k'ara tayi masa seda safe. Tana ajiye wayar tunanin Afzal ya sake dawowa mata, daga k'arshe de ta d'au wayarta ta kirasa sede har ya tsinke be d'aga ba se a karo na biyu.

   "Yaya?"

 "Na'am Lily" ya amsa yana mik'e akan gado daman tunaninta yake shima se gashi ta kira.

  "Yaya muna fad'a ne?" Ta tambayesa.

  "Kaman ya fad'a kuma Lily?"

 "Yaya ai ka fini sani."

  "Ban fahimce kiba Lily."

  "Yaya idan wani laifin ne nayi maka ka sanar dani in baka hak'uri wallahi I miss you, Yaya ko kirana baka yi sede idan ni na kira ka, rabonka da ka kawo mana gaisuwa har na manta daga yau kace ba kada lafiya se gobe kace aiki ya rik'e ka, Yaya what is happening? Wani laifin ne nayi maka ya 6ata maka rai haka wanda ni ban sani ba?"

  "Lily-"

  "I'm sorry" ta katse sa "It's just that I miss you so much. I've had sleepless nights thinking about where and how I've wronged you amman nakasa figuring out komai" ta sanar da shi sincerely. Shiru Afzal yayi na d'an lokaci, gabad'aya se yaji ba dad'i tabbas yasan be kyauta mata ba kuma ko shi d'inma bawai yana jin dad'in zamansu hakan bane. He misses her dearly, he misses being with her, he misses her smiles and laughter, he misses picking up fights with her. A takaice yayi missing komai dangane da ita amman ba yadda ya iya ne. Ya zame masa dole ya nisantar da kansa daga gareta saboda gudun 6acin ransa da kuma jefa kansa acikin damuwanda yafi wannan da yake ciki yanzu. Baze iya jure ganin Amal da wani d'a na miji ba shi ba, baze iya jure ganin minti-minti wani na kiranta yana tambayan lafiyanta ba a takaice baze iya jure ganin wani d'a na miji da ba shiba yana sanya Lilirsa farin ciki, gara suyita tura tafiyan haka.

  "Yaya baza kayi magana ba?" Tayi maganan yayinda idanunta ke cikowa da hawaye.

  "I'm sorry kinji?" Ya tsinci kanta yana fad'a mata dan ko besan mey zey ce bayan hakan ba.

  "Yaya ni ba hak'uri nakeso ba just tell me mey nayi maka in baka hak'uri wallahi bazan iya yafewa kaina ba idan har na 6ata maka rai ba tare da baka hak'uri ba" kawai seta sa kuka. "Yaya I'm sorry please forgive me."

  "Lily bade kuka kike ba?" Ya tambaya da mamaki.

  "Yaya taya bazan yi kuka ba bayan kana fushi dani har nagaji da had'awa Papi k'arya kullum se yace mun kunyi waya kana lafiya amman ya rasa dalilin da ke hana ka zuwa, gani yake kaman ni nayi maka wani laifin, haka sede inyi masa k'arya ince aiki ne ya rik'e ka please forgive me."

   "Ya isa haka kinji? Ya isa bar kukan haka."

  "I can't bazan iya ba."

  "Are you free gobe?"

  "Eh" ta amsa tana share hawayenta.

  "Toh shikenan share hawayenki, se na shigo."

  "Dagaske Yaya zaka zo?"

  "Everything for my Lily. Zanzo muje duk inda kikeso."

  "Toh Allah kaimu" ta amsa cike da jin dad'i.

 "Ameen."

  "Amma bazaka sanar dani abinda nayi maka ba ko?"

  "Lily bakiyi mun laifi ba ai na sha fad'a miki Lily bata laifi."

  "Toh shikenan nagode sosai ka gaishe da Nazeefah."  Washegari kamar yadda yayi mata alk'awari bayan da ya dawo daga sallar jum'ah ya canza kaya ya sanya wata burgundy half jamfan daya mugun amshe skin colorsa da kuma figure. Wankan turare yayi ya sanya accessories nasa sannan ya d'au wayarsa ya fice. Yana cikin locking d'akinsa ne wayansa dake aljihu ya shiga ruri da sauri ya sa key'n ya zaro wayar se gani yayi Amal ke kira da alama don taji sa shiru ne takeson jin ko lafiya. Murmusawa kad'an yayi tare da sliding ya amsa sannan ya shiga tafiya.

  "Halo Lily?"

  "Yaya naji shiru kode ka canza ra'ayinka ne?"

  "Na isa?"

  "Toh gashi har k'arfe hud'u baka zo ba" ta amsa had'e da zum6uro baki.

  "Gani nan zuwa yanzun nan ki bani like 20 minutes okay?"

  "Alright toh seka iso" cike da farin ciki ta katse wayan. Nazeefah dake zaune kan kujera a parlour tuni ta cika dam da kishi, zuciyarta ta gama ta fasa sauran k'onuwa kawai. Wato duk uban wankan nan gun karuwarsa zasa ko? Da kyau ai bata basa izinin k'arisawa bakin k'ofa ba ta sha gabansa.

  "Lafiya?" Ya tambayeta da mamaki had'e da d'age gira d'aya.

  "Se ina kuma?" Ta tambayesa cike da kishi.

  "Wai tsaya ni dake wake zaman wani ne kam a gidan nan?" Shi dariya ma ta basa.

  "It doesn't matter, taya ina ji ina gani zaka gun wata daban?"

 "Aww ashe kinsan inda zani" yayi maganan cike da rainin wayo.

  "Wallahi bazaka ba" tasa rantsuwa.

  "Hana ni zakiyi?"

  "Wallahi idan ta kama zan hanaka ita karuwar taka bata san kana da aure bane?"

  "Nifa na gaya miki ki dena kwatanta yarinyar nan da karuwa."

  "Da malama kakeson in kwatanta da? Haba mana Afzal yanzu duk hak'urin da na baka da wanda Ummi ta baka be isheka ba, bazaka dena neme nemen matan nan ba?"

  "Kar ki sake kwatantani dame neme nemen mata kuma koda nayin ma you think kina da right na min magana ne? Look at you" ya tsaya yana k'are mata kallo "Tun yaushe kika fara regarding d'ina as your husband and incase you forget I'm a husband to four wives."

  "Wato ko kunyan ido na ma bakayi gar da gar kake fad'a min kana da budurwa ko?"

  "Lmao kunyan mara kunya asara ko inji bahaushe?"

  "Wallahi Afzal ka cigaba kuma kaji rantsuwa ba kaffara wallahi ko 'yar gidan ubanwa kake nema muddin na samu information akanta believe me sena rabaku ka nemi waje ka rubuta."

  "I would love to see you try" yayi maganan disgustedly yana mey watsa mata mumunan harara sannan ya fice. Rushewa tayi gun tana kuka na hak'ik'a bata san ya akayi soyayyar Afzal ya kamata haka ba, gani take kamar idan be zame nata ba tana iya rasa rayuwarta. Oh Allah ya kawo mata sauk'i.

  **
  Yana isa gaban gidan nasu yayi ma Amal waya, nan da nan tayi touching over 'yar kwaliyarta ta sanya hijabinta sannan ta cire sim nata ta ajiye a gefe gudun kar Ya Abdul yazo ya kirata suna tare da Afzal hakan ya sake janyo mata wata matsalar. Da farin ciki kwance fal a ranta ta fice taje ta samesa, kamar yadda take masa fara'a shima hakan yake mata, ba k'arya sunyi kewar junansu. Hira sosai sukayi sannan ya tambayeta inda takeson suje ita dan murna ma kawai ce masa tayi suyita zagaya garin Maiduguri har se sun gaji. Haka suka d'au hanyan federal low cost chan farin Maiduguri suka kai suka sake d'auko hanyan University dake k'arshen Maiduguri daga chan suka bi ta gidan madara ya sai mata chocolates da dama. Bayan ya dawo da ita gida ta buk'aci ya jirata tana zuwa, fitowanta ta taho masa da aldeb da ginger. Sosai yaji dad'i danko yayi missing had'ad'd'en aldeb natan nan ba k'arya. Ba gardama ya amsa yayi mata godiya sannan ya tambayeta ko su Mami suna gida ya shiga su gaisa. Sosai su Papi suka ji dad'in ganinsa, sunyi hira kad'an Afzal yace ze tafi Maghrib ya gabato har waje duka suka raka sa sukayi sallama.

   Haka Amal keyi duk sanda Afzal zezo mata seta cire sim nata ta ajiye, da ikon Allah kuma Afzal be sake d'auko mata maganan Ya Abdul ba, a hankali shak'uwa ya sake shiga tsakaninsu as duk abinda Amal tasan ze 6atawa Afzal rai gamw da Ya Abdul tana avoiding. Nazeefah bak'in ciki kaman ze kasheta ta rasa ya zatayi da ranta gashi har yau ta rasa information akan Amal ko idan Afzal ya fita tace zata bi bayansa kullum seya kamata seya canza gun zuwa kokuwa ya shiga nan ya shiga chan har se tayi losing track nasa. A haka ne har aka bud'e makaranta, su Amal 'yan part two. Wannan karan da kanta tayi registrations nata, koda Afzal yace ze taimaka mata ma k'i tayi tace zata iya da kanta. Bada dad'ewa ba suka fara lectures.

  Yau bayan lectures ya k'are, Amal da Maamah suna zaune akan slab suna jiran Ya Abdul yazo suje su ci abinci sega Afzal na sauk'owa daga kan stairs tare da wani abokinsa wanda ya kasance assistant lecturer. Amal na ganinsa zuciyarta ta fad'i kafin tace zata tare fuskarta inaa Afzal har ya hangeta. Suna sallama da abokin nasa ya shiga dosan inda suke zaune da Maamah sede beyi nisa ba sega motan Ya Abdul yazo dai-dai gaban su Amal ya tsaya hakan yasa Afzal dakatawa shima se gani yayi mutumin ya fito cike da farin ciki ya tsaya akan su Amal. Wani irin k'ona zuciyansa ya shiga yi masa bade wannan bane saurayinta Abdul d'in ya tambayi kansa. Se chan yaga Amal ta mik'e sede har yanzun ta kasa juyawa ta kalli Afzal da k'afafunsa ke kakkarwa. Ba haka taso abun ba, bata som abinda ze 6ata wa Afzal rai. A hankali ta juyo tana kallonsa, excusing kanta tayi daga gun Ya Abdul akan tana zuwa, nan ta nufi gun Afzal yayinda shi da Maamah suka zuba mata ido. Tana k'arisawa ta la6e daga jikin wata bishiya.

  "Yaya" ta kirasa cike da kunya ko kallon cikin idanunsa ta kasa. Danne zuciyarsa yayi da k'yar ya iya amsata "Na'am Lily."

  "Yaya good afternoon."

 "Afternoon ya lectures?"

  "Alhamdulillah Yaya shine zaka shigo school ba zaka sanar dani ba?"

  "Ba zama zanyi ba shiyasa lemmi get going" ya sanar da ita yana neman juyawa.

  "Yaya bazaka tsaya ku gaisa da Ya Abdul ba? Tun ba yau ba yake son ku had'u."
 
  D'aga ido yai ya kalli Ya Abdul dake kallonsa shima, kau da kansa yayi take yace da ita, "Maybe next time Lily I'll be late for the meeting" be bata daman sake magana ba ya fice ya nufi motarsa tare da bata wuta. Kaman wanda k'wai ya fashewa a ciki Amal ta k'arisa gun su Maamah da suke kallonta har anan.

  "Omg! Amal kinga ban yi mana submitting assignment namu ba, lemmi hurry" Maamah ta fad'a kafin Amal tace mata ai nayi d'azu har ta fice dama da gan-gan tace hakan don ta basu daman yin magana ne don tasan ko ba'a tambaya ba Ya Abdul na da abin cewa game da wannan abinda ya faru yanzu.

  "Amal?" Ya kira sunanta a hankali bayan ficewan Maamah sede sam hankalinta yabar jikinta. "Amal?" Ya sake kirarta se a karo na uku ta amsa a firgice. "Amal meya faru?"

  "Babu I'm sorry mu tafi ko?"

  "Ba inda zamu sekin fad'amin abinda ke damunki."

  "Allah babu komai Ya Abdul lets go yunwa nakeji." Hijabinta ya ja seda ya zaunar da ita sannan ya zauna agefenta tare da barin rata a tsakaninsu. "Meya faru tell me kinji? Waye wancan da ya tafin?"

  "Ina Yaya na da nake fad'a maka? Shine ya tafi yanzun." A lokaci guda Ya Abdul yaji zuciyansa ya tsinke karde d'an wannan ne yayan da Amal ke damunsa da shi kullum? Lallai akwai k'ura shi a iya tunaninsa wani babba ne da ya girmesa ashe de yaro ne, ai ko be tambaya ba yasan ya girmesa. Inko wannan ne yayan nata shikenan ya tabbatar da zarginsa batun lokacin da Amal tace masa yayanta yayi fushi saboda yaji tana da saurayi.

  "Baki fad'a masa ina son mu gaisa ba?"

  "I told him yace wai yana da meeting seko wataran" amsanta ne ya sake tabbatar masa da zarginsa ba shakka kaman yadda yake gudu wannan yayan nata sonta yake. Shin ita Amal bata sani bane? Kokuwa bata son shi ne? Amman kuma daga yadda take mganansa mutum ma ze san tana sonsa. Yau ya zeyi? Baya son ya rasa Amal baze iya jura rashinta ba.
  Ka kwantar da zuciyanka wata ra'ayin tace dashi dan kawai be k'ariso kun gaisa ba doesn't mean yana gaba da kai ne ko wani abun ze iya yuwu wa meeting d'in zasa dagaske. Hakan ne ya d'an kwantar masa da hankali amma fa still hankalinsa be bar tashi.

  "Tashi muje kici abinci toh, you're hungry aren't you?" Kai ta gyad'a masa "Maamah fah?"

  "She'll catch up with us mu tafi" ba gardama ta mik'e ta bisa a baya sede tun da ta shiga motar har suka isa restaurant d'in Amal shiru take a motar gabad'aya hankalinta ya duk'ufa akan Afzal. Duk yadda yaso 6oye haushi da kishin daya tokaresa yau da ya ga Ya Abdul abin ya gagara har seda Amal ta d'an gano wani abun don haka ta fara kawo tunanin abinda Falmata ta ta6a fad'a mata sede kuma gabad'aya abun be yi making sense mata ba. Taya wai Yaya ze fara sonta ne? Maybe kawai ya damu ne kar Ya Abdul ya d'aukar mata da hankali daga kan karatu. Amma kuma meyasa jikinsa yayi sanyi yau tun ganin Ya Abdul da yayi?
   Haka har Ya Abdul yayi parking motar ya fito ya bud'e mata k'ofar Amal bata ma san yayi hakan ba.

  "Baby?" Ya kirata a firgice ta d'ago kai "Sorry" wur-wur tayi ta fito suka k'arisa ciki. Bayan orders nasu sun iso Ya Abdul ya shiga ci Amal kam se ido.

  "Tunaninshi kikeyi?" Ya tambayeta a hankali yana mey tsamota daga duniyan tunanin data fad'a.

  "I'm sorry" ta furta tare da d'ago spoon nata.

  "Fad'amun Amal mey tsakaninki da wannan Yayan naki?"

  "Wallahi Ya Abdul ba komai kar kayi tunanin wani abun" tayi saurin basa amsa.

  "Taya bazanyi ba Amal bayan tun da ya ganmu tare kika rasa nutsuwar ki."

  "Ya Abdul wallahi ba haka bane kaima kasan kai kad'ai nakeso kai kuma zan aura kawai Yaya is a part of me ne, ya zama wani sashi a jikina wanda farin cikinsa matters to me alot bana son ganinsa a damuwa."

  "Kina ganin kuma kallon mu da yayi tare ya sanya sa a matsala?"

  "I fear so" ta amsa a hankali.

  "Kina son shi kema?" Ido ta d'ago a razane tana kallonsa bata ta6a tsammanin irin wannan kalamu daga bakinsa ba. "Ya Abdul wani irin magana ne kuma haka?" Abinda bakinta ya iya ya furta kad'ai kenan yayinda mamaki ya gama mamaye mata zuciya.

  "It's a question Amal answer me do you love him too?"

  "Ya Abdul gaskiya banji dad'in wannan kalamu daga bakinka ba, bayan kasan kai kad'ai nakeso kuma kace ko ina son Yaya? I told you ni ba komai tsakani na da Yaya ko shi Yayan ne ya sameka yace maka yana so na da har zaka tambayeni ko nima ina sonsa? I'm very upset with you right now."

  "I'm sorry I'm just curious, yadda yake kallona d'azu was more of na sace masa sanyin idanunsa da farin cikin rayuwansa, naga soyayyar ki a cikin idonsa Amal don't blame me." Ran Amal in yayi dubu be 6aci ba, abubuwanta ta shiga tattarawa taya akan kowa Ya Abdul ze ce mata ko tana son Yaya? Ai wannan ma iskanci ne. "Ina kuma zakije?" Yayi saurin tambayarta.

  "Anywhere better than here" ta fad'a cike da 6acin rai. Hijabinta yayi saurin rik'ewa "I'm sorry I take whatever I've said back kiyi hak'uri kinji?"

  "Na rasa appetite d'ina ni zan tafi gida."

  "Shine nace kiyi hak'uri, yi hak'uri ki zauna kinji? I'm sorry" hak'uri yayi ta bata da k'yar ya samu ta koma ta zaunan chan bada dad'ewa ba sega Maamah ta shigo d'adi sosai Ya Abdul yaji inda yayi mata fillanci (yaransu) kan ta bawa Amal hak'uri ze koma office. Ko da yake yi mata sallama ma tak'i amsawa sam bata ji dad'in maganan da yayi mata ba.

  "Meya faru ne Amal?" Maamah ta tambaya bayan ficewan Ya Abdul. "Ya na ganki haka?"

  "Meya ce miki da yaren naku? Gulma ta kukayi ko?"

  "Taya kuma gulmar ki? Wallahi hak'uri zalla yace in baki."

  "K'arya kike na sanki da Ya Abdul nakin ai."

  "Wallahi hak'uri ce zallah, tell me mey ya had'aku?"

  "Yayanki ne mana" se kuma tayi shiru.

  "Yayi mey?"

  "Taya ze kalleni yace mun wai ko ina son Yaya ne bayan yasan sarai shi nakeso."

  "Ayyah Amal kiyi hak'uri shi ba da wata manufa ya fad'a hakan ba gani yayi kaman shi Yayan naki na sonki ne."

  "Aww kema abinda zakice kenan? Wai yaushe ne dukanku zaku gane cewa Yaya ba so na yake ba he's just being overly protective of me a matsayina na k'anwarsa, yanzu ko ke Ya Abdul ya ganki da wani baze had'a mishi rai bane?" Cikin 6acin rai take maganan hakan yasa Maamah ta soma bata hak'uri.

  "Tabbas ze ji haushi Amal amma kuma" se kuma tayi shiru sakamakon mumunar kallon da Amal ke watsa mata.

  "Amma kuma mey?" Ta tambayeta a fusace.

  "Amma bakiga kallon da Yayanki yayi wa Ya Abdul ba wallahi dole Ya Abdul yaji wani iri a matsayinsa na wanda yake sonki Amal."

  "Wani irin kallo yayi masa?"
 
  "Wannan ma a gefe a tunaninki haka ne kawai Yayan naki yak'i k'arisowa su gaisa da Ya Abdul? I'm sorry to say amma Amal komin ya kika musanta Yayan nan naki sonki yake ni yanzu ba abinda yafi damuna kaman Ya Abdul, wallahi shi nake tausayawa bana son ki tafi ki barsa Amal."

  "Shaidan da zaki yimun kenan Maamah a matsayinki na very close friend d'ina? So kike kice duk soyayyan da nake yi wa Yayanki na k'arya ne kenan? Wow!" Ta numfasa "I'm totally speechless dake da Yayan naki duk haushin ku nakeji yau" tana kaiwa nan ta fishe jakanta ta fice, da wuri Maamah tabi bayanta tana k'wala mata kira amma ina tak'i koda juyawa. Keke ta tsara ta wuce park daga chan ta tsari na gida. Akan gadon d'akinta ta fad'a yayinda ta shiga yin kuka. Haka kawai taji komi ya dak'ule mata kuma kuka ne kawai solution, wayanta dake ringing ta zaro daga jakarta dubawan da zatayi taga Ya Abdul ke kira dan haushi ma hanging tayi gabad'aya be dad'e ba se gashi yana sake kira nan ma kashewan ta kuma yi se a karo na biyar ta d'aga. Hak'uri ya shiga bata amman tak'i hak'uran seda yayi dagaske har kaman zeyi mata kuka a wayan sannan ya samu ya shawo kanta, yazo ma tace ita kar yazo she wants to be alone da haka sukayi sallama akan ze kirata anjima.

***
   Ta fannin Afzal kuwa ikon Allah kad'ai ya kaisa gida sabida tuk'in gangancin da ya rink'ayi a hanya. Gabad'aya ji yayi rayuwarsa bata da wata ma'ana ashe haka kullum shi Abdul d'in yake kaiwa Amal ziyara makaranta? Time d'in da ya kamata shida Amal su sake shak'uwa da junansu Abdul ke amfani da ita yana matsowa kusa da zuciyar Amal? Oh Allah! D'akinsa ya zarce ko ta kan Nazeefah dake yi masa sannu da zuwa beyi ba yana isa ya fa'a kan gadonsa had'e da rik'e dai-dai saitin zuciyansa inda keyi masa k'una sosai. A d'akin ya yini ranan, k'arshe sallah ma a zaune yazo ya k'arisa saboda wani irin zazza6in daya rufesa lokaci guda. Wajajen goman dare Amal ta kira layinsa sede wayan yata ringing Afzal be d'aga ba, ko energy'n da ze mik'e ya d'au wayan daga wardrobe nasa ma bayi da shi kuma yana da tabbacin cewa Amal ce ke kira, ko mey zata fad'a masa? Haka tayita kiran nasa har ta gaji ta hak'ura. Washegari ko office Afzal ya kasa fita saboda tsananin da jikinsa yayi.

   Chan Azahar Nazeefah taji shirun yayi yawa don haka tayi tunanin gwada lek'asa kode lafiya dan ko breakfast be fito yayi ba. K'ofan nasa ta gwada turewa taji a rufe da key, knocking tayita yi amman ba response. Bata 6ata lokaci ba ta zagaya ta window inda ta tarar da sumemmiyar jikin Afzal a kan sallaya. Wani irin d'ankaren ihu tasa tuni me gadi yayi kanta yana tambayarta ko lafiya. Tsabagen yadda ta tsure ta kuma rikice ko magana ta kasa banda nuni da takeyi masa da cikin d'akin da yatsa. A guje suka yo ciki ya shiga k'ok'arin 6alla k'ofar sede ina security door ce hakan seya gagara daga k'arshe welder aka kira yazo ya cire lock d'in gabad'aya, da haka ne aka samu akayi waje da Afzal. Nazeefah se kuka, ko kiran Ummi ta kasa.

  Suna isa asibitin akayi emergency room da Afzal yayin da aka bawa Nazeefah wasu papers tayi signing da k'yar ta iya tayi signing d'in se anan ta shiga neman wayarta ashe ko fitowa da ita ma batayi ba. Takalman k'afaya ya duba taga ashe sawu d'aya ma na Afzal tasa. Wayan wata nurse ta ara agun ta zuba layin Mummy sannan ta kira. A karo na farko Mummy ta d'aga.

  "Mummy" ta kirata cike da tashin hankali.

  "Nazeefah?" Mummy ta tambaya.

  "Mummy kizo kizo da sauri dan Allah" tayi maganan tana kuka.

  "Meya faru? Kina ina?"

  "Afzal."

  "Meya samesa?" Ta tambaya take.

  "Mummy kizo kawai muna TH shi kad'ansa ya sume wallahi bani bace ni ban yi mishi komi ba wallahi."

  "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Mummy ta furta cike da tashin hankali "Shikenan ina zuwa" tana sauk'e wayan ta cigaba da salati yau Nazeefah ta gama da ita shikenan ta kashe wa mutane d'a yau ina zata sa kanta? Hasbunallahi wa ni'imal wakeel. Hannunta na kakkarwa  ta nemi lamban Ummi ta shiga kira bada dad'ewa ba sega Ummi ta d'auka.

  "Halo In law?" Fad'in Ummi.

  "Hajiya Mariam."

  "Na'am Hajiya Fatsuma ya kike?"

  "Hajiya Mariam ki shirya ki taho TH yanzun ba lafiya."

  "Subhanallahi waye ba lafiya? Bade autan mu ba?"

  "Afzal ne kiyi sauri."

  "Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!" Ummi ta furta yayinda zuciyarta ta tsinke "Afzal?! Afzal d'ina?? Meya samesa?"

  "Wallahi nima ban sani ba yanzun Nazeefah ke sanar dani kiyi sauri kekam." Take Ummi ta ajiye wayan ta janyo hijabinta da hanzari tayi waje tana k'walla wa driver kira. Kusan a tare ita da Mummy suka isa asibitin suka nufi emergency ward inda suka tarar da Nazeefah zaune kan benci ta had'a tagumi se aikin kuka take. Da hanzari suka nufi kanta suna tambayarta ina Afzal d'in. Wani sabon kukan tasa musu a wajen tare da hugging Mummy, d'agata Mummy tayi take daga jikinta had'e da kifa mata wata zazzafan mari. Tunda Nazeefah tasan kanta ba a ta6a marinta a fuska ba se yau. Rikicaccen ihu tasa yayinda Ummi tayi sauri ta shiga tsakaninsu.

  "Haba Hajiya Fatsuma! Meyayi zafi haka?"

  "Kin kyauta min kenan Nazeefah? Da abinda zaki sak'a min kenan? Ai kin huta yanzu da kika tura shi har gadon asibiti burin ki ya cika."

  "Mummy wallahi ni ban yi mishi komai ba Ummi wallahi bani ce sanadin halin da Afzal ke ciki ba, dan Allah ki yarda da ni wallahi a sume na tarar da shi a d'akinsa" ta jero amsa tana kuka sosai.

  "K'arya kike! Nace k'arya kike" Mummy ta k'aryatata tana me sake k'ok'arin kai mata wani marin yayinda Ummi ta tareta.

  "Ya isa haka please ya isa mu jira muji fitowan likitocin" da haka ne su uku suka koma suka zauna kan benchin d'azu. Nazeefah bata bar kuka ba har yanzu sede abinda ya k'aru ba wanda yayi ta kanta kuwa as duk tunanin wani hali Afzal ke ciki suke barin ma Ummi dake jin tana iya rasa ranta idan Afzal ya rasa nata. Chan red globe na d'akin ya mutu yayinda k'ofan ya bud'u revealing a doctor with two nurses behind him. A gigice su Ummi sukayi kansa suna masu jero masa tambayoyi, da k'yar ya samu sukayi shiru sannan yayi gyaran murya.

  "Ko wacece mahaifiyarsa a cikinku?"

  "Dukan mune" Mummy ta amsa. Kallo yayi mata na d'an lokaci sannan ya gyad'a kai "Wannan kuma fa?" Yayi nuni da Nazeefah.

  "Matarsa ce" Ummi ta amsa "Please Dr ka fad'a mun ya condition na d'an nawa yake."

  "Hajiya bazan 6oye miki ba amman condition na d'anki ba kyau, rayuwansa yana cikin matsala."

  "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" dukansu uku suka furta a tare yayinda Ummi ta shiga nanata hasbunallahu wa ni'imal wakil gabad'aya hanjalinta ya fita yabar jikinta.

  "Dr meya samesa?" Mummy da tayi k'arfin hali ta tambaya.

  "D'anki ya kamu da ciwon zuciya, base on gwajin da muka d'auka sakamako ya nuna cewa ya samu heart attack ne dalilin sumewanda yayi kenan."

  "Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un" suka kuma furtawa yayinda idanun Ummi suka kad'a sukayi ja nan take. "Heart attack? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" A raunane ta juyo tana kallon Nazeefah.
 
  "Nazeefah mey kikayi wa Afzal? Me kikayi wa d'a na? Mey kika masa?" Take ta rushe da kuka.



RANA D'AYA
#RD

Love... King Miemiebee👄✨

6 comments:

Unknown said...

tnxs much sis plxxx a dinga mana update kullum. plxx Allah ya kara basira

Anonymous said...

Tnx pls update plsssssssssssss

Unknown said...

Tanx waiting for the next update

Unknown said...

Ameen in shaa Allah

Unknown said...

Uw

Unknown said...

Uw