BY MIEMIEBEE
PAGE 37
*January, 2017*
_Assalamu Alaikum, literally I don’t even know where to start from my family, to friends, to fans, supporters, readers and to everyone who missed either my book or me, know that I missed you guys as much and am so sorry for keeping you people in such a non ending but now ended suspense and also that I can't reply back to each and everyone of you that cared and stopped by to ask for me privately, or on the blog or in groups or even tried calling me. The messages are over Alhamdulillah I have such awesome people that care for me, nagode sosai for your maxi support, care and love I love y'all oceans and galaxies❤❤. With your prayers, Allah ya dawo dani safe and sound se muyi firing on da *™YGC*💞_
_2 days later..._
Ba inda Zeezee bata taka ba da sabuwar motarta a garin Bauchi tana bawa mutane assignment. Duk mutan arziki sun taya ta murna barin ma Baba da Mama they can’t ask for a better son-in-law than Al’ameen. They are sure ko bayan ransu ze cigaba da kula da Zeezee, nasiha again Baba yata mata amman haka baiwar Allahn nan ta ajiye mai abinsa a wajen da tazo tafiya.
_Afternoon hours..._
Kasancewar Al’ameen be ta6a jimawa haka a gari ba se wannan karan yasa mutanensa da suke Bauchi duk suka soma hallaro gidan nasa suna zuwa yimai gaisuwa. Duk yadda yayi dan kada su san yana gari abin ya gagara babban mutum kamanshi se a hankali. Suna zaune da mutanen nasa a parlour yayi excusing kansa ya shiga d’akin Zeezee alokacin ma waya da Adeel take wanda da sauri ta katse ganin Al’ameen. Kai kawai ya kad’a yace da ita, “Zainab white rice nakeson ki dafa wa bak’in danayi sekiyi slicing carrots akai dakuma peas da za’a sa akai kinji?”
“Kut! Nice zanma duka wannan aikin? Wallahi k’arya ne ni banida lafiya.” tayi maganan cike da rashin kunya.
“Ki dafa white rice shine bakida lafiya Zainab? Bance fa zakiyi stew ba, na riga nasa an siyo stew shinkafan kawai zaki dafa thats all.”
“Yo dama kace nayi stew’n mana in bakayi asaran kayan miya ba kuma ma wai su abokan naka basuda mata ne kokuwa iskanci da son sa mutum aiki ne ke hanasu zama a gidansu suci abinci se sunzo gidan mutane? Allah wadai d’in mutane kaman su wallahi mschww.”
“Ya isa haka toh wuce kije ki dafa kiyi sauri.”
“Kuma wallahi in shinkafan be dahu yadda kakeso ba don’t blame me bani nace ka kawo bak’i ba aikin banza.” Mayafinta ta taje ta fice mai, in less than one hour shinakfan ya dahu yadda Al’ameen ya buk’ata sede ruwa yaso yi mata yawa kad’an amman de tayi k’ok’ari. Ita bama haka taso ba, taso ace shinkafan yayi fate-fate yadda ko a mafarki baze sake sata dafa mai abu ba.
A food warmer ta juye ta basshi a kitchen d’in sannan ta nufi parlour inda yake zaune da mutanen nasa ta bisu da dirty look sannan tace, “Daddy kaje ga abincin bak’in naka yayi.” Da mamaki friends nasan suka juyo suna kallonta taya zata kira mijinta da Daddy? Ignoring this thought suka gaisheta kusan a tare dukansu tunda ita tak’i gaishesu. “Ba gaisuwarku nake buk’ata ba ni, inda hali daga yau karku sake zuwa gidana tunda kwad’ayin abinci ke kawo ku.” Tana kaiwa nan tayi d’akinta binta da kallo duka sukayi wide in shock sannan back to Al’ameen “kuyi hak’uri dan Allah, kuyi mata uzuri yarinya ce har yanzu.”
“Bakomai Maj-Gen Allah rufa mana asiri” cewar d’aya daga cikinsu. Haka dan kansa yaje ya d’auko wa bak’in nasa abinci sukaci bayan tafiyansu ya tara plates yakai kitchen. Banda kuda dake yawo suna bin wanke-wanke tun na shekaran jiya ba abinda ke gudana a kitchen d’in. Beso ba amman dan dolensa ya nufi d’akinta be sameta ciki ba kasancewar tana wanka zaman jiranta yayi. Kaman me haihuwa seda tayi spending numerous minutes ta fito da towel nata iyaka tsakiyan cinyarta.
“Haka kawai ba sallama seka na fad’omin d’aki inda kuma ba komi a jikina na fito fah?”
“Am sorry, in kin gama shiri kije ki rage wanke-wanken kuma its hightime ko sau d’aya ne kibi gidan nan da shara Zainab, ko ke zama cikin dottin na miki dad’i sede kiyita tsaftace jikinki amman banda na muhalli.”
“Look at who’s talking dan Allah” tayi maganan tana tafe hannu “bakason ganin gidanka da dotti fine and good kana iya saka na right now ka auro wacce zatayi maka wannan bauta. Kafa sani niba boyi-boyi bace bazaka na kawomin so called friends naka suna taramin wanke-wanke ba and expect me to be washing the dishes for you, uh-uh baka da wannan gatan Daddy.”
“Zainab mesa kike haka ne? Baki tsoron tsinuwan mala’ikun Allah ne ke? In ni ina barinki sufa bazasu barki ba.”
“Ai tsoronsun yasa nake tambayar takarda na saboda in samu wanda zan na mai bauta wanda nake so ba kai ba.”
“Naji bakiya sona but you can’t change the fact that am your husband koba haka ba? Kije kiyi wanke-wanken nace” yayi maganan this time a bit tensed.
“Bazan yiba inma zan wanke se wanda nida kai mukaci abinci akai ba wanda wad’ancan bak’in naka suka ci abinci akai ba in kanason ana maka wanke-wanke kana iya kawo me aiki.”
“Naji zan kawo me aikin amman yanzu kije ki wanke na kitchen d’in in shaa Allah zan d’auko miki me aiki.”
“Ma kanka de ba mani ba yanzu excuse me zan sa kaya.” Be sake cemata komi ba ya fice. Nan da nan tagama shiri tafito kitchen kenan taji an danna door bell tana dubawa taga Mama salati kawai tahau yi har anan Al’ameen na zaune a kan sofa be motsa ba. “Ki bud’e k’ofan mana Zainab waye ne? ”
“Mama ce nawa ya k’are!” tayi maganan hankali a tashe. Murmushi me sake k’ayatasa ya saki seda dimples nasa suka lotse sosai sannan ya kad’a kai ya kawar da kansa daga kallonta. “Aww ma dariya kake min ko? Mugu kawai, mutum babba amman wai da dimples mschw” Da k’yar ta bud’e k’ofan atare ita da Al’ameen suka yima Mama sannu da zuwa. Drink da snacks ta kawo tayi serving Mama dashi.
“Ai na d’au ma ko ka koma Abujan ne Maj-Gen.” Maa tayi maganan tana cin kad’an daga cikin cin-cin dake gabanta.
“A’a wallahi se next week in shaa Allah.”
“Toh Allah ya kaimu, bazan gaji da maka godiya bafa naga sabuwar motar da ka sai wa Zeezee Allah k’ara bud’i mungode sosai.”
“Ba komai Mama an zamo d’aya ai yanzu, barin shiga ciki toh.”
“Nazo na koreka ko? Kayi zamanka de zamu shiga ni da ita.”
“A’a please kuyi zamanku anan” yana kaiwa nan ya fice. “Ke kin mai godiya kuwa daya sai miki motan?”
“Nayi mana Mama nayi sosai ma.”
“Toh ki rik’e mijinki hannu bibbiyu Zeezee aljannarki a tafin k’afafunsa yake ba a nawa ba yanzu duk lokacinda ya nemi had’a kwanciya dake karki hanasa sannan duk abinda kika san bayaso ki kiyaye wanda yakeso kuma kina mishi kina jina ko?”
“Eh Mama inayi sosai nagode.” Hira kad’an suka ta6a can Mama tace zata kai plate nata kitchen nan Zeezee ta dage atapir ita zata kai mata sanin kitchen natan bamai ganuwa bane. “Kibari mana meh haka? Bak’uwa ce ni?”
“A’a amman kibari zan kai da kaina.”
“Matsa min da Allah kaman dagaske.” ta tureta ta shiga kitchen d’in, baki kawai ta sake wide in shock tama kasa believing abinda idanunta ke gane mata. “Ke! Me wannan? Kitchen d’in mahaukaciya komeh?”
“Mama wallahi nad’anyi rashin lafiya ne kwana biyu shiyasa wanke-wanken ya taru.”
“K’arya zakiyi min? Ba two days back bane Maj-Gen ya sai miki motan kika rik’a fita yawo anyhow shine zaki cemin bakida lafiya iyyeh?” Mari lafiyayye Mama takai mata a baya. “Rashin hankalin da kikeyi agidan naki kenan ko wanke-wanke bakiyi?” K’walla na cika a idonta ta kad’a kai “wallahi a’a da Allah karki gayawa Baba wallahi ze kasheni.”
“Me ze hanani gaya mishi? Ke bazaki ta6a shiga hankalinki bako? Wannan wanke-wanke tun na yaushe?”
“Mama wallahi be jima ba kuma yau ma nakeda niyyan wankesu, MP ne ya sani gaba shiyasa.”
“Na yaushene nace? Bazaki amsa bane? Kuma wallahi kimin k’arya kiga inban kira Maj-Gen. ba na tambayesa, na yaushe ne nace?!”
“Wallahi na shekaranjiya ne.”
“Innalillahi! tun shekaran jiya? Yanzu na shekaran jiyan ne be jima ba? Ma’ana har na sati kina tarawa kenan ko?”
“Wallahi a’a Mama wannan d’inma sharrin shed’an ne” Ajiye cup d’in Mama tayi ta jawo hannun Zeezee sannan ta shiga kai mata mari kota ina, ihu Zeezee ta shiga rusawa har seda Al’ameen ya fito da mamaki yayi sauri ya k’wato Zeezee yana bawa Mama hak’uri.
Kama shirt nasa Zeezee tayi gagam tana b’oye jikinta a bayansa. “Ni zakiyi wa abin kunya iyye? Kalan tarbiyyan dana baki kenan, tunda kike kin ta6a ganin wanke-wanke ya kwana a gida na dake zaki bar har na shekaran jiya? Maj-Gen in kanayi wa Allah dan Allah ka fita kabarni da wannan maras kunyan.”
“A’a Mama dan Allah kiyi hak’uri duk beyi zafi haka ba ita kanta tanada niyyan wanke dishes d’in yau.”
“Aww ai dama nasan kai kake d’aure mata gindi, haba Maj-Gen. kai da ya kamata ka gyara mata zama se kuma ka zuba mata ido tana rashin hankali iya son ranta gaskiya am very disappointed in you. Wannan abu dame yayi kama?”
“Kiyi hak’uri Mama.”
“Ka gayamin bayan wannan wani rashin hankali kuma take again?” Shirt nasa Zeezee ta shiga tukiukuyawa tana mai nufin kar ya tozarta ta.
“Babu wannan ne kad’ai kuma shima zata gyara ko Zainab?” Tana riqe da shirt nasan ta gyad’a kai “eh eh wallahi.”
“Zan samo mata me aiki ma tana taimaka mata tunda gidan yayi girma da yawa.”
“Me aiki?” exclaimed Mama. “Wallahi bame aikin da zaka nemo ma wannan ‘yar, shara da mopping d’inne shine se an nemo mata me aiki? Da wanke wanken da befi a k’irga ba? Inhar kana k’aunan Allah kaja baya da wannan zance, ban yarda ba. Koda wasa karka d’aukan mata me aiki, kajini ko?”
“Naji Mama amman-”
“Don Allah nace Maj-Gen kai wai bakasan halin Zeezee bane? ka fara mata da haka by the time kuka zo kuka haifafa fah? Ya gidan naku ze kasance tunda yanzu da take ‘yar amaryarta ma baka barinta tayi aiki.”
“Toh Mama za’ayi kaman yadda kikace kiyi hak’uri.”
“Yauwa yanzu inason kabani waje kuma kabarni da ita kad’ai.”
“A’a Ya Al’ameen dan Allah karka fita wallahi dukana zatayi” Zeezee tayi maganan tana sake matsesa a jikinta.
“Mama please kiyi hak’uri karki ta6ata zatayi wanke-wanken.”
“Naji bazan ta6a ta ba ka fita to mu samu mu had’a kitchen d’in.”
“Ya Al’ameen wallahi kafita duka na zatayi.” Seda Mama tayi dagaske tasamu ta fito da Al’ameen. “Maza kama yin wanke-wanken wawiya kawai.” Nan da nan Zeezee ta shiga washing dishes d’in sama-sama kaman yadda ta saba ashe duk kallonta kawai Mama take, ta gama zata fara jerawa Mama tace, “dawo dawo dasu nan” cup d’aya ta d’aga ta shafa jikin se maik’o kawai malam sekace be shiga cikin ruwan kumfa ba. Lafiyayyen mari Mama ta kai mata a baya kafin tasa ihu Mama ta aza hannunta akan lips nata tana mata alaman tayi shiru. “Wallahi kika bari Maj-Gen ya fito kinji na rantse sena gayawa Babanki har nan ya biki ya baki d’ankaren duka” jin haka ta had’iye ihun nata tare da shanye hawayen nata.
“Hakane kin wanke? Bazaki bar aikin cuwa-cuwan nan da kika saba bako? Kanki ma yanzu zaki cutar tunda tun chan agida haka kikeyi.” Mama na tsaye a kanta Zeezee ta sake bin wanke-wanken seda suka fita k’al sannan ta share kitchen d’in tayi mopping ta goggoge kan counter dasu gas cooker and microwave. Bayanta kan ze 6alle, tunda tasan kanta bayan aikin wankin da Ya Ibraheem ya ta6a sata bata sake aikatuwa kaman na yau ba. “Shara fa kinayi?”
“Mama dan Allah kiyi hak’uri ki tafi gida wallahi nayi shara yau bayana yana iya 6allewa.”
“Ma’ana bakiyi kenan?”
“Zan fara gobe dan Allah kiyi hak’uri.”
“Maza d’ago tsintsiya ki bini ashe ba sharri idona suka miki ba tun shigowana na karanci gidan naku da k’ura” haka Zeezee tana tura baki tana matse k’walla tabi bayan Mama, kap gidan ranan seda Mama ta sata ta share ta kuma yi mopping harda dusting sannan tabi gidan duka da turaren wuta. Tanayi tana kuka amman hakan besa Mama ta k’yaleta ba.
“Wayyo Allah zan mutu!” tayi maganan baje akan tiles tana riqe da bayanta.
“Tashi kije ki kiramin Maj-Gen. d’in.”
“Mama wallahi bazan iya tashi ba.”
“Aww na saki share cikin gidan naki kenan ko?”
”A’a zan tashi zan tashi” tana bud’e d’akin nasa ta tarar dashi akan laptop yana aiki “wai kaje Mama na maka magana.”
“My Princess ya haka da riqe baya?”
“Ban sani ba ai wallahi ka kyauta nikan kazo.” Bayanta yabi suka fice akan kujera opposite na Mama suka zauna “gani Mama.” yayi maganan gentlemanly.
“Yauwa Maj-Gen ka bud’e kunnuwanka da kyau ka saurareni don Allah nace.”
“Toh Mama.”
“Take a look at your house now what can you say?” Yadda Mama ta buk’acesa yayi. He couldn’t believe it ko ina se sparkling yake ga k’amshin turare na tashi. A rayuwa yanason yaga muhallinsa da tsafta kaman haka “wow” yayi breathing “its sparkling yayi kyau sosai.”
“Good toh haka nakeson gidanka ya kasance a kullum, alk’awarin abu d’aya nakeson kamin, ka tabbata ko wani safiya Zeezee tayi shara tayi moppkng after each 3-4 days kuma tayi dusting, wanke-wanke kuma ban yarda wanke-wanke ya kwana a gidanka ba inba wai rashin lafiya take ba. Kar ya zamana takai sati bata wanke muku toilets ba. Zancen me aiki kuma banason ka d’au ma Zeezee me aiki dukkanin aikin nan dana lissafo ita nakeson tanayi can I count on you?”
“Uhmm Mama you see-”
“Bazaka iya min ba kenan?”
“A’a bawai haka bane-” saurin katsesa tayi “then can you promise me all that?”
“Yes Mama, I promise in shaa Allah.” wani mugun kallo Zeezee ke binsa dashi sannan ta sauk’a har k’asa tana kukan munafirci “Mama dan Allah kiyi hak’uri wallahi inhar na cigaba da aikatuwa haka kullum wataran gawa na zaku cire daga gidan nan, kiyi hak’uri dan Allah kibar Ya Al’ameen ya d’aukomin me aiki I promise tare zamuna yin aikin da ita Allah wallahi.”
“Zainab banason sakarci kina jina koh? In kinga Maj-Gen. ya d’au miki me aiki toh wallahi se in kin haifafa hidiman yara ya fara miki yawa, kana jina ai Maj-Gen?”
“Eh Mama naji.”
“Good ke kuma addu’a zan yita miki Allah shiryeki don zagi bashida amfani, amman kisani duk ranan da garin Allah ya waye baki aikata wannan aiki dana lissafo ba bakuma dan wani k’wararren dalili ba Allah ya isa na yana kanki.”
“A’a Mama please, kiyi hak’uri in shaa Allah ma zata nayi ba sekin ja Allah ya isa ba.” cewar Al'ameen.
“No ka barni da ita nasan halinta sarai ina barin nan bazata sake d’aga tsintsiya ba tunda kai na lura baka mata magana.”
“Kin jini ko bakiji ba?” Shiru Zeezee tayi not ready to talk.
“Aw in kira Babanki na fad’a
mishi.”
“A’a wallahi naji, naji karki kirasa dan Allah” tayi maganan fear na building a tare da ita. Da mamaki Al’ameen ke kallonta ashe duk rashin kunyarta tanada weak point, da kyau. Hak’uri Mama ta sake bawa Al’ameen akan rashin hankali irin na Zeezee sannan kuma a gabansa tayita yiwa Zeezee fad’a sosai sannan ta bisa da nasiha.
Bada jimawa ba tace zata tafi wanda Al’ameen yasa driver’n sa yayi dropping nata. Tana tafiya Zeezee ta zarce d’akinta tana me rusa kuka tsakaninta da Allah yanzu shikenan ita hutunta ya k’are kenan? Kukan ta cigaba dayi koda Al’ameen ya ganta be mata magana ba sabida yasan theres no point doing so in banda rashin kunya ba abinda zata masa don haka ya zarce d’akinsa shima.
*~ *~ *~
Washegari Zeezee ta tashi da sassafe ta gama ayyukanta tas, ji take wane bayanta ze 6alle dan azaba. Al’ameen na fitowa yaga ko ina sparkling clean ga kuma k’amshin turare d’akin Zeezee ya nufa ya sameta miqe kan gado tayi ruf da ciki. A nitse ya k’arisa ya zauna kan side drawer nan ta juya mai baya. “My Princess?”shiru ba amsa, “My Princess sannu da aiki kinji? Everywhere is sparkling clean ga wannan tukuicin aikin da kikayi.” ya ajiye mata bundle na N50.
Juyawa tayi don ganin meye tukuicin tana ganin kud’in ta d’aga bako kunya. “Bayanki na miki ciwo ne?” Kaman bazata amsa saba se kuma ta gyad’a kai. “Do you need a massage?” Tana so tana kaiwa kasuwa “ni banaso kafita min daga d’aki ai duk kaine.”
“Yi hak’uri toh.”
“Ni kafita min.” Besake ce mata komi ba ya miqe, ya kaiga bakin k’ofa ta tsayar dashi “kazo kamin wallahi bayana kaman ze 6alle” murmushi kawai ya saki yana kallonta da take rage kayan jikin nata, bajewa ta sake kan gadon tana jiran ya fara mata tausar. A hankali taji sauk’an hannunsa akan bare back nata, take heart nata yayi skyrocketing ita kanta ta rasa dalilin da yasa every single touch na Al’ameen yakeda strong influence akanta.
Massaging mata baya ya shiga yi a hankali wanda don dad’i har wani bacci Zeezee ta soma ji, hakan ya cigaba da mata har seda tayi bacci. Kwanciyarta ya gyara mata sannan yaja comforter ya rufeta da shi tare da rage speed na AC’n tunda batada kaya. Dawowa yayi ya zauna akan side drawer yana k’are mata kallo a yayinda wani irin wutan sonta ke sake ruruwa a zuciyarsa, he can’t wait for the day Zeezee zatayi accepting nasa as her husband, surely that day will come shiyasa baze gaji da trying to make her happy ba. What a gentleman!
Hannunsa ya d’aga a hankali ya aza akan fuskarta yana shafawa sam bata motsa ba seda yaja hancinta. Hannun nasa ta kama tasa k’ark’ashin kumatunta duk a cikin baccin, ta sake kuma tak’i ta sake hakan ya sanya Al’ameen murmushi sosai. Haka ya cigaba da zama a wajen yana k’arewa beautacious innocent while at sleeping face nata kallo, da k’yar ya samu ya iya ya zare hannun nasa tare da pecking forehead nata yayi whispering “I love you Princess” sannan ya fice.
_5 days later..._
Gabad’aya rayuwan kanta tabar yiwa Zeezee dad’i dalili kuwa shine wannan aiki da Mama ta aza mata shi na dole, domin haka tayi coming up da plan. Tana idar da sallan Asuba yau ta d’au towel ta tsoma cikin warm water sannan ta mammatsa a jikinta seda ya d’au zafi. Tana jin dawowan Al’ameen daga masallaci ta ruga gado ta kwanta tare da jan comforter ta rufe duka jikinta dashi harda kanta ciki tana kakkarwa. Not long enough ya shigo d’akin nata as usual don duba ko tayi Sallah tunda yanzu ba kwana d’aki d’aya suke ba.
“Princess kinyi sallah?” Yayi maganan some inches away from her bed har anan bata motsa ba. “Zainab?” Cike da kasala wane wacce batada lafiya ta leqo da fuskarta waje “Ya Al’ameen...” Ta fad’a cikin wani irin muryan dake nuni da mutum baida lafiya.
“Subhanallah! Princess are you okay?” Ya k’are maganan yana zaune akan gadon a gefenta. “Meke damunki Princess?”
“Zazza6i nakeji.”
“Zazza6i?” Ya miqa hannu tare da feeling body tempreture’nta extremely high ya jisa. “Subhanallah! Princess you are sick, sannu kinji?” Wutan d’akin ya kunna ya shiga toilet tare da fitowa da bowl cike da ruwan sanyi kad’an. Matsa mata jiki dashi ya shiga yi da towel d’in idan ya tsoma cikin ruwan. Ahaka har fake hot tempreture’n nata ya sauk’o se kukan shagwa6a take ta mai.
“Sannu kinji? First thing in the morning za muje asibiti, sannu koh?” Comforter yaja ya gyaggyara mata kwanciya, ya miqe ze fice kenan ta riqo hannunsa “Ya Al’ameen Mama nakeso, dan Allah ka kaini wajen Mama ita kad’ai zata iya taking care of me.”
“Toh karki damu sleep now, later on semu kaiki gida kinji?” Dad’i kasheta finally her plan has finally worked out! Kai kawai ta gyad’a mai kaman dagaske. Yana barin d’akin tahau daka tsalle sauk’a tayi daga kan gadon tare da jan d’aya daga cikin trolleys nata tahau had’a kayakinta ciki. Ai ba jaka bace ita da zata riga shara kullum tana dafa farin shinkafa, spaghetti kokuwa macroni wa bak’in Al’ameen gwara taje gida chan ta huta abinta.
*© MIEMIEBEE ™YGC!*
www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
No comments:
Post a Comment