BY MIEMIEBEE
PAGE 09
*December, 2016*
D’akinsu Ibraheem ta nufa direct, kwance ta tarar da shi bisa gado da laptop nasa zaune kan cikinsa ya had’a da earpieace da alama kallo yake. “Ya Ibraheem wai kaje kayi wa Zeezee wanka” tayi informing nasa. Earpieace d’in yacire tare da miqewa zaune “what?!” Yayi exclaiming. “Inyi ma waye meh?”
“Kayi wa Zeezee wanka.”
“Buro-uba zan mata ba wanka ba, in ba iskanci ba I have three siblings kizo kina wani cemin ni zan ma wancan Zeezeen wanka toh barin yi ba kije kice barin yi ba, aikin banza kawai! Mschw!”
“Oho bani zaka gaya wa hakan ba se kaje kasamu Baban daya saka yimatan ka fad’a mai anan ne zan san eh ka cika saurayin Eesha White.” yi yayi kan beji last statement nata ba;
“Baba ne yace in mata wanka?” Yayi maganan a bit shocked.
“Eh naje Zeezee tace se kai.”
“Wallahi se naci uwar yarinyan nan kap gidan nan ba wanda ta raina se ni” Mariam de bata sake cewa komi ba ta fice kitchen dan had’a musu breakfast.
_10 Minutes Later..._
“Wai kam ina Ibraheem ne? Yazo yayi ma yarinyan nan wanka ne yake b’atan lokaci haka?” Baba dake riqe da Zeezee a hannu yayi maganar a fusace. “Wai Hafsah ni kad’ai ne a d’akin?”
“A’a kaida K’anwarka ne a d’akin” ta miyar masa da amsa tare da juya mai baya. “Oya kema tashi yau ‘yarki zata fara zuwa school kin kama kin wani baje kan gado ga ke baki damu ba koh? Tashi da Allah kije ki had’a mata lunch pack nata, ki sa mata komi bibbiyu sannan ki soya mata k’wai biyu ki dafa mata biyu up you go.”
“Alhj!” Mama ta zaro ido waje, “k’wai hud’u ita kad’ai?”
“Ina ruwanki da kud’in ki ake siya?”
“Allah kawo ranan da zaka ce min bakada kud’i.”
“Kan ki akeji, ke wai bakisan ana hakan bane don asa mata son makarantar a ranta? Kinada matsala wallahi.”
“Allah kyauta” tace tare da miqewa, dai-dai nan Ibraheem shima dake sanye da singlet da ¾ trouser yayi sallama ya shigo d’akin.
“Se yanzu kaga daman zuwa?” Shiru... “Magana nake ma da wani d’an banzan farin fuskan ka kamar k’osai a wajen.”
“A’a” ya sadda kansa k’ansa.
“Zoka d’auketa da Allah.” Kai ya d’ago in disbelief yana kallon Baba shin Zeezee batada k’afa ne da za’a ce masa yazo ya d’auketa? Halan k’afafun nata na kwalya ne.
“Me kake jira wai?” Da wuri yayi kan Baba yasa hannu ze amshe Zeezee dake bacci abinta, hannunsa na tab’a jikinta ta hau shure sa “ni banasho.”
“Zeezee Ibraheem nefah tashi ya miki wankan” a hankali ta bud’e idanunta tana kallon Ibraheem sannan ta yarda ya d’auketa. Maimakon yayi hanyan bathroom dake d’akin, se ya hau hanyan barin d’akin, ya kai dab ga fita Baba yace, “d’an fari ina kuma zaka kaita? Ko ka manta hanyan bayin neh?”
“Zanje na mata a bathroom namu ne.”
“Brush nata da sponge nata kuma fah?”
“Bari in d’auk-”
“Wuce da Allah kayi mata anan kaima kayi wayo wai ko? So kake kaje can ka mata mugunta mugu kawai wuce ina ganin ka.” Haka Ibraheem kaman yayi kuka ya shiga bayin da Zeezee ya cire mata kaya ya mata brushing sannan ya hau mata wanka yana tab’a mata fuska tasa wani d’ankaren ihu, take Baba ya shigo “ya haka? Me kake mata?”
“Meh kuwa Baba? Wanka nake mata.”
“Kayyanshi ne Baba ya matse min fuska.”
“Ai nasani mugu kawai” Baba yakai masa bugi a baya “yimata a hankali nace!” kuka ne kawai Ibraheem beyi ba da zaran yad’an tab’a mata fuska seta sa ihu Baba ya mauje sa shikuma, a haka har suka samu suka gama wankan yafito da ita nannad’e cikin towel. Man shafawanta ya d’auko da niyan shafa mata ta shiga turesa.
“Meh haka? Da Allah nikam ki tsaya in shafa miki.”
“O’o nishe jikina ya bushe.”
“Yaushe ne jikin naki ze bushe? Ki tsaya in goge jikin naki da towel.”
“O’o ni banasho.”
“Baba kace mata ta tsaya.”
“Zeezee tsaya ya shafa miki kinji?”
“O’o ni banashon Ibyaheem (yau ba Yayan ma) ni Yashmeen nake sho.”
“Tafi nono fari” cewar Ibraheem tare da galla mata harara. “Oya Ibraheem jeka kira Yasmen kace tazo ta shafa wa Zeezee mai.”
*** A kitchen...
Dawowan Mama kitchen Mariam dake riqe da stirring spoon a hannunta tana kula da indomie’n su tace, “wai Mama kam ina zaki kai wannan eggs haka?”
“Sekin tambaya ne? Na Zeezee mana.”
“4 eggs ita kad’ai?”
“Iyi kuwa.”
“Wallahi baramu yarda ba muma, ai muma haifan mu akayi mu ace mu d’au k’wai dai-dai ita hud’u? Hud’u? Nima bibbiyu zan d’aukan mana yau.”
“Na yaushe kuma bayan an riga an aza k’wan kan wuta.”
“Soya mana zan” nan ta nufi fridge ta ciro musu k’wai ta hau soyawa.
“Kins-” shigowan Baba kitchen d’in ya sa Mama katse maganarta.
“Wai ina breakfast na yarinyan nan ne? Ko sekun sata latti tukuna?”
“Gashi nan fa Alhj mu fita nikam.”
“K’wan can fa nawaye?”
“Na Zeezee.” cewar Mama.
“Kamar ya na Zeezee? Ba biyu nace ki soya mata ba?”
“Kai ni Alhj ka cika bin diddigin abu wallahi ga breakfast na K’anwarka nan ba seka fice ba, ina ruwanka da abinda ke gudana cikin kitchen d’in kuma?”
“Ke Mariam k’wai nawa kika d’aukar muku yau?” Shiru... “Dake fa nake!”
“Bibbiyu.” tayi maganan a tsorace.
“Bibbiyu? Ban hana ba?”
“Ka hana amma naga Zeezee fa har guda hud’u ita kad’ai.”
“Uwaki nan da kike had’a kanki da Zeezee toh wallahi daga yau in sake ganin me d’aukan k’wai biyu a gidan nan ya soya yaga abinda zan mai” yana kaiwa nan ya wabje plate daga hannun Mama yayi ficewarsa.
~* ~* ~*
7:07AM aka gama shirya Zeezee, kowa a gidan seda yayi contributing to shirinta as Baba yayi ta tada musu hankali. Pink leggings da vest meh crossed arms fari me kwalyan pink aka sanya mata sannan aka d’aura mata k’aramar blazer pink akai. Shoes nata kuwa pink ne seda farin socks sosai tayi kyau wane ‘yar turawa wai ahaka ma tasa an cire mata beads nata jiya. Bayan Baba ya gama yi mata wanka da designer turarukansa ya saqala mata pink disney bag princesses nata a baya sannan ya riqe mata had’ad’d’en lunch pack nata me heart shape suka hau tafiya, ganin sun iso har bakin k’ofar barin d’akin Mama batace komi ba, bata kuma da niyan cewa komin Baba yace, “ke wai haka akeyi neh? Yau ranar farkon zuwan ‘yarki school bako Allah yabada sa’a? A wani wajen ma ke da kanki zaki kaita.”
“Toh Alhj naji nayi laifi, Zeezee Allah ya bada sa’a kinji Mamana?”
“Niba Mamanki bane niba shohuwa bane.” Ta k’are maganan tana bubbuga k’afa, dariya ne yaso kub’uce wa Mama amman batason yi kada Baba yad’au wai ta huce seta maze.
“Toh Auta na Allah yabada sa’a ayi karatu sosai fah.”
“Toh ba-bye” se anan suka fice da Baba har sun iso tsakar gidan amman cikin sauran yaran kap ba wanda ya fito duk suna ciki suna kan shiri Yasmeen kamma ko uniform bata sa ba.
“Ibraheem! Ina kuke? Zaku fito ne ko sekun sa min K’anwa latti tukuna?”
“Baba gamu nan” Ibraheem yayi ihu daga ciki yana k’ok’arin sa oil a hannunsa dan shafawa a kai.
_2 more minutes..._
“Baku san ni bane wallahi tafiya zan in barku, taho mu tafi Zeezee” dai-dai nan Ibraheem da Omar suka fito. “Su Mariam fah?”
“Bansani ba nima” cewar Omar yana adjusting collar rigarsa.
“Da kyau mutafi, Mariam! Ke da Yasmeen seku biya ta keke napep kokuma ku taka da k’afa mu mun tafi.”
“Allah sarki Baba gamu nan zuwa fah” cewar Mariam da ihu tana sa kajol a idonta, Yasmeen dake gefen gado tana pulling socks tace, “ba duk shi yasamu lattin ba aka fara shirya Zeezee kaman tashin duniya.”
“Kede bari ina lip gloss yake?”
“Na cikin chess of drawer’n farkon nan ki duba.” Har seda Baba ya kunna mota ready to leave them behind sannan su Mariam suka samu suka fito nan ma Mariam bata sa socks ba wai se a cikin mota.
As always Ibraheem ya nufa k’ofan gaba ze shiga da wuri Zeezee ta sha gabansa ta rik’e handle d’in restarining him. “Ke ya haka?”
“Ni jan jauna a gaba.” Tayi stating confidently cike da rashin kunya.
“Ke asuwa? K’aramar kwaro dake matsa min da Allah!” ya tunkud’e ta. D’ankaren ihu ta saki wanda ya dawo da attention na Baba kansu.
“Ya haka meke faruwa?”
“Ya... Nama fasa ce maka Ya d’in” ta harare sa sannan ta cigaba, “Ibyaheem ne ya mareni a kaina.”
“Mari?!” Exclaimed Baba, “ba kada hankali ne? Yarinya zata school ka sata kuka? Ka kiyaye nifa.” Baba yayi scolding nasa.
“Baba ni yaushe na mareta? Ta matsamin na shiga gaba wai a’a.”
“Eh ni jan jauna kaje baya.”
“Oya koma baya toh Ibraheem.”
“In koma baya?”
“Kaji ni deh” ze saki magana Baba ya katse sa “ka shiga ko kuwa ka tafi da kanka.”
“Ai wallahi gwara na tafi da kainan” ya juya kenan Baba ya kirasa “maras kunyan yaro kawai dawo! Dawo nan dan Ubanka seka zauna a bayan wuce ina ganinka!” Ya tsawata masa haka yana kumbure kumbure yayi joining k’annensa a baya, suka matsu su had’u a yayinda Zeezee ke gaba ita kad’ai tana shanawa abinta. Su aka soma dropping sannan Zeezee, a inda aka tanadar dan parking motoci wato parking space Baba yayi parking motarsa sannan ya zagayo ya ciro Zeezee a hannu ya riqeta suka k’arisa class nasu Nursery 1.
Form teacher’n su Zeezee Mrs. Anderson na hango Baba tayi sauri taje ta taresa wato tun ranan da akayi interview Zeezee ta shige wa Aunty’n su rai, ba yadda Aunty’n batai ba amman Zeezee tak’i zuwa wajenta. Bayan sun gaisa da Baba ta nuna masa seat na Zeezee wanda yake nan close to her table, ajiye Zeezee Baba yayi yamata adjusting kayanta sannan yace, “se kiyi karatu ko K’anwata in kun tashi by 12:30PM zanzo in d’auke ki okay?” Cike da rashin fahimta tace, “Baba tafiya zakayi ka banni?”
“Eh Zeezee bakiga sauran ‘yan class naku suma iyayensu sun ajiye su sun koma gida ba?” Mai da kallonta tayi kan ‘yan class d’in tana binsu da kallo taga duk ba parent bayan nan gashi duk yara matan an musu kitso da beads gwanin sha’awa, ita yanzu bama wannan ba wai tafiya Baba zeyi ya barta ta d’au yadda suka zo tare haka zasu koma kamar a kyaftawan ido ta sauk’o daga kan seat d’in ta shige jikin Baba “ni o’o tare zamu tafi mu koma gida na fasa makalantan.”
“Zeezee kin tab’a ganin inda aka fasa karatu? Yi hak’uri ki zauna kinji? Anjima kad’an zan zo in d’auke ki.”
“Ni o’o” ta b’arke da kuka tabar Mrs. Anderson ta tab’a tama tak’i duk ‘yan ajin se kallonta suke.
Ana cikin haka wani mutum wanda a shekaru ze girmi Baba koda irin 5 years haka ya shigo, babban mutum ne da an gansa, hannunsa riqe yake da wata little angel wanda ga dukkan alamu ‘yarsa ce saboda tsantsan kaman da suke. Mrs. Anderson na ganinsu tayi excusing kanga gun Baba ta nufa wajen mutumin.
“Lubabatu right?” Tayi maganan tana kallon ‘yar mutumin data sha ado sosai wane Zeezee ga beads kota ina akanta, “follow me please Mr. Maitafseer” tace da mutumin. Seat na Zeezee ta ajiyewa Lubabatu jakarta tace da Zeezee, “look here, I’ve made you a friend her name is Lubabatu Maitafseer so stop crying okay?” Zeezeen da tunda Aunty ta fara magana ba gane abinda take fad’i tayi ba banda Lubabatu dataji ta ambata ta sake sa kuka bayan data k’are wa Lubabatu kallo, sosai Baba ya shiga lalashinta “shikenan toh ya isa Lubabatu koh? Ta tab’a min ke? Sorry toh” Kukan take har yanzu ba makawa, Lubabatu da dad nata suka tsaya kallon ta chan Zeezee tace, “an yima Lubabatu kitson beads ni ba’a min ba” ta kuma fashewa da kuka. Dariya sosai dukansu wajen suka hau yi Alhj. Matafseer ya nisanta yace, “da alama wannan itace auta koh?”
“Itace” Baba ya amsa mai yana murmushi, miqewa yayi da Zeezee a hannunsa suka gaisa da Alhj. Maitafseer tare da yin formal introduction. “Zeezee sauk’a kije ki zauna kinji K’anwata?”
“O’o se ammin ilin kishon Lubabatu.” Baba ya kalli Dad na Lubiee dake murmushi yace, “karka manta fa an mata kitso da beads me kyau tasa mahaifiyarta a gaba sam se an cire mata take wanan fitina yanzu.”
“Ahab! Ko Lubiee nan jiya seda tace a cire mata na hana uwar, ba duk abinda yara suke so zamuna musu ba.”
“Hakane...” cewar Baba kamar dagaske.
“Zeezee mama na sauk’o kinji? Ga k’awa nan na miki kinji sunan ta Lubiee.”
“O’o ni ba maman ka bane niba shohuwa bane.” tasa kuka. Dariya duk suka tsaya yi at her comment, “ya isa, sauk’a toh K’anwata” da k’yar ya samu ya sauk’e ta, ta tsaya tana kallon kitson Lubiee “ni se ammin ilin wannan.”
“Karki damu, muka koma gida za’a miki” Baba yayi assuring nata. “Sunan ki Lubiee?” Zeezee ta tambayi Lubiee.
Kai Lubiee ta d’aga in response “ke kuma Zeezee?” Itama ta gyad’a mata kan.
“Yauwa jeku zauna toh se kuyi karatu fah” hannunta Lubiee taja suka zauna ko ba’a tambaya ba za’a san Lubiee ta girmi Zeezee danko ta fita wayo, shiru Zeezee tayi bata sake cewa komi ba seda taga Baba ya d’au hanyan barin ajin ta sake sa ihu shima se yaji bare iya barinta ba, da k’yar Dad na Lubiee yajasa sukayi waje. Kuka kenan! Kuka Zeezee ke wane ana cire mata rai Lubiee ce ke lalashinta har ta samu tayi shiru ko da aka fita break Aunty da Nanny suka bubbud’ewa kowa lunch pack nasa seda suka sha mamaki ganin yadda aka cika wa Zeezee nata.
Sede wani abin mamaki sekace ba Zeezee me rowan da muka sani ba, ganin nata chocolates d’in sunfi na Lubiee yawa ta d’ibi guda biyu ta bata cikin d’an k’ank’anin lokaci wasa da shak’uwa ya shiga tsakanin Zeezee da Lubiee.
~* ~* ~*
Ko minti d’aya Baba be k’ara kan 12:30PM (lokacin tashin su Zeezee) ba, ana ringing bell ya shiga school yayi class nasu Zeezee alokacin suna ta wasa ita da Lubiee da sauran ‘yan class nasu, tana ganin sa taje tayi hugging nasa, sosai Aunty ta sake yabawa k’ok’ari irin na Zeezee dai-dai Baba yazo fitowa suka had’u da Baban Lubiee gaisuwa kad’an sukayi kowa yabi path nasa.
~* ~* ~*
Dawowan su Baba gida Zeezee tayi ciki da gudu, Mama ta tarar tsaye a tsakar gida da gudu taje tayi mata oyoyo Mama ta d’agata sama “yaya school d’in?”
“Mama nayi k’awa sunanta Lubiee ko Baba?”
“Sannu da zuwa Alhj.”
“Yauwa sannu”
“Zeezee tayi kuka da ka ajiye ta?”
“Sosai ma se a hankali zata saba ai.”
“Toh Auta na me aka koya muku?”
“Littin (written) form of A and sound ‘ahh’, and litten form of B and sound bhh.”
“Ahh gaskiya autan nawa na ja.”
****
Da yamma bayan tafiyan yaran islamiyya Baba kuma masallaci Zeezee ta samu kanta, k’usa ta samu ta nufa garriage inda Baba ke parking motarsa da yake mugun ji dashi fiye da duk wani abinda ya mallaka. Dai-dai driver’s door ta zana babban letter A sannan da small one a gefensa haka tabi other side d’in ma tayi thesame thing with letter B, jiki ta sata wane batai komai ba taje tasamu Mama dake zaune tsakar gida tana tsifa, “Mama zan tayaki.”
“Inba kaud’i ba ina ke ina tsifa?”
“Ni shena miki.”
“Nace baza kiyi ba kuma ki yasar da k’usan” ihu tasa ta soma kuka, badan Mama na so ba tace ta taso ta tayata. Tsifan da ba’ayi ba ranan kenan, ita ta hana Mama yi ita kuma bawai iyawa tayi ba.
Atare Baba da yaransa suka iso gida kaman ance Baba duba motanka yana kai dubansa yaga letter A na mai sallama “subhanallai me wannan? Waya min wannan d’anyen aikin? ‘yan unguwa ko meh?”
“Laaa Baba gashi ma har a nan!” cewar Yasmeen da hanzari ya zagaya ya duba.
“Aiko ba’a tambaya ba ansan Zeezee ce” cewar Mariam, a rayuwa ba abinda tafiso kan taga Baba da Zeezee suna fad’a. A fusace Baba ya nufa ciki su Mariam ne a sahun baya suna binsa.
“Zeezee! Zeezee! Zo nan!” tana jin muryan Baba ta lab’e bayan Mama dake zaune kan sofa a parlour. “Ba babanki bane yake kiranki? Kije mana!”
“O’o, Mama karki bari ya tab’ani jan baki shweet d’ina.”
“Me kika masa tukuna?”
“Bab-” bata k’are maganan ba sega Baba da gayyansa suna shigowa cikin parlourn, cusa kanta tayi jikin Mama.
“Ya haka Alhj wani abu ne?”
“Zeezee!” Ya kira sunanta a tsawace, kakkarwa ta soma, “mesa kika zana min jikin mota? Dan bana dukanki koh? Wayace ki zana min mota?” Shiru... “Dake fa nake magana!” Ya sake fad’a a tsawace. Kuka Zeezee tasa “toh kayi hak’uri amman kad’an ka gani wallahi ai nasha gaya maka kadena biyewa ‘yar nan bakaji ga irin ta ai.” Ignoring what Mama said yace, “kika sake zana min mota sena zane k’afafuwanki da tsintsiya ce miki akayi mota gun rubutu ne?” Hannu ta d’aga ta zagi Baba, baki kap dukansu including Baban suka sake in shock.
“Zagi! Ni kika zaga Zeezee?” D’ayan hannunta ta d’aga ta sake zaginsa sannan daga bisani ta sauk’e duka ta b’uya bayan Mama “ai kad’an ka gani nasha gaya maka adinga taka mata birki bakaji yau kanka abin ya koma ai.”
“Waya koya miki zagi? Iyyeh! Zan zane kifa! Ni kika zaga? Toh ki sake ki gani da wayan charger zan shod’e kafafunki!” ya tsawata mata sosai, kuka ta shiga yi sosai ko ta kanta beyi ba yabar parlour’n.
Dariya kenan! Ibraheem and others dariya suke tsakanin su da Allah wane dan shi aka turo su duniya, suna dariya suna yimata rawa da wak’ar shoki ita ko se k’ara volume na kukan nata take Mama ce kad’ai ke lalashinta “yi hak’uri amman kema kar ki sake, ba kyau zagin Baba ku kuma haka akeyi ne? K’anwar ku ce fah.”
“Ai Mama ajiye wanga zance a gefe” cewar Mariam in between laughter.
“Ahtoh! Bature beyi k’arya ba, 9 days for the thieve one day for the owner.” Omar ya mara mata baya suka cigaba da yiwa Zeezee dariya ita ko se kuka take.
Da dariyan yayyun nata ya isheta ta fice musu daga parlour’n gabad’ai taje chan bayan BQ ta baje a k’asa se kukanta take sha kan ba gobe.
*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com
No comments:
Post a Comment