Friday, 9 December 2016

‘YAR GATA CE!

BY MIEMIEBEE
PAGE 10

_Words can’t ever explain how much I love you *AUNTY SIS*, thank you for everything, thank you for being that one great special person to me. ILY eternally😘😘😘😘 I devote this page in special honour to you! Don’t thank me you deserve more and more!_




      _5 minutes later..._
    Baba ya dawo parlour da alama ya huce yanzu, Mama kad’ai ya tarar a parlour’n tana tsifa, “Ina Zeezee?” Ya tambaya.
   “Oho yayun ta sun sata gaba suna mata dariya ta fice ban san ina ta shiga ba” ba tare da ya amsa taba ya fice tsakar gida ya shiga k’olla wa Zeezee kira tana jinsa tak’i amsawa har a yanzu kukan take. Nemanta ya shiga yi chan bayan BQ ya tsince ta nishinta har wani sama-sama yake sekuma tabasa tausayi yaji dama be mata masifan ba, a nitse ya k’arisa gabanta yace, “Zeezee” kanta ta kawar daga kallon sa.
  “K’anwata yi hak’uri kinji? Tashi mu koma ciki” nan ma shiru. “Yi hak’uri kinji K’anwata Baba is sorry amman kema karki sake zana min mota kinji? In rubutu kikeson yi let me know sena baki paper ko book kiyi. Mota ba wajen rubutu bane kinji?” da k’yar ya samu ya shawo kanta dan banzan zuciya irin na Zeezee, bayan ta yarda ya d’auketa yace, “su Ibraheem sun yita miki dariya ko?” Ta gyad’a kai a shagwabance.
  “Yi hak’uri toh muje su baki hak’uri” a k’aramar parlour Baba ya tadda yaran, “waya miki dariya cikinsu?” Ya tambayi Zeezee.

   “Dukan su” tayi pointing nasu da finger.
  “Oya ku bata hak’uri.”
  “Hak’uri?” Exclaimed Ibraheem, “meh muka yi mata da zamu bata hak’uri?”
  “Uwarka kayi mata, d’an banzan yaro bata hak’uri nace!” Chan k’asa-k’asa alsmost like mumbling Ibraheem yace, “yi hak’uri.”
  “Ban jika bafa, ka bata hak’uri kace Zeezee kiyi hak’uri, oya ina jinka.”
  “Wallahi Baba raina ni zatayi.” yayi protesting.
  “Da kai da rainin duk uwaku, bata hak’uri nace!” Haka Baba ya sasu individually sukayi ma Zeezee apologising.

  “Shikenan koh K’anwata yi hak’uri” sauk’eta yayi tare da ficewa. Habaici ‘yan uwan nata suka hau yi suna zaginta kota kansu batayi ba taje ta d’ibo baby dolls nata da teddy bears ta jerasu kan table a waje sannan ta d’au ruwa cikin wani d’an karamin bucket ta ajiye se sponge case nata ta shiga ta d’auko. Wanka ta shiga yima dolls natan tafara da teddy’n kenan Allah ya fito da Mama “kai! Kai! Karki sa ma teddy’n ruwa!” dakatawa Zeezee tayi tana kallon Mama, “‘yar k’auye kawai wayace miki ana wanke teddy bear?”
  “Ni shena wanke, tunda Baba ya shiyo min su bashuyi wanka ba.”
  “Ce maki akayi mutane nesu? Karki sa musu ruwa nace!”
  “Ni shena sa, Baba! Baba!”
“Na’am K’anwata, Hafsah dan Allah kifita daga harkan yarinyan nan, dan Allah nace” Baba yayi maganan daga cikin d’aki.
  “Teddy bears fa zata ma wanka.”
  “Eh kibarta please.”
   “Dama ai ta nan kafi kauri, d’aure wa k’arya gindi, gidan wa aka tab’ayi wa teddy bears wanka?” Dawo da kallonta tayi kan Zeezee “kinji wallahi karki kuskura ki shigo min da su ciki in kin jik’an kinaji ko?”
  “Shena shigo dasun” tana kaiwa nan ta kwarawa teddies d’in ruwa tahau musu wanka jak’ab ta jik’asu da ruwa tazo shigowa dasu Mama ta bud’e mata ido sosai koda Baba yayi magana ta nuna mai she’s damn serious baza’a shigo dasu ba.
  “Shikenan K’anwata karki kula Mama kinji? In sun bushe seki shigo dasu, jeki cigaba da wasan ki” ciki tayi ta d’auko mai sannan ta bud’e kit na Mama ta zaro scissors ta fice da wuri bayan ta bi baby dolls da teddies d’in ta goggoga musu mai ta d’au d’ayan baby doll me uban gashin tasata gaba ta yayyanke gashin tas, haka tayi da sauran gabad’aya tayi musu aski Yasmeen ce tafito ta kamata in the act.

    “Laaaha’ila! Bade aski kika yiwa dolls nakin ba?” Dariya tasa ta kira Mariam, “Adda Mariam! Zokiga wani abu” atare Mariam da sauran suka fito, dariya suka hau yi ganin yadda Zeezee ta tand’e gashin kan baby dolls natan wane aikin wanzami. Dariya suka tsaya yi har seda Mama dake kitchen ta fito “wai haka kuka ta dariya lafiya dai ko?”
   “Dubi fa Mama” Yasmeen tayi maganan tana k’ok’orin d’ago d’aya daga cikin dolls d’in cizo Zeezee takai mata “kal ki tab’a min Baby na.”
  “Zeezee yanzu aski kika ma baby dolls nakin? Meye amfanin hakan?”
  “Gashin je fito ai, ba Mulan (cartoon) ma ta ashke gashinta ba kuma ya shake fitowa, nashu shuma je fito.”
   Habbaa!! Dariya dukansu suka sa gun, saura harda hawaye da k’yar Mama ta iya tayi shiru tace, “sekuma aka cemaki wannan cartoon ne? Ai tunda kika aske musu bai sake fitowa.”
  “Sheya fito”****


  Kasancewar yaran basu je islamiyya ba yasa bayan Sallan La’asr kowannensu ya kwanta yin bacci, Mama ma can ad’akinta ta mik’e tana bacci Baba da Zeezee ne kad’ai idonsu biyu shima don yana buga lisafi ne yana gamawa ya mik’e kan gadon d’akinsa “K’anwata zo mu kwanta kinji? Ajiye Ipad d’in kinga kinje school yau kamata yayi ki huta kema, bakiga sauran yayyun naki duk sunyi bacci ba?”
  “Ni o’o banajin basshi.”
  “Toh Allah baki hak’uri ni zan kwanta” nan da nan Zeezee tabar d’akinsa tayi nasu Mariam kulle ta tarar da k’ofan nasu, ba kalan knocking da batayi na suna ji suka k’i bud’ewa dan kanta ta nufi nasu Ibraheem suma haka suna jinta tana knocking suka k’i bud’e mata. D’an shirme tayi a tsakar gida, data gaji don kanta taje ta samu Baba a d’aki ta mik’e gefensa itama tana wasa da d’an gemun dayake ajiewa. Ahaka har bacci yayi gaba da ita ba ita ta tashi ba se 7:35PM alokacin gari yayi duhu shaarrr. Bayan ta fito daga parlour ta nufi parlour inda ta tarar da ‘yan uwan nata suna kallo “ni ahad’a min tea shafe yayi.”

   “Ke waya gaya miki safe yayi? 7pm nefa yanzu.” Cewar Yasmeen.
  “Meh 7pm? Ni a had’a min tea shafe yayi.”
  “Shareta Yasmeen fitina ne da ita ai Baba ya hanata shan tea da daddare ba abinda za’a had’a miki.” Mariam tayi stating. Kuka Zeezee tasa awajen tana kiran sunan Baba seda yafito tayi shiru, “K’anwata kin tashi neh?”
  “Baba kace Adda Mayyam ta had’a min tea.”
  “Babu shan tea da daddare yana saki fitsarin kwance, in kina jin yunwa a dafa miki indomie da egg naki koh?”
   “Yanzu ai shafe ne ba dale ba ni a had’a min tea.”
   “Dan fa bata saba baccin yamma bane shiyasa take gani kaman safe ne yanzun” Ibraheem yayi explaining.
  “Ba shakka kam, K’anwata ba safe bane fa yanzu dare ne.” Mik’ewa tayi k’asa agun tana birgima tana ihu ita a had’a mata tea, ba yadda Baba beyi da ita ba ta gane fa ba safiya bane dare ne yanzun amman inaaa sam takasa ganewa ita tunda tayi bacci ta tashi toh safe yayi don haka kuma a had’a mata tea. Haka Mariam ta had’a mata tean itade Mama tausayin katifanta take gudun kar Zeezee ta tsula mata fitsarin kwance.



**** 8:23PM
  Baba da kansa ya taya Zeezee suka yi mata homework, bayan sun gama yasa mata book nata cikin jaka “sauran bacci ko K’anwata? Akwai school gobe.”
  “Nishe an sha min beads ilin na Lubiee” nan Mama dake karatun Qur’ani ta juyo ta watsa mata harara “waye boyi-boyin ki agidan nan? Jiya kice se an cire yau kice a miyar? Kinyi k’arya.”
   “Ni nace ke jaki shamin ne” tayi maganan tare da murgud’a wa Mama baki.
  “Ai ko kince nima ba sa miki zan ba.”
  “Toh ya isa haka da Allah, kisa ‘yar yarinya a gaba kina exchanging words da ita, Zeezee asa miki beads?”
  “Eh” ta gyad’a kai.
  “Oya Hafsah ibo beads d’in maza ki sa mata.”
  “Wallahi-”
  “Ni banashon Mama Ya Omal nakeso” Zeezee tayi sauri katse Mama.
  “Omar kuma?” asked Baba.
  “Eh shi.”
  “Toh Hafsah mik’a mata beads d’in taje ta same shi ya samata.” Bayan Mama ta mik’a mata ta fice a k’aramin parlour ta tsinci yayyun nata suna kallon King Of Hearts gaban Omar tasha yayi saurin fad’in “ya haka? Matsa min nikam” beads natan ta nuna mishi “gashi ka samin.” Wani kallon rainin hankali ya sakar mata sannan yasa dariya ba shi kad’ai ba har sauran ‘yan uwan nasa.
  “D’an daudu ne ni da zakice in sa miki beads?”
  “Ni kasha min.”
  “Bazan san ba maras kunya kawai, matsa min ko na gaggaura miki mari inba iskanci ba ki dubi Adda Mariam da Yasmeen ki wani ce wai ni zan sa miki beads bakida kai.” Kuka tasa wajen har seda Baba ya fito tayi shiru, “ya haka? Meke faruwa?”
   “Omal ne yashamin beads wai o’o.”
  “Laha ila! Ni? Yaushe nace barin sa miki ba?” Cewar Omar.
  “Munafiki na sanka sarai maza zaunar da ita ka fara sa mata” ba tare da ya sake musu ba ya soma aiwatar da abinda aka sashi.
  “Ni banashon wannan film asa min dijney junior.” Banza da ita sukayi kaman basu jita ba.
   “Ashamin dijney” ta k’are maganar a shagwabance.
  “Shin baku jita bane?” Asked Baba.
  “Ayyah Baba yanzu fa ze k’are” cewar Mariam calmly.
  “Wayyayi kayya ne ni asamin disney.”
  Dogor tsuka Ibraheem yaja ya sa mata disney’n “kalli fa Baba shirme ake.”
  “Eh bar mata shi takeso” yana kaiwa nan ya fice, habaici yaran sukayi tayi tsakaninsu suna zagin Zeezee a yayinda Omar keta samata beads na mugunta yana d’ad’d’angale gashin bayan ya gama mata ta wuce d’aki ta kwanta tsakiyan su Baba ma yau.

***Washegari...
  _6:05AM_
   Bayan Mariam ta shigo ta gaishe da Baba kaman jiya ta gaya mai dalilin zuwanta da ‘toh’ ya juya ya shiga tada Zeezee dake ta sharb’an bacci.
  “Zeezee tashi kinji? Akwai school yau ko bakison kije kiga Lubiee?” Shiru... “Tashi kinji K’anwata.”
  “Ni o’o bayin jeba.”
  “School d’in?”
  “Eh bayin jeba.”
“Yi hak’uri.”
  “Ni o’o” ba yadda Baba beyi da ita ta tashi ba tak’i. Bayan sunci fiye da minti goma Zeezee tak’i tashi Baba yace da Mama “to ke bazaki sa baki bane?”
  “Ni asuwa? Wai daddawa acikin kunu, bayan kai Zeezee tana jin maganan wani a gidan nan ne? Tsakaninku” tana kaiwa nan ta juya mai baya tare da jan comforter.
  “Zeezee tashi kinji?”
  “Baba ni bayin jeba” tasa kuka, kuka take tsakaninta da Allah ita bazata jeba, at long last Baba ya amince mata “jeki Mariam, Zeezee bazata je school ba yau se gobe.” Kai kawai ta gyad’a cike da mamaki sannan ta fice bayan ficewarta Mama tace, “lallai ka cigaba da yima yarinyan nan duk abinda takeso muga ina ze kai ka da ita duka” banza da ita Baba yayi yaja Zeezee sukayi kwanciyar su.

*** A takaice ranan ba abinda Zeezee ta tsinana banda yima Mama rashin kunya da rashin ji, washegari ma da k’yar Baba ya iya tadata aka shirya ta school. Koda taje yau ma tayita kukan shagwaba seda taga Lubiee hankalinta ya d’an kwanta. Cikin sati Zeezee ta saba da school sede kullum kafin a tasheta se anyi drama ga zab’an wanda zeyi mata wanka, sa mata uniform, yi mata polish na takalami sa mata, do komi.

   _Saturday afternoon 2:32PM_
   Bajewa Zeezee tayi a tsakar gida tana kukan banza ita se an kaita gidan su Lubiee tunda yau ba school. Kota kanta Mama batai ba, hasali ma ignoring nata tayi ta shige d’akinta ta kwanta 2:40PM Baba ya dawo gida as always ya tambayeta whats the problem bayan ta irga masa ya share mata hawaye tare da fad’a mata ta kwantar da hankalin ta ze kaita gidan su Lubiee tunda yanada lambar Alhj. Maitafseer. Ba tare da b’ata lokaci ba ya kirasa bayan sun gaisa ya sanar dashi halin da ake ciki, cike da jin dad’i Alhj. Maitafseer yama Baba bayanin gidan sa dake Old GRA. D’aki direct Baba ya wuce ya tarar da Mama kwance “Hafsah! Hafsah tashi ko bacci kike?”
   “Ya akayi Alhj? So nake in huta kafin La’asr please.”
  “Hutu? Ai hutu be kama kiba.”
  “Me kake nufi?” tayi maganan tare da miqewa zaune.
  “Zaki shirya kanki da Zeezee yanzu in kaiku unguwa.”
  “Unguwa? Unguwa a ina?”
  “Zaki raka Zeezee gidan k’awarta Lubiee” yayi stating in an I-don’t-care manner.
  “Lallai kuwa!” Mama tasa hannunta a kunkumi “ba inda zani, akan ganin k’awarta za’a tauye min hak’k’i, ina nan ba inda zani.”
  “Semuga in zaman kanki kike a gidan nan na baki minti talatin ki shirya kanki da Zeezee wallahi in bakiyi haka ba ranki yana iya b’aci” nan ya sauk’e Zeezee k’asa, “karki damu kinji K’anwata zan kaiki gidan su Lubiee.”
  “Toh Baba” anan ya fice. Mama tafi minti biyar a zaune tana hararar Zeezee sannan daga bisani ta mik’e ta hau shiri exactly after 30 minutes Baba yadawo d’akin ya tarar da ita sun gama shiri tsaf, dad’i sosai yaji “kaiii masha Allah, Hafsah ta bade kyau ba tsaya keda K’anwata in d’auke ku hoto.”
  Dad’i sosai Mama taji dan yadda Baba ya yaba kyanta da kuma kwalyanta amman sede me? Batason nuna masa ta huce kan abinda yayi minutes ago, burning face tayi kan bataji me yace ba.

   “Haba Hafsah ta? Menayi kuma yanzu? Hoton ne bakiso?”
  “Ban sani ba” tayi speaking up finally.
  “Yi hak’uri toh ki tsaya” remembering that tana son ta tambayesa kud’in ankon bikin ‘yar k’awarta yasa ta saki fuska taja Zeezee ya d’auke su hoton. “Yauwa masha Allah, gaskiya in godewa Allah da yasa a beautacious woman like you ta kasance mata ta” yayi maganar yana editing picture nasun.
  “Uhm! Alhj ba de zak’in baki ba.”
  “Ai kema kin sani Hafsah, a kullum dad’a kyau kike.”
  “Uhm Alhj nace bikin ‘yar Aunty SDY fa ya matso.”
  “Toh Allah sa ayi a sa’a ya kuma bada zaman lafiya mu tafi ko? Inason in wuce kasuwa bayan nayi dropping naku.”
  “Ameen kud’in ashobe nakeso.” Ai take mood na Baba ya canza, a rayuwa ba abinda ya tsana kaman a tambayesa kud’i.
  “Ke shikenan kullum cikin tambayan kud’i kina ruining happy moments? Mu tafi da Allah.”
  “Bangane ruining happy momnts ba daga tambayan kud’i seka haura min sama.”
  “Toh ni banida tashi mu tafi kina b’ata min lokaci.” Komawa tayi ta zauna tace;
  “Ai wallahi ba inda zani ina nan seka bada kud’in nan had it been matter’n ya shafi Zeezee da without a second thought ka cire kud’i ka biya mata buk’ata wallahi nima ko ka bani kud’in ashobe dana gudumawa ko kuwa kaida K’anwarka kuyi ficewar ku” tayi stating in a serious tone. Ganin eh fa dagaske take ba inda zata inbe bata kud’in ba ya nisanta yace, “haka zaku k’are ai mutane sun d’au rayuwan k’arya sun aza wa kansu wai ba’a zuwa gidan biki seda ashobe toh Allah ya shirya ku wallahi”Zeezee kam se raba ido take ta kalli Mama ta kalli Baba.
   “Ameen ka fad’i koma meh nide ka bani kud’in kawai shikenan.” Dogon tsuka yaja “mschww! Nawa ne kud’in?”
  “Dubu ishirin ne duka, dubu goma na ashobe goma na gudumawa.”
  “Har dubu goma zaki kai as gudumawa saboda auren Aneesa ne?” (blood sister ta)
  “Muna zumunci sosai da Aunty SDY da kunya in kai mata abinda ya gaza dubu goma tunda akwai kawai ka kawo.”
  “Mschw! Allah shiryaki wallahi” hannu ya sa a aljihu yaciro wallet nasa tare da irga fifteen thousand (15K) “amshi.” Hannu ta mik’a ta karb’a tare da irgawa bayan da tagama taga be cika ba, “ya haka Alhj? Sauran biyar d’in fa?”
   “Abinda nake dashi kenan in na kwashe duka kud’in na baki me zamuyi cafani dashi gobe? Ki cikata da kud’inki maza tashi mu tafi.” Chan k’asa-k’asa tace, “ko a babu na rage hanya” wardrobe nata ta nufa ta adana kud’in sannan suka fice.

~* ~* ~*
   Dai-dai 3:07PM suka isa gidan su Lubiee bayan sun fito daga motan Baba dake daga ciki yace, “se bayan La’asr in shaa Allah zanzo in d’auke ku.”
  “Kai balaka shiga bane Baba?” Asked Zeezee.
  “A’a K’anwata keda Mama na kawo ku ba-bye.”
  “Toh se anjima” cewar Mama tare da jan hannun Zeezee suka shige.

  *** Cikin d’an k’ank’anin lokaci Mama da Ummin Lubiee suka saba se hira suketa zubawa wane sun san juna dama da jimawa, a yayinda Zeezee da Lubiee ke chan suna ta wasa, sosai Lubiee taji dad’in ganin Zeezee, su ci abinci ma sunk’i se wasa suke a tsakar gida kasancewar gidan nasu nada sarari sosai. Chan suka shigo ciki suka sami su Mama a parlour inda ake ajiyewa Lubiee motar wasanta wanda yake nan Babba sosai, ciki ta shiga ta tuk’a sannan tasa Zeezee ma ganin Zeezee bata iya ba tad’au remote control d’in tana driving nata dashi. A hankali Zeezee ta koyi driving d’in itama seyi takeyi ana cikin haka Baba yayi wa Mama waya kan gashi shigowa zasu gaisa da Abban Lubiee se su tafi.
   Bayan sun gaggaisa Mama ta d’ibo takalaman Zeezee dan sa mata ai atafir Zeezee tace bazata koma gida ba anan zata kwana in ma zata koma chan gida sede in da motan Lubiee zata tafi.
  “Shin motan naki neda zakice zaki tafi dashi?” Lectures Mama. Cikin kuka Zeezee tace, “ni wayyayi shena tafi dashi” tana shure k’afa.
  Se hak’uri parents na Lubiee da Lubiee ke bata amman ina se kaman ma sake tinzirata suke, if only zasu iya cewa ta d’au motan, atlast Baba yayi speaking up “taso toh K’anwata irin wannan kikeso?” Nan ta gyad’a mai kai.

  _Bade sai mata zakace zakayi ba?_ Mama tayi maganan unbelievably a zuci.
  “Toh shikenan za’a saya miki” Baba ya fad’a tabbatar wa Mama da zarginta.
   “Alhj a ina ne ka sayo wa Lubiee?”
“Anan Central...” nan yama Baba kwatancen shagon.
  “Toh thank you.”
  “You’re welcome incase ya ganka Alhj ya bugeka price d’in is 42K.”
   “Haha toh nagode mu tafi Hafsah” ya k’are maganan yana sharewa Zeezee hawaye. Baki Mama ta tab’e batare da tace komai ba, har gun motansu parents na Lubiee sukayi masu rakiya akayi ba-bye sannan Baba ya kunna mota suka tafi. A maimakon yayi hanyan gida seya kama hanyan kasuwa da Mama ta gano hakan se kawai ta girgiza kai “bade central d’in zaka wuce siyo wa K’anwarka motan ba.”
   “Toh ina ruwanki? Ke bakiga kukan datake tayi bane?”
  “Toh wallahi in haka ne nima se ka cika min dubu biyar d’in.”
  “Se mugani ai” haka Mama naji tana gani Baba yaje ya siyawa Zeezee motar itama sede nata har yafi na Lubiee ma girma, her’s costs 50K. Ba rigimar da batai wa Baba ba amman yak’i cika mata wai se k’arshen wata itan da za’ayi biki tsakiyan watan yau.
 
 
*© MIEMIEBEE*
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
  www.beeenovels.blogspot.com

No comments: