Saturday, 3 September 2016

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 27
BY MIEMIEBEE

Ko cikakken minti d’aya ba’a yiba Ahmad ya turo masa lambar PA’n Manager’n FCB ltd kasancewar Manager’n ya canza number kuma bayi sabon. Nan Anas ya kira PA’n ringing d’aya biyu PA’n ya d’aga gaisuwa ya fara wanda Anas ya dakatar dashi ransa se tafasa yake dan yadda ya b’aci. “Ka kai wa Boss naka wayan” ya fad’a authorititavely.

        “Wa ke magana please?” Cewar PA’n saboda bada layin office Anas ya kirasa ba.
     Ba k’aramin fusatar dashi tambayan PA’n yayi ba. Cike da b’acin rai yace, “Tambaya na ma kake wake magana? Inba wai so kake ka rasa aikinka a yinin yau ba give the damn phone ro your Boss.” Ya sake daka masa tsawa.
    “Sir I’m sorry but ya kamata insan wake magana kafin in maka abinda kake buk’ata.”
     “You’re stupid kajini? Nace you are stupid, ANAS IBRAHIM FAUZI ke magana CEO’n FLAMES ENTERPRISES.”
     “Omg! Sir dan Allah kayi hak’uri wallahi ban san kai bane,my apologies please kayi hak’uri.”
    Tsuka Anas yaja “mschww damuwanka wannan kuma, where is your boss ka kai masa wayan.”
    “Sir d’azu da safe Boss d’ina da family’nsa suka tafi trip zuwa Hungary.”
   “Meaning what? Meaning baraka kirasa kace inasan masa magana ba kenan ko meh?”
   “Sir I’m so sorry amman sanda ya fad’a min koda wasa kar na kirasa in batun aiki ne dan Allah kayi hak’uri. Hutu ya tafi”
     “Lalle kanasan rasa aikin ka nace call your Boss kace masa ina san masa magana.”
   “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri wallahi banasan rasa aiki na.”
    “Damn it!” ya buga hannun sa kan table, “what of business kuna running har yanzu ko shima kun dakatar?”

          Dadai lokacin knock yashigo daga k’ofar office nasa “come” yace bayan an bud’e k’ofar cleaners mata biyu suka bayyana. Tun daga bakin k’ofa suke gaishesa har suka k’ariso ciki. Papers d’in ya nuna masu nan d’ayan ta hau sharewa kallonsu ya tsaya yi bayan yayi holding call dayakeyi da PA’n.
      Har sun kai da bakin k’ofa ya kirawo su, dawowa sukayi suka tsaya gabansa “yyyess Sir” har i’ina suke dan tsoro. “Haka ne kin share nan wajen?” Yana nuna wanda ta share wajen “bakiga wancan paper’n bane?” Ya nuna mata wani piece na paper a k’asa. “Me amfaninki a nan in har shara ma baki iya ba se an koya miki? Eh?? Useless kawai.”

          “Boss dan Allah kayi hak’uri” tana b’ari taje ta share gudan paper’n kallonta yake sannan cike da nuna rashin damuwa yace, “you are fired ki tattara kanki kibar min building kije kisamu Adam yayi settling miki salary’nki. You are dismissed.” Kuka ta fashe da “Boss dan Allah kayi hak’uri wallahi ban gani bane hakan bare sake faruwa ba.” D’ayan ce tasa baki dan ganin yadda ‘yar uwarta ke kuka. “Boss dan Allah kamata hak’uri bada-”

       Mugun kallo kawai ya mata wanda yasa take tayi shiru. “Kekuma waya jefa bakinki cikin wannan matter? Nasan kinada dogon baki ba sekin nuna min ba I have eyes to see. You two dukan biyu are fired, kuje kusamu Adam yayi settling muku albashinku now leave my office.” Suna kuka suna had’asa da Allah amman ko a kwalan rigarsa tashin hankalin Fannah tabar masa aiki bame had’asa masa coffee ke damunsa nan ya dawo kan wayar.

         “Nace kun rufe business naku ne ko kuna running har yanzu?” Ya tambayi PA’n.
    “Muna running Sir komi munayi.”
    “Good” Anas yace, “kwanan nan kukayi hiring ma’aikata koh?”
    “Eh Sir just jiya muka musu sending letter ran monday zasu soma aiki.”
     “Ka bud’e kunnuwanka da kyau kajini. Inasan kaje kabi list d’in kayi firing FANNAH ALEEYU. kajini?”
   “Naji Sir yanzu zanje in samu secretary in masa magana in shaa Allah za’ayi firing natan. Amman mesa Sir?”
           “Wannan kuma ba damuwanka bane, inajiran feedback nanda like 10ninutes”
         “Okay Sir” nan Anas ya katse wayar. Bakinsa ya cize yana murmushin mugunta. Telephone na office nasa ne yasoma ringing nan ya d’aga.

       “Hello Boss an buga a press da jaridu gobe in shaa Allahu masu degree da masters harda PHD ma zasu soma applying batun coffeen”
     “Good banasan failure.”
    “In shaa Allah Boss.” Shide Ahmad mamaki yake har yanzu wai yaushe aka soma yin degree kan had’a banzan shayin da ake had’awa kan tebur akan layi safe rana dare, wani abu se Boss.
   Kai ya jingina jikin kujerar sa yana juyawa a hankali chan ya mik’e ya bud’e fridge tare da ciro barasar sa kusan rabi ya kurb’e ya koma d’aki ya baje ya kwanta ko problem nasa ze d’an tafi. Sanda ya kusan kai minti goma sannan yasamu yayi bacci abinda kullum daya sha befi minti uku bacci ya rufesa. Bacci me nauyi ne ya rufesa wayarsa dake kan table se ringing yake PA’n Manager’n FCB ltd ke kira. Two missed calls yamasa sannan ya hak’ura.

     Bayan minti ishirin da kwanciyar Anas, Kacallah ya taho yana knocking bakin k’ofa se sauri yake kwata kwata ya manta Anas nada board meeting da zeyi attending yau saboda yadda aiki ya masa yawa gashi in less than 10 minutes za’a fara. Knocking yake sosai Anas dake bacci ko kad’an baiji daga k’arshe shiga kawai yayi yana kiransa da “Boss” shiru kukeji. D’akin ya lek’a yaga Anas yayi ruf da ciki se bacci yake sha harda minshari necktie nasa yayi gefe guda takalmansa ma d’aya na kudu da’aya kuwa arewa. Ido ya zaro wuru wuru mekuma yasami Boss nasa yake bacci in the middle of the day.
      K’arisawa cikin d’akin yayi shi kansa tsoron tada Anas yake gudun kar ya rasa aikinsa dan kuwa yaga Hussaina da Zainab da akayi firing d’azu se kuka suke. A hankali ya tsuguna gaban fuskar Anas. “Boss!” ya fad’i murya na b’ari. “Boss!” Nan ma shiru dan haka yad’an jijjik’a sa ko kad’an Anas be motsa ba se bacci yakeyi. “Boss!” Kacallah ya kira sa sosai cikin kunnen sa nan ya yamutsa fuska. “Boss kayi hak’uri ka tashi akoi board meeting da za’ayi wanda yazama dole kaje you are needed please.”

     Cikin bacci yace, “dole? Se a sani inga. Barin je ba leave ko baka ga bacci nakeyi ba?” Pillow yaja ya rufe fuskarsa. Fuskar Kacallah kan wanda zeyi kuka “Boss kayi hak’uri ka tashi please you have to be there.”
     “Wake magana?” Anas ya tambayi Kacallah fuskarsa rufe da pillow dan yama kasa recognising muryar meshi.
   “Kacallah ne Boss, Kacallah ne.”
   “Kacallah kanason aikinka?” Anas ya tambayesa fuskarsa cikin pillown har yanzu.
    “Eh Boss inason aiki na sosai” ya fad’i yana giad’a kai.
    “To ka tashi kabani waje, fita min daga office in na sake jin muryaraka you’ll be fired.”
    “Fired?” Kacallah ya nanata a zuciyarsa. Meyayi zafi harda firing. Da sauri ya tashi ya bar d’akin hak’urin da yakeson badan ma yafasa dan ko Anas yace baisan sake jin muryar sa. Bayan ya isa office nasu na ma’aikata ya zauna kan table nasa tunanin wani k’arya ze had’ama wanda zasui meeting d’in yake chan ya d’au telephone ya kira assistant coordinator’n meeting d’in bayan ya gaishesa ya fara kamar haka;

        “Uhm Sir dan Allah kayi hak’uri for the inconvenience da aka samu.”
   “Wani incovinience kenan?” Mutumin ya tambaya.
      “Boss d’ina ne mahaifiyarsa ba tada lafiya, bareyi yasamu attending meeting d’inba, kuyi hak’uri please.”
     “Toh Allah sawak’e amman gaskia bareyi ace Flames Enterprises basu hallaci wannan meeting ba saboda  na board ne gabaki d’aya, ka turo d’aya daga cikin staffs naku ya ko ta wakilce sa.”
       “Yes Sir thank you so much.” Nan ya katse ya kira wata ma’aikaciya Suwaiba dake 6th floor yamata bayanin komi take ta shirya ta tafi zuwa meeting d’in. Nanne Kacallah yad’an samu peace of mind se addu’a yake Allah sa kar emergency ya taso dan besan ya zeyi ba Boss yace bayasan sake jin muryarsa.

          Bacci sosai Anas yasha kusan to 2:00PM ya tashi da k’yar yayi alwala yayi sallah yayi ordering  kawo masa abinci daga kitchen, a lokacin ya duba wayarsa yaga missed calls from PA. Nan ya kirasa, “hello Sir good afternoon.”
   Ba takan gaisuwar yake ba dan haka ko amsa sa beyi ba, “yes anyi firing natan?”
     “Unfortunately Sir wallahi secretary’n yace ba abinda tayi wai bareyi firing nata ba-”
   “What!??” Anas ya daka tsawa. “Bareyi firing nata ba? Waye shi?” Daidai lokacin knock yazo daga k’ofa ransa b’ace yace, “who is it?”
      Tana b’ari tace, “Boss Leemcy ce abincin ka na kawo”
      “Banaso, get the hell out of my office you are fired kije ki samu Adam.” Aguje ta koma k’asa tana kuka. “Kace meh? Bareyi firing nata ba? Kai masa wayan.” Bayan minti d’aya aka kaiwa secretary wayar.
   “Hello yace.”
   “Hellon k’aniya?” Anas ya tambayesa “kasan dawa kake magana?”
   “A’a seka fad’a” cewar secretary’n.
   “Nonsense you are speaking with ANAS IBRAHIM FAUZI.”
   “Sir! Ran ka ya dad’e kayi hak’uri dan Allah wallahi Kabir be sanar dani wane kai ba.”
    “Yanzu daka sani seka yi abinda ya kamata” amsar da Anas ya basa kenan.    “Yes ofcourse Sir yanzu zan tura mata message d’in.”
   “Good, inajiran feedback nanda 5minutes.” Karap yayi hanging call d’in.

     Nan da nan yasa akayi typing message na Fannah daidai lokacin za’a tura Manager’n wajen ya turo sak’o kan kar a d’iba kuma kar a sakar da masu aiki saboda wasu k’wararrun dalilu. Aiko ba halin korar Fannah. Nan ya kira Anas ya masa bayani.
    “What rubbish are you saying? Ku had’ani da manager’n naku.”
    “Sir wallahi kayi hak’uri nan da sati biyu ze dawo in ya dawo everything will go your way, sosai Boss yana mutunta ka duk abinda kakeso shi zai maka, ka k’ara hak’uri please ni da kaina zan sanar dakai duk sanda yayi landing.” Dan haushi bema amsa sa ba ya katse wayar. Zuciyarsa tafasa yake kamar ze k’one “mstchwww.” Ma akan Fannah da bata kai ta kawo ba yana ta tada hankalinsa inde coffee ne ai yasa job on sale daga gobe za’a fara applying, se meh dan Fannah tabar masa aiki, aikin banza. Tun lokacin tashi beyi ba ya tattara wayoyinsa ya sauk’a. Chan ma by mistake wata ma’aikaciya tasha gabansa saboda saurin da take tayi submitting wasu files take aka buga mata fire! Itama. A ranan Anas yayi firing mutane ba adadi kowa mamaki yake at thesame time being cautious kuma shima kar a koresa. Kacallah de ba halin yima Boss magana dukda there is so much to tell.

     Washegari ta kasance thursday ‘yan garin Maiduguri kap angani kuma an karanta a news cewa Flames Enterprises suna neman masu aikin had’a coffee. Zokuga yadda maza da mata suka taru bakin building na Anas yau. Da k’yar yasamu passage. 10-10 ake d’ibansu ake kaisu kitchen kowa da coffee machine dakuma ingredients na had’awa. First set suna gamawa Mr. Fauzi ya sauk’o tasting na wanda yafi masa dad’i seya samu aiki ya maye gurbin Fannah dan ko bacci ya kasa jiya se tunanin coffeen Fannah yake duk yadda yayi ya mance coffeen Fannah ya kasa, he is addicted to it dak’yar yasamu yayi bacci bayan syrup dayasha.

    Yana kai na farkon baki ya mayar cikin cup d’in “meh wannan? Ruwan wanki ko meh? take her out.”
    “Yes  Sir” cewar Adam. Nan na biyu ta matso itama yana kaiwa baki ya mayar cikin cup d’in “ke kinma san meya kawo ki nan kuwa? Take her out.”
  “Yes Sir.”
    Na uku ma takawo nata shima yana kaiwa baki ya miyar cikin cup d’in. “Take her out bana san sake ganin fuskarta.”

     Haka de bayin Allah suketa shigowa anayin round-round, na mutane 25 maza da mata Anas ya tab’a dukka ba wanda ya masa koda kusa da na Fannah ne.
      “Fire them all, duk ka koresu bana san sake ganinsu. Fire them now!” Yaja tsuka sannan ya shiga elevator’nsa ya haura zuwa office. A ranan yayi firing ma’aikantansa guda biyar plus na jiya abin de ba dad’in ji. Hankalin kowa tashe yake abu kad’an kayi a danna maka fire. Yau yini biyu kenan Anas be sha coffeen Fannah ba amman ji yake kamar shekaru aru aru ne. Yarasa ina ze sa kansa, abinci ma ba sosai yake ci ba koda ya gwada had’a coffeen baya masa dad’i bai ma iya sha gashi wannan karan ko Shettima ma be sanar dashi abinda ke damin sa ba kamar yadda ya hana Amal ma. Kawai in an tambayesa cewa yake rasuwar Baba (Mr. Muh’d) ya tuna.

      Yau k’imanin sati kenan da barin Fannah aiki gun Anas, k’imanin sati be d’and’ana coffeen ta me dad’i a bakinsa ba. Ba yadda beyi ba dan mancewa da coffeen nata amman yakasa shi daga baya nema yagano ba coffee natan kad’ai yake missing ba ita kanta Fannan ma missing nata yake, yes yayi missing Fannah, yayi missing innocent face nata, yayi missing kukanta dakuma muryarta me dad’in gaske, yayi missing kamilallen shirinta na kullum, komai yayi missing akan Fannah. Yabi ya k’osa next week ya iso ya kira Manager’n FCB ltd.

       Fannah kuwa rayuwarta ta juma batayi dad’i kamar yadda take ba yanzu, ba ruwanta da wani tashin hankali, aikinta tana yinsa me kyau ba ruwan asst. Manager’n ta da shiga harkar mutum bale ma ya mata masifa. Sosai take jin dad’i aiki wajen. Amal kuwa duk da erin warning da Anas ya mata ta kasa dena kiran Fannah saboda hankalinta. Wannan shine karo na farko da take sab’awa umurnin Anas.

 
  *© miemiebee*

No comments:

Post a Comment