Saturday, 3 September 2016

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 29
BY MIEMIEBEE


 
  “Kasan Fannah Aleeyu ko wacce ta tab’a aiki anan?”
    “Wacce take had’a maka coffee Boss?”
   “Yes ita.” ya amsa sa a takaice.
   “Sosai nagane ta friend na Yusuf ce.”
    “Toh ban tambayeka ba.” Ya tsawata masa.
    “I’m sorry” Boss ya sunkuyar da kansa.
    “You better be, bawani aiki zan baka ba illa spying akan Fannah dana keson kana min, inasan yazamo duk inda zataje dakuma duk abinda take ciki ka sani kana turo min rahoto.”
    “Okay Boss nagane.”
      “Good, karka bari ko da information d’aya ne ya wuce ka, do you get me?”
    “Yes sir.”
   “Good inka min wannan zan baka mak’udan kud’ad’e. Off you go, ga number’nta” nan ya mik’a masa rubucaccen number’n Fannah kan wata paper. “Ka kirata yanzu seka samu kayi tracing inda take.”
     “Yes Sir” nan ya fice.

   _30 minutes later..._
   
     “Hello Boss yanzu Fannah tabar state secreterial.”
    “Good ka shiga ka tambaya min ko aiki suka bata”
      “okay sir.” Nan ya katse wayar ya shiga. Tambayoyi yariga ma receptionist na wajen itako jaka ta riga basa information saboda tagansa kyakkyawa ba laifi, dama da biyu Anas yayi assigining Idrees yin aikin. “Kina nufin har kunbawa Fannah aikin kenan?” Idrees ya tambayeta.
    “Eh Idrees mun bata saboda takardun ta sunada kyau.” Ta fad’a ta na kashe masa ido
    “Okay inasan number’n Manager’n ku if possible.”
   “Sure Idrees” nan ta basa dan sokanci godiya ya mata sannan ya fice “se na kira ki koh?”
   “Okay!” tace masa tana nin dad’i. Aiko yana fita yayi blocking number’nta bata sake ganinsa ba tun daga ranan.

     Anas ya kira “hello Boss nayi tambaya wai eh tasamu aiki a ma’aikatan amman na amso maka number’n boss d’in sekuyi magana.”
     “Excellent! Ka iya aiki” yayi exclaiming “turo min lambar and kacigaba da binta aikinka na kyau.” Bayan minti d’aya Idrees ya masa sendn number’n Manager’n wajen. Da telephone office nasa ya kira Manger’n. Manager’n na ganin Flames Enterprises ya d’aga jiki na rawa.
   “Ranka ya dad’e Mr. Fauzi ina gaisuwa.”
   “Yawwa barka” straight to the point ya wuce “Fannah Aleeyu da kuka bawa aiki yanzu nakeson kuyi firing nata.”
     “Amman Si-”
    Katse sa Anas yayi “zan baka dubu d’ari biyar.”
       “Toh anyi an gama Sir bari in ta dawo gobe ina jiran alert.”
    “Karka damu just do as I say ina jiran feedback.”

       Idrees be bar bibiyar Fannah ba sanda yaga tashiga gida sannan ya kira Anas ya fad’a masa.
     Fannah ta shiga cikin gida da farin ciki fal a ranta ta sanar da family’nta aikin da ta samu sosai suka tayata murna. Washegari ta koma ma’aikatan suka tareta da sad news na fasa bata aikin da sukayi. Zuciyarta taji ya kariya. “Dan Allah kode wani abun nayi kuka hana ni aikin kuyi hak’uri, ina buk’atar aikin nan. Kefa jiya kika kai wa Manager’nku takardu na yakuma yaba, yau kuma kice kun fasa?”

    “Eh an fasa seki k’ara mai please.” Abin tausayi Fannah taja jakarta ta fice wani ma’aikatan ta wuce neman aiki take suma suka bata aiki. Bayan tafiyarta aka koma gidan jiya Idrees yabi sahu yau ma mace yasamu as receptionist d’in ya tsarata yasamu ya ta fad’a masa news dayakeso tare da basa number’n Manager’n.
     Shima kud’i da dama Anas yabasa ya yarda yayi firing Fannah.

    Duk aikin da Fannah ta samu da ta koma washegari se suce sun fasa sun canza mind nasu, sosai abin yake daminta ranan harda kuka. A inda tasamu aiki a k’arshen ne bayan tafiyanta Idrees ya shiga to his suprise yaga wani santalelen gardi as receptionist d’in yasan koda mutuwa zeyi ba basa information da yakeso ze masa ba. Fita kawai yayi ya kira Anas nan ya masa kwatancen ma’aikatan. Meeting Anas yakeda amman yayi cancelling in akan Fannah da coffeen ta ne baya wasa.

    Bayan like 15 minutes Anas ya iso wajen tare suka shigo cikin building d’in atare wajen receptionist d’in suka nufa. Bayan ya gaishesu Anas yace, “take me to your Manager.”
    “Sir I'm sorry amman se in kanada appointment dashi tukuna, me sunanka in duba.”
    “Tambaya ma kake waye shi? Bakasan Mr. Fauzi bane?” Cewar Idrees dake tsaye bayan Anas.
   “I’m sorry Mr. Fauzi amman bakada appointment dashi.”
    “You’re very stupid and zan tabbata an koreka daga aiki anan stupid kawai” Chan ya hango wani na wucewa “hey!” Ya danna masa kira jiki na rawa mutumin ya iso “ranka ya dad’e, sannu da zuwa yau manyan bak’i mukeda a office namu? Kai D’anladi bakasan mutane bane? Ai Mr. Fauzi ba’a had’a masa appointment. Koda yaushe yazo he is welcomed”


    “Ahto gaya masa de” cewar Idrees.

    Kallo Anas ya watsa ma D’anladin sannan ya dawo da kallonsa kan Isah “so nake ayi firing wannan mutumin.” ya nuna D’anladi da yatsa.
    Hak’uri Isah ya soma bawa Anas. “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri shekaran jiya ya shigo gari, be sanka bane, kai D’anladi baraka basa hak’uri bane?” Ya daka wa D’anladi tsawa.
   “Kayi hak’uri Sir.” Kallon sa Anas yake cike da rashin isa “sede D’anladin kam. Uhm Isah Mr. Abdullahi na nan kuwa?”
    “Eh Manager na nan mu haura sama please.” Nan sukayi sama kamar yadda Anas ya saba siye mutane da kud’i haka ya siye Mr. Abdullahi. A dad’insa yanzu kap inda Fannah zata samu aiki yayi blocking batada wata option other than ta masa aiki.

  ****
   Kuka Fannah take sosai Mami na bata hak’uri. “Haba! Fannah sekace ba muslima ba? Ke da nasanki da rungumar k’addara kiyi shiru kukan ya isa.”
    “Haba Mami abin ba daidai ba, ace duk inda naje se bayan sun d’aukeni in nakoma washegary kuma suce sun fasa.”
    “Ya isa Fannah akoi Allah ki dad’a hak’uri.”
     “Kiyi hak’uri Ya Fannah” cewar Afrah tana bubbuga bayanta a hankali cike da tausayi da damuwa.

    Fannah bata sake lek’a waje ba tun daga ranan. Sosai rashin aikinta yake damunta in kud’in hannunta ya k’are bata san ina zata samu kud’i tabiya kud’in asibiti da magunan Baba ba. Tasan sarai inda a yanzu zata je wajen Anas ze bata aiki amman barata iya jure wulak’ancin sa ba, mutum ne ace ko kad’an baida slightest regard wa d’an adam. Ita dashi har abada in shaa Allah ta gommaci talauci ya kashe ta data sake masa aiki.
 
     _One week later..._

    Haukacewa ne kawai Anas beyi ba yarasa me ke ajiye Fannah har yanzu batazo neman aiki gunsa ba. Gashi koya tura Idrees ce masa yake Fannah bata fita, toh why? Ta hak’ura da neman aiki kenan komeh? Bare iya explaining ya yayi missing coffeen ta ba tun rananda tabar masa aiki har ila yau baicin abinci kamar yadda ya saba ci da. Shi yanzu abu d’aya ne yasan inya aiwatar dolen Fannah zata dawo masa aiki shine in zeje gidansu, gashi dama Idrees yamasa bayanin yadda gidansu Fannah yake basuda arziki. Wayarsa ya d’auko ya kira Ahmad. “Hello Boss good day.”
   “Yawwa kaje ka d’au credit card d’ina cikin mota a bud’e ne kayi duk siyayyan dakasan magidanci zeyi wa family’nsa I mean food items, kayan sawa home appliances komi da komi ka gane?”
    “Yes Boss angama.” Nan ya katse wayarsa. “In baraki dawo ba Fannah I will force you to.”

    _5 hours later..._

    Anas na zaune a office nasa yana jiran call daga Ahmad baya son se Maghrib yayi, aikuwa a lokacin Ahmad ya kirasa “Hello Boss komai is in place kamar yadda ka buk’ata motan kayan na nan pake a bakin main gate.”
     “Good gani fitowa.” Turare ya sake feshe jikinsa dashi ya giara gashin kansa ya tabbata he is looking okay sannan ya fice. Motarsa ya shiga motan kayan kuwa Ahmad ne ciki yana gaba Anas na biye dashi har gaban gidansu Fannah suka tsaya. Sosai yasha mamaki ashe saisa Fannah batta wasa da aikinta ashe basu da k’arfi ne sosai. Kallon gidan ya tsaya yi dan ko a Bama gidansu yafi wannan kyau.

    Daidai lokacin Aiman ta taso daga islamiya se b’antare charbin Malam dake hannunta take tana nufowa kusa da gidan alokacin data d’aga fuskarta Anas yaga alaman kamannin Fannah tattare da ita nan take ya yanke hukuncin kasancewar ‘yar yarinyar k’anwar Fannah. Daidai tazo shiga gidan ya dakatar da ita ta hanyan kiran ta da “‘yan mata.” A hankali ta d’ago kai tana kallonsa bata gane kamanninsa ba kasancewar yasa sunglasses.
   “Wace ‘yanmatan” ta kalli left and right “ni? Barin d’an maka tambaya bature ne kai please naga kayi fari dayawa”
   Dariya sosai Anas ya tsaya yi sekace ba shi ba, kawai se yarinyan ta tuna masa da Angel nasa Amal.
   “ A’a ni ba bature bane ‘yanmata”
   “ Nifa kadena cemin ‘yanmata, ai Ya Fannah tace ni yarinya ce ba ‘yan mata ba wai ita da Ya Afrah ne ‘yan mata.”
    “Toh Ya Fannah ta miki k’arya ai ‘yan mata ce ke.”
   “Toh kaikuma fa? Samari?” Ta tambayesa tana jefa charbin malam data b’are a baki tare da taunawa.
    “Ni big uncle ne suna na Anas, kinacemin Ya Anas.”
   “Ya Anas.. Ya Anas ni Aiman a ina na tab’a jin wannan suna?” Ta tsaya tana tambayar kanta.
   Yana ciro glasses nasa aiko kamanninsa ya bayyana.
  “Laaaaa!!! Blue eyes na TV. Me kazo yi agidan mu? Ashe ba bature ne kai ba, kazo ne muma asamu a TV’n?”
   Dariya sosai yake wanda ya mugun masa kyau, fararen hak’waransa suka bayyana, dimple nasa d’aya ya lotse. “Kinasan kiga kanki a TV?”
  “Eh mana ai social studies teacher’n mu tace celebrities kawai ake gani a TV nima inasan in zama d’aya.”
   “Toh kar ki damu, yanzu kizo ki kaini cikin gidanku.”
“A'a'a'ahhhh chabdi! Ai Ya Fannah ta hana. Maza basu shiga gidanmu gaskia me blue eyes kayi hak’uri karka sace min iyaye da yayu. You are a stranger.”

   “Kefa kikace kina gani na a TV karki damu b abinda zan miki. Ahmad ina sweet d’incan?” nan Ahmad ya koma mota ya ciro packet na sweet Anas ya amshi, “ungo zo ki karb’a.” Ya fad’i yana mik’a mata.
    “Blue eyes tsakanin ka da Allah baka sa abin sace yara ciki ba?” dariya sosai Ahmad yake.
   “Kice min Ya Anas ba blue eyes ba.”
    “Toh Ya Anas.” Ta fad’a yawunta na d’iga k’asa.

      “Bari kiga” nan ya bud’e ya ciro d’aya tare da sha “kinga ba abinda yamin. Zoki karb’a se ki kaini gidanku. Ya Fannah tasanni, nine Mr. Fauzi. ”
    “Ohhh ashe kaine me sa Ya Fannah kuka.” Yi yayi kamar be jita ba yace, “karb’a mu shiga toh.” Ba musu ta amshi pack na sweet d’in “muje toh Ya Anas.” Bayan ta yabi suka shiga gidan kam ba laifi tsatsaf ba k’azanta.
    “Mami! Ya Fannah! Ya Afrah! kufito munyi bak’o kuma ya bani sweet har packet.” Fannah ce ta soma fitowa ko hijabi batada ‘yar vest ne kawai jikinta tana shan iska.

      “Aiman ban hanaki shig-” bata k’are maganar ba suka had’a ido hud’u da Anas ai a guje ta koma ciki se nishi take. K’wak’walwar Anas sanda yabar functioning na d’an lokaci ganin Fannah ba kayan arziki. “Ke Ya Fannah wa kika gani haka kike wannan nishi” cewar Afrah dake game as always. Kasa magana Fannah tayi kawai waje take nuna mata da hannu. “Meh gamo kikayi?” Kai ta kad’a mata still tana nuna waje. Kafin Afrah ta tashi suka jiyo muryan Mami na masa lale su Mami anga Mr. Fauzi. Lek’awa Afrah tayi tagansa zaune kan tabarma d’aya da Mami.

    Ashe haka bawan Allan keda kyau, yama fi kyau a fili akan a gidan TV lallai Allah yayi hallita. “Ya Fannah Mr. Fauzi nefa! Mr. Fauzi a gidanmu!” ai da gudu tayi wajen sa kayansu taciro kayan sallarta. “Ki sa hijabi mu fita mu gaishe sa. Ma meyazo yi tukun? Halan bikonki” Duk ta kidime se suratai take tayi.
      Hannunta Fannah ta rik’o “ke jakar ina ce? Ina zaki? Meh Mr. Fauzi yazo yi gidan mu? Nashiga uku Allah sa ba sharri ya taho dashi ba.” Afrah ta bud’e baki zatayi magana suka jiyo kiran Mami “Fannah! Afrah! kufito mana Mr. Fauzi nefa yazo.”
    “A’a Mami Anas de” cewar Anas sewani behaving yake kamar d’an arziki. “Kufito da sauri” Mami ta sake k’olla masu kira. “Toh” Afrah tace. “Ya Fannah kiyi sauri.”
  “O’o ni barin fita ba ni yama yasan gidanmu? Ya Allah help me!” Hannunta Afrah ta fisga daga rik’on Fannah ta fice a guje har k’asa ta gaishe da Anas ya amsa da fara’a se murmushin show off yake. “Aiman kawo wa Ya Anas ruwa kinji?”
   “A’a Mami ta bari daga office nake yanzu naci abinci.”
   “Allah Babana ko ruwa bara ka sha ba?”
   “Eh Mami, ina Baba? Ya jikin nasa?” Fannah dake mak’ale jikin window tana jinsa ji take kamar taje ta shak’uresa ji yadda yake abu kamar d’an arziki.
   “Jikin Baba da sauki. Afrah ina Fannah newai? Fannah!” Ta danna mata kira.
     “Na’am Mami” ta amsa kan wanda zatayi kuka. “Kifito mana me kikeyi ne?”
    “Mami gani nan.” Hijabi ta zumbura sewani kumbure kumbure take.
   Koda ta fito bata d’aga kai ta kalli Anas ba shikuwa idanunsa na kan ta rabuwansa daya sata a ido har ya manta.

    “Baki ga Mr. Fauzi bane da baraki gaishe sa ba?” yi tayi kamar bata ji me Mami tace ba.

*© miemiebee*



No comments: