BY MIEMIEBEE
Da yammacin ranar Juma’a bayan Anas ya dawo daga office yayi firing mutane 6 shida ranan. Kwance yake kan gado a d’akinsa ya zura wa ceiling ido yayi zurfi cikin tunani. Har Shettima yayi sallama ya shigo beyi noticing ba. D’an tab’a sa yayi a hannu firgit ya dawo daga duniyar tunanin daya fad’a. “Ya Anas yaukuma tunanin me kake haka? Na Ummimi kokuma na yarinyan?” ya tambayesa yana k’ok’arin zama kusa dashi.
“Ko d’aya” ya amsa sa alokacin dayake k’ok’arin zama.
“Then mene? Kasan ban maka magana bane amman Yusuf yabani labarin abinda kake tayi a Enterprise naka, me yayi zafi ace cikin sati kayi firing mutane 31 haba Ya Anas.”
“Oh haka shi Yusuf nakan yace? Allah kaimu monday shima ya jira nasa.”
“Ya Anas wai me haka, friend nawan zaka kora? Wace kuma Fannah?” Cike da mamaki Anas ya kewayo da blue eyes nasa kan Shettima. “A ina kuma kaji wannan batu? Still gun Yusuf?”
“It doesn matter Ya Anas saboda ita kake firing ma’aikatan ka kana kashe Enterprise naka da kanka, ajinka yanzu in za’a dawo da Baba zeyi appreciating abinda kakeyi ne?”
“Toh yimin lectures Shettima, please ni banasan maganan nan excuse me.”
“Saboda yarinyan ne Ya Anas, kanasan ta dawo maka aiki ne? Do you miss her?”
A fusace yace, “Yes Shettima I do, I miss her.”
“Toh mesa kake treating nata badly lokacin da take nan? Kaifa kasa tayi resigning tabar maka aiki.”
“Shettima ni ba abinda yake damuna ba kenan, abinda yake damuna shine tadawo.”
“Toh ta yaya?”
“Ta duk yadda nasan zan iya.”
Shiru Shettima yayi yana nazarin wani abu. “What are you thinking of?” Anas ya tambayesa. “Ya Anas kode san ta kake? Yaushe ka fara damuwa da rashin mutum a kusa da kai?”
“San ta? Are you kidding me Shettima? Me zan so a jikinta? Ni kawai I miss her saboda coffeen da take making min.” Yama Shettima k’arya dan shi kansa yanzu yasan ba coffeen Fannah kad’ai yake missing ba no matter how yayi denying Fannah ta daban ce, kayan duniya be dame ta ba, kyansa dayasa mata suke binsa ma be dameta ba yaci ace Fannah ta kamu da ciwon sansa amman ko kad’an beyi noticing hakan ba a tattare da ita.
“Amman da akoi abin duba anan mata nawa wanda suka fi Fannah komai suke fad’in suna sanka baka tab’a saurara musu ba hasali ma koda sun shigo rayuwarka k’ok’arin koransu kake amman when it comes to Fannah, ita ta tafi da kanta but kanasan dawo da ita. Ya Anas ina yarinyan dakace *_TANA TARE DA KAI?_* Ko hala itace Fannan.”
“Non sense. Wani erin jagual guale kake fad’i Shettima? That girl can’t be Fannah in da ace itace da nayi recognising nata. Ka manta lokacin da abinda ya faru a buge kake?”
“Toh ita fah? Ai in ni a buge nake ita ba’a buge take ba, da itace da ta gane ni.”
“Not really” Shettima ya fad’a yana kad’a kai.
“Noo Shettima wancan yarinyan ba Fannah bace kadena had’ani da Fannah please ni ba wai santa nake ba, batta,da abinda zan gani har ince inaso duk mata ma ba wacce take dashi illa yarinyar dake *_TARE DA NI._* so please kabar had’ani da Fannah, coffeen ta nakeso ba itaba.” Shettima ze sake magana Anas ya katse sa “maganan Fannan kuma ya isa please. Zan kwanta excuse me” kallonsa kawai Shettima yayi ya kad’a kai sannan ya fice.
“Mesa Shettima zece inasan Fannah? Mesa yake tunanin itace yarinyar da nake nema har yau, eh nasani yarinyar *_TANA TARE DA NI_* amman ba itace Fannah ba, banasan Fannah barin tab’a santa ba coffeen ta kawai nakeso. Coffeen ma daga yau zan dena missing saboda in manta da ita a rayuwa na forever”
Washegari ya kasance Asabar ko tashi daga kan gado Anas beyi ba ya fara tuna Asabar daya kira Fannah zuwa gidansa had’a masa coffee, k’irjinta daya gani tun ranan har yau yakasa deleting image d’in daga k’wak’walwar sa. Kai ya kad’a dan ya gusar da tunanin nan ya mik’e ya shiga bathroom ya kunna shower yabar ruwan na sauk’a kansa. Duk yadda yayi ya mance Fannah ya kasa, yarasa dalili is not as if yasan how it feels to be in love.
_One week 2 days later..._
A shekaran jiya Manager’n FCB ltd ya dawo tun a ranan secretary’n yama Anas sending number’n Boss nasa as promised sede abin mamaki har yau Sunday Anas be kira manager’n ba. Kwance yake a d’akinsa da wayarsa a hannunsa ya zura wa lambar Manager’n ido yakasa kira. Anas ya koma wani abu daban. Sati biyu ne tun rabuwarsa da Fannah amman seji yake kamar irin shekara da shekaru. Abin nasa se worse yake dukda maganar da Shettima yamasa amman ina. A yanzu haka yayi firing about 60 something staffs nasa kullum cikin kawo sabi ake, hankalin kowa ya tashi a office sede ba kamar yadda na Anas ya tashi ba. Mutuwa ne kawai beyi ba dan hana kansa tunanin Fannah da coffeen ta. Yanzu haka ma ga number’n Manager’n amman ya kasa kira dan girman kai.
Seda yammacin ranan ya danna wa manager’n kira, he can’t take it anymore. Manager be d’aga ba a karo na farko se ana biyu nan ma sanda ya kusa tsinkewa.
“Hello” Manager’n yace bayan ya d’aga.
“Mr. Azeez, Anas Fauzi ne.”
“Ohh our youngest billonaire! Kwana dayawa.”
“Alhamdulillah tun last 2 weeks nake neman ka akacemin ka tafi trip hungary, I had to wait ka dawo.”
“Taya Kabeer ze maka haka? Besan ko waye kai bane? Ai be fad’a min ba I’m sorry.”
“Ba komai ya wuce dama aiki nakeson baka.”
“Toh billonaire inaji...”
“About last 2-3 weeks kukayi employing ma’aikata koh?”
“Eh suna nan ma munajin dad’in aiki dasu musamman wata Fannah something yarinyan akoi hardwork ina tunanin k’ara mata matsayi ma.”
D’an murmushi Anas yayi “ita nakeso kayi firing Mr. Azeez.”
Ido wuru wuru ya zaro “inyi firing nata kuma billonaire? Mesa?”
“Saboda ni nace.”
“Toh nawa kuma zaka bani wannan karan?”
Murmushi yasaki kad’an again. “Miliyin d’aya yayi?”
Mr. Azeez lips nasa ya tand’e tas “amman barin samu k’ari ba?” saboda yasan irin kud’ad’en da Anas yakeda.
“Inde zakayi firing nata zan k’ara maka 1.5 yayi?”
“Wow! consider it done Mr. Fauzi saisa nakeson aiki da kai wallahi. Gobe gobe za’ayi kamar yadda kakeso.”
“Good” Anas yace yana me jin dad’i “amman kasan be kamata kayi firing nata haka kawai ba zan turo maka 50k akai se ka bata please make sure ka bata, banaso na bata kud’i dayawa tak’i dawowa wajen aiki”
“Karka damu Mr. Fauzi zan san yadda zan b’ullo mata da lamarin ta yadda barata fahimci you have something to do with this ba.”
“Good nagode.”
“Ai ba godiya tsakanin wa da k’ani. Take care” ahaka sukayi sallama.
Sosai Anas yaji dad’i dan dolen Fannah ta dawo masa aiki yanzu kuma wannan karan ma better job ze bata yadda bara ta sake tunanin tafiya ba, yasamu yasha coffee iya san ransa. Aiki kamar Personal Assistance nasa tunda dama baida shi. Jira kawai yake gobe ko jibi yayi Fannah ta dawo masa aiki.
****
Fannah na zaune d’aki ita da Afrah se hira sukeyi cike da nishad’i. Har wani fresh Fannah ta k’ara dan yadda batta da wani matsala yanzu. Wayarta ce ta soma ruri nan da nan ta duba ganin Yusuf ke kira yasa ta d’aga da wuri. “Assalamu alaikum Yusuf”
“Wa’alakissalam Fannah ya kike? Ya aiki?”
“Lafiya qalou, aiki alhamdulillah, naka fah?”
“Fannah wallahi wajen aiki ya zamo kamar hell.”
“Mesa kace haka Yusuf?” Ta tambaya cike da rashin fahimta.
“Wallahi Boss ne Fannah, Boss yazama wani abu daban tun tafiyar ki, da barin ki office d’in wallahi yayi firing mutane sittin da abu ka.”
“What! Allah shirya!” Fannah tayi exclaming cike da mamaki. “Sittin da abu? Dalili?”
“Saboda ke mana Fannah, wallahi Boss yayi missing naki frustration na rasa ki yasa yake duk abinda yakeyi.”
“A’a kam bade ni ba, nikuma me had’ina da Mr. Fauzi? Ai Allah ya riga ya rabani dashi har abada in shaa Allah.”
“Fannah ki tausaya mana ki dawo please, wallahi kina dawowa komi ze dawo normal.”
“Yusuf!” Ta kira sunansa cike da mamaki “nima ka tausaya min mana, ashe de baka sona kafi kowa sanin abinda Mr. Fauzi yakemin ni barin aiki dashi shine mafi alkhairi a gareni kukuma Allah k’ara maku hak’uri amman inde dan in dawo aiki k’ark’ashin wancan mugun mutumin ne ka kirani I’m sorry I can’t.” Karap ta katse wayarta.
“Wani mara imanin ne Ya Fannah?” Afrah dake game a wayarta ta tambayeta.
“Yusuf ne wai in dawo aiki a Flames Enterprises...” nan de ta labarce mata komi.
“Ayya amman sun ban tausayi gaskia shege Mr. Fauzi an gasu!” ta fad'a tana dariya. Dariyan itama Fannah takeyi “ai ya gasu ya k’one Allah ya riga ya rabani dashi har abada!”
_Washegary..._
As usual k’arfe takwas dadai ya cika wa Fannah a office kap co workers nata suna santa dan hali irin nata me kyau. Chan around 10:30AM tana zaune tana faxing wasu papers aka danna mata kira daga Manager’s office zuciyarta fal taje sam basu tab’a samin matsala dashi ba tun dawowarsa ita ta d’au ma batun promotion dayace ze mata ne. Bayan ta shiga office nasan ta gaishesa cike da girmamawa kamar yadda ta saba da fara’a ya amsata sannan ya nuna mata kujera ta zauna. “Fannah Aleeyu kamar yadda kika sani kina d’aya daga cikin hard working employees d’ina ko kad’an bansan rasaki amman in yazama dole kinga ba yadda na iya.”
Murmushin dake fuskarta ne ya gushe a hankali. “Bangane ba Mr. Azeez.”
“Fannah babban matsala na samu da wannan organisation namu wanda yazama dole in rage ma’aikatan da aka d’iba last 3 weeks wanda nakeso da alkhairi kenan wanda kuma ba haka ba, zasu cigaba da aiki nan amman ba albashi. Inasan ki da alkhairi Fannah sesa zan fara sallamar ki and already na riga na samo miki aiki ma me kyan gaske.”
“Allah sarki Mr. Azeez ni ko ba albashin ‘yan watanni zan maka aiki karka damu, inasan aiki anan sosai.”
“A’a Fannah” I insist please. “Ga wannan” nan yaciro envelope “dubu hamsin ne ciki albashinki na wata gabad’aya.”
“Mr. Azeez ai banyi aikin wata ba kayi deducting please seka samu ka biya wasu dashi..”
“Ni na baki Fannah ki rik’e karki damu”
“Toh nagode sosai Allah saka da alkhairi, matsalar da organisation naka yasamu kuma Allah takaita.”
“Ameen” yace yana mata murmushi
“Toh Mr. Azeez ina ne inda kace ka sama min aikin?”
“Ba ko ina bane se Flames Enterprises.” Take taji zuciyarta ta buga ai ba Flames Enterprises ba sunan chan wajen, hell shi yakamata ana kiran wajen da.
“Lafiya Miss Aleeyu?” ya tambayeta.
A kid’ime tace, “a’a, a’a nagode Mr. Azeez gobe in shaa Allah zanje nagode.”
“You’re welcome, yawwa please karki sanar da wani ko wata maganar da mukayi dake kar su gudu in rasa ma’aikata.”
“In shaa Allah na gode da erin karamcin da ka min Allah saka.” Da “Ameen” daya amsata ta fice. Jakarta ta d’auka tama sauran ‘yan uwan nata k’arya kan zata gida.
Bayan ta isa gida ta tarar da duka family member’nta banda Aiman dake school zaune suna hira harda Baba dad’i taji sosai Babanta na samun sauk’i. “Fannah ya haka yau?” Tambayar Mami.
Murmushi ta musu duka “wallahi matsala aka samu da ma’aikatanmu...” nan de ta zayyana masu komi. Ba wanda yaji dad’i cikinsu saboda sun san wahalar neman aiki.
“Karki damu ‘yata zamu taya ki da addu’a in shaa Allahu nan da lokaci kad’an zaki sake samun wani aikin.” Baba ya tabbatar mata yana me mata murmushi.
“Gaskiyan Babanku ne Fannah karki damu akoi Allah.”
“In shaa Allah Mami gashi kuwa ya biyani albashi na na wata kinga zamu samu mud’an yi siyayya. Afrah zo mu shiga daga ciki.” Shigarsu ciki Fannah tabata labarin aikin da Mr. Kabeer ya nemo mata a Flames Enterprises.
K’irji ta dafe tare da zaro ido. “Kin gudu baki tsira ba Ya Fannah ya zakiyi yanzu?”
“Nikuwa na gudu na tsira Afrah banga abinda ze sake sani ma Mr. Fauzi aiki ba. Chab! Aiko Mr. Azeez yazo ya kirani nan gaba ce masa kawai zan nasamu wani aikin daban.”
Shiru Afrah tayi tana nazarin abu. “Tunanin me kike haka?” Fannah ta tambayeta tare da d’an bugin ta a hannu. “Something smells fishy anan.” Afrah tace tana tunani.
“Meh kenan?” Fannah ta tambayeta a takaice.
“Mesa Mr. Azeez ze tura ki Flames Enterprises kinsan me nake gani? Gani nake kamar Mr. Fauzi nada hannu cikin wannan abu.” Shiru itama Fannah tayi tana nazarin abinda Afrah tace. Chan ta murmusa “ko kad’an Afrah kin manta Yusuf yace kullum cikin koran ma’aikata yake ai kinga kuwa dole yana neman masu aiki safe da dare and ko ba dan haka bama I trust Mr. Azeez”
Kai Afrah ta giad’a nufin ta gane. “Kinyi gaskia kuma fa mude fatan mu Allah baki wani aikin ba sekin wahala.”
“Ameen Afrah gobe zan shiga nema in shaa Allah.”
*****
Tun k’arfe 9:00AM Fannah tabar gida bayan addu’o’in da su Mami suka ta suburbud’a mata. Mr. Fauzi kuwa yau office nasan ma yak’i shiga yana tsaye bakin k’ofa shi a dole yana jiran isowar Fannah dan tun daren jiya da Mr. Kabeer ya fad’a masa yayi firing nata yakasa hak’ura se Allah Allah yake gobe yayi. Mamaki ne ya cika kowa a building d’in wai yau Mr. Fauzi ke tsaye bakin k’ofa ko wa yake jira se Allah! Ganin har 11:00AM ba alaman Fannah ya dawo ciki da disappointment karara a fuskarsa. Bade ta samu wani aikin ba? In bahaka ba me ze hanata zuwa? Ai sosai Fannah bata wasa da aiki, what could be the problem? Wayarsa ya d’au ya kira Idrees bayan kamar minti biyu Idrees ya iso bayan gaisuwa yace, “yes Boss you called for me.” Giaran murya Anas yayi “aiki nakeson saka and banasan failure, kanajina?”
“Inaji Boss fad’a min duk abinda kakeso ayi maka.”
*© miemiebee*
No comments:
Post a Comment