Saturday, 3 September 2016

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 46
BY MIEMIEBEE

    Wajen elevator’nsa ya jata bayan sun shiga tace, “Mr. Fauzi where are you taking me to?” Be amsata ba illa wayansa da ya ciro daga aljihunsa yayi waya wanda ga dukkan alamu da polisawa ne. Bayan ya gama Fannah ta maraice “Mr. Fauzi not again please, kayi hak’uri dan Allah.” Beko saurare ta ba. Bayan da elevator’n ya bud’u yaja hannunta daidai gaban motarsa ya tsaya tare da bud’e k’ofar gaba wa Fannah. “Enter” yace ba tare da ya kalleta ba. Dakewa tayi “barin shiga ba Sir, kabari mana dan Allah duk abinda ka masa yanzu nasan Ya Farouq he will fight back, fad’an ya cigaba kenan kuma.”
     “Get in the damn car!!” ya fad’a a tsawace. Ta tsorta iya tsoro amman kuma tak’i shiga.
   “Miss Aleeyu I said get in, karki bari raina ya b’aci in d’aga ki in saki ciki da kaina.”
   “Sir promise me ba wajen Ya Farouq zamuje ba.” Kai ya giad’a.
    “Promise?” Ta tambayesa. “Yes” ya bata amsa nan ne tashiga bayan ya rufo k’ofar ya zaga ta driver’s side yashiga shima. This is the first time yake driving nasu bibbiyu. Ganin hanyan gidansu yake nufa tace, “Sir you promised kace ba wajen Ya Farouq zamuje ba dan Allah ka juya.” Banza da ita yaui sanda suka isa gidan yayi parking tare da fitowa a fusace ya zaga ya fito da Fannah hannunta rik’e cikin nasa tayi tayi ta k’wace amman ta kasa. Ai kaman an turo Farouq se gashi ya yanko corner’n gidan hankalinsa kwance yana tafiya idanunsa suna sauk’a kan Anas yaga yadda yawani rik’e hannun Fannah. Ita kuwa ganin Farouq ta cigaba da k’ok’arin k’watan hannunta daga na Anas amman ta kasa. “Stop it” yayi warning nata. “Sir please ka sakeni kafin ya k’ariso.” Nan da nan Farouq ya iso gabansu se nishi yake kaman zaki dan wani bak’in kishin daya rufesa.

       Hannun nasu ya sake kalla sannan ya kalli Fannah, kanta ta sunkuyar tare da lab’ewa bayan Anas a hankali tace, “Ya Farouq I can explain this dan Allah kayi hak’uri, Mr. Fauzi please ka sakemin hannu.”
     “Bakaji me tace bane?” Ka sake mata hannu.
    “Banji ba” Anas yace kamar kyaftawan ido ya sake hannun Fannah tare da cikumo kolar rigan Farouq punches guda uku lafiyayyu yakai masa har k’asa Farouq ya sauka se zuban jini fuskarsa yake. Binsa k’asan Anas yayi tare da tsugunawa a kansa da k’afafunsa side-by-side na Farouq. Nan ma be bar kai masa bugin ba. Fannah dake basa hak’uri har bakinta yayi dogo “Mr. Fauzi please ya isa.” Se huci yake yana dukansa ba makawa. Hannun Mr. Fauzi ta gwada rik’ewa ya k’wata abinsa da zafi sauran kad’an ta fad’i k’asa. Ganin an kusan sumar da Farouq Fannah ta ruga a guje tare da hugging Anas ta baya cije da tashin hankali, abinda kad’ai yazo mata kai kenan duk da tasan yin hakan haramun ne, in bahakan tayi ba tana ganin Anas ze iya kashe Farouq da yadda yake ta kai masa bugi. Hannu ya d’aga ze sake kaiwa Farouq punch yaji jikin Fannah a nasa, wani irin electrification ya jiyo a jikinsa tun daga tsakiyar kansa har k’afa, wanda be tab’a ji ba tunda yasan kansa. Hawaye take sosai wanda har kad’an daga ciki ya tab’a rigarsa “Mr. Fauzi please ya isa dan Allah kayi hak’uri in ka cigaba zaka kashe sa ya isa dan Allah, please...” Se kuka.

     Ganin jikinsa ya mutu ta matsa baya tana share hawayenta mik’ewa yayi ya nufa wajenta “is okay kukan ya isa kinji?”
     Numfashi take ja dan yadda tasha kuka “please ya isa Sir karka sake tab’a masa.” Kai ya gyad’a mata “stop crying.” Itama kan ta giad’a masa. Da k’yar Farouq ya mik’e se jiri ke k’ok’arin d’ibansa, fuskar nan nasa ya ninka abinda yasa a kayi wa Anas, kayan sa duk ya b’aci da jini, da k’yar yake maganar a wahale. “Wallahi Mr. Fauzi you won’t get away with this, Fannah tawa ce! Fannah mata tace! Ni zan auri Fannah!”
 
     “No Farouq you are wrong *FANNAH TAWA CE! FANNAH MATA TACE! NI ZAN AURI FANNAH* and not you.” Shi kansa besan sanda yafad’i wannan kalamu ba. Fannah kam mutuwan tsaye tayi. Daidai lokacin motan polisawan suka iso guda biyu. Handcuff aka sawa Farouq a hannu “wallahi Mr. Fauzi kasani you won’t get away with this, duk ranan da na fito se na k’wato Fannah daga gareka, sena kashe ka in ban kashe ka ba sena kashe ta dan in barin samu Fannah ba, bawanda ze same ta.” Kansa aka tusa cikin motar. Daidai lokacin Ya Khaleel ya hallaro shima, ganin d’ansa cikin motan polisawa ya falfala da gudu izuwa wajen.

    “Officer ina zaku kaimin d’a dan Allah ku sako shi kuyi hak’uri. Farouq me kayi?” Nan ya juyo wajen Anas da Fannah. “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri kasa su sake min d’a wayyo Allah! Kayi hak’uri dan Allah bare sake ba.”
    “Ka sake had’a ni da Allah believe me kaima zaka bisa cell d’in. Take him away” yace da polisawan.
    “Fannah dan Allah karki bari atafi miki da miji ki rok’i Mr. Fauzi please.” Hawaye sosai Fannah take dan tausayi irin nata setaji duk she is ready to forgive them abubuwan da suka mata. “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri.”
   “NO” yace mata a tsawace “take him away, NOW!” A 360 suka bar wajen da Farouq. Kuka Ya Khaleel yake “Allah ze sak’a min wallahi, d’a na be maka komai ba kasa aka tafi dashi simply because kaga baida gata in shaa Allahu zan tara kud’i inyi bailing nasa, kekuma Fannah kisani Farouq shine mijinki ba wannan dayake miki wasa da hankali ba.” Yana kaiwa nan ya fice.

    Kuka me sautin gaske Fannah ta fashe da, “Mr. Fauzi why? Dan Allah ka dawo dashi I beg you please, banasan ka mutu, banasan wani abu ya tab’a ka. Ni nace zan aure sa ka sa a sakar dashi, ka sakar min miji.”
    “*Nine mijinki Miss Aleeyu* and that stays that.”
    Cikin kuka tace, “what are you saying Mr. Fauzi kana cikin right mind naka kuwa taya zakace kaine mijina? Ko baka san ba’a wasa da kalman aure bane? Ni ka sa su sake Farouq kawai dan Allah.”
    “Yes Miss Aleeyu nasan me nake fad’a ni zan aureki ba Farouq ba, you are going to be my wife” hannunta yaja tare da zaunar da ita cikin motar. Shima ya zaga ya zauna.

     Hawaye take sosai “Miss Aleeyu for goodness sake kukan ya isa. I’m going to marry you so as to protect you from Farouq atleast duk rashin kunyarsa inyaga ke matar aure ce ze saurara miki koda Babansa yayi bailing nasa, marry me Miss Aleeyu.”
    Kai take girgizawa continiously No! No! No! This can’t be happening bareyi in auri Boss d’ina koba dan haka bama bareyi in barsa ya aureni ba, *BANIDA BUDURCI, BANIDA MARTABA* duk ranan da Mr. Fauzi ya gano hakan ze tsaneni fiye da yadda ya tsani mutuwar sa, I can’t marry him saboda barin iya fad’a masa sirri na ba kamar yadda barin bari yagano hakan ba da kansa kuma.

     “No Sir I can’t marry you, I can’t dan Allah kabar wannan magana, ni kawai release Ya Farouq.”
   
   “Yes, yes you will marry me Fannah Aleeyu. In ma tunani kike ko wani abu ze shiga tsakanin mu ki kwantar da hankalinki. *CONTRACT MARRIAGE* zamuyi.”
   “Contract marriage?” Ta tambayesa cike da rashin fahimta.
   “Yes contract marriage nima some weeks ago Abuu yace se nayi aure, seya aura min wata ‘yar uwarshi Falmata saboda yana ganin I’m still young wataran baran iya managing Enterprise d’ina ba kuma wai ban gama mallakin hankali na ba so yakeson yamin aure, nikuma nace masa barin aureta ba, mukayi deal dashi akan in 6 months time zan nemo mace in kawo masa gida wanda zan aura. Ni koda nan da infinity, k’arshen duniya za’a bani banga macen da zata min ba har inji ina sonta zan aureta ba, I will use you  Miss Aleeyu and fake up a relationshop with you. Ni a rayuwa na banason aure, duk abinda ze had’ani da mace ma hasali banaso ke kad’ai ne...” Ya nisanta “when it comes to you I just don’t feel thesame way. Mu rufa wa junan mu asiri and help each other. Zan aureki for just *6 MONTHS TIME* after then semu rabu ince wa Abuu kinci amana na kin tafi kin barni, kince you don’t love me anymore, you see daga lokacin nan bare sake tak’ura na da zancen aure ba zece I’m broken I cannot move on kamar yadda shima har yau yakasa sake aure tunda Ummimi ta tafi ta barsa. Ke kuwa kinga nasan by 6 months time d’innan Farouq halan ya gaji da jira ya koma inda yafito kinga seki cigaba da tafiyar rayuwarki kamar yadda take da. Nikuma I promise you a k’arshen 6 months d’innan bayan munyi ending marriage d’in zan baki 6 million tunda dama contract marriage ne.” Ido sosai Fannah ta zaro 6 million???? Ta fad’i a ranta.

   
        “Kinga inma so kike kubar garin nan da family’nki zuwa wani garin zaku iya, yadda Farouq bare sake tak’ura muku ba. Kuma a kowani k’arshen wata zanna biyanki albashinki na aiki N500,000 sede bawai zakina min aiki bane still, zan sauk’e ki daga zama min PA, bareyi ace mata ta PA ta ba. I’ll get the papers ready gobe, all you have to do is sign them So what do you say?”

     Shiruu tayi dan tunanin ma ta kasa. Taya zatayi agreeing wa qudurin nan? Contract marriage, how? Setayi decieving kowa kenan tasa su yarda eh soyayya sukayi da Mr. Fauzi har ya kai ga aure? Kuma seya b’ata mata image gun iyayensa, yace taci amanar sa? Gaskia baratayi ba amman kuma intayi la’akari itace ma zata fi benefiting. Dubu d’ari biyar sau 6 miliyan uku kenan plus miliyan shida daze bata ta tashi da miliyan tara kenan. Wow! Zata samu takai Babanta har k’asar waje ayi masa aiki takuma tattara family’nta subar Maiduguri su koma ko Kano ko Kaduna inda su Farouq bara su sake saminsu ba. Zata samu ta sa Afrah ma a makaranta. To yanzu ya? Ta yarda kenan?

     “Miss Aleeyu?” Ya tsamota daga cikin duniyar tunanin data wula. “Have you make up your mind?”
    “Sir naji komai amman seka b’ata min image gaban iyayenka ne su d’au mutumiyar banza ce ni?”
    “Yes Miss Aleeyu this is the only way zan kub’uta, the only way Abuu zeji tausayi na bare sake min maganar aure ba har se in ni na masa.” Kai ta gyad’a a hankali “Sir amman baramu na had’a kwanciya bako?”
    Lallai ma yace a ransa, shi d’inda ko wace mace nada burin ganinsa kan gadonta ita tasamu zata tsaya tana masa tsiya.

     “Miss Aleeyu nima ba so nake ba dan yazama dole ne, ofcourse we will share a bed amman ba abinda ze shiga tsakanin mu, in ma gudun abinda kike kenan, kisani banida interest cikin wancan abin ko physical contact ban yarda ba, lokacin da zamu iya tab’a juna shine only if either your family or my family visits saboda kar su gane faking auren mukeyi.”
     “Sir you mean barin sanar da su Mami ba? Ai ya kamatasu su sani-”
     “Bekamata ba” ya katse ta. “Ko Afrah ban yarda ki fad’a mata ba, this is our secret dan the moment kika sanar da mutum d’aya kin mana ruining komai kenan. Don’t tell anyone, clear?”

    Kai ta gyad’a tana nazarin ya zata soma b’ullo wa family’nta da wannan zancen auren Mr. Fauzi. Ai se suce dama tuni soayyaya ke kai ta office nasa ba aiki ba.
     “Good” yace. “So starting today zakiyi faking zama girl friend d’ina saboda kar mutane suyi suspecting relationship namun bana gaskia bane.”
       “Is that necessary Sir? Senayi pretending zama girlfriend naka a idan mutane?”
     “Yes Miss Aleeyu kidena san abu kina kaiwa kasuwa, bakiya san zama girlfriend d’inan ne? Sure kinaso so stop pretending and let urself celebrate.”

    “No ni banaso” ta kare kanta.
   Wani shu’umin murmushi ya saki mata. “In ma saboda Yusuf saurayin kine kike wannan abu gwamma tun wuri ki bari, kije kiyi breaking up dashi dawuri dan baraki b’ata min reputation ba ace kina dating d’ina kuma kina dating me aiki k’ark’ashi na ba.”
     “Sir Yusuf ba saurayi na bane.”
   “Allah sa” yace ba tare da ya nuna danuwa ba. “So ki bud’e kunnwanki da kyau ki jini, akwai rules da zan kafa miki regarding wannan aure;.
   Na farko shine don’t fall for me, saboda fake relationship ne I will show you love and care amman kisani bana tsakani da Allah bane, so in kika yi falling min ba ruwa na ke zaki karya wa kanki zuciya dan ni ba sanki zanyi in return ba.” Dad’in abin ba yau ta soma jin munanan kalamunsa ba so ko damuwa batai ba. “Ka kwantar da hankalinka Sir ni barin tab’a falling maka ba, business is business”
         “Allah sa ki iya ignoring beauty na. Na biyu we will be hanging out tare, duk inda zanje tare zamuna zuwa irin su dinner ko lunch da ake inviting d’ina so as inyi introducing naki wa bussiness colluegues d’ina. Inada business trip nan da 1 month da 2 weeks zuwa Morocco dake zanje.
   Na uku, I will re transform you, you are now my girlfriend ya kamata ki fara sa kayaki masu tsada saboda mu nuna wa public kin kai ince ina sonki.” Wannan wace erin zagi ne? Meyake nufi? Kaya masu arha take sawa kenan ko meh? Baki ta bud’e zata masa gana. Ya dakatar da ita ta hanyan aza hannunsa kan lips nasa “shh! Bangama ba karki katse ni. I know kinasan kice you are not ashamed, if you are not toh ni I am and that stays that. Hope am clear for now, more rules will follow afterwards...”

*© miemiebee*
 

1 comment:

  1. Ya yi kyau muna godia, Allah ya ba Mama lafia, ya qaro miki basira.Ina tare dake.
    Fatima Na'abba.

    ReplyDelete